Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
komai shiyasa nace kazo sai naji daga bakin ka malik yace eh , babu damuwa Allh musa yace to daga gobe in sha Allah zaa fara aikin site din kaine babban engineer malik yayi godiya kafin Allh musa ya fiddo 5k yabasa yace transports ne.plate din chips yasiya kwara biyu shi daya ita daya tun kofar gidan Allh musa suka rabu da dr ibrahim kasancewar akwai inda zaije ,yasiya man mata fresh green apple sai water melon yahau keke ya dawo gida,a plate ya juye kafin yayi sliced din apple din da kankanan dakin yashiga da sallama,can kasa ta amsa sa yashigo. Zaune take ta jinginan da kanta a wall,ahankali take breathing kallo daya zaka mata kasan she is sick fuskan nan tayi karkar kaman madara,idonta ya dan fada ciki ahankali take rufe idon tana budewa kaman wani yasata, kallonta yake ko kiftawa babu kafin ya dauke ido,ahankali ya ajiye plates din hannunshi dukka biyun “ murya can kasa yace how are you feeling now? Kaman bazata ce komai ba,tace better daga nan taja bakinta tayi shiru shima shirun yayi kafin yace “sit” tashi tayi ta zauna ahankali kanta kasa plate din chips ya dauka ya daura matakan laps dinta kafin straightly yace “eat” hannunta yabi da kallo yanda take juya fork din a mugun gayence rings din hannunta masu masifan kyau da daukar ido bakaramin karama hannun nata kyau yayi babu digon lalle ko kadan, chips din data ci bai fi 8 ba egg din ma rabi taci,ta ture ‘plate din chips din ya dauka yasake mayar mata a cinya kafin yace eat it all! Kallonshi tayi kadan kafin ta kalli plate din tayi raurau da ido alaman kuka zatayi kafin ta girgiza kai,muryanta irin masu gaf dayin kuka taci na koshi ai “ baisake cewa komai ba ya kwashe plate din chips din ya fidda a warmer yazuba sa, sannan ya dawo ,ko baiyi magana tasan abunda yake nufi,ahankali ta dauki sliced din apple daya tana tauna kadan kadan ba laifi tace kusan 4sliced kankanan ma taci kusan uku satar kallonshi tayi kafin ta ajiye plate din, kusan 10mins suna zaune a haka babu wanda yayiwa daya magana,mikewa yayi ya zuba mata ido yace akwai abunda kike so kuma?batayi magana ba sai gyada masa kai kadan datayi alamar babu fita yayi daga dakin ya koma parlor. Inna dake tsaye bakin ventilation din su da katuwar jikkanta sai gwada sallama dake,jin ana sallama kuma da alama na ne yasa shi ajiye tsintsiyar dake hannunsa ya nufi kofan part din inna yagani tsaye,murmushi yayi ya shafa kai yace inna sannu da zuwa ina kwana? Inna tace na ma fayi tunanin hala cutar kurumtaka yasame ka ace na kusa tanminid ina banka sallama amma shiru baa amsa ba kuma baa zo aka bude ba,malik yace ina can ciki fa yanzu shigo, shigowa tayi ta zauna kan carpet din ta ajiye jikkarta gefenta malik ma ya zauna yace inna ina kwana?ya gidan mun tashi lapia?inna tace lahiya lau audu ya kwanan mai jikin kuma?yace Alhamdulilah “tashi yayi yashiga kitchen sauran fruits din daya siyo mata ya ma inna slicing ya kawo mata yasan ko ya kawo mata abinci bazata ci ba ma, inna ta bi fruits din da kallo kafin tace ohhni hajara banda kai daga nashigo dubiya kuma sai ahadani da kayan karin ciwo ni dana zo dubiya,malik yace babu komai fa inna,yawwa inna nace jiya an bawa hafsa kayan?inna ta juya kai ta kalli kofa kamar mai tsoron magana ta dauki kankana daya ta sa baki tana sha,kafin tace eh ta karba tau Allah natuba audu miye wani abun bawa hafsa ta kai wa matarka dinki ita kanta ba fa wani masu dinki arziki ta sani a kanon nan ba wallahi,dan dai babu ruwana amma da jiyan nan nace kabani na kai idan ake man nawa dinki,malik can’t hold it but to laugh dariya yake irin wace yajima baiyi kalar ta ba hadda rike ciki,inna ta ajiye slice din apple din data dauko tana kallonshi ko kiftawa babu “ idan tana kallon malik sai ya dinga tuno mata dawasu mutane a rayuwarta amma har yau ta kasa fahimtar su waye,saida yayi shiru kafin inna ta dawo daga tunanin data tafi,yace tau inna ai da hakane tun jiyan da baki ba ita hafsa din ba,inna tawani daure fuska tace dariyan dakakeyi nabari kagama kafin nayi ma bayanin waya wayar da hafsa din,malik da har yanzu dariya ke cin sa yace yanzu dai duk abar wannan zancan amma ai kowa yasan wacece ke wajan gayu inna tawani tabe baki irin kai ma kafada din nan, Dasauri ta ture plate din tace astagafirrillahi nabani ni hajara,dubiya fa nazo ina matar dabata da lahiyan,malik yace ai surutu ma yasa kin manta abunda yakawo ki bara nakira ta”,Baiyi knocking ba ahankali ya tura kofan da sallama can kasan throat,ko kadan bataji motsi ko alamar shigowan sa ba tsaye take ta fito wanka ta baza gashinta data wanke da shampoo din da maman dr ibrahim tasa ya kawo mata ko daya fada mata bata gane wa yake nufi ba ya ajiye dai kawai, tana son wanke kanta saboda she forget when last taje saloon tun tana adamawa wanda ka’ida ne duk two weeks ake mata gyaran gashi duk da bata so amma rashin son kazanta ke sata zama a wanke mata dakuma fadan da oum keyi idan bata wanke ba,pink towel din nan ke daure a kugunta bra dinta nan kwara daya tagama sawa yanzu wanda ta fito a toilet wanke tass tana ta kamshin detergents daba ya wasa wajan siya a ajiye mata a toilet tagama sa bra din tana kokarin mayarda towel din a kirji ya karasa shigowa baki da daya bataji motsin sa ba still,wallahi saura kadan numfashin sa yafita jikinsa bayanta yabi da kallo this is the forst time daya taba ganin wata diya mace ahaka,bai san magnet din dake jan idonshi wajan kallon bayan nata ba yarda bra din ya zauna a haddadan bayan nata da yarda milky clean skin dinta da babu spot ko wani stain ko daya ke mahaukacin glowing yaraina girmanta gani yake yar karama ce amma yau sai yasamu kanshi da karyata hakan, ahankali ta juya tana daga hannunta dukka biyun zatayi parking gashinta still towel din na a wrist dinta tana juyuwa kallo daya yayiwa boobs din yawani irin dauke kai kamar zai karya wuyan shi ,saura kadan bata suma ba yarda ta tsorata dawani irin speed ta jawo duvet ta rufe jikinta baki daya hawaye na zarya a kumatun ta, kafin tafashe da kuka yagama da ita yagama da rayuwarta, how long yake tsaye a wajan inalilahi waina illahil rajiun shi kansa malik din duk ya rude bai san miya yaja sa ya tsaya yana mata irin wannan kallon ba,juyawa yayi dasauri har yakai kofa kafin ahankali,yace inna ce tazo dubaki “bai jira amsarta ba yafice ya ja kofan,Time din daya dawo parlor inna har ta shanye fruits din tass zama yayi kanshi a kasa yace,wanka ta fito shiryawa take yanzu zata fito inna tace Allah sarki, fira suka cigaba dayi duk da yau innar ce kawai ke zuba surutun ta malik abunda yafaru yanzu duk yasa shi jin wani iri,Bude kofar akayi ta fito kanta kasa kamar marar gaskia tana wannan tafiyan ta ta,kallo daya yayi mata ya dauke idonshi ko ganin sa ma batayi ba kanta kasa,ahankali ta zauna kafin ta gaishe da inna,inna ta washe baki ita ko kadan bata lura da mood din aydarh ba tace lahiya lau diyar nan ya karfin jiki?ashe baki ji dadi ba?Aydarh tace Alhamdulilah,bata sake magana ba domin ji take kamar zatayi hauka zama inda yake yana sata jin girman laifin daya aikata mata, inna dai sai zuba take ko shiru babu jefi jefi malik na biyeta, Ahankali cikin voice din ta dayayi kasa sosai innocently tace inna nagode sai anjima,inna tace nima tafi zanyi bara kigani mikewa inna tayi ta maka jikkarta a kafada tayi masu bankwana malik yatafi ya rakata,aydarh tayi saurin shiga bedroom tafada kan katifa kuka take sosai iya karfinta pillows din dake kan katifan ta dinga watsar wa hatta da duvet din da bedsheet din sai data watsa kasa,malik dai natsaye jikin kofan da bata rufe ba yadaga curtain yana ta kallonta baki daya rayuwarta abun tausai ce ansaba mata da irin dabi’ar turawa na watsar da abubuwa idan suna cikin kunci,parlor yadawo bai shiga bedroom din ba,tunanin ta inda zai fara billowa lamarin ta yakeyi,wata zuciya tace masa wannan duk mai sauki ne ka fara aikin tukunan da haka ya yanke shawara yakasa manta abunda yafaru dazu daya juya sai ya tuno hakan yasa shi daukar al”Qurani dake nan ajiye a parlor ya bude muryan shi yana rera karatu baki daya part din babu inda sautin muryan shi baiyi amsa kuwa ba,Har cikin jikinta karatun ke shiga wani sanyi take ji a zuciyarta wanda bata san daga inda yake ba ahaka har bacci ya dauke ta,yayi spending almost 2hrs yana karatu kafin ya rufe ganin time din lunch ya kusa saboda lokacin azahar dake kunnu kai.Yau ma kamar kullun sai datayi masa magana amma Ko kallonta baiyi ba, har tana tuntube ta bi sa har waje, bata gaji ba har wajan inda zaiyi cefane ta bisa bai tanka ta ba dan yi yayi kamar bai san da wanzuwar ta a wajan ba kayan miya yasiya na 300h kafin yasiya salad na dari sai da beef na 500h kafin ya mika kudin har ta riga ta bayar sanin ko wacece ita yasa mai cefanan cewa hajiya Ramlah shine yasaki?tana taunar chewing gum irin na kwararun yan barikin nan papa (Sosai) tace miyayi ruwanka kudinka ne biya ka ka rike sauran change din, mai cefane dai yasaki baki yana bin ta da kallo,wani kaskantacan kallo malik yabi Ramlah dashi kafin ya sake daura fuskar nan kamar hadari,wallahi Ramlah idan tana kallonsa har loosing control take, daura fuskar nan dayake ba karamin tafiya yake da ita ba haka ranar da taga suna dariya shida dr ibrahim a kofan gidansu har mutuwan tsaye tayi,bai ce komai ba cikin wannan isan nashi ya Zaro 1k ya mikawa mai cefane mai cefane baiyi musu ba dauki 200h yabashi chanji,juyawa yayi yatafi bai kara bin ta ita ba, ko kadan abunda yayi mata bai dameta ba ko taji kunyar abunda yafaru ganin akwai mutane sai ma kara gyara calaban attachment din kanta blue and green tayi gaba mai cefane yace kudin hala kin bar mun?wata banzar harara ta watsa masa tace kaine dan wahala ai sai ka rike ta juya ta tafi mai cefanan ya daga murya yace gaki nan yar wahala yar asara ma Allah ya shiryaki matasan dake tsaye wajan suka sa baki,dayan yace ai wannan yarinyar yar wahala ce kullun fa ina nan kusan ko yaushe sai ta biyo balaraben nan shi kau ko ta ita baiyi ni bana ganin ma yana shiga harkan kowa a anguwar nan, mai cefane yace ai baya ma fitowa cikin layin nan indai kagansa waje tau gidan hajiya inna zai shiga sai kau wani abokinsa dake zuwa wajansa mutunmin ma dabaya magana kamar jinin sarauta kullun anan yake cefane gaisuwa kawai ke shiga tsakanin mu yasiya abunda zai siya yayi gaba.sai daya shiga provision shop yasiya spices da maggi ya siya kwai kafin ya koma gida, yana shiga kitchen yafara yashiga yadaura ruwan da zai dafa shinkafa kiran sallarh akayi ya rage wutan gas din yafita massallaci,white rice ya dafa da stew ya yanka salad yayi boiling 3 eggs din da ya siyo tsaf ya shirya mata a plate,kudin hannunshi sun kare tass ga abincin daya siyan masu yakare daman ba mai yawa bane shinkafa ne tiya daya sai macaroni biyu taliya hudu da indomie six,bakaramin dadi yakeji bi idan ya tuno da maganar aikin daya samu bazai taba mantawa da dr ibrahim ba a rayuwar sa domin yayi mashi hallacin da har abada bazai iya mantawa ba, pure water ya daura mata a plate wanda bag daya yake siyowa ya ajiye kan tiles din kitchen sanyi damuna ke dan cooling ruwan, da sallama yashiga dakin tana jinsa tayi maza ta rufe idonta,yaga abunda tayi bai ce komai ya ajiye plates din hannunsa yace stand up and eat”kafin ya juya yayi ficewar sa Dr hafsa ta juya atamphar kafin ta mayar a leda,tabi inna da kallo tace shi yakawo a kai a dinkawa Asseeyan?inna tace wacece kuma asiya?dr hafsa tace matar tashi inna tayi ma dr hafsa wani kallo tace tau uban waye wanda yace maki sunanta haka?dr hafsa dake kallon inna da mamaki tace tau ai sai kibata wani sunan idan ba sunanta haka ba,inna tace aaaa gaskia katuwar karya kike daman dai kowa yasan ke ba kaunar Allah kike ba,amma shi audu bah aka yake fadi ba sunan ma da kamar da larabci yake fadinsa “dr hafsa tamike tsaye ta dauki handbag din da wayar ta sai ledan atamphar kafin tace sai kiyi kuma kawai dais hi haka yake fadan sunan ne sai kiji kamar larabci amma dai sunan ta Asseeyah ni nafita,daga haka dr hafsa ta juya tayi tafiyan ta, inna data kasa shiru tace kai amma gaskia audu bai kaunar Allah ashe duk zaman nan damuke sunan matar nan asiya yaja bana kiran sunanta saboda kar na fada a raina ni ban iya ba, ni fa idan naji yafada sai nayi tunani sunan larabawa ne ashe duk kwarewa ce,sai kuma tayi shiru ta tabe baki tace tau dan kanshi.Jin knocking din da akeyi yayi yawa yasata fara tunani ko dai shine yafita kofan ta rufe,sai kuma ta tabe baki ta juya sake buga kofan akayi ahankali ta tashi ta bude veil din abayar ta tayafa bude kofan bedroom din tayi taga bai parlor ga kofar kitchen din a rufe tau kodai shine tasamu kanta da tambayar kanta,ahankali tasa hannunta kan Handle din kofar kamar kuma mai tsoron bude kofan tace waye?dr hafsa da har tagaji da tsayuwa zata juya a tunaninta ko basa nan tace nice,Kamar taso tagane waye amma kawa isai da bude tsaf tagane dr hafsa,murmushi dr hafsa tayi tace da har zan juya nayi tunanin ba kwa nan ai,aydarh tayi murmushi kadan tace ina wuni?sannu,dr hafsa ta amsa mata,anan parlor suka zauna babu wanda yakara magana cikin su,so take ta tuno abunda malik keyi idan anyi guest,kitchen tashiga ta dinga bin koi na da kallo pure water tagani asaka biyu ta dauka ta daura a plate takawo wa dr hafsa din kafin ta koma ta bude warmer da ta gani a kitchen din abinci daya dafa ne da rana white din ta zuba a plate tasaka mata stew kadan sai salad takawo wa dr hafsa,dr hafsa na murmushi tace lah ai da baki kawo abinci ba yanzu naci abinci kafin na fito kuma ma sauri nake,aydarh tace aa fa sai kici ko kadan ne “kanta akasa tana wasa da zuben hannunta kadan kadan dr hafsa ke mata fira murmushi kawai ne nata dan bata cewa komai itama dr hafsa din bawai tafiye surutu ba, ba laifi taci abincin tasha ruwa,ta kalli aydarh tace mai gidan baya nan ne?tsaf aydarh tagane wanda take nufi hakan yasata cewa erh”dr hafsa tace kinga sauri nake jiya ne yakai wa inna wannan atamphar yace tabani na kai maki dinki, so bansan measuring din ba,aydarh tayi shiru kafin can tace kawai ayi tunda ban san style din ba,dr hafsa tace aaa ga styles nan kala kala sai wanda kika zaba, murmushi tayi tace aa ayi kawai,dr hafsa tace no kafin tayi unlocking wayanta tashiga photos screenshots din styles din dinki ta nuna mata wanda tayi a ig, ita dai aydarh sai bin dinkuna da kallo take, bata wanda zata ce yayi mata ba amma hakan nan ta zabi wani free straight yayi kyau sosai, dr hafsa tace kuma zai maki kyau sosai masha Allah, miye measuring din nan aydarh tagaya mata domin komai nata tasani kuma bata mantawa,har kofar part din ta rako dr hafsa din tayi mata godiya ta wuce, tana dawowa ta kwashe plates din ta kai kitchen ta jawo takalman sa slippers dake nan bakin kofar toilet din ta bi da kallo ta dauke ido tana tsakin siririn tsaki iya lips dinta, hakanan taji tana son zama parlor sosai taji dadin zuwan dr hafsa ashe mutun rahama ne,duk sai taji bata ji wani damuwa Sosai, yau din nan, nan kan carpet ta zauna ta kura wa wuri daya ido,kara knocking kofar akai tanaji har sai da akayi sau uku kafin ta mike taje ta bude, Ramlah ce tsaye sai wani taunar chewing gum take kamshin karamin perfume dinta kalar na yan bori duk ya cika ma aydarh hanci babu alamar wasa ko wani murmushi a fuskanta ta koma real aydarh ta na can baya take kallon Ramlah da kusa shidewa wajan kallonta batayi tunani takai haka ba domin bata taba yi mata kallon gab da gab ba, maganar da aydarh tayi yasata dawowa cikin hayacinta,tace lapia? Ramlah ta aro jarumta domin kwarjinin aydarh yasata firgita daidai nutsuwan ta tayi kafin tace lafiyan kenan yayah malik nake nema idan yana kije ki ce masa gani nan nazo,kallonta tayi sama da kasa kamar taga wani abun kyama. Ganin irin kallon datake binta shi yasa Ramlah gyara tsayuwar ta, Aydarh bata ce komai ba tajuya ta koma ciki tayi banging door din a fuskar Ramlah,wani irin mugun ashar Ramlah tayi “ kamar zatayi hauka a inda take tsaye ita tayi ma wannan rashin mutuncin tau wallahi bazata yarda ba.fadila tayi shiru tace umm ni wallahi baki birgeni ba da baki tatakata a wajan ba tau wacece ita haka?maman Ramlah datayi shiru tace nidai ku bi komai ahankali kar fa ace mutanan batar da sahu sukayi ,kuyi masu rashin mutunci ayaye ku a daure wallahi,fadila tayi kasa da murya tace wallahi fa maman Ramlah ni har tsoro suke bani daka gansu fa kaga kudi da mulki kar fa dai yaran sarkin makka ne?ramlah tayi wani uban tsaki tana hararar fadila da maman tasu baki daya tace ku fa matsalana da ku har yanzu kanku a duhu yake kauyawa ne ku wallahi bacin haka miye wani abu danganta su da wani sarkin makka miye ma tau zai kawo su nan in har hakane?kawai da wallahi abunda tayi mun sai narama shine kawai,duk shiru sukayi babu wanda ya tanka ta cikin su. Ko data koma daki tunanin ramlah ta yakasa barin ranta,tau wacece wannan kazamiyar da zata zo neman sa kuma,sai kuma taja dogon tsaki tace miye ruwanki dashi, nan take abunda yafaru da inna tazo yadawo mata a rai tayi tsaki yafi a irga,kwanciya tayi tana ta juye juye idonta ya sauka kan wani karamin littafi na azkar na shi ya manta shi a carpet din dakin jiya,ahankali ta mike ta dauka budawa tayi tana dubawa sosai ta maida hankalinta wajan duba littafin bai fi addua biyar tasani a ciki ba tunuwa tayi da yarda yake raira karatun al quraani dazu ,wannan ne karon farko a rayuwanta dataji tana so sanin wani abu game da addini bayan wanda tasani wannan ne first time datayi hawayen kin tsayawa tasan abubuwa game da addini babu yarda oum batayi ba rufaidarh ma haka amma tasamu daurin kugu wajan abba nakin tsayawa ta koya din,abubuwa dayawa gasu rubuce a littafin amma bata iya karantawa da hausa sai kuma larabci akayi rubutun,ta iya ranta hausa tsaf amma batasan ma’anan adduo’in ba.Ba karamin gajiya yayi ba a yau din nan aiki ne wanda bai saba dashi ba duk da yanda ya taso amma kwata kwata jikinsa ba mai son wahala bane,aiki ne wanda bai taba yin irinsa ba shiyasa ya sha wahala duk da matsayin shi na babba a wurin yanada hutawa amma dai yayi wahala sosai,jikinshi duk yabaci da cement haka kayanshi duk sunyi kura kadan bayan sun tashi aikin kowa ake basa 2500 cash a hannu,duk da kudin babu yawa he appreciate tunda dole ya bukaci kudi ko dan saboda aydarh ko dan saboda yanayin rashin lafiyan ta,yana shiga kitchen kawai yawuce ya daura ruwa a gas yasan batayi wanka rana ba tunda bai nan balle ya dafa mata ruwan wanka,sai da ya daura kafin yashiga toilet dinshi nan parlor yayi wanka tass kayan jikin shi ya mayar yashiga dakin da sallama kallonta yake ko kiftawa babu har yanzu littafin ke hannunta tana karantawa duk da ba fahimta take ba,abunda yakawo shi dakin yayi ya fita, sai dayashirya ya jika kayan da ya cire a bucket kafin ya duba ruwan,bucket din toilet din ta ya dauko yajuye mata yafita,Sosai ya ci abinci kafin ya koma toilet ya wanke kayan shi tass ya fita ya shanya dan kwanciya yayi kadan kafin a kira sallarh magrib.Awara yasiya masu yashiga gida domin ba karamin gajiya yayi yau din nan ba kuma kwana biyu ma sai ahankali yake jin shi kamar zaiyi fever, AFTER A WEEK Alhamdulilah malik yanzu har ma yasaba da aikin ginin dasuke ga ta gefe guda wani irin kirki Allh musa yake masa kamar irin ya jima da sanin shin nan yana matukar jin dadin aiki dashi Sosai.kallon shi yake ko kiftawa babu har yayi shiru kafin malik yace har fa kwana biyu kace dr ibrahim ya gyara zaman sa a kujeran clinic yace eh kwana biyu zamuyi can nasarawan tunda kai ne babban aboki kaga dole mutafi tare,malik yayi shiru can yace tau Allah yakaimu “dr ibrahim yace Ameen kafin yace ya aikin?malik yace aiki Alhamdulilah,dr Ibrahim ya saukan da ajiyar zuciya yace take heart malik in sha Allah zamu samu wanda yafi wannan nasan baka saba ba nasan daurewa kawai ka ke kayi hakuri in sha Allah zaa samu wanda yafi wannan ,malik yayi murmushi yashafa kanshi yace kaga tashi muje gidan inna zan karbawa ASSEIYARH dinki gun dr hafsa dr Ibrahim yace tau badamuwa muje nima kwana biyun bamu gaisa da innan ba.inna ta kalli dr Ibrahim tace daga ina kai kuma? Lahiya dai ko?ko rashin tsoron Allah yasa wata katuwa taje tace maka banda lahiya aaa wallahi lahiya ta lau tambaye audu gashi nan shi ai yasan gaskia,dr Ibrahim dayake kallonta yasaba da halin ta basa shiri sam kullun idan yazo sai sunyi fada “yace tau ke dakika ga nashigo daga gaisuwa kinga nace maki wani abu ne?inna dai tayi banza ta kyale shi ta tashi ta shiga cikin daki , hadaddan kwadon zogale day asha kuli da kayan hade ta fido cikin kula, tace tun dazu nayi maka audu tau da nayi tunanin baza ka zo ba ,har ina cewa yamma tayi na kai ma matar ta aje maka, malik ya karbi kular yace tau shknn inna nagode shidai dr Ibrahim bai ce komai bas ai danna wayarsa yake, dr hafsa ta fito hannunta rike da dinki aydarh gaisawa sukayi cikin mutunci “ tana tsokanar shi ango ango dr Ibrahim yayi murmushi yace fadi ki kara,inna tawani tsuke fuska ta kalli malik kafin tayi kasa da murya tace kaji wani jafa’I bikin da saura kusan kwana sha biyu miye abun wani fara kiran mutun da ango banda neman magana,Allah dai ya kyauta shi dai malik bai ce komai ba yanata kallon inna, dr Ibrahim ya mike tsaye yace ma malik ka tashi mu tafi ni akwai inda zani,inna tasaki baki tayi shiru tana kallon dr Ibrahim tace aaa kai kau ibrahin kazama abun tsoro yanzu kai ina ruwanka da shi wuri daya kuke kwana ko kuma wani neman maganar ne,dr Ibrahim tace ni fa bana son kina yawan saman baki idan ina magana kema ina ruwanki fisabillahi? Malik yayi murmushi yace yanzu duk hakura inna na bara nakai ma jikarki sakon zan dawo in sha Allah,dr hafsa dai tayi shiru batace komai ba. Tsaf ya gyara gidan koi na fess babu abunda ke bukatan gyara, ranar tafara sa dinki Sosai take kallon kanta a mirror din window bedroom din tayi wani irin kyau mai fuzga bakaramin tuno mata da ummi atamphar take ba murmushi tayi ahankali kafin ta dauke body splash din ta fesa kanta tasamu tayi parking sumar can kasan kan babu saloon amma yayi matukar masifan kyau kallabin ta daura all back kafin

Chapter 12 of 83