Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ba almost 1min suna haka ganin baza tayi magana bayasa juyuwa cikin husky voice din sa yace didn’t you need anything? Bata dago kanta ba ta girgiza kai, shima mamaki ma take bashi fa hakan yasa shi folding hannunshi a kirji this time around kaf waennan idon nashi na kanta yakafe ta dasu ko janyewa babu,ahankali ta sauko daga kan gado ta saka flat shoe din ta tun wanda ta fito dashi daga gida, shidai kallonta yake ko kiftawa babu ta gyara zaman veil dinta, tana tafiya kamar bata son taka tiles din dakin jikinta sam babu kware ga duk yau bata sa ma cikin ta komai ba, har tazo inda yake tsaye ba dauke idonshi kanta ba, kanta na kasa kamar mai tsoron taba handle din kofar toilet dinta tasa ahannu ta murda ahankali ta shiga, sannan ta mayarda kofar ta rufe,ajiyar zuciya ya sauke sannan ya koma kan kujera ya zauna babu abunda suka bata Ko abunda zai shirya bags din su ne kwara biyu kacal kuma hade suke waje daya, pillow da bargo da tabarma da warmer din duk na dr ibrahim ne yasan zai sa a kwasa a mayar gida, kwata kwata jikinta is weak ahaka ta daure ta wanke pant din tass da detergent ta dauraye shi ta shanya saman wani karfe na toilet din, Ahankali take takowa cikin dakin tafiya take kamar da gaya tafiya take without making any sound, kafafunta yake kallo so yake ko sau daya ne yaga ta hanyar da zai shaida cewa bataji ko zata iya aikata abunda akace tayi kuma shine uban dan “kafin su sauka kano ya yarda ya amince amma zaman da sukayi na kwana daya ya karance halinta tsaf bata da sakin jiki Ko fuskar dazata bada damar faruwar hakan, kawai dai yasake tabattar dacewa kaddara ce kawai ta rayuwar su ahaka. Miyasa baki ci abinci ba yafada yana tsare ta da idonshi da babu alamar wasa fuskar nan tasa a daure, hannu tasa ta goge hawayen fuskar ta ahankali tace na koshi,bai sake kallonta ba yabude “warmer din yazuba mata white rice da stew ya mika mata” bata karba ba ya dire abinci kan gado sannan yace eat! Ahankali tasa hannu ta dauki abinci tafara ci kamar tana shan magani tanayi tana goge kananun kwallar dake sauka a idon,yana kallonta bai ce mata komai shima abinci yasa yafara ci domin yayi alkawarin mance duk wani damuwa a ransa sosai yaci abincin , har yanzu bata ci ko rabi ba, shidai Malik ya cigaba da ninke ma dr ibrahim bargon sa, can ya kalleta yace kisaka hijab dinki idan baza k ici abinci ba mu wuce, ture plate din abincin tayi kamar tana jira, dr ibrahim yayi ma dan sahun kwatancan idan zai kaisu yazaro 1k a pocket dinsa yabashi malik zuwa yanzu har bai iya irga a dadin alkhairin da dr ibrahim yayi masu har yagaji dayi masa godiya, yace Doctor ga bargon can da pillow da tabarma sai acewa iya mungode Allah yasaka da alkhairi, dr ibrahim yace aaa fa malik ai na kune nason kuna bukatar su,malik yace aaaa Doctor iyakar abunda kayi manah mungode dan Allah ka barshi, dr ibrahim yace ma mai dan sahun tada babur din ku wuce, madam nasan tana da bukatar hutu anjima zan shigo Allah yakara sauki, daga haka mai keke ya ja suka tafi.Anguwar sam babu hayaniya duk dacewa anguwar masu karamin karfi ce sosai kasancewar gini anguwar kusan duk unfinished buildings new asu sa plasta babu shafe balle paint wasu kuma ko kofar kirki babu “kofar wani gida ya tsaya duk layin shine babba duk dacewa gidan kofa ce amma kallo daya zakayi mashi kasan cewa cikin gidan compound ne, sauke kayan malik yayi yana kallon aydarh da yanzu fuskarta babu hawaye amma kallon daya zakayi mata kasan she is sick domin babu walwalla sam a fuskarta duk tazama kamar wata marainiya, ahankali yace mata sauko. Da sallama suka shiga cikin gidan apartments biyar ne a gidan ko wane akwai dan space tsakanin shi da dayan, da kallo waenda ke zaune tsakar gidan suka bisu suna kafe su da ido Kamar mayu,gaishe su malik yayi dasauri suka amsa ita dai aydarh kanta nakasa ko iskan da ya kwaso su bata kalla bad uk kanta nakasa hakan bai hana matan dake tsakar gidan kare ma hallita kallo ba tunda malik yashigo wata budurwa take tsaye kallon shi take kamar tsohuwar mayya, har kofar dakin yayi dropping kayan dake hannun shi yafido ke. Babban parlor ne yaji tiles sai bedroom daya da kitchen sai toilet a bedroom din dakuma wani a parlor, parlor babu komai sai karamin carpet a tsakiyar parlor “ babu kura ko kadan wajan tass yake,Tunda ta tsaya bakin kofar dakin bata motsa ba kamar wacce aka dasa,kayan dake hannunshi yasauke tareda saukar da ajiyar zuciya mai karfi ahankali yake tafiya zuwa bedroom din dashi ma kofar shi ke a rufe sake fido key yayi daga aljihun shi ya bude dakin sai dayayi sallama kafin ya shiga , bedroom din dan madaidaici da katifa akasa nan ma akwai carpet da wardrobe like a bangon dakin taga dayace da plain ash curtains a both kofan da tagan, babu bedsheet a katifa sai rigar katifar kawai da pillow kwara biyu, “kallon dakin yake ko kiftawa babu anan kuma rayuwa ta kawo su anan kuma rayuwa ta maido su anan kuma zanan kaddarar su zata cigaba da kudana Yah rabbi ya furta ahankali tare buda kofar ya dawo parlor “idan take tsaye tun shigowar su anan take ta gaji da tsayuwar domin jikinta sam babu kwari amma bata jin zata iya zama sai lumshe idonta datayi ta jinginar da keyarta a bango tana sauke ajiyar zuciya ahankali da gani kasan bata son tsayuwar da take “kallonta yayi cikin few seconds ya dauke idonshi yayi kasa da kanshi tun tahowar su this is the first time data bashi wani irin mugun tausai haka nan yaji yana tausayin ta dagani kasan deep inside she is hurt, bayan dogon nazari dayayi ya fuskance abubuwa dayawa game da ita, Ahankali yake matsawa towards her “cikin wannan muryar tashi but this time can kasa yayi maganar yace ki shigo , bata ce komai bas ai buda idonta datayi tana kallon parlor, duvet din da pillow ya dauka ya juya yasake cewa follow me “ koda suka shiga bedroom din nan ma dakin take kallo ko dauke ido babu “yana lura da duk wani motsin ta bags dinsu ya aje , ya daura duvet din kan katifar da pillow dake hannunshi “ mikewa yayi ya kalleta yace come and have a set “ shiru tayi Kamar bataji shi ba kusan 2mins bai sake magana ba sai can ahankali kamar tana taka garwashi ta zauna kan katifar ahankali tana takure kanta cikin hijabin dake jikinta “ fita yayi ya koma parlor ya jinginar da tabarmar a bango kafin yabude kitchen din yashiga dan karami ne kitchen din babu komai ciki sai camping gas karami da pot a gefe da alama dai mai gidan daya tashi tafiya duk ya barsu. Kusan 1hr tana kwance babu ko alamar bacci a idonta tun dazu take kanannun hawaye takasa jurewa takasa mantawa so take kawai ta mutu domin duniyar ta isheta,knocking yayi ahankali kafin ya tura kofar dakin yashigo kwance take ta ba kofar baya yarda take curewa waje daya yana bashi mamaki kamar bata da k’ashi da sallama yashigo dakin bata amsa ba domin Hankalinta sam baya jikinta kallon bayan nata yake kamar zai gano wani abu a bayan ‘ kusan 3mins yana ahaka ahankali kuma ya matsa kusada da katifar da take kwance ganin bata ji motsin shi ba ko alamar tasan dashigowar sa dakin hakan yasa shi yin gyaran murya “dasauri ta tashi zaune ganin mutun tsaye a kanta idonta yayi raurau alamar zatayi kuka don ta tsorata kallonta yayi ya dauke ido “ yace sannu ya jikinki? Fuskar nan kamar za shi yak’I batace mashi komai bas ai sa bayan hannunta datayi ta goge fuskarta shima bai sake magana ba yabude bag dinshi yafido kudin da abby yabasa 20k ne cif domin baa cikin su yataba kudin mota bay ana son ya fita ya siyo abubuwan amfani amma bai san inda zaije ba hakan yasashi tunani zuwa clinic wajan dr ibrahim duk yace mashi zai shigo da,daddare amma kafin daran sun bukaci wani abun kamar bockets sponge toothpaste da sauran su, har yakai kofa zai fita yajuyo ya kalleta yace stay here don’t out I will not stay long “aydarh batace masa komai ta koma ta kwanta, Dr ibrahim ya kalli malik yace amma ai akwai gas da tukunya a kitchen din ba? Malik ya gyada kai sannan yace masa eh akwai, dr ibrahim yace tau Alhamdulilah yanzu bara lokacin tashina yakarasa sai mu shiga kasuwa mu siyo dan abunda ba’a rasa ba wanda zaku nema right? Malik yace eh hakane ina jiranka tau. Keke suka hau har central market din garin babu nisa Sosai daga clinic zuwa kasuwan cikin few minutes suka karasa, zanin gado suka fara yanka aka dinka musu da four pillows kamar yarda malik din yace babu bata lokaci aka gama suka karba suka wuce, bockets suka siya na wanka kwara biyu sai plate 6 spoon 6 cups ma haka sai knife da container karama daya babba daya sai warmer masu kwara uku kanana masu saukin kudi nan yabiya suka wuce wani shago yasiya soaps detergent da kuma sponges sai toothpaste da Vaseline babba daya sai karami daya, nan malik ya mika kudi “dr ibrahim yakalle shi yaso yayi shiru amma yakasa sai yace ka manta baka siyan ma madam perfume ba koh? Shaf ma ya manta a ranshi yace ka kasan kamshin datakeyi da baza kayi magana ba,baice komai ya koma ya daukar mata wani medium perfume body splash ne bai da karfi sosai yabiya kudin suka kwashe kayan suka fice fira suke ammar abin da kwatan firan dr ibrahim ke yinshi shidai malik daga um sai aa idan kuma abun dariya ne yayi wannan miskilin murmushi nasa “ malik yace please ina zamu samu abinci nasiyan mata? Dr ibrahim ya girgiza yace aaa bara mu fara biyawa gidan sai a karbar mata wajan iya kafin taji sauki tafara girki,malik yace aaa Doctor dawainiyan yayi yawa kuma “ mu dai sami inda ake siyarwa ko da restaurant ne sai muyi takeaway “Dr ibrahim yace na lura har yanzu baka daukeni yarda na dauke bah? Malik yayi kasa da murya yace aaa sam bahaka bane kawai dai naga anyi wahala damu dayawa ne “dr ibrahim yace indai ka daukeni yarda na dauke ka muje mu karbar mata abincin can wajan iyan, keke su ka hau har kofar madaidaicin gidan, sallamar shi sukayi suka kwashe kayan suka shiga gidan dasu dakun ne kwara biyu a jere sai wata rufa da nan ma daki ne sai filin tsakar gida da kitchen da toilet a dakin koi na shafe yake cement anshare gidan kwal,kamshin turaran tsinke da aka kunna a daki har tsakar gidan, da sallama dr ibrahim yasaka kai yashiga rumfar malik na biye dashi baya dauke da ledojin siyayyar dasukayi a hannun sa,daga cikin dakin aka amsar sallamar dare bada izinin shigowa “babbar mace ce zaune kallo tayi saar ummi kallo daya zakayi mata kasan mahaifiyar Doctor ibrahim ce saboda tsananin kama dasukayi dashi cikin ladabi malik ya gaishe ta cike da kamala da fara’a ta amsa bata gane shi ba hakan yasa ta cema dr ibrahim bako mukayi ne? Gyada kai yayi yace eh iya ABDOOLMALIK ne wanda nake baki labarin sa, ohh Allah sarki tasake fadada fara’arta tace Abdul sannu ina gajiya ya mai jikin takara ji? Da sauki alhamdulilah iya,iya tace tau madallah Allah yakara sauki,Ameen suka amsa atare dr ibrahim yace iya ina yaran gidan suke su hadawa ABDOOLMALIK abinci a warmer ,iya tace duk sun tafi wajan biki nan baya bara natashi na hada da kaina bata jira amsar su,ba ta mike “a kula biyu ta hada masu lafiyayan tuwo da miyar danyan kubewa dayasha naman karamin dabba da man shanu sai kamshi yake “ sallama sukayi da iya tareda yi ma malik alkawarin zasu shigo su duba jikin aydarh in sha Allah Sosai yayi mata godiya har cikin ranshi yaji iya kamar umminsa. Saidai ya shirya duk abunda suka siyo a muhallinsa tun can daman yana taya su aysha aiki shiyasa duk wani aikin gida ya iyasu babu abunda yake basa wahala, toilet din dake parlor yashiga yayi wanka” wani cotton yard yasaka black duk da ya kwana biyu amma yayi masifar karban jikinshi kamar wani baindiye,shiga yayi dakin har yanzu bata ci abincin daya zuba mata ,kallonta yayi ya dauke ido bai ce mata komai ba yawuce bathroom din sai dayasa detergent ya wanke bayin duk da babu wani dirty a ciki fitowa yayi tareda komawa kitchen yana tunanin inda zai je ayi mashi refeling gas, yasan bazata iya sakawa jikinta ruwan sanyi ba.kallonshi take ko kiftawa babu gani irin kallon dake mashi yasa bata ranshi yana jan karamin tsaki a ransa har zai gota ta yawuce cike da iyayi tace hey handsome ina zuwa haka? Bai ce mata komai ya wuceta bin shi tayi a baya har yafita kofar gida, Daga murya tayi tace bawan Allah magana fa nake. Malik dai sai wage wage yake yana neman wanda zai tambaya yayi masa kwantancan inda ake siyar da gas, budurwa dake tsaye mai suna ramlah,takasa shiru sai magana take masa wanda ya maida ta da ita da banza duk daya “gajiya yayi da maganar da take masa,ya juya yayi tafiyarsa, dasauri ta like jingin bangon dan karamin gidan nata da parker rike a hannu da alama dai shara ta zubar sai faman sababi take ganin malik yasata likewa jin bango tace “wa’inahu min sulaimanu wa’inahu bismillahil rahamanin rahim,sai gwale ido take tana kallonshi kamar taga mutuwa shi mamaki ma tabasa yatsaya yana kallon ikon Allah,ganin yarda take yasa shi ajiye gas din hannun sa ya matsa kusa da ita, kara shigewa tayi jikin bangon tana rufe idon zuwa yanzu malik yarasa abunyi hakan yasa shi cewa baba lafiya? Har sai daya maimaita sau uku sannan tsohuwar ta bude idonta,tana kallonshi murmushi yayi mata yace ina wuni? Inna dai bata amsa bas ai kankance ido datayi ,malik yace baki da lapia ne baba? Sai sannan ina ta sauke ajiyar zuciya tace ohh ashe daman mutun ne kai ka razana ni hakan nan? Yanzu fa Ko Allah ya isa na banka sai ta bika ahtau wannan abunda kayi man tunda nazo duniya ba ataba firgita ni irin haka ba,malik was confused and speechless at the same time “ ya firgita takuma ta ina?shida ko magana baiyi mata ba and tafiya yakeyi lafiya lau he see nothing wrong kaf a jikinshi da zai firgita ta “bai ce komai bas ai gyara tsayuwar shi dayayi sannan yace Tau ayi hakuri “ inna tayi kasa da murya tace daga wace duniyar kake, kuma naji kana hausa anya yaro? Malik yashafa sumar kanshin nan kamar ta irin yan gayun larabawa yace daga sama ta bakwai inna ta tabe baki tayi shiru “kallo daya malik yayi mata kawai ta tuna masa da hajajju saboda har kama suke kuma ma kusan shekarun su daya,”Sake daukar gas dinsa yayi yace yanzu kiga ni bak’o baa nan nake ba zanje na saka gas ban san kuma inda ake sawa bak o zaki hadani da yaro sai yarakani,dafe kirji tayi tare da kwada wani irin salati tace wasu yagagun yaran na isa dasu a fadin anguwar nan dazanyi wani neman suna nasa su raka ka wanene wanda ya fada maka a nan akwai yaron dana isa dashi nasa ya raka ka,daga su har iyayansu ya’yan Allah bani ne woo tau nidai gaskiya ba ruwana bana shiga harkan kowa a fadin kano shiyasa kagani zamana , yanzu ka sakar ma mata fuska ta dinga kwaso ma yara suna shigo maka gida a zuba ma cuta suna tafe daudaa na zuba,shiyasa kaga babu mai shigowa waje na dagani sa ini idan takama dole ma sai mutun yazo wajena ko wanene saidai ya tsaya waje na fito nasame shi saboda bana kaunar azaba ni a dinga cutar mutane da wari ahtau, shidai malik sauraron ta yakeyi har tayi shiru bai ce komai ba, tace jirani yanzu na dauko mayafi sai naraka, malik yace tau “nagode “fitowa tayi da katon mayafinta da jikka tasa makulli ta rufe gidan tace yawwa muje tau tayi gaba malik yabita baya suna tafiya sai surutu take ko shiru babu shidai malik yayi shiru yana sauraron ta ,Tace wai kai daga wacce duniyar ma kake? Malik yayi murmushi yace adamawa “tayi shiru tace minene kuma Adamawa? Yola ko Ina? Yace ehh can tayi kasa da murya tace tau wa ya aiko ka kano kuma kai? Malik yace ba kowa, tayi mitsi mitsi da ido tace kai dawa kazo? Yace mata nida matata,inna takalleshi tace tau Allah ya kyauta babu wanda yasake magana cikinsu har suka isa bakin hanya inda ake siyar da gas din babu wani tafiya sosai daga gidansu zuwa nan din,3kg yake dauka sai da aka cika sa yabada kudin suka tafi, inna tace tau kaga gidana nan ka gaishe da mai dakin naka,malik yafiddo 1k yamikawa inna yace tau gashi babu yawwa in sha Allah naga gidan ai zan shigo ko nima dai saidai mu tsaya kofar gida kar nashigo inna tace, injiwa kai da ba rubabbe ba miye wani abun nace kar kashigo mung ida amma dai bara nasa maka lambata sai ka gayaman karka cuceni ka shigo man gidan ban shirya bah ,shidai malik dariya yayi ,yayi mata sallama ya wuce.Ramlah na tsaye kofar gidan wannan karon ta chanza kaya fitted gown ce ta atampha Jikinta bakin nan yasha lipstick kamar tashafa rubber guda astagfirullah ga bakin kamar filin jirgi washe shi tayi tana karya jiki kamar kara jikin nan kau bleaching yayi gardama “shi Malik ma wllh kyamar ta yake cikin five seconds yakalleta amma yaji sam batayi masa ba “barka da zuwa yallabai tafada tana kashe kanannun idonta kamar Chinese ko kallonta side din datake baiyi ba yashige cikin gidan” part dinsu ya nufa ya fiddo key dinsa ya bude,da sallama yashiga yawuce kitchen ya hada gas din cikin few seconds ya cika tukunyar ya daura mata ruwan zafin da zatayi wanka kafin ahankali yashiga dakin , zaune take amma ta cusa kanta tsakanin kafanta ta takure kanta wuri daya kamar mai jin sanyi,plate din daya saka mata tuwo yabi da kallo tace dan kadan ko rabin malmala baiyi basai pure water daya aje mata shima tasha kusan rabi duk da she cannot recall when last ta sha pure water a rayuwarta, zama yayi ahankali kan carpet din dakin ya bude ledan dake da maganin ta yana dubawa, babu alamar duk yau tasha, maidawa yayi ya aje bai ce mata komai ba itama bata dago kanta ba duk da taje shigowarsa,kusan six minutes babu wanda yayi ma wani magana, tashi yayi “yashiga toilet yadauko sabon bocket din daya siyo kasuwa yafito dashi yashiga kitchen ya juye ruwan da har sun tafasa kashe gas din yayi sannan yarufu kofan kitchen din, ruwan yakaimata already yashirya sponge da soap din tare da toothpaste da brush din daya siyan mata tunda aka kwantar da ita asibiti,har yanzu tana yarda take saidai yanzu ta saussauta curewan datayi wa jikinta, jikkarsa yabude ya dauko wani pink clean toilet babba, ya ajiye kusa da kafanta, sannan yace ki tashi ki shiga kiyi wanka, bai jira amsarta ba ya fice daga dakin zuwa parlor kwantawa yayi kasan carpet yana son yayi bacci kona two hours ne. Spain > Bakaramin haduwa gidan yayi ba duk da ba wani babban bane amma yasha wani hadaddun flowers masu kyau da daukan ido wani red blocks akayi amfani wajan ginin gidan, oum ce zaune saman wata mad Expensive sofa tayi bala’In kyau cikin atampha normal riga da zani tayi wani ubansu daure ta fito da gashinta da tayi packing can kasan keya irin daurin ture kaga tsiyan nan amma tsabar gayu da iya ado salon daurin daban yake karamin bowl ne rike a hannunta da wuka tana slicing green apple wanda ke very fresh dagani yanzu a tsinko su,karo na ba dadi abba yakalleta ,kasa hakuri yayi yace nifa kamar da gayya kike sliced din apple din nan ahankali,murmushi tayi wanda zallar kyanta ya fito tace nifa babu wani abunda kayi mun dan kun gaisa da ita ai ni bana cewai dole kuna da affairs tsakani ba kawai dai bana son yarda kake sakewa da mata nidai gaskia,takarasa maganar tana raurau da ido “abba yayi murmushi yace tau shknn your majesty daga yau angama, dariya yabata yarda yayi kamar wani indian hadda dafa kirjinsa ya ware dayan hannun kamar zaiyi worshipping dinta, kallon shi tayi tace tunda muka sauka ban kira rufaidarh ba , bara nakirata definitely nasan yanzu tana can tana tunanin mu a ranta, abba yace ohh eh yakamata gaskia kiji ya wannan tsohuwar ma,tunowa da hajajju yasa oum yin murmushi har tafara missing magana da ita. Rufaidarh tace mutanan spain, tun dazu nake tunanin kiranku tau danaji shiru baki kirani ba shiyasa nayi tunani ko bakuyi landing ba ko kuma kun tsaya wani wajan tafa sautin murmushi na fita a muryanta “oum tace aaa fah kawai dai agajiye muka sauka sai da muka huta kafin” gaisawa sukayi da rufaidarh “tana tambayar ta ina hajajju “rufaidarh ta sauke ajiyar zuciya tace hmmm hajiya na kasa wajan maids ai yau labari sai wanda ta manta kawai ke bata basu ba, kiji fa “nidai har na gaji da jiran ta dawo saman ma inga dai bin ta zanyi na dawo da ita tabar su su huta suma “oum tayi dariya tace ai hajiya halinta sai ita ki gaisheta tau and kibi ta ahankali kafin takare maki tanadi kinsan ta, dariya rufaidarh tayi tace ba ko wuya “can kuma tayi kasa da murya tace yallabai dai ya nutsu yafara dawowa daga damuwan right?oum ta lumshe ido cikin sanyin murya tace uktiee saidai idan bana duniyar nan zai zauna cikin damuwa amma tuni ya saki waccan tunani ‘rufaidarh ta washe baki tace tau alhamdulilah nasan baki da wasa uktiee,ayo manah tsaraban twins daga spain tafada tana kwashewa da dariya tayi maza tana rufe baki kamar tana gaban oum, bata jira amsar da oum ke bata ba tayi saurin kashe kiran .Zan kwanta , bana son kowa yasan ina garin nan domin bazan ma je company ba oum tayi kasa da murya tace tau shknn ni bara naje muyi dinner karkayi bacci amma saboda yamma yayi,murmushi yayi yana gyada kai yace in sha Allah “ Juyawa yayi yafita,sosai take son tayi wanka amma tana tsoron ace ruwan sanyi ne,daurewa tayi ta tashi, ahankali take wannan tafiyan nata kamar tana yi da gayya , Kamar mai tsoron kofar haka takarasa wajanta duk da a rufe take amma sai da ta jinjina ta tabbatar domin bata son yashigo dakin, kayanta tacire kafin tasa hannu ta dauke pink clean towel din ta daura kamar dan ita akayi towel din kamar dan fatan ta aka saka zaran towel din hannu tasa ta zare ribbon din kanta yah rabbil alameen “hair dinta har wuce kafada, sanyi take ji haka yasata daukar hijabi tanufi toilet din,koina very need ta kalli bucket din da alama ruwan zafi ne a ciki bata wanka da bucket hakan yasa ta jin wani kala”pampo yayi mata wani kala duk da ba local pampo bane amma ita bata saba amfani da irin wannan ba ,sirka ruwan tayi daidai yanda take so wanka tayi,tayi brush tareda wanke pant din da tacire, ahankali ta bude kofar toilet din ta fito har sai da gabanta yafadi ganin shi zaune cikin dakin kallo daya yayi mata ya janye ido kamar ma bai ganta ba da sauri ta koma toilet din,tana tura kofar idonta cike da kwalla ta tsani wani ya ganta haka ko dasu oum ne kau, duk da towel din babba ne hijab din ma har kusan kneels dinta hakan bai hanashi jin wani kala ba domin

Chapter 9 of 83