Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
hakanan tau yanzu tunda ga ka sai muje ka gani idan yayi maka, malik was speechless he is out of words tun haduwar shi da dr ibrahim yake masa kirki kala kala…….. Dr ibrahim yace zuwa gobe dasafe kafin a sallameta sai muje tare ka ga gidan daga nan din zuwa can 200 ake zuwa a keke, malik yace tau shknn Doctor Allah yakaimu nagode “ dr ibrahim yace babu komai yanzu lokacin tashi na yayi daman bama kwana a nan din mu uku ne kawai ke aiki a nan din sai shi mai clinic din da ai chemist ne sai kuma mayarda wurin clinic ,malik ya danyi murmushi zuwa yanzu har yasaba da surutun Doctor ibrahim din. Sai da yafara shiga dakin da aydarh ke kwance ya sake gwada bp ta kafin suyi sallama da malik nurse saratu da 8 tayi take tafi sai dayar ita Doctor ce ita kawai ke kwana itama ba kullun saidai in har akwai patient din da aka kwantar basu ma cika kwantar da mutane ba a clinic din, Akwai wadatacan haske a clinic din, da sallama mai gadin clinic din yashigo hannu shi rike da tabarma dakuma prayer mat sai bargo da pillow mikawa malik yayi dake zaune a reception ,” da mamaki malik ke bin mai gadi da kallo shima mai gadin kallon malik yake kamar yasamu t.v bai taba ganin mai irin Kamar shi a zahiri ba saidai a indian flim “ ganin yarda yake kallonshi ko kiftawa babu yasaki baki yasa malik mikewa tsaye, yace lafiya dai? Sai sannan mai gadin ya washe baki yace aaaa lafiya lau yallabai dakta ibrahim ne yace a kawo maku wannan hannu malik yasa yakarba yana jinjina kirki irin na Doctor ibrahim, mai gadin yace ina waje ranka ya dade idan akwai abunda ake bukata ayi man magana “ko rufe baki bai yi su kaji takon tafiya a bayansu mai gadin ne ya waiwaya yace ahh barka da zuwa dakta yanzu nake zancan ki a raina nace ko dai dakta ibrahim bai gaya maki da marar sa lafiya bam asu kwana “dan murmushi wacce yakira Doctor din tayi tace aaa ya fadamun ina hanya bana jin dadin jikina ne sam ,cikin jimami yace Asha kam Allah yabada lafiya,Ameen kawai tace tayi gaba ko kallonta malik baiyi ba ya kwashe kayan da Doctor ibrahim ya aiko masa yashige dakin. Ahankali ya tura dakin ta takure kanta waje daya bacci take amma a wahale da alama ma sanyin damuna da akeyi garin na damun ta domin ta kudundene kanta cikin hijabi kallonta yayi for few seconds yadauke kanshi ya ajiye kayan, bargon yasha jiki amma duk da haka fess yake a wanke sai kamshin klin yake “ warware shi yayi tass sannan ahankali ya matsa kusa da gadon karamin tsaki yasaki kafin yasa hannu gently ya kwashe hijabin, dasauri ya dauke kanshi ganin yarda zip din abayar jikinta ya dan bude har kana iya ganin whitest boobs dinta wanda skin din ke kamar madara har wani shining yake , tsaki yasaki a fili kafin ya yafa mata bargon “komawa yayi ya zauna kan rubber chair dake dakin yayi alkawarin mantawa da komai yayi alkawarin karbar kaddararshi shiyasa ko kadan baya son sake tuna komai. Without making any sound ya buda warm din yana kallon abinci bazai iya tuna when last yaci abinci ba irin mutanan ne shi wanda sam basa wasa da cikin su amma yau gashi baya son ko kallon abinci, white rice ce da stew sai kifi cikin jug din kuma zobo ne still akwai ice a ciki batayi melting ba kadan yaci abincin ,yana tuna yarda take cin Abinci dazo kamar magani batayi three spoon ba ta aje, girgiza kanshi a ranshi yana tunanin ita din amanace a wajanshi ita din ticket ce ta yafiyar da mahaifiyarshi zatayi masa kan laifin da bai aikata ba “cike da kwarin gwiwa yayi ma kanshi alkawarin fuskantar sabuwar rayuwar shi da kuma gogaya tsakanin shi da kaddararshi. Tabarmar ya shimfida yasaka pillow ya kwanta sam baya jin bacci amma wata irin gajiya ke tattare dashi, Almost thirty minutes yana ahaka idonshi rufe amma ba bacci yake ba,knocking kofar akayi ahankali yamike yace who’s that? Daga waje Doctor hafsa tace Doctor ce zan duba ko drip din yakare, “bude kofar yayi tareda bata hanya tashigo zata kai saar shi koma tafishi, ahankali tace ina wuni ya mai jikin? Lapia, da sauki kawai yace ya koma kan kujerar ya zauna ,duba drip din tayi taga still da saura, sannan ta dan yaye bargon kadan tashafa goshin aydarh taji temperature din jikinta normal normal kafin ta mayarda da bargon ta rufe ta, tunda Doctor hafsa tayi knocking ta farka taki buda idonta tana sauraron duk abunda ke faruwa, Doctor hafsa ta kalli malik tayi murmushi ahankali ta saukar da muryar kamar mai tsoron yin magana tace is she your sister or your wife sir? Malik yayi shiru har ta fidda ran zai amsata can yace “both” Dr hafsa tace Allah sarki Allah yabata lapia ,anan anguwar kuke ne? Malik ya girgiza kai yace aaaa , dr hafsa tace alright idan drip din yakare please let me know am in the office, Alright yace “daga haka Doctor hafsa ta juya ta fita. Har wajan 12 na dare malik ya nemi bacci yarasa itama aydarh sam ba bacci take kasancewar kadan kadan drip din ke sauka shiyasa har yanzu bai kare ba, har yanzu idonta rufe yake and bata fito da fuskar ta waje ba,ganin ya kasa bacci hakan yasa shi shiga toilet ya daura alwalla ya fito ya shimfida prayer mat din ya kabara sallarh, sai wajan one kafin drip din yakare lokacin malik ya sallame sallarh, sai sannan ya tuna da zancan kiran dr hafsa idan drip din yakare mikewa yayi tsaye ya matsa kusa da gadon yaga drip din yakare,without making any sound ya buda kofar yafita zuwa office din dr hafsa sai da yayi knocking sau uku sannan cikin muryar bacci dr hafsa tace am coming, bai sake cewa komai ba ya juya ya koma dakin, Dr hafsa ta kalli aydarh tace ko zaki shiga toilet din? ahankali ta gyada mata kai sai kuma tayi kasa da murya kamar zatayi kuka tace I need to change kuma ina son warm water,ita dai Doctor hafsa kallonta take ko kiftawa babu ganin yarda take magana cike da shegen shagwaba da tsananin izza da kuma aji gauraye a muryan ta kar ma aje batun kyau wannan zata ce tunda Allah ya hallice ta she never meet a beautiful persons irin aydarh da malik duk da bata da lapia amma asalin gayu ya bayyana a jikinta asalin hutu yanuna ajikinta babu abun da take kallo a sai diamond rings din dake hannun aydarh masu masifar kyau da daukar ido, murmushi dr hafsa tayi tace alright am coming, bayan fitar ta shima malik ya tashi ya kasake kabara sallarh ita dai aydarh har yanzu bata yarda ta sake hada ido dashi ba . Dr hafsa tadawo dauke da flask a hannunta ta wuce toilet ta hada ruwan toilet din is very neat daman bawani amfani ake dashi ba, fitowa tayi tace muje na hada, bata ce mata komai ba ta tashi ahankali tana wannan tafiyan nata mai daukar hankali,dr hafsa dai sai kallonta take yah rabbi duk shape din nata ne ko na ciko ne this girl fine finish Allahumma bareek, fitsari tayi dr hafsa ta mika mata pad da pant duk malik na kallon su bayan ya sallame sallarh har su kagama sannan dr hafsa ta kalli malik tace yallabai sai dasafe,sannan ta juya ta kalli aydarh itama tayi mata murmushi tace sai dasafe madam Allah yakara sauki aydarh bata ce komai ba, sai malik ne yace angode kwarai Allah yasaka , babu komai dr hafsa tace sannan ta fita ta ja musu kofa, Malik ya kalleta bai san sunan da ya dace ya kirata ba, Ahankali yace how was your body? Shiru tayi kanta na kasa tace fine, babu wanda yasake magana cikin su. Hajajju ta kalli oum tace to pah, wanene abba? Oum ta gyara tsayuwar ta tace habib, hajajju tace shi habibun yace zaku tafi can kasar din? Oum tace ehh ba jimawa zamuyi ba , hajajju tayi kasa da murya tace tau nidai ina nan bazan koma wannan kuturun gidan na yaya ba gaskia,oum tayi murmushi tace tau shknn nima na fi son ki zauna nan din tunda rufaidarh na nan itama hajajju dai tayi shiru bata ce komai ba oum tace tau idan gari ya waye ma karasa maganar tau Allah yakaimu hajajju tace,oum ta fita. Wajan karfe 10 flight dinsu ya tashi zuwa kasar spain hajajju dai hada kukanta,tace Allah sarki rayuwa famelin Habibu duk sun yaye sun barmu daga mu sai halin ko awani hali yaran can ke ciki Allah kawai yasani andai cuce su an cuce rayuwar su ita yarinya an banka mata aure da wannan basamudan mutumin, shikuma an lika mashi yarinya ga ba isassar lafiya Allah dai yasaka masu, rufaidarh dai sai kallon hajajju take inda sabo har tasaba da halin hajajjun. Hajajju tashiga kitchen ta iske daya daga cikin maids din gidan tsaye tana goge kitchen cabinet. Hajajju tayi mitsi mitsi da ido tace hup dai an gaya maku matsayina a gidan tau idan baku sani ba daga yau kusani daga yanzu har su habibu su dawo nice zan dinga bada umarnin duk abunda zaayi a gidan nan , ita dai mai aikin na tsaye da dan karamin towel a hannunta tana kallon hajajju, ko kiftawa babu “can hajajju tayi kasa da murya tace wai ita waccan dayar balarabiyar ita bata da mai so ne komai? Allah na tuba tunda nasanta ban taba jin labarin wani na neman auranta ba gaskia, mai aikin tace wacce balarabiyar ? Hajajju ta juya ta juyo Kamar mai gudun wani ya ganta tace waccan abun manah watake yauwa rufaidarh, “mai aikin ta girgiza kai tace aaa mama tanada masu so sosai amma kila ita ce dai bata bada fuska”hajajju tayi shiru can kuma tace kai kuji rubabba yoo Allah na tuba bata ga ita yar uwar ba ma da auranta kuma tafita komai ma,amma sai ita tau nidai ba ruwana bara nakama bakina nayi shiru kingan ni nan babu abunda yashafe ni da rayuwar mutune, ni ko maganar mutane bana son ana mun, shiyasa kullun nake zamana lapia,kema ga shawara ki kama bakinki ba ruwanki da maganar bil’adama “ ta sake kasa da murya tace kinga habibu duk cikin mu shine kawai ba rubabbe ba da kudinshi tau sai ni din nan dakika gani tsaye a gabanki famelin mu duk sun yaye sun rasu daga ni sai wata mata da muke uwa daya uba daya muka rage sai kuma ibrahin da ya’yanshi “ ta gyara tsayuwar ta tace wai fa shine dan tsoron Allah da kaunar ma’aiki da yanzu ba ‘ayi za a hadani da jafa’I wai wani abu na koma kuturun gidan matar da zama “ita a wa?ita ame? Da zasu hadani da zama waje daya da ita babu iskan kirki gidan ba kai babu kugu haka take rayuwa ba da ba jikah daman mu famelin mu munada tsari bama sakin jiki mu dinga zazaga yara kamar tsuma shiyasa kikaga bamu da yawa ma “ ita dai mai aikin har ta gaji da sauraron hajajju she see no reason da zata dinga mata wannan zubar, bata ce mata komai ba har tayi shiru “sannan tace tau Allah ya kyauta mama”hajajju tace haram haram badani ba aikata wannan baqin kantameman zunubin miye wani mama, sau biyu ina zuwa makkah fa wanda a famelin mu bayan ni sai habibu da wannan matar tasa dakuma diyarsu wanda a halin yanzu bamu san inda suke ba, still dai maid din she is eager hajajju tafita takarasa aikinta tun tana bata dariya har labarin yafara fita kanta nan fa take ce mata ita bata maganar mutane amma tun dazu take bata labarin abunda bai shafe ta ba “ can wani dabara ya fado mata tace am hajiya mi kike bukata na kumallo “hajajju ta washe baki tace daman tun jiya rabo na da sa ma cikina wani abu tashin hankali ya hanani sakat billahi “maid din tace Allah sarki, hajajju tace shayi zaki hadaman ki suya dankali da kwai takwas sai sabon biredi da farfesu yanzu ina jiranki ,maid din tace tau shknn hajiya dana gama sai na kawo maki a nan dining hajajju bata ce komai ba ta juya tafita. Doctor hafsa ta kalli malik tace ya jikin nata tasamu bacci kuwa? Sai da malik ya sace kallon aydarh dake zaune ta rabe waje guda kamar marainiya kallo daya zakayi mata kaga alamar tana cikin damuwa sosai she is helpless and she’s alone,can ya kalli dr hafsa yace jiki da sauki alhamdulilah amma ina ga gaskia batayi bacci ba, duk maganar da suke aydarh na jinsu ko kallo basu ishe ta ba,ahankali dr hafsa ta taka kusa da ita tace good morning ma’am how was your body? Kamar bazata magana ba kamar batagane da yaran da dr hafsa ke tambayan ta ba , bata motsa ba kuma bata dago kanta ba jikinta na cure waje daya daidai numfashinta ahankali take shakar sa take kuma fidda shi, dr hafsa dake kallonta ko kiftawa babu bata gaji ba tasake maimaita tambayar da take mata, kusan 2mins lokacin dakin yayi shiru malik kau bakin ciki kamar ya kashe shi ji yake kamar ya rufeta da duka ganin irin yarda ta maida dr hafsa kamar wata shashasha tana tambayar ta tayi mata shiru, dr hafsa tayi murmushi ta girgiza kai tace Allah yakara sauki bara na hada mata ruwa tayi wanka malik yace tau nagode,daga haka dr hafsa ta fita zata dago flask din ruwan zafi data sa aka kawo mata daga gida “kallo daya yayi mata ya dauke idonshi sannan ya mike tsaye baya son raini baya kuma wulakanta mutane duk halin san e rashin son magana amma idan har yazo wajan fagen kulawa yana nuna juriya da hakuri akan kowace tambaya dakuma amsarta ita amana ce wajan shi da kuma alaqar dake tsakanin su na yan uwa bayajin zai bar tarbiyyarta da rayuwarta su cigaba da wanzuwa ahaka ba, yana cikin jerin mutanan masu saurin karantar halin dan adam tsaf ya karanci girman kai izza izgili dakuma raini a tattare da ita, yarda yayi alkawarin karbar wannan kaddarar ahaka yayi alkawarin rike amanar da hallita mafi daraja da ki’ma a idonshi mafi koluluwar soyayyya a idonshi ta basa, bayajin sonta ko diko a ranshi kwata kwata halinta baya cikin jerin matan dayake son zama dasu matsayin matar aure tanada amfani da kyau wajan raina duk wani bil’adam shikuma bazai dauki hakan bah, wata zuciya tace masa tau wannan ai ba aure bane kamar kowane! “Cikin tsananin tsara gida ya kalle ta yace,she is not your mate she’s older than you so don’t take for granted, yasa kai yafice,kallonshi take ko janye ido babu batasan miyasa ba take wani jin shakku mai kama da tsoro idan yayi mata magana ba har faduwa gabanta keyi idan yayi mata magana wasu irin kwalla taji masu masifan zafi na bin kuncinta ta she can’t hold it but cry, kuka tafa rerawa kamar karamar yarinya har cikin ranta take jin babu wanda yayi saura a rayuwarta wani irin zafin oum da abba take ji har cikin ranta ko tuno bata son yi (subhanallah) Dr hafsa ce tashigo tasame aydarh na kuka kallonta tayi ahankali tayi dropping flask din kan med-drower ,kallonta takeyi batasan abunda zata ce mata saboda bata son kan mi take kukan bah almost five minutes suna haka ,sannan dr hafsa tace you are sick komai yafaru ki bar isai kinji sauki sannan ki ji da duk wani damun wanki for now dai keep anything aside recovered first,daga haka dr hafsa ta hada mata ruwa a toilet,sai da tayi wanka tass Doctor ta taimaka mata tashirya babu kayan da zata chanza illa rigar da ta kwana dashi hakan yasa ta jin kamar zatayi kuka dr hafsa na kula da ita bata ce mata komai ba tana son ta wanke mata pant din datacire ganin yayi stain amma gani take kamar batada wannan hurumin domin ta fuskanci daga matar har mijin bahagwaye ne gashi babu yarda zaayi ita aydarh ta wanke kasancewar da abu a hannunta, fitowa tayi daga toilet din tasame ta kwance ta rufe dukkan jikinta ruf, a reception ta iske malik da Doctor ibrahim cikin Fara’a suka gaisa sannan ya tambayeta ya mai jiki dasauki alhamdulilah Doctor ya aikin? Doctor ibrahim yace mata Alhamdulilah sannan yace tunda nazo sai ki tafi maybe yau ma ayi discharging dinsu tunda jikinta dasauki right?dr hafsa tayi murmushi tace ehh Alhamdulilah daman jira nake kazo sai na wuce nima,sai ta kalli malik tace ehen yallabai akwai abu a toilet nasaka a bucket akwai detergent sai ka wanke mata, then a nemo mata abunda zatace, tunda tafara magana malik bai ce komai ma sai da tagama sannan yace “thanks”.Bayan tafiyar dr hafsa suka cigaba da maganar dasuke shida dr ibrahim kan gidan dazasu zauna yana fada masa ai makwabta mane su da dr hafsa itama a anguwar take, Yau ma kamar jiya rabi’ah ce rike da food flask tasaha well ironed hijab dinta sai baza kamshin turaranta mai saukin kudi take,sai satar kallon malik tace bata taba ganin mutun mai kyaun shi ba,ko a indiyan flim din ma mamakin yarda yake da wannan mugun kwarjinin take bata ma iya kallonshi face face ko da ta gaishe sa ya amsa bata kallesa ba,taji yayan nata yace matar sa ce ba lafiya ita kam tana son ganin matar tasa taga ya take da har wannan mai zubin larabawan zai aureta,hakan yasa da dr ibrahim ke shirin karbar food flask din hannunta ya mikawa malik tayi karaf tace aaa yayah barsa kawai bara na shiga najiye sai na duba ta da jiki ma, dr ibrahim yace tau shknn, bude kofar dakin tayi ahankali tashiga “har numfashin ta sai dayayi barazanar daukewa, a kallo daya datayi ma aydarh Yah rabbil alameen, tau daga wace kasar suke tasamu kanta da wannan tambayar a zuciyarta,wani abu taji mai kama da bakin ciki hassada ya darso a ranta ganin aydarh da tayi ahankali ta ajiye food flask duk sai taji ta muzanta ashe karyar body structure suke ashe karyar kyau suke ashe karyar skin care suke ashe yar ubansu karyar body scent suke, warabul ka’aba she never imagined this type of beauty in the whole world? A gadon asibiti kenan fa tasamu zancan a zuciyarta bazata manta ba sun taba ganin hoton rigar jikin aydarh a wayar siyama kawarta itama a instagram ta gani wai three hundred k a lokacin mamaki suke wasu kalan kudi mutun zaiyi dazai siye wannan rigan sai yau taganshi jikin aydarh, ahankali tace mata ya jikin ki? Kallonta tayi lokaci daya taji wani irin bata ji haka ba kan dr hafsa da nurse saratu , sam ji tayi zuciyar ta tayi mata wani kala ganin rabi’ah ta bin ta da kallo kamar mayya, duk sun suna kallonta amma na rabi’ah yafi bata mata rai, rabi’ah tace daman yayah ne yace akawo maki breakfast, Akawo maki breakfast, aydarh ko kallon rabi’ah batayi ba balle tasa ran amsata “ rabi’ah dai natsaye ta zuba ma aydarh idon ta namata wani irin kallo, can tasake cewa magana nake maki malama ko baki jina ne ? cikin dan daga murya rabi’ah tayi maganar, Wani irin duba aydarh tayi ma rabi’ah cikin few seconds ta dauke kanta batace mata komai ba sai rufe ma fuskanta datayi da veil din kanta “ta bar rabi’ah nan tsaye kamar status “wani irin haushi ya kama rabi’ah watau yar iska ta mayarda da ita kenan marar lissafi da zata dinga mata magana tayi shiru “ juyawa rabi’ah tayi ta rufe kofar da mugun karfi har sai da aydarh ta mike tana kallon kofar wani irin harara tabi kofar dashi kamar idonta zai fado taja siririn tsaki, duk wani kala take ji amfani da riga daya dakuma brassiere daya datakeyi “she wish all this was dream ba reality bane, duk wani kala take jinta kamar wata daban ba ita ba she is totally lose take ji, ita salmarh da Doctor ashraff sukayi wa sharri irin haka “and without any investigation kuma suka saka aka koreta ba koran kawai ba hadda daura mata aure da waccan mutumin da bata ma sani ba, she didn’t have anyway to go “bata dakowa a duniyar batasan yanzu idan ta gudu daga wurin shi ina zata kuma ba she promise herself bazata sake komawa gida ba , she has no other option but to stay!” Zuciyar ta,tasake maimaita kalamanta na karshe, hawaye sharr suka zubo daga idonta.Tare suka shigo da Doctor ibrahim bayan sun dawo daga ganin gidan, ahankali ya turo dakin da sallama Doctor ibrahim na mara masa baya “ kuka take fuskar ta tayi jawur eyelashes dinta sun jiqe sun tattare waje daya hakan yaba idon damar fito da asalin kyawu da girman da Allah yabasa “ Doctor ibrahim yakalleta cikin few seconds ya dauke idonshi sannan ya juya ya kalli malik dake jingine a kofar dakin shima kallonta yakeyi ko dauke ido babu cikin wannan yanayin fuskan nashi ba yabo ba fallasa, duk da suna shigowa ta saukar da kanta kasa hakan bai hanata jin kamar ana kallonta ba, bayan hannu tasa tashare hawayenta tass sai sauke ajiyar zuciya take, Doctor ibrahim bai ce komai bah aka shima malik din duk shiru sukayi Doctor ibrahim a zuciyarsa yake tambaya tau mi yaakayi mata na kuka?baya son zagewa a lamarin su shiyasa yaja bakinsa yayi shiru, sake dubu bugun zuciyarta yayi yaga komai daidai, file dinta ya bude tare da dubawa ya rubuta masu takarda sallama. Malik ya sai ke kallon Doctor ibrahim yace taya Doctor zaka ce basai nayi biya ba naga nan din private clinic ne, kuma kace mun bana ka bane “dr ibrahim yayi murmushi yace babu komai wllh nasan da haka idan wata yayi sai a fidda a salary na, Malik dai hakan sam bai mashi dadi ba domin ya lura shima dr ibrahim kamar bawani hali garesu ba “idan kau suna da hali bazai yiyuwa ba ace da kwallin shi na degree kuma ma medicine ya karanta ace yatsaya yana aiki anan din dake kamar chemist,” Malik yace nagode Allah yasaka maka da alkhairi “ dr ibrahim yace babu komai yanzu kaje ku shirya sai na tare mai keke ya kaiku can gidan, in sha Allah da magrib sai nashigo akwai sakon da zan kawo maku,malik yace sako kuma dr sako nami?dr ibrahim ya girgiza kai yace kawai dai sai nashigo, fita malik yayi yashiga dakin “zaune take tacire veil din kanta fever dake jikinta ta sauka sai ciwon kai kadan kadan zafi takeji hakan yasata cire veil din, kanta datayi parking a keya daga gaba an rabashi biyu yayi wani musulmin kyau sai shining yake kamar wace tafito daga shagon saloon yanzu , jin alamar shigowar shi yasata saurin mayarda veil din a kanta tana cusa kanta tsakanin kafafunta ita ala dole bata son ko ganinsa, toilet ya wuce direct dan bai manta maganar Doctor hafsa ba to miye abun da tace tajika a bayi, taba kofar toilet din dayayi yasa aydarh saurin dago kanta domin ta san pant dinta na ciki,wani irin yankewa gabanta yayi yafadi to ya idan yaga pant din ta fa kuma jikinshi hadda stain,ko a gida rufaidarh ce kawai ke wanke mata pant shima sai idan ciwon nata yaci karfin ta duk ranar da oum ta taba mata pant kau dasunan wankewa kunya take wuni ji domin bata son kowa yaga private abunta abunda tsani wani gaya jikinta ko daoum ce kau har ta da rufaidarh ko bata da lapia saidai a taimaka mata akama ta taje toilet din ko ta shirya shi ma saidai adinga mika mata abubuwa, har yasa kai zai shiga,yace wannan soft muryan nata na baby’s ahankali kamar bata so na waje yajita tace “stop” tsayawa yayi bakin kofar bai juyu ba kuma bai ce komai

Chapter 8 of 83