Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
“sai lokacin ta juyo ta watsa matsa masa harara tace kuma yau dai bazaka sake siyan komai ba balle kaje ka sake ganin watan kuma “malik yayi shiru kafin ya juyan da kai yayi wani smile yana shafa kansa “yace tau kiyi hakuri kinga ga mai pos can naje na fiddo kudi I didn’t have cash hajiya “kallon wurin daya nuna mata tay isai kuma ta kallesa tace to kaje kuma Allah ina nan ina kallonka duk wacce kasake kallo “sai kuma tayi shiru yace bafa zan sake kallon kowa ba kedai kawai Allah yabaki hakuri hajiya cike da tsiwa tace Ameen”bayan kusan five minutes sai gashi yadawo yana kallon agogon wayansa “yace tau koma muje eatery sai muyi takeaway bas ai kinyi girki ba?without looking at his face tace zanyi girki ahankali yace ohk “mai keke ya taran musu suka shiga har kofan gida ya ajiye su,malik ya kwashe ledojin su kafin yabiyasa kudin sa “daga bayan su sukaji magana aydarh na juyawa sai ga dr hafsa,ta wara ido tace auntie ‘kwana biyu nayi fushi dr hafsa tayi murmushi tace sorry lil sis kwana biyun nan aiki yayi mun yawa yanzu haka fa yau ne kawai nasamu kaina zanje suna friend dina ta haihu “ Aydarh tayi murmushi kafin tace eyyerh auntie Allah yaraya kafin tayi kasa da kai tace kinyi kyau auntie,dr hafsa tayi yar dariya tace kai haba really ?malik day agama biyan mai keken kudinsa kuma duk yana jinsu yace sure “Wallahi aydarh sai dataji wani kala dayace sure dinnan don bai san yarda takeji bane idan yana magana da mata har kwara auntie hafsa din bata fiye jin damuwa bai dan suna magana amma nan dayace tayi kyau sai taji wani irin yarr “dr hafsa tace ah yallabai ina wuni sannunku da dawowa “malik yace yauwa dr yakike? Dr hafsa tace lafiya lau ya shirin tafiya kuma?yace Alhamdulilah tace when ne tafiyan yace saura six days In sha Allah dr hafsa tace eyyerh we will surely miss you both Allah malik yace same here ita dai aydarh na sauraronsu bata sake cewa komai ba tayi shiru malik yace anguwa ma zakije ba “sai lokacin aydarh ta dan hararesa ta gefen ido kafin tace naming ceremony zataje sai kabar ta tafi kar tayi yamma “malik ya lura masifa yarinyar nan ke ji Allah ya shafa kansa kafin ya fiddo kudin kusan 10k daga aljihunsa ya mikawa Aydarh yace tau gashi ki ba dr sai takai wajan sunan “Aydarh ta kalli dr hafsa sai lokacin tayi murmushi tace gashi auntie yace na baki,dr hafsa ta girgiza kai tace aaaa fa aydarh ki mayar masa ku dake shirin tafiya idan baa baku ba ba za”a karba ba malik yace no hafsa don inda shi shiyasa nabaki bakomai sai kin dawo dr hafsa ta karbi kudin tace nagode sosai aydarh tace bye auntie sai kin dawo dr hafsa tayi murmushi tace Alright aydarh sai na dawo am off tomorrow zan shigo sai mu sha fira aydarh tace to auntie “daga haka dr hafsa tayi gaba shima malik hanyar gidan ya nufa tabisa a baya.Tunda suka dawo take ta fama daure fuska shidai bai ce komai ba yana bude ledan kayan dasuka siyo yana jera mata a wardrobe har yakawo kan brassiere din yayi tunanin zata kwace kaman yanda ta saba sai yaga ko tasuwa batayi ba duk datagani tass ya gama jeran kayan kafin ya rufe wardrobe din mikewa tayi ahankali ta karasa bathroom yana jin ta kunna pampoo ya girgiza kai yasan wanka zatayi bai tashi ba ya zauna yafiddo wayansa daga aljihu ya cigaba da dannawa duk research yake kan asibitin can kasar din da location din da aka tura masa wanda zasu zauna har picture din gidan dr usama yasa antura masa ta mail dinsa,can tafito daure da sabon black towel din daya siyo mata “sai satan kallonta yake ta kasan ido mamakin yarinyar nan na neman kashe sa kishin ta yayi yawa kuma idan ana kishin ka that means ana sonka fa?yayi shiru har ta karaso ya dinga bin white legs din ta da kallo masu kyau da daukan hankali kamshin jikinta na kashe masa jiki har sai da takai wajan wardrobe kafin yadaga kai yabita da kallo yanda ass dinta ke wani masifan shaking ta cikin towel din yasa shi kasa dauke idonsa “ hijab dinta tasaka ta dauki pant da bra ta koma toilet din tasaka ta fito Still yana nan zaune sabon cream din dasuka siyo ta fiddo “Wallahi kasa hakuri yay isai daya dago kai ya kalleta yace “lotion din ke wannan kamshin cuddle bug? Batace masa komai ba ta gyada masa kai kawai yace tau idan kingama shiryawa zan nuna miki abubuwan da aka tura mun sai kid uba nan ma ta gyada masa kai yayi dropping wayan kan karifa yace let me refresh nima tayi masa banza fita yayi yashiga toilet din parlor yana rike dariya sa yana fita yasake ta “ahankali yace stubborn bea “kaji wani kamshi malan woaw “ashe kamshin jikinta asali yasamu “yanda fatan nan nata ke wannan cream creamy din idan tacigaba using this lotion Wallahi bazai cigaba da barinta tana fita ba “da wannan tunanin yacigaba da wankan sa,tana gama shafa lotion din ta mike tacire hijab din tajawo wani simple plain gown na material pink tasaka kafin tasaka hula shima pink amma mai haske perfume tashafa as usual yau ko powder baa shafa bai ta fa ala dole laifi yayi mata can ta dinga bin wayansa da kallo vibrating wayan keyi number ne babu suna ahankali zuciyanta ya dinga bata tadaga har ta tsinke sai kuma akasake kira hannu tasa ta dauki wayan kafin tayi shiru “daga can akayi sallama jin murya mace yasa aydarh yin folding hannunta a kirji “tasake daure fuskanta daga can rabiah tace ina wuni yayana?ina ta kiraka baya shiga nasan blocking dayan layina kayi ni ban taba ganin inda masoyi ke zama makiyi ba fa yayana “Aydarh ta wani hade rai tsab tagane wacece “cikin muryanta cike da izza tac eke hold on ‘rabiah kike ko wa I didn’t even care ‘stay away from my husband ba tsaranki bane duk ranan dakika sake kiransa kuma zan nuna maki my madness past yours stupid tana fadin haka ta kashe wayan ta wurgar kan katifan ta fice daga bedroom din a parlor suka hadu yafito wanka yana faman goge jikinsa “ta dauke kai tashige kitchen kawai pasta ta fiddo kafin ta dauko pot ta dauraye ta zuba ruwa ta daura kan gas kafin ta kunna “saura chicken din daya siyo ta dauko ta sake gyara shi kafin ta dauki kayan miya zata gyara ,tana cikin aiki sai gashi yashigo “ahankali ya tsaya kusa da ita yace mi zanyi ko kallonsa batayi ba ta miko masa fruit da knife sai wani bowl mai dan girma “fuskan nan a daure tace sliced it “karba yayi yafara yanka fruit din ita kuma ta cigaba da abunda takeyi duk bayan seconds sai ta kama sa yana kallonta “duk wani motsi nata a idonsa takeyi ‘can ta waiwayo takallesa tace idan ka yanke sir ai kadaina kallona kuma idan tasake kiranka billahi har wajan iya zanje na fada mata sai sannan malik ya ajiye water melon din dake hannunsa ya dauraye hannun yamike tsaye kawai ya kwantar da jikinsa a bayanta yana saka kansa a wuyanta ya lumshe ido dan wani irin rahaman scent da ya shakka mai kashe jiki “wara manyan idonta tayi tana sauraron sa da har wani iri taji but ta daure bata ce masa komai ba ahankali ya juyo ta suna facing juna hannu yasaka yana shafa tummy ta dake very flat kaman ma babu ciki a wurin sai wani curve hips dayayi shaping waist dinta perfect shape a ke magana “yace wacece ta kirani cike da masifa tace ita rabiah manah yayi murmushi yace wacece haka kuma?ganin yana niyyar zautar da ita yasata cewa kaga fa bana son pretending abar magananta I already warn her “malik yace ahh wa kikayi warning kinganki yafada yana jan long point nose dinta “ ta tura masa baki ya dinga kallonta he cannot hold it but to kiss her,light kiss yabata wanda yasa ta dinga jin butterflies a jikinta wani yarr kafin ya kama cheeks dinta yace ai nace kiyi hakuri ni fa babu abunda yahadani da ita hajiya “Aydarh tace dagaske?ya gyada mata kai yace you are my only girl and my only wife kinji cuddle bug ta gyada masa kai kafin tayi kasa da kanta saboda kunyar sa da taji ‘kafin tace kuma miyasa kace wa auntie tayi kyau?malik yawara ido yana bude hannu yace lahh ke fa kika fada “tace erh miyasa data ce dagaske kayi saurin ce mata erh?malik yace tau naji kiyi hakuri bazan sake ba “murmushi tayi tana jinjina masa kai kafin tace to ka karasa slicing fruits din nima na kusa karasawa yace ohk hajiya “cikin few minutes suka karasa girkin kafin suka gyara kitchen din tass suka wuce parlor da kayan abincin white pasta ta dafa sai haddan sauce din dayaji chicken sai fruits salad, shi yayi feeding dinsu har suk agama kafin ya gyara parlor duk da bawani dirty yayi bai ta tawuce ta wanke plates da cups din dasuka bata yanzu,tana gamawa tashige bedroom yana nan zaune kan carpet yana sake duba abu a wayansa sallama tayi ya amsa mata ahankali yace tau zo sai ki gani “tahowa tayi ta zauna gefensa ya mika mata wayan ta dinga bin pictures din gidan da asibitin da kallo can tace inyee “yayi murmushi yace nima yayi mun kyau gidan aydarh ta gyada kai tace erh sosai fa “yace tau yanzu maganar school fa?ta kallesa don bata gane bay ace yeah school dinki “tace oh yace Mamanarh da voice din dayayi amfani ya kira sunan nata sai taji har cikin zuciyanta kaman ya saukan mata dawani kasala sai ta mayar da duk attention dinta kansa tana kallonsa ko kiftawa babu shima ita yake kallo can ta janye idonta don bazata iya juran kallonsa bama ita Wallahi wani irin girman girman sa take gani da kwarjininsa ita dai yana debe mata kewar abba “yace kiyi hakuri amma bazan iya barinki ki cigaba da karatuba wani irin faduwa gabanta yayi ta dai yi shiru kanta akasa tana sauraron sa yace you are under my control inada kishin da zai saka na hanaki ko da fita ne kiyi hakuri I promise to be the best for you babu abunda zaki rasa in this duniya in sha Allah kinji mamanarh kiyi hakuri daga haka yayi shiru hannu tasa ta share hawayen dasuka zubo mata kanta still akasa ahankali ta gyada masa kai kafin tace to”muryan ta na rawa hannu yasa yajawo ta jikinsa ya dinga shafa bayanta “tayi lamo a jikinsa hannu yasa yana goge mata hawayen datake yi duk da taki dago kanta ta kallesa ‘yace shshsh ya isa kiyi hakuri ta cigaba da gyada masa kai kawai deep inside he is hurt seeing her in suchs situation sai yaji duk wani kala bai ji dadi ba ahankali ya kira sunanta “ta amsa yace look up ido ta dago ta kallesa, yace shknn zaki cigaba “hannunsa ta kama ta girgiza masa kai muryanta in a crying tone tace nayarda ba zanyi ba “sai yaji wani kala wani irin sonta na sake bin duk wani parts na body dinsa “ yayi Hugging dinta very tight yace Allah yayi miki Albarka Allah yasaka miki da alkhairi in sha Allah I will be the best husband for you ASSEIYARH “Aydarh dai aydarh tayi shiru daga kukan datake tana sauraron sa “ ahankali yace did you accept me as your husband?tambayan yazo mata duk wani kala hakan yasata yin shiru batace masa komai ba shima basake cewa komai ba Still dai tana jikinsa “har aka kira salla kafin yamike ahankali ya mikar da ita yace go and pray nima zanje masallaci ta gyada masa kai yafita kafin tajuya ta shiga toilet sai data jingina da kofan toilet din ta dinga kallon kanta a mirror kewayan tana son takarasa karatu amma she has no other choice except to accept his decision “tunda yanzu bata da kowa sai shi “hawayanta tasake sharewa kafin ta kunna tap ta wanke fuskan ta tadauro alwalla. Tace to nasaka uniform ko?ya girgiza mata kai yace no basai kin saka ba, tace haka zamuje?yace eh da personal ba kisaka hijab kawai sai ki daura nikkab mu wuce tace Alright your majesty “murmushi malik yayi dahar sai da ta tsaya tana kallonsa kafin yace kallona zakiyi mu fasa zuwa hajiya?ta saurin girgiza masa kai ta bude wardrobe tafito da well ironed hijab dinta tasaka kafin ta fito da nikkab din ta mika masa yace tau muje parlor sai na daura miki a can princess ta gyada masa kai har ta dauko perfume yayi saurin karba yace ya isa haka kar yayi yawa ta mayar atare suka fito ta jawo kofan bedroom din “tsayawa tayi tace to daura mun “yace tau smile tukun “ tayi murmushi har white clean teeths dinta suka fito wanda hakorin gwal dinta ya kara musu kyau “shagala yayi da kallonta can yace sau nawa kikaje hajji?tayi shiru kafin ta nuna masa da hannu yace woaw you are not hajiya ma you are hajajju tayi dariya tace you are very funny “nikkab din ya daura mata yakama hannunta suka fita. Tace can shagon zamu sake zuwa dr hafsa tace erh can ko bana nan basai shi yaje yakai ki ba?aydarh ta gyada kai kafin tace to “zan masa magana can dr hafsa ta dago kai ta kalli aydarh tace maganar karatu fa zaki cigaba a can right “Aydarh tayi shiru daman kullun da abun take kwana dashi take tashi tunda yace baza tayi karatun nan bad uk sai taji wani irin she wished zai barta tayi but she have no way out bayan taji maganarsa “sai da tayi kasa da kai kafin ta girgiza kai tace ah’ah auntie dr tace aa mi?aydarh tace ba zanyi ba,dr hafsa tayi shiru tace bazakiyi ba fa kikace tau Saboda me?aydarh tace he just said no “dr hafsa tace ohk ohk nagane “Allah yasa hakan shine mafi alkhari Allah na tuba yanzu masu karatun ma abubuwan are not going right sai hakuri kawai aydarh ta gyada kai tace yes” dr hafsa tace yanzu fa cikin ikon Allah next zuwan dazakuyi lil sis said ai naganki da ciki aydarh tayi tawani murmushi tana sa hannu ta rufe fuska dr hafsa ma murmushi take tace Wallahi Allah idan Washington ma ta karbi ki kawai fa sai kiga har triplets kin haifa,aydarh tawara manya idonta take nan kaman ansaka madara a ciki tsaban kyau tace wa ni auntie triplets kuma?dr hafsa tace tau miye a cikin su yan ukkun? Aydarh ta turo baki tana kawar da kanta gefe tace ai am too small “dr hafsa ta bude baki tana kallonta tac eke wai kodai bakya duba mirror ne ko shi mijin naki baya fadi miki yanda kike ne?aydarh tace ina dubawa fa “tace kinyi karama idan kukaje jera da mijin ko amma n isai kiba da tsawo kai na fiki aydarh kefa full option ce ke anbiya yallabai a wurin nan kawai Wallahi ‘aydarh tayi shiru tace kingani ba kinfini tsawo da kiba fa duka “dr hafsa tayi murmushi tac eke kiba fa suna ta tara yanzu fisabillahi aydarh dubeki ki dubeni are we the same siket dinki fa Wallahi yayi mun yawa nesa ba kusa ba aydarh curve hips ne dake yah rabbil alameen your body structure past your age level 22 fa amma duba tabarakallah “Aydarh tayi kasa da kai dr hafsat ace kuma sai ki gaya mun kin karama da haihuwa bayan masha Allah duk girman mijinki kina dauke abunki kuma sai haihuwa kice kinyi karama irin fa kiran karfafan mazan nan dashi ba kiba sai tsawo da kwari “idan kuka jera dash isai kiyi kaman yar diyar sa fa yar kadan dake kiji ranan a asibiti yanda ya miki daukan jarirai “ Aydarh ta dai yi shiru tana sauraron dr hafsa ita kanta tana san yayi babba dayawa Allah bai ta bak o dr ibrahim shima namiji kuma bai laifi yanada girman malik can carry him balle ita da ranan cewa yayi kaman ya dauki paper “ dr hafsa data gama cin pepper chicken dinta tace bara kiga nazo na wuce yamma yayi yanzu yallabai ya dawo aydarh tace dan Allah auntie ki bari sai magrib please ‘dr hafsa tace magrib din lapia yanzu zan tafi kuwa, aydarh tace eyyerh auntie dr hafsa tace na fa sha wuni a gidan nan “ Aydarh ta langwabar da kanta dr hafsa ta rike baki tace nidai bara na tafi ki adana shagwaban ki wanda zakiyi ma wa yakusa karaso shine zai biyeki aydarh tayi saurin mikewa don taji kunya ta rufe fuska har bakin kofan part dinsu taraka kafin ta rufe kofan tadawo parlor bowl din ta dauke kafin ta fito da tsintsiya ta share parlor duk da babu wani dirty a parlor hadda moping kafin tasaka freshener ta koma bedroom nan a gyare yake tsaf gwanin kyau .Da sallama yashigo bedroom din bayan yadawo masallaci Still tana kan prayer mat tunda yafita magrib bai dawo ba tayi tunanin sai anyi isha kuma dai taji shiru bayan angama “duk da babu agogo amma tasan kusan pass nine yanzu yana shigo ta mike zaune tana kallonsa ko kiftawa babu he his making call and his eyes are on her “wayan ya kashe yana kallonta har yanzu murya babu yabo babu fallasa tace ina kaje?malik yashafa kansa yace number wata aka bani tana siyar da perfect cake can naje nasiyo “Aydarh ta dinga kallonsa idonta har ya tara kwalla tace wata fa kace sir “malik da iyakan gaskiyan shi kenan yace ehh hajiya is there anything wrong? Aydarh tayi shiru tana dauke kanta “shidai sai kallonta yake har yazo kusa da ita ya ajiye ledan perfect cake din mai dankaran kyau ga sunan mai yin a jiki ya zauna kusa da ita ya kamo hannunta yace wife “is anything wrong ?kaman tana jiransa tace nothing is wrong kaji malan har yaso yayi dariya don tabashi dariya sai ya daure yace tau talk me miya faru “jawosa tayi kawai ya kwanta kan cinyanta ya dinga kallon kwayar idonta dake shinning ruwan hawaye saboda yanda ta kwantan dashi kaman irin zatayi feeding dinsa ya dinga kallonta fuskan ta shi baya gajiya da kallonta gashi tasaka black hijab sabo fil sai kamshin rahama take “ hannunta tasaka a suman sa tace ni dai don Allah koma miye indai sai kaje wajan mace zaka siya nidai na yafe don Allah nace sir “malik ya dinga kallonta kafin yayi kasa da murya yace in sha Allah wannan ma kawai abokin dr ibrahim yabani dazu naci shine na tambayesa yace yarinyar dazai aura ke siyar tare dashi mukaje mu siya hadda dr ibrahim ma shima ya siyan ma matarshi su sukayi dropping dina kafin su wuce aydarh ta gyada kai kawai kafin tace to tashi “yace naga bani na kwanta bake kika kwantar dani “sai lokacin ma ta tuna abunda tayi ta dan daure fuska tace erh kuma shine nace ka tashi kafiye nauyi “malik yace kuma kina cewa ni kato ne zan nuna miki wani abu anan yafada yana placing hannunsa a can “tayi saurin dauke kai kawai kusan two mins taki juyuwa yace tau tadani sai na tashi hannu tasa tana kokarin mikan dashi aikam yayi saurin rike hannu yatashi da kanshi dasauri ya dinga kissing fuskanta zuwa bakinta “bata masan yanda zatayi dashi ba kawai ta kyale sh isai dayayi mai isan sa kafin ya rabu da ita yana kamo hannunta yace you looks more than pretty a hijab din nan “kaya baki suit you everything ma suit you angel “Aydarh tayi dan murmushi kafin taja long nose dinsa yace okay tashi ki cire hijab din sai mu ci cake din “Aydarh tace no basai na cire ba malik yakalleta yace it’s alright,ledan yajawo ya tura mata nata kafin ya dauki nashi yana kallon yanda take ci sai yama kasa cin nashi kallonta kawai yake ko kiftawa babu his heart beats for love “he go anywhere to anything for this girl yana son ta whattttt,malan billahi yana sonta can tadago suka hada ido ta shagwabe masa fuska tace what ?yace you “tawara ido tace ni kuma yace eh tace mi nayi kuma yace komai ma tace to sorry yace naki ‘tace to ai ban san abunda nayi maka idan kaji haushin fadan danayi maka sorry ya girgiza kai yace nothing lily continue eating the cake tace kai miyasa kadaina ci yasaka spoon ya ballo yace Ina ci manah tace to “kafin ahankali takallesa kaman mai son tuno wani abu tace ehen auntien tazo yace wacece kuma tayi yar dariya tace auntie hafsa fa Yace ohh kai haba tace erh “yace ta kyauta aydarh tace daman kitso nake so da lalle malik yace nima da kaman nace miki kiyi but this time kiyi kitso kinji ta gyada masa kai yace lallan banda black only red nake so tayi shiru kafin tace to “yaushe zanje?yace gobe sai muje aydarh ta kallesa kafin tace no banda kai yace tau sknn ai mai kyau kalan wanda ya fita “tayi murmushi tace ohk”kafin yace ai bai fita dawuri why?tace nima I didn’t know why auntie hafsa tace wai don inada cin lalle ‘’malik ya kwashe da dariya yace oh cin lalle kike ta daure fuska tace bafa wannan ba sir lalle yana zauna mun a hannu yace oh tau gobe sai kuje kinga jibi zamu tafi flight dinmu na four ne da yamma “Aydarh ta gyada masa kai tace Allah yakaimu lapia yace Ameen Ameen bata karasa cin cake din batace ta koshi “karba yayi danasa ya hada baki daya yakarasa cinyewa tashi tayi ya bi bayanta da kallo har tashiga toilet ta turo kofan “sabulu tasaka ta wanke fuskanta kafin tayi brush ta fito baya dakin perfume kawai tashafa kafin ta linke hijab din tasaka wardrobe ta linke sallayan kafin “ ta kwanta kan katifan tasaka duvet ta rufe har kanta “ahankali yashigo dakin ya dinga kallonta kafin yasa hannu ya kashe hasken kafin ya rage gudun fanka yazo kusa da ita ya kwanta yasan batayi bacci ba amma taki bude idon idonta malik ya dinga kallonta kafin yace ai shknn yasaka ta jikinsa har shima baccin ya daukesa “yace da wuri zamu fita yanda bazai ja time ba tace to kira mun auntie a waya yace ohk”kafin yayi dialing number dr hafsa har takusa yankewa tadaga ahankali aydarh tace hello auntie “daga can dr hafsa tace aydarh,Aydarh tace ina kwana auntie ya inna dr hafsa tace lafiya lau y yallabai aydarh tace he is fine auntie yace dasafe zamuje dr hafsat ace alright idan kingama shiryawa ki kirani sai nafito mu wuce bara nakirata yanzu aydarh ta gyada kai kafin tace thanks ta mika masa wayansa ya karba” yace tau mukarasa breakfast din tunda kinyi wanka kaya kawai zaki saka ta gyada masa kai “tea da bread sai fried eggs sukayi break dashi “dakin tashiga bayan sun wanke kayan dasuka bata for breakfast “ black abaya tasaka tayi rolling veil din hadda powder tashafa da kwalli tasaka lipstick wanda yayi masifan yiwa lips din kyau ta saka perfume kafin ta fito da flat shoe shima wani mad black color wanda suka siyo yanda kafan yayi cikin takalmin yah rahamanu ya Allah daga parlor ya dan daga murya yace lokaci naja fa fitowa tayi ahankali tana ce masa ai nagama ma “yah rabbi mikewa kawai yayi yakasa rufe bakin sa ma yazai misilta kyawunta yazai kwatanta kyaun datayi tabarakallah har ta karaso yakasa ko kifta idonsa ahankali ta busa masa iskan bakinta firgigi yayi kafin yashafa kansa yana murmushi yace kinyi kyau tasaukan da kanta tace ka kira auntie wayan yamika mata da kanta tayi dialing number dr hafsa na dauka aydarh tace auntie nashirya dr hafsa tace tau bara na fito takashe wayan “malik yace muje kofan gida sai mujira ta

Chapter 38 of 83