Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
saka a bulan su, gajiya yayi da tunanin dakuma binta da kallo dayake faman yi kuma yana son magana da ita,kafin ahankali ya mike yaje saman kanta yatsaya sai kuma ya duka ya buga pillow datake kai,jin ana buga pillow yasata bude idonta dake cike da bacci ahankali har takarasa bude idonta a kanshi,sai kuma ta juya kafin ta mike tana kallonsa,yace ki daina barin wutan dakin nan kunne batace komai ba tayi maza ta dauki hulan kanta ta mayar, ya dauki plate din fruits din ya daura mata a laps, ta dinga bin kankanan da apple din da kallo can kuma sai ta dauke ido, bata fara shan fruit din ba shima kuma bai tashi ba,kuma baiyi magana ba ya dai dinga kallon waje daya kafin ya mike tsaye ya zuba duk hannunsa biyun a pocket din jeans dinsa yace ki shirya gobe zamu fita dasafe,taji abunda yace haka yasata dago kanta ta zuba masa ido kafin tace, ina kuma zamuje?kamar ba zaiyi magana ba har yakusa fita daga dakin kafin yace, zuwa zanyi na siyar dake,daga haka yafita hararar bayansa tayi ,kafin ta dauki fork din ahankali tafara daukan apple din ta kai baki , tass ta shanye kafin ta dauki plate din walking slowly ta tura kofan kitchen din ta shiga plate din ta dauraye tana mamakin inda yaje don bata gansa a parlor ba, yana shigowa yasa key ya rufe kofan kafin yayi switching off din globs din parlor,tana sa kafa ta fito daga kitchen din ta ga ankashe wutan parlor tasan shine dan har yanzu akwai wuta tana ganin hasken globes din compound din duk da hasken baya shigo har cikin part din nasu, bata son duhu hakan yasata dinga bin bango, lafiyan sa yake hankali kwance dan bai kawo ma ransa tana parlor ba, wani irin karo suka ci dashi har sai da kafanta yayi bending tafadi kasa,the incident cames suddenly shiyasa he can hold it kawai yabita suka fadi itace akasa shine a sama,jinsa kanta yasa hankalinshi yayi masifan tashi bata ma ji zafin faduwan batasa hannu iyakan karfinta ta dinga ture sa tana hawaye yayi mata nauyi sosai har kirjin su daya hadu waje daya nasa numfashin ta yin sama sama,malik kau da bai masan yanayin dayake ciki ba ko gizau bai yi ba jin shi plate a jikinta bakaramin birkita sa ba yayi,yama kasa yin komai he already lose his weight, hankalinsa bai dawo jikinsa ba sai dayaji tasaki wani kara sannan cikin hanzari yayi saurin tashi akanta,ahankali ta mike ko juyuwa batayi ta shige bedroom din kan katifan ta kwanta ta rufe idonta da karfi still hawaye ke ta zuba a idonta,tun daya kwanta yakasa bacci,sai dawo masa abunda yafaru keyi akai.Kallonta yake ko kiftawa babu ta yafa mayafin gown din, still tak’I yarda su hada ido sai kallon waje daban take,yayi kasa da murya babu wasa ko kadan a fuskan sa yace ai da baki yafa mayafin ba ma kin tafi ahaka “ sai yanzu tajuyu ta kallesa batace komai ba ta dauke kanta,ta nufi hanyar kofa,har takusa fita kafin yabude wardrobe ya dauko mata hijab dinta daya goge mata, bai ce mata komai ba ya warware abayan ya mika mata bata karbi abayan ba kuma bata kallesa ba ganin tana bata masa lokaci yasa shi zare mayafin kafin yasaka mata hijab din duk abunan dayake ko motsawa batayi ba har yagama yafice yabarta nan tsaye ajiyan zuciya kawai ta sauke kafin ta bisa ba,kofan part din ya kulle ya saka mukullin a aljihun wanda yard dinsa yayi matukar karban jikinsa zaka rantse da Allah yaron wani babban ambassador ne ko kuma wani minister kudi duk da yard ne mai karamin kudi ne amma bakaramin haduwa malik din yayi ba cikin yard din, baby pink din hijab din daya saka mata ya hau sosai da touches din flower gown din nata Sosai yahau da gown din, daidai kofan gidansu suka hadu da dr hafsa itama ta fito daga gida tana neman keke zata tafi clinic,murmushi tasake tana kallonsa tace Good morning my couples malik yayi murmushi yace morning dr yah inna?dr hafsa tace inna lafiya lau,aydarh ta kalli dr hafsa kafin tayi wani cute simle tace Good morning auntie,dr hafsa tace morning mrs malik mun tashi lafiya yajikin yallabai? Aydarh tace Alhamdulilah ,dr hafsa tace yau fitan safe za’ayi ba? Aydarh ta kalli malik ta gefen ido hankalin sa na kan keken dake tahowa kafin tace Erh dr hafsa tace wannan kauna haka aydarh dai tayi murmushi ta saukan da kanta kasa dr hafsa tace ni bara na kara gaba maybe nasamu keken a can tunda kila ba hanya damu mukayi ba right?Aydarh taware hannu kafin tace bansan inda zamuje ba,ko ki tambayesa,dr hafsa ta girgiza kai tace aaa fa sai kundawo kawai sallama tayi da malik kafin tawuce, keke suka shiga yayi masa kwatancan inda zasuje,shiga sukayi mai keken ya sauke su har kofan islamiyan da babu wani nisa sosai daga anguwar su, aydarh dai sai bin makaranta take da kallo bayan sun sauka malik yakalleta yace muje ciki, office din Headmaster suka shiga already sunyi waya tun a hanya kafin su iso suna shiga cikin mutunci suka gaisa da malik da headmaster, kafin aydarh ta gaishe sa ya amsa ta batare da ya kalle ta ba, headmaster dake sauraron bayani da malik ke masa yayi shiru kafin yace tau shknn yallabai in sha Allah babu abunda zai gagara nafahimce ka kuma mostly sauran daliban ma duk hakan ne shiyasa ma aka gina islamiyan,malik yace Tau Alhamdulilah,ita dai aydarh tayi shiru sai sauraron su take,nan akayi komai malik yabiya bill din komai kafin ya karbi kalan yard din uniform din kafin sukayi sallama cikin mutunci yafada masa ranar da zata fara zuwa makaranta.saidai sukaje kasuwa anan suka yanke yard din uniform din kafin yatambaye inda ake dinkawa mai siyan da yard din yace anan din ma suna dinkawa hijab aka dinka mata har kasa sai doguwan riga marar hannu,light blue ne uniform din hakan yasa shi siyan mata light blue din inner cap anan shagon har zasu tafi sai ya juyu yace amm a ina ake siyar da nikkab? Mai shagon yahada su da yaron yace yaraka su wajan dake siyarwa, kala biyu ya siyan mata kafin su hau keke suka tafi gida, suna isa gida time din har ankusa azahar,sharp sharp yadaura macaroni fari sai stew already suna da cefane cikin 40mins yagama komai ya juye a warmer kafin yashiga toilet yadauro alwalla yawuce masallaci, shigowar sa kenan daga masallaci duk yau bai ganta ba sai yanzu ta gefenta yarabe zai shiga cikin gidan tayi saurin tara gabansa, hakanan kawai yaji yau yana son mata warning , chewing gum take chewing irin yarda cikakun mararsa kunyar nan ke ci wani irin baci ransa yayi bai dai ce mata komai yana jiran yaji abunda zatace din, inna ranka dade?ya karfin jiki? Kar ka damu fa kan abunda yarinyar nan tamun jiya ni bai dameni ba sam saboda ni bama da riko ko kadan,malik dake tsaye nan fuskar sa babu alaman wasa cikin isa yace “hey”quiet “ sai da gabanta yafadi yarda sound din muryansa yafita, yace this should be the first and last time dazaki dinga mun irin haukan nan, don’t repeat this mistake again karki sake shiga gabana idan ina tafiya not only me,even my wife she is not your mate, wucewa yayi yabar ta nan tsaye baki bude, yana shiga ya tarar da ita kofar bedroom da alama yanzu tafito, sallama yayi ta amsa kafin kuma ta juya takoma bedroom ,kitchen yashiga ya zuba mata abinci a plate yakawo mata sharp sharp yagama cin nasa abinci daman uzuri ya dauka yace zai je wani waje bazai dawo da wuri ba, yau ma bashi ya gyara mata bedroom din ba ita ta gyara abun ta tsaf kafin kuma ta shiga kitchen ta wanke few plates din da yabata bai tsaya wankewa ba.. Malik yace tau fa bai kai nan ba tun farko ai laifinka ne mi zai sa kace musu zakayi event daga baya kuma ka fasa?dr ibrahim yashafa kansa yace aie ni fa banma san lokacin da nace haka ba , malik yace au haba? Giyan soyayya ya dibeka kenan kayi musu karya,dr ibrahim yayi dariya kafin yace wallahi fa,malik ya gyara zamansa yace tau gashi ai yanzu ta sake ka,kaga dagaske hidiman zaayi dr ibrahim yace wallahi fa,kafin yace ni yanzu ba wannan ba number yarinyar nan zan baka ka kirata please kadan bata hakuri saboda yanzu haka fa fushi take dani,Malik yace aaa ni na aike ka kayi musu karya? Dr ibrahim yayi kasa da murya yace kai fa matsala gareka,ka taimaka please kasan fa yarda auran zumunci yake malik yace nikam taya zan san yarda yake,dr ibrahim yadinga bin malik da kallo baki sake yace ina kaima auran zumuncin ne,malik dai yayi shiru bai ce masa komai ba sai can yace yanzu naji zan kirata nabata hakuri nace mata yau har masu ciwon ido ma allura ka basu, su biyun babu wanda baiyi dariya ba,dr ibrahim yace nidai najib a komai idan zaka bata hakurin, Aydarh tabude kofan bedroom din tafito ahankali har tazo tsakiyan parlor taga dr ibrahim,ahankali tace ina wuni,dr ibrahim yace lafiya lau alhamdulilah madam ya gida ya mai jiki? Aydarh tace Alhamdulilah dr ibrahim yace madallah, malik dake kallonta ko dauke ido babu ya mike tsaye ya kalleta yace nazo ne? Batace komai ba ta girgiza kai murya can kasa tace “inna” yafahimce abunda take nufi mamaki take basa yarda take abu kamar wata yar yarinya nufinta fa gidan inna zataje, malik bai ce mata komai ba ya juya ya kalli, dr ibrahim yace dr bara na rakata gidan inna ina dawowa yanzu dr ibrahim yayi murmushi yace tau shknn, tunda nan da gidan innan ma bazaka barta taje ita daya ba, malik bai ce masa komai ba yabi bayanta har ta riga tayi gaba,kowa na gidan nan compound din zaune in banda mazajen su, yarda suke kallon su kamar zasu cinye su yasa aydarh saukan da kanta kasa ranta a mugun bace bata son kallo ko dan shi kau malik har yasaba ma ko a jikinsa kallonsu bai dame su ba, yau ma tana nan tsaye bakin kofan tunda suka fito take kallonsu kamar mayya, malik ko sau daya bai daga kai ya kalleta ba daman ko mutuwa zatayi. Dr hafsa dake kallon aydarh ko dauke ido babu tace tau ke kuma sai kika ce mi?aydarh ta girgiza kai tace say no word I just kept shut lokacin,dr hafsa tayi murmushi tace kamar da baki da kishi aydarh ai idan nice wallahi sai na wanke wannan karamar fuskan nata da mari,aydarh ta kalle dr hafsa bata ce komai ba tayi shiru, kafin dr hafsa ta cigaba da cewa kinsan mi kin birgeni ma da baki yi mata maganan ba tunda dai ke bat saran yin ta bace,waennan dasuka saba da hau a titi kingani babu ruwanki da ita, nan ma dai aydarh tayi shiru, kafin tace he is said wai gurl dinsa ce, nikuma nace there’s none of my business koma wace even if she is his wife I don’t bother care kawai tafita harkana ta daina kallona bana son raini, dr hafsa ta dinga bin aydarh da kallo baki bude, tace anya kau Aydarh kanki daya kuwa? You didn’t care fa kai mace na shiga sabgar mijinki kice baki damu ba,mijinki fa yanmata fa inalilahi, aydarh dai ta dinga kallon dr hafsa ganin ta dauki lamarin babba tau ina ruwanta dan yana magana dawasu,dr hafsa takalli aydarh tace kinsan mi?aydarh ta girgiza kai kafin ahankali tace ah’ah dr hafsa ta cigaba dacewa na lura har yanzu kina fama da yarinta kuma dai aydarh kin kusan 22ko kin mayi kinga ba auran wuri akayi maki ba right? Aydarh ta gyada mata kai,dr hafsa tace tau miyasa kike abu kamar baki kishin yallabai ne? Wait aydarh ko dai kawai auran hadi ne irin wanda akeyi na zumunci? Aydarh tayi shiru gabanta na faduwa don batayi tunanin dr hafsa zata mata wannan tambayar ba,dr hafsa tayi saurin cewa sorry for my questions aydarh kawai dai yarda ke kiyi din ne ke bani mamaki assuming that you love malik baza ki dinga behaving this childish way ba kan shi, feel free aydarh kaman yarda nagaya maki abaya ki daukeni matsayin babbar yayar Am 34 aydarh kinga akwai kusan tazaran 12 years tsakanin mu kinga sai dai nazo daya da malik , Aydarh tayi shiru tana sauraron dr hafsa,bata gaji ba tasake cewa aydarh sai kin maido fa da hankalin ki jikinki, you are not longer a child da idan kina ganinki gaban su mama kina tunanin har yanzu ke yar yarinya yace noo yanzu komai ya chanza yanzu ke matar aure ce kinada aure nan dawasu months ma idan Allah ya amince sai ki ganki da baby, kinga kau dolene ki chanza wannan halin naki na I didn’t care, namiji bai da tabbas haka sharrin yan matan yanzu ba kamar yarda suke ganin yallaban dayawan su sunyi tunanin balaraben qatar ne yarda suke crushing kansa sai yabaki mamaki dan ma mijin naki neb a wasa kallon sa kawai sai yasa matsoraci fitsari,sai yanzu aydarh tayi murmushi ta sunkuyar da kanta kasa saboda dariya dr hafsa din tabata wai fitsari, dr hafsa tace Aydarh kinga duk yarda kike nan kamar ke kikayi kanki komai naki sai an kusa zagaye Nigeria kafin asamu mace haka ko tau wallahi rawar kan yaran nan na iya dauke maki hankalinta miji, yanzu jira daya rako ki komawa gida yayi Ko wajan aiki yatafi? Aydarh ta girgiza kai tace ah’ah yanada bako a gida, dr ibraheem ne yazo,dr hafsa tace ohh Allah sarki, dr hafsa tace kinga Ko lokacin daya kwanta asibiti naso nayi maki fada amma kawai naga kamar baki son maganar yasa na rabu dake, Aydarh malik yana bala’In kaunarki duk baya nunawa,ko ba a fada ba nasan malik ba wai yanada karfi bane yanzu saboda aikin gini fa kawai yakeyi amma aydarh dube ki dubi kayan dakike sakawa ko wata matan minister haka har yanzu ina mamakin kaddaran daya dawo daku rayuwa cikin mu duk iya lokacin da zaku dauka kuna boye reality ku,alama dakuma kamanin sun nuna ku yaran wasu ne a kasar nan, aydarh dai tayi shiru abba da kullun ke cikin ranta tunanin sa yasake fadu mata arai tana yawan tuna sa, dr hafsa tace tunda bakya son maganar bara na kawo maki abinci nasan inna ma tana hanyar dawowa yanzu, aydarh ta girgiza kai tace ah’ah fa kawai dai bansan abunda zan fada ba ne, dr hafsa tayi murmushi tace na fahimta Allah yakara muku zaman lafiya, kafin tace ehen aydarh natuna miyasa baku dawo aka sake p-test din ba aydarh ta dago kai ta kalli dr hafsa kafin tace babu komai, dr hafsa tace yakamata dai ku dawo saboda wannan kyaun dakike karawa kullun baki da giba amma ko’ina na jikinki na acike gaskia ciki ne,aydarh tayi murmushi tace ai na rame kuma nayi duhu a da bahaka nake ba ,dr hafsa taware ido tace kai haba,aydarh tayi murmushi bata ce komai ba nan dr hafsa ta cigaba da jan ta da fira yawancin firan abunda yashafi zaman aure ne bakaramin catching abubuwa take ba a firan nasu, sosai dr hafsa ta saki baki suna fira da aydarh duk a tunanin aydarh tasan abunda take nufi,wanda a wurin aydarh daga erh ko ah’ah sai idan abun dariya ne tayi murmushi,sosai takaro a firan nasu yamma tayi lis har yanzu inna shiru bata dawo ba,dr hafsa tace yau kinji ni sakat wannan tsohuwar bata nan ba,aydarh tace hajiya inna sarkin labari,bata gaji ma ita,dr hafsa tace wai ahaka fa cewa take bata son mutun yacika surutu ita bata son cutan dimi,aydarh tayi dariya dr hafsa tace yau dai kin wunar manah, Aydarh tace ai daman ina so nazo kawai Allah ne baiyi ba,dr hafsa tace ko kuma yallabai ke baya son kina fita aydarh tace ah’ah fa babu ruwansa shi dr aah idan ba haka ba ai da kin zo, aydarh tayi shiru, dr hafsat ace bara kiga natashi ko wainan flour sai nayi manah tunda dai kin ki cin tuwo aydarh ta girgiza kai tace ah’ah nagode bana jin yunwa ne, dr hafsa tace no sai fa nayi sharp sharp dr hafsa ta hada komai kafin ta kunna murhun gawaye tafara suyan wainan flour anan tsakar gidan suka zauna tsaf Aydarh ke kallon yarda dr hafsa ke komai na wainan flour sai data mayarda hankalinta kaf ta na kallonta suna yi suna fira kadan kadan duk da dr hafsa ce mai firan, sallama suka ji abakin kofa dr hafsa ta amsa masa yashigo gaisawa sukayi da dr hafsa kafin cikin zolaya dr hafsa tace ai na sha kwana tazo yi manah yayi murmushi yashafa kansa yace sai ki bamu dakinki nida ita din,dr hafsa tayi dariya ta nuna masa kusa da aydarh inda take zaune tace ka zauna sai kayi joining dinmu wainan flour muke, malik ya gyara tsayuwar kafin yace ke keyi dai ita wannan da bata son aiki haka fa take kullun,Aydarh ta kallesa batace komai ba ta dauke kai yayi kasa da murya ya zauna kusa da ita,yace ki tashi mutafi kallonsa tayi kafin tace ina nan kasame ni? Malik yace ehhh shiyasa nace ki tashi mu tafi din duk maganar nan dasuke dr hafsa bata jinsu, Mike wa yayi gently ya kamata hannunta ta kwace tana tura masa baki , baice mata komai ba ya kalli dr hafsa yace tau dr zamu tafi sai Anjima ki gaishe mun da inna idan ta dawo please, dr hafsa tace aaa yallabai kabari na karasa idan yaso sai na zuba muku a warmer please saboda ita fa nayi malik yayi shiru kafin can kuma yace ko da kin bata baci fa zatayi ba nasani, Aydarh tace zan ci “kallonta yayi baki bude dr hafsa dai tayi murmushi kafin tashiga kitchen ta dauko warmer ta juye masu duk wanda ta suya kafin ta samu wani clean rubber ta zuba masu yajin a ciki tamikawa Malik har zai karba aydarh tayi saurin sa hannu ta karbi kulan ya dinga bin ta da kallo kafin tace karki basa abuna ai bana sa bane, dr hafsa tayi murmushi tace yau yallabai ka ja fada fa yashafa kansa yace ba fa ni nasa yarinya ta harareta ba kuma tabani sako and nagaya wa yarinya fisabillahi hafsa miye laifina yafada yana murmushi dr hafsa ta girgiza kai itama dariyan take ta kalli aydarh tace tau kinji har sakonki yabata ma, Aydarh tayi shiru kafin tace tau ta daina yi masa magana bana so,malik yayi shiru yana ta kallonta har cikin ranshi yaji maganar datayin, ahankali yayi kasa da murya yarda ita kawai zata iya jinsa yace tunda ke bakya kulani kuma kar kowa ya kulani right? Batace masa komai ba sai kallonsa datayi da sauri, ta kuma kawan da kanta gefe, dr hafsa dai ta cigaba da suyan wainan flour ta, Aydarh takalli dr hafsa kafin tace thank you auntie sai anjima, dr hafsat ace don’t mention aydarh ki gaida gida, gaba tayi yana binta baya har suka isa cikin gidan babu wanda yayi ma wani magana cikin su key yasa ya bude kofan part din nasu ta riga sa shiga ya tsaya nan ya kulle kofan kafin shima ya shiga,da warmer wainan flour ta tashige bedroom din ta ajiye kafin ta shiga toilet ta zuba ruwan zafin flask dinta a bucket dan wanka take son yi ga magrib ta kusa, towel ta daura kafin ta cire kayan ta, sharp sharp tayi wankan tafito Vaseline kawai tashafa sama sama sai perfume still bata cire towel din jikinta ba inners kawai tasaka tabar towel din daure a jikinta, black inner cap dinta kawai tasaka ta zauna kan katifan ta bude warmer kamshin wainan flour yayi mata ta dinga bin wainan flour da kallo kafin ta ware kwara 4 a gefe hakan taji bazata iya hanasa ba kwara 4 din tace tayi dadi sosai Amma ka koshi rufe warmer din tayi tashiga toilet din ta wanke hannunta,ahankali ya tura kofan dakin yashigo da sallama can kasan throat dinsa daidai itama ta fito daga toilet din tana gyara daurin towel dinta, bata lura dashi ba har takara so cikin dakin, sai sannan tagansa ta firgita ta juya babu abunda zatasa ko ta rufe jikinta sai kawai tashige jikin bango tana saukar da kanta kaf size din bra din dasuka siyo yayi mata kadan kusan half din boobs dinta a waje yake yarda tayi daurin towel din har kana iya hangowa,yi yayi kamar bai san abunda take nufi ba kamar bai san da shigan datake ba kallonta yayi kafin ya janye ido kuma ya lumshe su,kamar zatayi kuka kuma a tsoraci tace to ka dauke warmer ka fita manah ni banda kaya fa,yarda tayi maganar yasa shi hade fuska yadinga tahowa towards her har yakawo inda take jikin bangon, kallonsa take a rude ganin yana nufuta har yayi mata rumfa da fadaddan kirjinsa ta rufe idonta kam jikin ko’ ina rawa yake cikin wannan muryan tasa ba wasa yace bazan dauka na fita ba sai kin gaya mun wanda kika raina,kike harara kike gaya ma bakar maganar,girgiza kai tace wallahi Allah ban raina ka ba ni bana hara..ra.nka tafada tana ina ina malik yace idan kinga na fita sai kingaya mun wanda daya mike magana sai kin mayar masa da baka, gabanta faduwa kawai yake hankalinta yayi masifan tashi tace ni dai bakai bane ka yiakuri dan Allah wallahi ba da kai nake ba ka yiakuri malik yace idan kinga na hakura fa sai idan kin gaya mun dawanda kike yafada yana bin da kallo wani irin extraordinarily kyau take dashi yarda baby pink din towel din yabi fatan jikinta haka ma bra din baby pink ce ga towel din dake nan daure ba sosai ba,so yake ta kiyayyesa ta dinga jin tsoron sa ko abubuwan sun zo masa dasauki hakan yasa shi gently ya kai hannunsa kan towel din wllh jin hannunsa a towel din har wani fizga numfashin ta yayi suddenly taji kasancewar idonta a rufe yake shikansa sai dayaji wani kala amma ya daure dai har yana iya jin yarda gabanta ke wani irin faduwa bakaramin tsorata tayi ba, hannunta dake wani irin rawa kamar yarda jikinta keyi tasa tana kokarin cire hannunsa daga wajan tunda ga brain dinsa har tafin kafar sa yaji wani irin abu ya tsarga masa jin hannunsu ya hadu wuri guda wani irin ajiyar zuciya yasauke ahankali yafara ja da baya sai kuma yayi Saurin fita yabar dakin ,takai kusan 3mins bayan fitan sa bata motsa daga jikin bangon dake ba yarda kirjinta ke over racing kai kaje wasan gudu tayi ahankali ta zame nan kasa ta zauna ta fashe dawani irin kuka har shedewa take takama jikinta ta kankame waje daya kamar irin yayi mata wani abu, har sai dataji numfashin ta nafita da karfi kafin ta saurara daga kukan datake. Anan kofan gidan yazauna ,yazuba ma waje daya ido babu abunda yakeyi irin tunanin rayuwarsa yanzu haka shi mijin aure ne nauyin ci,sha surutu da kuma tarbiyyar yarinyar na hannunshi,duk ya dauke wannan kuma ai yana yi bakin karfi da ikonsa tunda duk saboda da ita yake duk wani abunda yakeyi, da kuma amanar ta da ummi tabasa ,tunani ne kala kala a ransa tau yanzu idan yasake kamar yarda zuciyar sa ke raya masa fa?idan yabari soyayyar yarinyar da tausayinta yakarasa shiga zuciyarsa da ruhinsa fa? Yasan kiyayyyar da mahaifinta ke ma abby, yasan yarda mahaifinta yake kar ya shimfida rayuwa da ita daga baya mahaifinta yazo ya raba su fa? Duk duniya bai taba jin wata a rai ba bayan ummi dasu aysha sai ita,saukar da ajiyar zuciya yayi ahankali yatashi ya shiga cikin gidan sai da yarufe kofan part din kafin yazauna parlor yana kallon kofan bedroom din ji yake kamar yashiga,amma yafasa. Kasancewan yayi daran bacci shiyasa ya makara sallan asuba ma a gida yayi ta Sai da ya gyara ko ina kafin ya dafa masu

Chapter 16 of 83