Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta dauki well iron hijab din sabowan wanda bata cika sawa ba tasaka malik ne ya goge hijab din da iron din da ya siyan masu,a parlor ta iske sa yashirya yana jiranta babu wanda yayi ma wani magana dr hafsa ce tace mata tazo tayi mata calaba daman tana so batasan gidan ba kuma batasan yarda zata ce mata bata sani din ba ,sai gashi malik yace tashirya yarakata gidan inna,har yanzu magana bata shiga tsakanin su duk da a yanzu suna zama parlor tare amma babu wanda ke ma wani Magana. Sa kai kawai yayi,yafita ganin hakan yasa ta bi bayansa da harara tana tura masa baki “ shi yasa key ya rufe kofan part din nasu yana gaba tana biye dashi ba,maman Ramlah dake wanki a can ventilation dinta har ta hango su ,dasauri tanuna ma,fadila dake nan tsaye tana sanaar surutu kamar mai cutan dimi, itama kallon tabi su dashi kamar zata hadiye su, cikinsu babu wanda ya juyu balle ya kalli iskan daya kwaso su,tafiya yake kamar wani boss sai sauri yakeyi fita sukayi kofan gida,ya tarar musu keke kallonshi take ko kiftawa babu bata shiga napep din ba, bai lura da bata shiga dan shi har yashiga ya zauna ,can ya lura da ita da kallon datake masa, ahankali yayi kasa da murya yawani kafe da ido yace ko komawa zaki ni natafi? Tawani juyan da kai ta balla masa harara kafin tace ina fa inna tacemun anan anguwan suke?bai ce komai sai yayi shiru ya saako daga napep din side din datake tsaye yaje yakama hannunta tawani zaro ido tana kallonsa bai ko kalleta ba ya turata napep din shima ya zagayo yashiga yace wa mai keke sutafi har suka isa kasuwan babu wanda yayi ma wani magana cikin su suna sauka yafido kudi yabiya mai keken ganin yasauka yasa itama ta sauka tanata kallon inda suke ko kiftawa babu kamar tana tsoron wani abu haka tayi raurau da ido tace masa ina ne nan? Gaba yayi batare da ya kalle ta bayace siyar dake zanyi,duk da abun datake ji bai hanata hararar shi ba yana juyuwa karaf suka hada ido yaganta tsaf bai ce mata komai ba dan wannan bashi bane first time daya taba kamata tana hararan shi ba,duk inda yasa kafanshi sai tasa nata kamar wani zai dauke ta indan ta daina binsa,kanta ta saukar kasa ganin irin kallon da mutane ke binsu dashi, wani babban shago suka shiga babu abunda ake siyarwa sai inner wears Abayas da kuma bubu gown pure cotton, gaisawa sukayi da mai shagon mace ce wata hadadadiyar Hajiya tasha atampha vilisco taci uban gayu,sannu da zuwa tayi masu hadda wurin zama shagon sai kamshin turaran wuta yake da khumra kasancewar duk tana siyarwa, tambayar su abunda suke bukata tayi ya kalli aydarh sannan ya mayar da kallonsa kan matar yace inner wears zata zaba daga nan bai sake magana ba ya saukan da kanshi kasa yana latsa wayanshi, mata tace Hajiya mi da mi zan dauko maki?sai da ta dago kai taga bai kallonta kafin ta yi ma matar nuni da hannu wasu classic brassiere ta nuna mata masu tsada saboda hakan ma yasa ta fidda su gefe guda foreign ne matar tayi murmushi tace tau size nawa aydarh tafada mata cikin wannan voice din nata, matar ta bi aydarh da kallo a ranta tana mamakin size din da ta gaya mata anya bai mata yawa ba,batace komai ba ta dauko mata wani hadaddan black lace form bra sai baby pink dark green da kuma red aydarh tabi su da kallo imagination din nata ne na gida, tasan price dinsu bai kai natan ba,amma duk da haka sunada kyau pants tasa aka dauko mata this time matar kasa shiru tayi sai datace diyata anya size din daidai kika fade sa?aydarh tayi kasa da kai sannan ta gyada mata kai malik najin duk abunda ke faruwa amma ya ki dago kansa balle ya kalle su ita dai aydarh takagara agama su tafi bata son ya dago kansa yagani,shima pants din kwara hudu ta dauko mata kowani irin bra din, matar ta tambaye ta hadda undies aydarh ta girgiza kai kafin tace aa sai sannan malik ya dago kai yace shima a saka kwara hudun,bai jira amsar matar ba dan yasan ma aydarh bazata ce komai ba ya fita kofar shagon, wani bubu gown ya dauko light purple mai haske Sosai duk jikinshi sai flowers din jiki black har zip din gaban gown din purple ne da black mai shining ba karamin kyau tayi irin ta yan gayu na sosai da sosai yashigo dashi rike ahannu babu wanda ya kalla cikin su ya ajiye ya koma inda yake zaune ya zauna matar tayi packaging rigan da mayafinta babba ne ba laifi tana yabon zaben dayayi kafin tace tau ranka ya dade an mance da inner caps suma muna siyarwa na lura matar taka bata son kana wahalar kashe kudi, malik yayi murmushi kadan yace tau ba damuwa hajiya a dauko guda hudu shima aydarh najin su dai batace komai ba matar ta dauko wani karamin basket cike da plain inner caps yards din masu kyau masu tsada, ta ajiye gaban malik tace zabi”sai daya kalli aydarh kafin ya maida duban shi a basket din light purple yafara daukan mata sai ya dauki black da pink sai wata kamar ash kamar grey, duk kayan ta hada masu cikin ledan shagon ta lissafa masa kudin ya fido 35k daidai yace ta bata turaran na 5k matar ta washe baki tace tau shknn turaran kaya dana jiki ta dauko ma aydarh masu dadin kamshi Sosai tayi packaging din a tasu leda kafin ta hada su waje daya cikin ledan kayan godiya matar tayi masu sukayi bankwana har zasu fita kafin tace yawa ranka ya dade dan Allah zan iya samun number madam ko naka idan kuna son gyaran jiki ko lalle duk ina yi har kayan sawa na maza ina siyarwa, kafin ta rufe baki aydarh tace “no”shidai malik baki bude yake bin aydarh da ta tsare shi da ido da kallo tawani hada fuska kamar irin yaji tsoron ta kar yayi din nan, sai ya juya ya kalli matar yace sorry Hajiya zamu dawo wata rana ai in sha Allah ,matar tayi murmushi tace babu komai Allah yatsare,suna fita tace wai bansan mi ma yahanani tambayar su daga wani kasar suke ba wallahi sai kuma tace umm ina fuskar hakan cikinsu kowa kamar sarki duk sun tsare gida babu sakin fuska amma akwai dan banzan kyau wai Allah, ji yarinya karama amma ji body structure shiyasa aka ce natural daban yake da artificial mu dake bankar supplement ina zamu hadda kanmu da jikin yarinyar nan. Cikin 50k din da Allh musa yabashi jiya kyautan Allah saura 15k flask yasiya karami mai madaidaicin kudi wanda zai dinga ajiye mata ruwan zafi saboda yanayin aikin shi yanzu kusan sai yamma take wanka idan tayi dasafe mamadin tayi da rana sai yamma ga garin damuna gudun shi kuma sanyi ya kamata, man kitso yasiyan mata da pink oil sai comb da tsinke tunuwa daga nan gidan inna zasu wuce dr hafsa din tayi mata calaba kamar yarda inna ke gaya masa dan shi bai sani ba tunda ba wani shiga harkan juna suke ba,plate shoe yasiyan mata masu kyau sai yasiyan ma inna daya itama da sabulu da klin leda daban ya fidda kayan inna ita kuma yabar mata nata wuri daya babu abunda ya siyar ma kanshi,napep ya tarar masu suka isa har kofar gidan inna yabiya mai keken kudi kafin ya mika mata ledar kayan da yasiyawa inna da man kitso comb da tsinke din kallon shi tana turo baki tace ina kaima shiga zakayi ? Hannushi daya yasa cikin Aljihu yawani daure fuska yace eh shiga zanyi amma ke zaki rike wannan din,bata sake cewa komai ba tayi gaba ta bar masa kayansa a nan tashige gidan inna dasauri,bin ta ya dinga yi da kallo bata magana batada hayaniya amma akwai taurin kai da rashin kunya bakar magana kam sai wacce ta manta kawai ke bata gaya mashi girgiza kai yayi ya dauki kayan yabita baya inna nagani shigowar su ta mike tsaye tace kai kai kai kune tafe oyoyo asiya sannu da zuwa aydarh tayi murmushi ta dukar da kai kafin ta russuna tace ina wuni? Inna ta washe baki tace lahiya lau asiya ya gidan da audu baki daya?aydarh tace Alhamdulilah,malik ya bata fuska yace ni sai na koma ai,inna tayi kasa da murya tace ash eke dashi kuka zo aydarh dai kanta nakasa batace ma inna komai ba,inna ta kalli malik tace indai ba aikin sintiri kasamu ba yaci ace kashigo tunda kuka zo,inna takama hannun aydarh suka shiga cikin daki aka bar malik nan tsaye,inna ta kalli aydarh tace wallahi nake gaya maki tau bayan ma ba kaunar Allah yake ba tun farko basai ya gayaman sunanki haka ba fisabillahi,aydarh dake murmushi ta gyada wa inna kai,inna tacigaba dacewa “tau bai fada bas ai dai naji ya kira wani suna da larabci nidai ba fahimtan sunan nake bas ai fa ranar matar dake zaune nan gidan,wa take da suna ma hafsa ita ke fada mun sunan naki nidai ba ma yarda nake da maganar ta ba,sai dana tambayi shi audun da kanshi yake ce man ai sunanki haka aydarh dai sai murmushi take,malik yace ma dr hafsa suna ciki ni tafiya zanyi yau inna bata ni take ba daman kuma ba zama zanyi ba dr hafsa tayi murmushi tace tau kashiga sai kuyi bankwana da innar “da sallama yashiga dakin inna ta amsa masa kafin yace ga wannan babu yawa inna,inna tabi ledar da kallo kafin tace Allahu akbar audu nagode sosai Allah yasaka maka da alkhairi Allah yakawo zuri’a ya dayaba Amin dan nabiyyu rahamati malik yashafa kai yace Ameen inna ni bara na wuce idan anjima sai nadawo in sha Allah,inna tace tau Allahu yasha, ledar man kitso da pink oil din ya bar mata sai comb da tsinke tunda yasan dasu zaayi amfani babba leda kayan nata da turare ya dauka yafita dash isai dayayi enough cefane wanda zai ishe su “kafin yatsaya shago yasiya macaroni da pasta rabin cartons sai shinkafa tiya biyu da kanannun indomie carton daya sai maggi leda leda da spices sauran 15k din tass ya kashe . Sai da ya gyara koi na tsaf yashirya duk abunda yasiyo a muhallinsu inner wears din ma cikin wardrobe yasaka mata perfumes din ma bai fida su a ledan su ba yabar su, kitchen yawuce ya daura jallof din pasta da kifin da yasiyo sai daya gama kafin ya daura mata ruwan wanka sannan ya zuba pasta a plate wanda favorite dinsace ya zuba sauran a warmer, yaci ya shiga yayi wanka ya gaji bacci yake son yi dan akwai nepa sai daya juye mata ruwan zafin a sabon flask din dasuka siyo ya kai mata bedroom kafin ya dan kwanta. Inna tashirya ta dauki mayafinta da jikka,tasaka sabin takalmin da malik yakawo mata tace tau ni natafi asiya nasan kafin na dawo kun tafi gida in sha Allah gobe na shigo, aydarh tace to inna dr hafsa takalli inna tace tau hala idan kikaje wajan suna can zaki zauna?inna tace ina ruwanki nifa bana so shishigi da neman wajan zama dana tashi fita na kinga nayi magana dake baiwar Allah?dr hafsa tace Allah yabaki hakuri sai kin dawo na daura maki girkin ne kafin ki dawo?inna bata tanka ta ba tasa kai ta fice,dr hafsa tayi murmushi ta kalli aydarh tace haka nake fama da ita amma kullum cikin cewa take hakurin zama nake da ita,aydarh tayi murmushi tace she is really funny,dr hafsa tace ai ina tunanin mijinki ne kawai ke iya zama da ita shima kuma dan dai Allah yasa tanaji dashi ne aydarh batace komai ba dr hafsat ace mu fara ko? Aydarh ta gyada kai tacire hijab da dankwallin kanta tana warware uban tulin gashinta daga cikin ribbon dr hafsa ta dinga bin gashin da kallo tace masha Allah shiyasa bakya son kitso, aydarh tayi raurau da ido damuwa kan fuskanta tace akwai zafi hannunki ko?bakaramin dariya aydarh taba dr hafsa ba yarda tayi maganar kamar wata yarinya she always behaves childish dr hafsa tace no ai calaba bai da zafi ko kadan yallabai ma dan bai iya bane da ko shi ai sai yayi maki calaba aydarh bata fahimci abunda dr hafsa tace ba shiyasa tayi shiru, cikin few minutes aka fara tsagan calaba aydarh dai hadda kanannun kwallan ta a ido tasa bayan hannu tashare su,saboda dariyar da dr hafsa ke mata,dr tace nikam dai aydarh naso naga ranar haihuwanki ai wannan sai Doctors din Nigeria sun taro a kanki,kice hakanan ma yallaban ya matsu a samu cikin ashe matar tasa ragowa ce, aydarh batasan time din datace shi ne yace haka? Dr hafsa da har yanzu da sauran dariya a fuskarta tace eh cewa yayi nayi maki p-test ashe ashe ba jaruma bace matar tasa,aydarh batace komai a ranta take tunanin time din daba ta da lapia kenan hadda abunda yasa akayi mata kenan?babu mai bata amsa yasata yin shiru tana cigaba sauraron labarin da dr hafsa ke bata,dr hafsa tace wallahi aydarh wasu matan auran sai ahankali aydarh tayi murmushi dr hafsa ta cigaba dacewa wata friend din ace fa suka rabu da mijin kuma fa laifinta ne shiyasa yanzu duk ta zauna labarin sa takeyi,aydarh dai na sauraron dr hafsa tana fahimta labarin amma batasan ma’anar labarin ba dr hafsa tace kiji fa a zamanin nan wane namiji ne zai dauke ma shara wanke wanke girki ke hadda fa wankin bayi da kayan sawa,kiji fa ai wallahi indai ba shanye shi tayi ba babu namijin da zai maka irin wannan a yanzu,aydarh dai tayi shiru aranta take juya maganar dr hafsa din yanzu ita malik dakeyi mata duk wannan itama shanyesa tayi tau miye shanye war?sai kuma wata zuciya tace mata aa ai auranku bakalar na kowa bane,dr hafsa tace tau the worst part of it ma abunda yasa har maganar divorcé yashigo ciki fita take bata tambaye sa ba shikuma yaji bazai iya ba,aydarh tayi shiru kafin tace auntie hafsa minene shanyewan? Dr hafsa tayi murmushi tace eh gaskia ke ba lalle bane ki sani idan aka ce mace. Aydarh dai tayi shiru sai sauraron bayanin da dr hafsa ke mata take, batace komai ba har sai da dr hafsa tayi shiru kafin tace,idan matar ke yin komai fa?shine mijin ya shanye ta dr hafsa tayi wani irin dariya tace wallahi ke ma aydarh tau a normality na alada da addinin musulunci shi ya daurawa mace wannan nauyin na girki shara wanke wanke kula da yara a gida shi kuma mijin ya tafi office Ko wajan sanaar shi yafita ya nemo maku abunda zaku ci da duk wani abubuwa na yau da kullun,aydarh ta sauke wani irin ajiyan zuciya,tau ita miye matsayin auran su da malik shima ai aure tunda tasan aure dole sai da sadaki kuma aie aure aure ne,sai kuma wata zuciya tace mata aaa aurenki dashi ba kalar na kowa bane, bakya sonsa ko kadan sai ma tsoronsa da haushin sa dakike ji shima bakya sonki wannan ai ba aure bane,ta tura baki ahankali can ciki tace Mugu kawai,tunanin ne fal aranta so take dai tasan miye matsayin auran su da malik miye kuma sharudan auran da dr hafsa tace duk macan da bata cika su ba makoman ta wutan jahanama,bakaramin tsoron wuta take ba tun tana yarinya tana iya tuna time din rufaidarh ke gaya mata zafin wutar duniya ba komai bane kan lahira 1%din wutar lahira ne,wani irin yankewa gabanta yayi ya fadi batasan ta yarda zata fara tambayar dr hafsa ba shiyasa tayi shiru,wani irin kyau calaban keyi ba fatar kan fari tass yarda take fitan da tsagan kamar sai tasaka ruler tayi ta daidaita ita kanta dr hafsa duk zaman ta boarding bata taba sanin ta iya calaba ba kamar yau datayi wa aydarh masha Allah, yi ake yi ake amma gashin kamar ana kara masa yawa,duk da manyace akeyi, tun dasukayi magana da dr hafsa take ta juya zancan a ranta so take ta tambayi dr hafsa amma batasan ta yarda zata tambaye ta ba “can wani dabara ya fado mata a rai,tayi kasa da murya kafin tace auntie sai kuma tayi shiru ganin haka yasa dr hafsa cewa ina jinki aydarh,ajiyar zuciya ta sauki kafin cikin nutsuwa tace daman auntie a can akwai wata friend dina ita da mijinta basa son juna kwata kwata sun tsani juna ko magana ma basa yi kuma duk wani aikin gida shi keyi komai fa har ruwan zafi shi ke dafa mata tayi wanka,idan kinga sunyi magana sai idan batada lapia kawai fa, dr hafsa tace subhanallah amma gaskia wannan bata son ciwon kanta ba wait ba ma wannan miyasa sukayi aure while basa son juna?aydarh ta ware hannu tace nima ban sani ba kawai dai a daura ma su aure babu biki babu komai kawai anan take aka biya sadakin akayi komai a gabansu, dr hafsa tace duk da haka bata da wayo dai ai aure aure ne duk da bata son shi ai aljannarta nakasan kafar sa,kuma aure dole mata tayiwa miji biyayya ko da bata sonsa kinga shi ko da baya sonta alama ya nuna cewa yana tausanta kuma ya rike amanar Allah ita kuma ranar gobe kiyama sai Allah yakamata da laifi,aydarh naji duk abunda dr hafsa ke fada tayi shiru tana tunani tau ita ya zatayi? Har ga Allah bata son ma abunda zai dinga haddata da malik sam,dr hafsa tace tau kuma shi bayan haka baya siya mata komai?aydarh ta girgiza kai tace he is trying his best ya mata abubuwa ,dr hafsa tace kingani ba that’s means shi yasan hakkin aure kenan yasan miye aure ,ita kuma da bata da hankali saboda bata son sa kuma bata neman rahamar ubangiji ai ni atunani duk wani rashin kauna yakare daga ranar da aka daura ma aure da mutun,ba kamar idan yana kyautata maka kamar yarda wannan mijin kawar taki keyi mata shikenan rashin so ya kare ko da bata sonsa tayi hakuri ta dinga sauke hakkin aure yarda ta hakura har tayi biyayyan iyaye haka ya dace ta hakura tayi biyayyan Allah tasauke hakkin mijinta a kanta ta sauke hakkin gidan auranta,ta sauke ajiyar tace tau auntie ita fa batasan komai na aure ba tace,dr hafsa ta saki calaban datakeyi yanzu ta zagayo ta kalli fuskar aydarh tace daman akwai macan da batasan miye zaman aure ba aydarh? Aydarh da gabanta keta bugawa tace nima dai bansani ba amma haka tace batasan komai na aure ba dr hafsa ta dinga salati tace tau bata da yan uwa ke bata da mahaifiya ma forst? Aydarh ta girgiza kai tace bata da yan uwa tanada mahaifiya,dr hafsa tace tau miyasa ba a fada mata ba?aydarh tace itace bata tsayawa ta saurara kullun bata zama inda kowa yake idan ta tafi school shikenan wani time enma har sai tadawo nan kasar sannan zatayi magana dawani,dr hafsa tace gaskia kam ta cuce rayuwarta bata kyauta ma kanta ba kuma duk mai daure mata kugu tayi wannan abun shima ya cuce ta,ta tubar ma Allah ta fara shirin koyon rayuwa saboda batasan komai ba,aydarh tasauke ajiyar zuciya har zatayi magana sai kuma tayi shiru,can dr hafsa tace yawa mu’amalar aure fa? Aydarh bata gane tambayar da dr hafsa tayi mata bah akan yasata cewa na’am? Tace kina nufin wani abu bai taba shiga tsakanin su ba like sex or something like that?aydarh tawani zaro ido ta daga kanta tana kallon dr hafsa sai kuma tayi maza ta saukar da kanta kafin ta girgiza kai tana wasa da hannunta tace aaa dr hafsa ta rafka salati tace yau mun shiga uku ke yanzu a matsayinki na kawarta kuma ke kinada aure kinsan komai na aure zaki barta tana wannan rashin hankalin da wannan ai hauka ne , aydarh tace ranar ne ma tana shafa yazo yaganta da towel shine fa ta dinga kuka,dr hafsa da bakinciki ya cikata tace tau Allah ya kyauta amma tanaji tana gan isai ya auro wata,ko gwal ce ita ai sai haka wallahi kuma ranar lahira sai Allah yakamata red handed tunda ita shashasha ce wawiya har ga Allah dr hafsa bata kawo aydarh bace tayi tunanin kawar ta tace dagasken,Aydarh dai bata kara magana ba jikinta duk yayi sanyi tau ita yazatayi kenan babu abunda yafi firgita ta irin wutar dazaa sata kamar yarda dr hafsa din tace, gabanta sai faduwa yake tayi lamo dr hafsa ta cigaba da mata calaban babu wanda yasake magana cikin su aydarh hankalin ta baki daya ya koma kan maganar dasukayi da dr hafsa sai saka take da warwara.Da sallama yashigo gidan dr hafsa ta amsa masa,bai san inna bata nan ba kawai yasa kai yashiga dakin dr hafsa tace ahh yallabai sannu da zuwa ina wuni?malik yadanyi murmushi kadan yace lapia hafsa sannu da aiki dr hafsa tayi yar dariya tace yawwa ai dole kamun sannu,haka kuke da gashi tabarakallah,shidai malik murmushi yayi ya dinga bin gashin kanta da kallo calaban tayi mugun kyau masha Allah kamar karya dauke idonshi daga kallon calabar mutun ne shi mai mugun son gashi yana masifan son yaga anyi kitso kuma a da har parking gashinsa yakeyi ko kuma su aysha suyi mashi kitso sai daga bayan nan ne ma yake aski ya ke dan rage ta kadan, can yayi kasa da murya yazuba wa bayan ta ido murya babu wasa yace ko baki ji na shigo ba dabazaki gaishe nib a ko kicemun sannu da zuwa,Kamar daga sama taji maganar sa tayi niyyar daya shigo ta rufe kanta amma bata son dr hafsa ta fahimce komai yasata barin kan aka cigaba da kitson, sai da murda masa baki duk da bata ganin sa kafin ahankali tace in anima baka gaishe niba da kazo ?bai san ranin datayi masa ba har yakai haka ba,yayi tunani zata gaishe sa din ko dan dr hafsa din,bai ce komai ba yayi shiru,sai dr hafsa ce tayi dariya tace tau ai kinsan rijalu su kullun sun fi son ayi masu,aydarh dai tayi shiru,malik din ma bai kara cewa komai ba kuma bai fita ba,har suk agama calaban tass Allahumma bareek bakaramin kyau calaban yayi ba akayi parking dinshi can kasa tasa hannu tayi mashi wani irin style kafin ta mike ta dauki gashin da ya zuba kadan zata zubar a dustbin sai yanzu dr hafsa taga yarda dinki ya zauna a jikinta sai yanzu ta sake ganin wacece aydarh sai tunanin ta yabata ko dai sake p-test din zasuyi, maybe akwai cikin ko boyewa yayi tunda alama yanuna kamar hips ya shiga da boobs dinta yarda shape din jikinta yafita kallo daya malik yayi mata ya dauke ido yarda take tafiya kamar da gayya yasa shi dauke kai , shigowa dakin tayi ta zauna kusa da dr hafsa idan ta ajiye hijab dinta kallabinta take kokarin daurawa dr hafsa ta kalli malik tace yallabai nace ko sake mata p-test din zaayi naga kamar akwai shi maybe ko shigewa yayi ba? Malik ya shafa kasa yace anya kau ina ganin no need,dr hafsa ta gyara zaman tayi kasa da murya tace aa yallabai kamar fa akwai cikin ko dai shigewa yayi cikin hips da boobs ko kuma ranar ansamu matsala ne aydarh dai kalli malik suka hada ido sai kumayi tayi kasa da kai,malik yace ma dr hafsa tau shknn zamu zo din dahaka ya mike yayi ma dr hafsa godiya yace ki same ni a kofan gida, dr hafsa tayi mata sallama aydarh tace thank you auntie “dr hafsa tace don’t mention aydarh sai anjiman ku,ku gaida gida,a kofan gida ta same sa tsaye yana jiranta yana ganin ta fito yajuya yatafi ta bisa baya daidai kofan shiga gidan suka hadu da Ramlah tsaye ta tare kofan gidan tana ganinshi tawani washe baki cike da bariki tace welcome sir malik yace thanks a takaice yayi hanya zai wuce ta wani

Chapter 13 of 83