Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yadawo yazauna yana taba wayarsa kawai, ganin tana daukan lokaci har kwan ma yayi sanyi yace idan bakiyi sauri ba zan dura miki abun nan,aikam kaman jira take tayi saurin cinye last cut din kafin ta goge lips dinta da tissue dake nan gefen su a parlor, kafin tamike takawai plate da fork din sai cup da bread din kitchen tana shiga ta hada danasa danata ta wanke tass kafin tasa karamin towel ta sake goge sink din da ruwa yabata kafin ta fita bedroom ta wuce tana fito da kayan dirty ta duk da ba su dayawa ana daga suma kamshi kawai ke tashi (lemme use this opportunity please and please kuyiwa mahammada rasulilahi S.A.W ko baku da kudin perfume ku din shafa alimun na naira hamsin ya isa yana tsane zufa please, damsel zata baku labari saura kadan tayi barin dan cikinta a wani event damu kaje jiya tsaban an gigita da odor) yana ganin tashiga bedroom yatashi shima ya bita yadinga binta da kallo watau taji yace zasuyi wanki tsaban miskilanci ne yasa tayi masa banza baice komai ba ya dauke kai ya bude inda nashi suke, yacigaba da fitowa dasu, har sai daya gama time din itama tagama, toilet din ta yawuce yadauko buckets sai soap wanda can suke ajiyewa daman can gida yasaba wanki da fizz shiyasa ma dasuka zo nan shi yake siyowa (shima fizz baya da tsada a taimaka yan uwa Wallahi har wanka ana yi dashi shima yana taimakawa wajan yaye odor) kanshi yadaga yana kallon very clean and attractive brassiere dinta dake wanke kal tayi hanging dinsu a nan toilet din murmushi yayi shafa kansa kafin yasa hannu ya jawo su ya dauki bucket din da soap din yafita, yana fitowa ta lura da abunda ke hannunsa ai dawani irin speed takarasa gabansa ta sa hannu ta figze kaman zatayi kuka ta mayarda su bayan ta “malik yabude ido alaman bai ma gane abunda take nufi ba yace ko wanki nace miki zaayi ba? Tayi masa banza yace ko bazaa wanke su ba su? Sai sannan da muryanta har yayi na kuka tace ai dai kasan a wanke su ko,malik yabude hannu yace aaaaa relax hajia kar kiyi mun kuka a ina nasan kin wanke su nayi tunani ai bakima iya wanki ba shiyasa nadauko sai mun wanke,har kwalla ya kawo idonta tayi gaba zata mayarda su toilet din tayi hanging tace daga yau karka sake taba mun,yace Alright booby girl!! Ai har kusan faduwa tayi jin abunda yace aikam da mugun gudu ta kwasa ta shige toilet tana shiga ta fashe da kuka kaman irin sai daya sharara mata mari,ya lura wannan yarinya tafisa fitina rigima gareta da shegen shagwaba sai ka rantse kace she is 15 wani yarinyar ma yar 15 tafita wayyo bazaka tabawa cewa tayi ashirin da biyu ba,kawai dan Allah yayi ta hakane and she deserves to even do more than this duk wani gata na gidan duniyan nan babu wanda bata gani bah, girgiza kansa yayi kafin yadauki veil dinta yakai a nose dinsa lumshe ido yayi yana jin wani irin precious air na bi ta koi na a dakin he is mad akan kamshin nan nata yana son kamshinta fatar take ke very warm gawani natural scent mai yin kaman tana using da rose yana sa shi jin wani iri duk sanda suka samu kusance da juna “ tunda take kukanta yana jinta taki shiru kuma taki fitowa ita kunyar ta daya dayace mata booby girl,bakaramin kunya yasata ba,ganin taki fitowa yasa shi yin knocking tana jinsa tayi masa banza ta dinga zubawa kofan harara kaman irin shine a tsaye wajan,can yace open the door, nan ma tayi shiru kafin yace tau ai shknn bara naje sai ita Ramlah ta tayani tunda ke bazaki fito ba tanaji abunda yace tayi saurin bude kofa, tana kallonsa da fuskanta dahar tayi ja tace Wallahi bara ta taba kayana ba balle naka ma, idan bahaka ba I will beat her blue and black Allah, malik yayi murmushi yace tau kiyi hakuri yanzu mu tafi can ventilation sai muyi wankin ko? Aydarh ta gyada masa kai shi yadauki kayan dukka ita ta dauki musu bucket da soap, nata aka farawa da ya wanke sai yasa mata yayi tunani bata iya bas ai gashi yaga tana yi , har suka kusa gama nata babu mai magana cikin su amma there looks good kallo daya zakayi musu ka kasa dauke ido can yayi kasa da murya yace ashe kin iya wankin?ta dago tana kallonsa kafin tace erh yace kinyi kokari tayi murmushi kallonta yake ko kiftawa babu yace bana son asaka hakuri amma your own looks cute tayi murmushi tace thank you hakurin gwal din yasake kalla wanda yazauna mata dass a jerin white teeths dinsan sai shine shine yake sau dayawa idan tayi dariya yana so yayi magana shiru kawai yake can dai suka karasa nata ya kwasa ya wuce can bayan part dinsu zai shanya shanya su yayi kafin yadawo yana dawowan yace tau kiji ki huta sai na karasa nawa ko? Ta girgiza tana wasa da foam din dake cikin bucket dinta tace ah’ah zanyi “yayi shiru kafin yace okay wankin suka cigaba dayi babu wanda ke magana a cikinsu kowa da abunda yake ransa sallama akayi suka amsa dr hafsa ce tsaye suna hada ido tayi murmushi tace yau wankin kauna ake tau sannunku malik na murmushi ya amsa gaisuwan datake masa kafin Aydarh tace welcome auntie ina kwana? Dr hafsa tace lafiya alhamdulilah ya gida?aydarh tace lapia lau “kafin ta mike tana wanke hannunta tace ki shigo Auntie dr hafsa tace aaa kawai tunda mun gaisa bara na wuce ai aiki kuke, malik yace no sai fa kin shiga ai mun kusa gama ku shiga kawai nakarasa aydarh ta bude kofan babu yanda dr hafsa zata iya haka tashiga anan parlor suka zauna Aydarh nasake tambayan dr hafsa ya jikinta ina inna? Dr hafsat ace naji sauki sosai Aydarh ina na nan lafiya tama tafi kasuwa maybe yau ma ku ganta saboda naji tana cewa yau bazata kwana bata shigo ba “kwana biyu bata ga audu ba kila ke kika hanasa zuwa Aydarh tabude ido sosai kafin tace ah’ah auntie Wallahi bani bace,banma san yadaina zuwa ba tayi hakuri “dr hafsa tace ahtau idan tazo dai sai kuyi mata bayanin komai kenan Aydarh ta mike tana cewa Allah yakawo ta lapia shiga tayi kitchen ta fito hannunta rike da plate sai pure water biyu akai ta ajiye gaban dr hafsa,dr hafsa nayi mata sannu ta dauki ruwa daya tafasa tana sha,.hibba tayi shiru kafin tace tau yanzu wa zakayi wa maganan kasan yarda zaka samu shi Doctor? Dr ibrahim yayi shiru kafin yace akwai wani yaron gidansa abokina na ne munyi dinki shago daya kafin yasamu aiki a gidansa nikuma nakoma clinic duk karshan wata yake zuwa kano saboda Doctor usaman yasa mar masa aiki a can wani babban private hospital a lagos in sha Allah idan yazo komai yake nan nayi tunani abunyi,hibba ta gyada kai tace nan da kwana sha daya kenan? Dr ibrahim ya gyada kai tace tau Allah yakaimu lafiya asa munada rabo baki daya dr ibrahim yace Ameen wifey “kafin yawani marairaice fuska yace massage please,batace komai ba domin tasan abunda yake nufi hannunsa kawai takama suka tashi, anan bedroom suka zauna kan gado hibba ta cigaba dayin ta mijinta, kafin kuma suyi tafiya can.bilki ta dinga kallon rabiah ko dauke ido babu batace komai ba rabiah tace kiji wani iskanci niga banza sai surutu nake kinyi mun shiru bilki tace aaaaa wai ai jirana nake kigama tunda na lura kaman kin fara samun damuwa a kwalwa,rabiah tayi wani zagi tace ban ma gane ba mikike nufi ne?bilki tace rabiah banda mu bamu san ciwon kanmu ba kawa isai muje mu kama masa mata mu daka tsabar ke baki da kugu ke kanki dakikayi maganar kinji abun ya hau daidai fisabillahi?rabiah tayi shiru tana kallonta,kafin bilki tacigaba dacewa yoo ko shi bai ce manah komai yayah ibrahim bazai ya hallaka mu ba har lahira “balle wannan bawan Allah da idan kika yana kallon matar sa kamar ya afka mata jikin jamaa ke kalan jikinta ma yayi maki kama da jikin da ake duka?tau idan baki da lissafi ni inda shi babu ruwana kawai kibari mu samu kudi sai a koma wajan malam muga abunda Allah zaiyi,rabiah dai tayi shiru amma bakin ciki kamar ya kasheta so tayi suje su chanza mata kama ko kila ko sau dayane ya kalli ita rabiah da idonsa ko sau dayane tunda duk wani magani data karbo baya aiki har kudinta ma yakare yanzu haka so take tahada su koma amma abun ya faskara shiyasa take ganin shine mafita hakan. Bilki tace tau Wallahi babu ruwana a wannan hau din idan kingani a lahira fa kaine akai wooo ni shegiya kina ganin mutane jiki duk Hutu bakisan daga inda suke ba, kice zaki haye musu billahi babu ruwana, rabiah dai tayi shiru tana sauraron bilki har tayi shiru kafin tace tau ni Wallahi wayata zan siyar na koma wajan madawaki asan abun yi, bilki tace tau shknn ai yafi dai kafin ta mike tana daukar mayafinta tace rakani wajan anty hibba mu gaisa nawuce gida babah tace kar najima rabiah ta mike tace mutafi Allah yasa yayan bai nan kinsa sa mayyanta ne Wallahi ko da yaushe ya baibaye da ita Wallahi bilki tayi dariya tace halinsa guda da abokin nasa kenan rabiah tace uhm Allah ya kyauta bilki Tace Ameen , Sallama suka hibba ta amsa musu shiga sukayi tana nan zaune parlor tana kallo tana ganin su tayi murmushi tace sannunku da zuwa bilki tace yauwa anty ina wuni? Hibba tace lafiya lau ya gida? Bilki tawashe baki tace lafiya lau, rabiah ma tagaishe ta amsa kafin ta mike ta shiga kitchen zata kawo musu ruwa bilki ta kalli rabiah tace ashe matar nan da kyaunta har kiba ma tayi nagani rabiah dai ta tabe baki tac eke kullun sai kin gama yabon mutane ina dalili kam tafada tana tsaki ruwa ta kawo musu sai chin chin batayi girki bat ace su zauna ta daura ko indomie bilki tace aaaa sauri take idan tadawo zata ci wata rana hibbah tace Allah yakaimu ruwan suk asha da chin chin sama sama sukayi fira domin hibba sam bata son rawan kan yaran, har bakin kofa ta rako su sukayi sallama ta koma ciki. Kallonsa take har yagama kafin tace to ka kwanta Allah zanyi fa nace maka, malik dai sai kallonta yake kafin yace nace miki ciwon kan kadan ne saboda nashiga rana ne,tayi shiru bace masa komai ba ya mike,yace muje kitchen din suka shiga yayi mata blending, kayan miyan duk da daurewa kawai yake ji yake kaman zaiyi fever tana lura da yarda yake ta ciza lips dinsa ,can tace ka fita zan karasa ya girgiza kai kawai yacigaba da abunda yakeyi, bata sake magana bai ta ta cigaba da yanka vegetables din, kasa daurewa yayi kawai yamike yafice daga kitchen din nan parlor ya dawo ya kwanta kan carpet kansa na wani irin sarawa rufe idonsa kawai yayi yana sauraron yarda yake kyarma,kaman kar ta fita sai kuma ta wanke hannunta ahankali tasa karamin towel ta tsane hannu “ fitowa tayi yana kallonsa ko dauke ido babu karasawa tayi kusa dashi kafin ta kai hannu ta a neck dinsa temperature dinsa yayi high sosai dasauri ta dauke hannunta gabanta nafaduwa kafin tace,jikin yayi zafi sir daman baka da lapia? Girgiza kai yayi bai iya ce mata komai ba mikewa tayi ta nufi bedroom very clean duvet dinta ,ta dauko masa tadawo ta yafa masa, har kai ta rufe masa tama rasa mi zatace masa can tace sannu, tazuba masa ido kawai hankalinta bakaramin tashi yayi ba,tana tunani ko ta kira dr ibrahim can tace sir ka kira Doctor manah hannu yasa cike da dauriya yabude duvet din yace kije ki karasa girkin zan kira sa bata tashi ba kuma bata daina kallonsa ba, can dai ta mike ta koma kitchen din ta cigaba da girkin amma hankalinta na wajansa, sharp sharp takarasa ta fito tasame sa,zuwa yanzu ya daina zufan sai ajiyan zuciya dake saukewa kadan kadan alaman yayi bacci bude duvet din tayi ganin he is sweating yasata bude duvet din baki daya bedroom takoma ta dauko tissue tadawo parlor gently ta matsa kusa dashi ta warwari tissue din tana goge masa goshin dan bude idonsa yayi yakalleta kafin yarufe ahankali , sai da ta goge masa tass kafin ta koma bedroom din wanka tashiga few minutes tadauka a cikin toilet din kafin tafito vaseline kawai tashafa sai perfume tasaka kaya ta dawo nan Parlor ta zauna can karshan carpet daga ka ganta kasan bata da nutsuwa, ganin kaman yana dan motsi yasata matsawa kusa dashi jin alaman ta kusa dashi ,yabude duvet dinta ahankali yace kingama?ta gyada masa kai yace kinci? Ta girgiza masa kai bai ce komai ba yadauko kansa dake ciwo sosai kaman zai fadi ya daura a laps dinta Wallahi malik ji yayi kaman an daura sa a aljannan duniya wani irin ajiyan zuciya yasauke nutsuwa na baibaye jikinsa, ganin yarda yayi din yasata jin gabanta yafadi duk ta rude jin ya kwantar da kansa a cinyan ta yakure kan wajan cikin kaman zai mai kan a cikinta,ahankali yace miyasa baki ci ba?muryanta na rawa kaman zatayi kuka Tace nakoshi bai ce komai ba ya lumshe idonsa shiru cikinsu babu wanda yasake magana kusan 20mins suna ahaka kafin ahankali yamike taga ya nufi toilet yana shiga tamike itama ta wuce bedroom alwalla tayi itama ta kabara sallan la’asar ,bai ji masallaci ba saboda bazai iya ba anan gida yayi sallarnshi nan kana bun sallan ya zauna bai tashi bah, tana fito tagansa zaune bata ce masa komai ba ta dauke ido ta shiga kitchen warmer ta dauko da plates sai spoon da serving spoon ta ajiye nan gefen sa kafin takoma ta dauko ruwa pure water a kan plate shidai bai ce komai bas ai faman kallonta yake ko kiftawa babu,bude warmer tayi serving dinsa abincin kadan badayawa ba ta tura masa gabansa abincin ya kala kafin yasa spoon baya son ya nuna mata bazai iya ci ba, Ahankali yake cin abincin ita dai bata zuba bas ai kallon wuri daya take girgiza kai yayi kafin ya ture abincin yana kallonta murya can kasa yace mata bazaki ci abinci ba ta girgiza kai tace zan ci yace tau sa k ici yafada yana mika mata spoon tareda tura plate din dake gabansa tsakiya,spoon din tasa tafara ci kafin shima yasa atare suka cid uk da bai dayawa amma babu wanda yakara cikin su ruwan ya sha kafin ya mike zai kwashe kayan dasauri ta girgiza masa kai kafin tace kabar shi zan kai kitchen “bai ce komai ba yakoma ya zauna ta kwashe kayan tass tana dawowa yace kije kisaka hijab tace to “ daki takoma ta dako well iron hijab dinta ash tasaka perfume tafito tasame sa, tsaye yana jiranta bakin kofa kallonsa tayi kafin tace ina zamu je? Yace clinic batasake magana ba har ya kulle kofan suka fita anan bakin hanya suka samu keke yafada masa inada zai kai su kafin suka shiga .Dr ibrahim dake kallon malik yace tun yaushe? Malik yayi shiru kafin yace tun jiya nake jin ciwon kai kadan kadan so I didn’t take it that serious nayi tunanin dan nashiga rana ne tau sai yau natashi da fever dr ibrahim yace sannu “malik ya amsa aydarh dai na zaune tana sauraron su dr ibrahim yamike yace tau muje sai nayi maka allura yallabai malik ya mike suka fita ita dai anan office din dr ibrahim ta zauna ta tunanin ko dr hafsa tazo bata sani bad ai “kaman dr hafsat asan abunda take tunani sai gashi ta turo kofan office din tashigo bakinta dauke da sallama aydarh ta amsa mata dr hafsa na ganin Aydarh tawashe baki tana welcoming dinta kafin tace badai ke ce ba lafiya ba?aydarh ta girgiza kai tace ah’ah dr hafsaa tace ko yallabai?aydarh ta gyada mata kai dr hafsa na ajiye fili din hannunta tace asha kam subhanallah? Mike damunsa aydarh tayi kasa da kai tace fever “ dr hafsa tace subhanallah Allah yasawwake fita sukayi ne?aydarh tace erh sunje injection room dr hafsa tace eyyerh Allah yabasa lafiya Aydarh tace Ameen auntie,dr hafsa tace tau mu tafi can office dina kafin su gama koh?aydarh tace “ office din dr hafsa suka wuce, dr hafsa ta kalli aydarh tace Wallahi zazzabin nan ake ta fama Allah dai yasawwake aydarh tace eyyerh Ameen dr hafsa tace ai saboda weather nan ne Wallahi mutane duk ba lafiya mutun daya daya ne basuyi ba Allah Aydarh tace Allah yabasu lapia Dr hafsa tayi shiru kafin tace yauwa Allah yakawoki yau sai anyi kam,aydarh tadago kai kafin tace me fa? Dr hafsat ace yar rainin wayo ai duk sai wani fuzewa kike bakya son p-test din nikam ban yarda ba fa har yau kinsan akwai cikin da bayasa laulayin ke fa kullun naga wani sake fresh kike idan ba ciki ba Aydarh mi ke gareki kiji fa skin dinki kaman kina wanka da milk wannan uban glow datake haka ji fa yarda komai na fuskanki yasake wani extraordinarie kyau hakanan “ ji fa boobs dinki tabarakallah ko ta cikin hijab gwanin burgewa shikam yallabai ya iya kiwo Allah yakara bada zaman lafiya,takarasa maganan tana yar dariya tare da dauko wata karaman container tana mikawa aydarh,ita dai aydarh kanta nakasa bakaramin kunya da mamaki take jib a duk time din da dr hafsa zatayi mata maganan ciki har kaman tayi kuka take ji, dr hafsa tace kinga karba ki shiga nan toilet kiyi fitsari ko kadan ne sai ki kawo mun ‘Aydarh da kaman zata fashe da kuka muryanta cike da shagwaba tace bafa naji auntie Allah kuma ni bani da komai ki ma tambaye sa tafada har kwalla yakawo idonta dr hafsa ta rike baki tace ahhhh lalle Aydarh natambayesa shi sani zaiyi ne ki jimun yarinya “shi ai daya shagwaba ki yazo nan yasame n isai ku shiga toilet din yasa kiyi fitsarin ayi awon dan ban yarda dake ba “Aydarh dai ta dukar da kanta tana jan fingers dinta hawaye na bin cheeks dinta ta turo bakin irin shagwababun rich kids din nan, dr hafsa nagama wayan datake sai ga malik yashigo rike da ledan clinic din ahannunsa ciki maganin da dr ibrahim yabasa ne yadawo office din bai ganta ba yakoma wajan dr ibrahim,dr ibrahim yace yaduba office din dr hafsa yasan suna tare yaga yar gidanta ce,sallama yayi dr hafsa ta amsa tana gaishe sa amsawa yayi tana tambayansa ya jiki, yace Alhamdulilah Doctor ya aikin? Tace alhamdulilah yace Allah ya taimaka tace Ameen kafin tayi murmushi tace ina nan nida yar gidana ni fa yallabai nakasa hakura da zancan cikin nan nakasa yarda Allah ka dubeta fa,malik yadaga kai yana kallon aydarh datayi kasa da kanta yayi murmushi kafin yashafa sajansa yace koh Doctor?dr hafsa ta gyada kai tace sosai ma kau yallabai ga abu nan nabata nace tashiga tayi fitsari taki shiga nace idan kazo ai kasa ta tayi sai na gwada,murmushi yayi kafin yasa hannu yakarbi roban ya mike mata yayi kasa da murya yace just do what she said kinji hajia “yanda yayi mata maganan kaman yanda abbanta ke mata magana idan yana lallashinta, tadago suka hada ido hawaye suka sake zubu mata tana kallonsa ta makale kai a kafada ganin yarda tayi yasan halin yan kayansa bafa yin zatayi bay asa shi sakeyin kasa da murya yakai bakinsa daidai kunnanta yarda ita kawai zataji yace kije kiyi idan tayi test din ayi shikenan zata yarda bazata sake takura ki ba kinji cuddle bug ‘sunan dayakira ta nakarshe yasata saurin dagowa tana dubansa ko dauke ido babu kaman bashi yayi maganan ba yafiddo wayansa a pocket yana dubawa ya basar, dauke idonta tayi ita dai dr hafsa na ta kallonsu bakaramin yi mata kyau sukayi ba a haka,bata sake cewa komai ba ta dauki roban walking very slowly tashiga toilet din dake very clean kaman ba na asibiti ba.kusan 1hour sai ga dr hafsa tashigo da result din a hannu ta mikawa malik tace yallabai yanzu kaga na fita a kokwanto your baby is still free Allah yakawo masu albarka tau,malik yayi murmushi yace Ameen Ameen likita nagode, dr hafsa takalli Aydarh tace tau shagwabban audun inna hankalinki ya kwanta ba ciki amma very soon Allah zai kama ki,aydarh tayi dariya tana rufe fuska shidai malik murmushi kawai yake, can yamike yace yamma nayi dr bara mu wuce gida sai kin taso “dr hafsa tayi murmushi tace tau nagode yau ansha wuni a clinic,malik Yace gaskia “dr hafsa ta tako wata karamin shopping bag cike da candies ta mikawa Aydarh tace tau gasu iloka da gullisuwa mai tsoron ciki aydarh tasa hannun takarba tana dariya tace ah’ah fa Auntie bana tsoro,malik yace kai dr hadda wahala kuma tau angode Allah yasaka,dr hafsa na murmushi tace babu komai yallabai nima nagode, har bakin clinic suka rakasu ita da dr ibrahim suka hau keke suka wuce. Sai da ta chanza masa bedsheet kafin ya kwanta tana kallonsa tace ko zaka koma bedroom din?ya girgiza kai yace aaaa ai kin chanza bedsheet din zan kwanta anan din tace to sai dasafe, malik yace Allah yakaimu sarkin rowa “da sauri ta juyu tace waye mai rowan tafada tana bata fuska, yace wanda zaa bawa candies tahana mijinta, aydarh tawara ido tace lah kasan nafa manta dashi tace bara nakawo ni fa ban taba shan su ba yace kai haba?yafada yana mamaki kaman irin tafadi wani babban abu tace Allah kuwa,can ta fito da ledan ta zauna kusa dashi tabude tana ta kallon tuwan madara da iloka sai gullisuwa da medulla manya masu kyau sosai kwara daya ta mika masa he forgets when last da sha wannan abun murmushi yayi yasa hannu yakarba itama irinshi ta dauka tana sha taji wani mugun dadi dasauri tajuyu tana kallonsa tace kaji dadinsa kau ya gyada kai yana bude Ido sosai yace yayi dadi sosai tace ka iya yinsa ya girgiza kai yace aaaa saidai su aysha tace eyyerh su sun iya?yace Sosai kina son ki koya ne ta gyada kai yace tau mu sha sauran muje,tace ba fa dayawa zan baka ba. Yace tau naga dai tare aka bamu ko? Tace kuma da aka bam uba tare bane dai muna atare zaka ce sir ‘yace tau shknn ki sha candies a daran ma idan ina so zuwa dasafe zakiga ankawo mun su nan “taware ido tace wazai kawo makai ta Auntie zaka wa magana?yace wacece kuma auntie,tace ita dr hafsa din malik ya girgiza kai irin he is very serious din nan yace ni dake da budurwa kuma matan dazan aura har sai nemi abu wajan wani,aydarh tayi shiru dai tana kallonsa tana jiran yakarasa yace ita gurl zanwa magana cikin daran nan gobe tun eight zaki gansu anan,ta tabe baki kafin ta kallesa tace kai haba har sai ankai eight aie nayi tunani da subhi zata kawo maka “ya danne dariyan dake cin sa yace lafiya lau ma zata kawo da asuban ya dauko wayan yayi kaman zai yi dialing ya kirata aydarh ta kafe sa da ido tace yanzu fa sai kace zaka kirata din?yahade rai yace tau dawasa nake da? Aydarh tace Allah bazaka kirata ba,yace saboda mi? yafada yana wara ido tace miyasa ma zata kawo ma abu bayan ummi tace kowa amana ni,yace bangane ba tayi kaman zatayi kuka tace Allah kasani nidai karka kirata ka kira ita auntie hafsa kace ta koyamun kuma ma ai ni wasa nake tare zamu ci wannan din ma I can’t finished it kasani ma,yayi murmushi yana shafa kansa yace tau ai abun hannu wace ta damu dani zanci tayi shiru tana kallonsa dan ba wai ta fahimce abunda yake nufi bane ganin hakan yasa shi chanza magana yace tau zanyi wa dr magana idan nasamu

Chapter 26 of 83