Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yakara jaa sai fadawa dayayi kadan hadda suman kansa ya wanke tayi luff akansa,zaman yayi ya ajiye ledan wanda yazuba kayan da ya cire a drawer kafin yadawo ya zauna kan gadon “murya can kasa yace tau ko bazaki bani abinci ba?batace komai tabude warmer ta zuba masa abinci kafin ta dauko masa bottle water da dr hafsa tasaka a basket din ta ajiye masa a gefensa yadinga bin abincin da kallo kafin yace wannan naki ne?takalle sa ta dauke ido kafin tace ina kai kace zaka ci din”baice komai ba yajuya batare da yadauki plate din ba kallo ta dinga binsa dashi,kafin tace wai bazaka ci bane? Sai sannan malik yace hala baki san ni inada cin abinci ba dazaki saka mun wannan dan abinci kamar dai wani yaro sai sannan ta tuna da ranar data gansa ya zuba abinci a plate kamar zasu ci su hudu yana ci batace komai ta kara masa abinci ta daura masa a cinya,sai daya kusa cinye abinci sannan ya lura da ita bacci take nan kan kujera kallon rigan yayi yarda tayi mata kyau sosai duk yarda creams soap shower gels dinta suka chanza amma kalan fatan ta na nan babu abunda ya rage glowing take sosai,idonta a rufe hakan yasa ya dinga kallon fuskanta gashin gaban kanta yayi luff yadan fito har kana iya ganin calaban kanta yarda hulan yazame,dewdrop ya furta can kasan ranta sai yayi maza kuma yayi shiru saidai day agama cin abinci kafin ahankali ya mike ya ajiye plate din hannunsa yasha ruwan kadan kafin ya matsa kusa da ita yasa hannu yashafa cheeks dinta tayi sauri ta bude idonta, yawani hade fuska kafin yace wake up and eat bana son wannan rashin cin abinci, harara ta watsa masa,yayi sauri yasa yatsa ya buge mata baki wani shegen kara tasake kwalla yakawo idonta ta mike tsaye,wallahi saura kadan yafadi wannan abun datayi, kallonta yake ko dauke ido babu,ita shi take kallo kafin ta dauke ido bai ce mata komai sai juyawa dayayi walking majestically and slow har ya isa gaban basket din yabude yazuba mata abinci daidai yarda take ci ya yadaura mata kan cinya kafin ya koma kan gadon ya kwanta ya rufe idonsa yana sauraron yarda zuciyansa ke bugawa, Abinci take ci cike da aji da kuma nutsuwa bata ci dayawa ba ta ture ta bude ruwan nan ma kadan tasha tarufe yanajin duk motsin ta har time din data ajiye abinci ta rufe yaji,tashi yayi zaune yace ki kwanta bara naje wajen dr Ibrahim naga kaman bacci zakiyi right? Ahankali tace ahah ni ba bacci nakeji ba,bai sake magana ba yakoma ya kwanta itama kan kujeran ta zauna tayi shiru. Inna da tashigo yanzu ta goge hawayenta tace tau daman banda anyi niyyar audu ya tsane ni ya tsani kayana,sai a rasa matar dazata kirani nadawo daga wurin rubabban sunan nazo asibitin fisabillahi banda rashin kaunar Allah yayi yawa ace yaro tun jiya akawo sa nan ace babu wanda zai kirani ya gayamun sai tasake fashewa dakuka,malik dai yayi shiru can yace kiyi hakuri hajiya inna kinga sai fa da asuba kuma nayi tunanin ma kina gida ko hafsa ta gaya maki,inna ta mike tsaye ta aaaaa haram haramun wacece kuma haka? Matar da kowa yasan bata kaunar Allah, Aydarh dai na zaune batace komai ba inna ta shiga da masifa ta inda take shiga batanan take fita ba wulakanci sai wanda ta manta ke batayi wa dr hafsa ba ita dai tayi shiru batace komai sai danna wayan ta takeyi,malik yace yanzu dai ai nace kiyi hakuri ba?tunda yanzu kinsani kuma har gaki kinzo ai shikenan koh hajiya inna?inna ta goge sauran hawayan fuskar ta tace shikenan audu na hakura ya jikin naka?yace Alhamdulilah dasauki inna tace ai wannan masassara dai baa ji dadinta ba, waenda basuyi taba gaskia basu dayawa,nidai Allah ya tsallakar dani,daga ranar naje anguwa nadawo kaina naciwo sai ga wannan matar da magani waai nasha kila zazzabi ne ni dai dayake nasan ciwon kaina Ko kallonta banyi baita da maganin nata, malik yace Allah ya kyauta,can tayi kasa da murya ta kalli malik tace tare fa nake da ranla ita dayake babu ita a munafukai na, sai gashi tana ganin dawowa ta tashigo take fadamun tace na rufe gidan ma mutafi malik yace Allah sarki,kafin yarufe baki aka turo kofan dakin Ko sallama babu tashigo tasha wani fitted gown na atamphar rubber gawani uban jam baki tasha sai baza kamshin balila ake ga ubansu dauri ankashe anfito da calaban attach blue da green irin na asalin karuwan nan, tana tafiya kamar zata kare shidai malik kallo daya yayi mata ya dauke ido yarasa miyasa bai son yarinya kwata-kwata bayason yarda takenan babu kamun kai,dr hafsa dai sai binta da kallo take tana son taga inda zata da taho hakanan,tun shigowan ta aydarh ta ganta sai ta dauke ido tahade fuska kaman bata taba dariya bai ta Ramlan bata ma lura da aydarh basai said ai baza ido take taga ta ina zata hango ta, ganin malik yasata mance duk wani abu straightly gadon ta nufa tana isa idonta yasauka kan aydarh dake kujera can karshan bangon gadon a zaune kallo daya Ramlah tayi mata ta dauke ido duk sai taji ta muzanta tana san zaran ma bak alar yard din bane ita da aydarh amma ko zatayi yawo tsirara sai malik ya saurareta ko da sau dayane cike da duniyanci ta sace kallon aydarh taga hankalin ta baya kansu,dan daga murya tayi kafin tawani karyan da kai gefe tace “sorry dear”ya jikin naka,daman tun jiya dasafe na lura da yanayin ka nasan ko nafada ma baka da lafiya ba lallai ka aminci ba,tass aydarh taji abunda tace, saboda yarda take maganar kowa na dakin ma yaji balle ita aydarh dake gefensu shi wallahi ma mamaki abun yabasa bai ce mata komai sai sauraron ikon Allah dayakeyi,jin hakan yasa dr hafsa mikewa bata tolerating shits din yaran nan domin tun ba yau ba tana lura da duk wani movements din Ramlah kan malik bata taba maida hankalin ta ba saboda ba ruwanta dasu amma yanzu gani take kamar cin fuska ne ramlah keyi ma aydarh,hakan yasa cikin tsare gida dr hafsa tace Ramlah kiyi masa ya jiki kawai ki fita babu wanda yatambaye ki wani abu anan so better maintain your dignity here am I cleared? Wani banzan kallo Ramlah tayiwa dr hafsa dan ba bata raina taba shiyasa tayi shiru batace bata komai ba aydarh yi tayi Kamar batasan dasu hallitu ba a dakin baki daya,inna tasake baki tana kallon Ramlah kafin tace inalilahi waina illahil rajiun. Ta dinga bin Ramlah da kallo kafin tace aaa ranla ke kau kin zaqe dayawa, daga zuwa dubiya Sai ki tsatsallake mu,mu danginsa ki kai har nan ko ita asiyar baki ga inda ta zauna ba balle ke kwashe kwashe ki?Aydarh dai kanta nakasa bata dago ba tana dai jin su,dr hafsa tace fita zamuyi inna mu barsu da matanshi inna ta mike tsaye tace gaskia bara nakoma gida nasamu gayen in kwadawa audun kafin in dawo,dr hafsa tace tau shknn ,inna ta kalli Ramlah kafin tayi mitsi mitsi da ido tace tau ko dai baki ji ne? Matar dake aike wurin tace a fita katti sun zo sun cika daki ina yaro zai warke, dan baa kaunar Allah ai sai a sa masa wani cutan ma Allah natuba, Ramlah ta mike tsaye tana wani bata rai,tace Alright love Allah yabaka lafiya zuwa anjima nadawo, malik dai ya maida idonshi ya rufe bace komai ba inna tabi ta da kallo baki bude dr hafsa ma haka, mamakin Ramlah ya cikata,inna ta dauki jikkatar ta fice,dr hafsa ta kalli aydarh tace muje office kibar sa yayi bacci malik yabude ido yana kallon aydarh kafin yace ki rufan mu duvet din,bata masa komai ba ta warware duvet din gently ta rufa masa,ya’ki dauke ido akanta,hannunta ya kalla kafin ya rike hannu few seconds ya dauka yana kallon hannun kafin yasake ta,dr hafsa dai nagani haka tasa kai ta fice daga dakin, ta ja kofan malik yace “kunsan ba zama zakuyi ba kuma sai kisa ta koran mun budurwa?aydarh ta watsa mashi idonta kafin tace aaaa kasheta nasa tayi ba koranta ba ni miyayi ruwana da ita,put this into her head please am not a mate of a kid whether she is your girlfriend or you wife that’s none of my business am not her type,bana son raini and ta daina kallo na if not I surely deal with her I will deal with the stupidity out of her, kafin ta juya ta fita mamaki tabasa da dariya,yashafa kansa yabita da kallo yasha kansa ahankali yace masifafa ya lura yarda Ramlah bata birge sa itama haka,amma wannan masifan fa? Girgiza kawai yay isai kuri ga tsoro,sturbborn bae.ko da tashiga office din dr hafsa still bakinta na a tsuke ta hade giran sama da kasa,sallama tayi ta zauna kan kujeran dake facing din dr hafsa,dr hafsa data lura da yanayin aydarh tace miya faru naga fuskan ki a hade,sai sannan ta bude baki cike da tsiwa tace kiji sa fa auntie,wai nasa kin koreta nayi magana ko nasa da ita didn’t I even know her existence a dakin ne? Dr hafsa da tagama sauraron aydarh ta girgiza kai tace kiyi hakuri aydarh kuma tun farko laifinki waenan yaran basu da hankali basu da tunanin basu da kamun kai ma,maybe fa ko magana baya hadasu kawai daman opportunity take nema wanda zai hadasu tayi mashi magana sai ga dama tasamu don haka karki damu ba laifinsa bane,kawai kiyi kokari ki sa yafita harkan ta,aike ce matar sa babu fada babu tashin hankali zaki sa ta fita harkan sa,Aydarh dai tayi shiru bata sake cewa komai ba,dr hafsa tace bansan abunda ke damun yarinyar nan ba har ta bata kanta har haka wallahi, definitely nasan shidai yallabai ba shiga harkan ta zai dinga yi ba mutun da kullun fuskar sa nan babu wasa kwarjinin sa ma sai yahana kayi masa magana amma rashin kunya da tsaurin ido irin nata sai da tasamu waje har haka Allah natuba ma banda neman jafa’I irin na Ramlah ina ita ina kishi dake ni wallahi ko mijinki kawai ya rage a rayuwa wallahi aydarh na gwamaci na karasa rayuwana ahaka saboda nasan dai photo kawai na aure,ita dai aydarh sai sauraron dr hafsa take har tayi shiru kafin aydarh murya can kasa tace “why”? Dr hafsa ta gyara zama tace haba aydarh ki dube ki,ki dube Ramlah idan kina wuri har akwai wace ta isa tayi magana? Aydarh ta cigaba da bin dr hafsa da kallo itama dr hafsa din aydarh take kallo, babu wanda yasake magana cikin su ,tunani ne kala kala azuciyan aydarh. Inna tace sannu ko audu,malik ya amsa mata ta bude samiran data saka kwadon a ciki tace ka daure ka ci ko kadan ne,malik ya dinga bin kwadon da kallo ummi tafado masa a rai yayi murmushi yasaka cokalli yafara cin kwadon ahankali,inna ta kalli aydarh tace tunda nashigo naji ki shiru ko kema ba lahiyar?aydarh ta girgiza kai tace aa inna lapia na lau,inna tace tau ai shikenan bara yaci kwadon idan ya rage kema sai k ici, malik yajuya ya kalli aydarh kafin ya dauki samiran ya daura mata a cinya yace eat batace masa komai ba ta sa cokallin dake ciki tafara ci bakaramin dadi kwadon yayi mata bahakan yasa taci ba laifi shidai sai bin ta yake da kallo duk surutun da inna ke masa sama sama yake amsata,har tagaji tayi shiru bacci ma ya kwashe ta anan kan prayer mat din datake kwance.wajan 6:00pm dr ibrahim yashigo dauke da file ahannu ya kalli malik kafin yayi murmushi yace giwa tafadi daga ciwo kwana daya har kafada na lura madam ta ma fika dauriyan ciwo wallahi,malik yakalli dr ibrahim kafin yace sallamana zakayi right?yarda yayi maganar bakaramin dariya yaba dr ibrahim ba saboda yasan haushin maganar daya gaya masa ne,dr ibrahim yace aaa gaskia maybe sai zuwa jibi tace kar na sallame ka dan yanzu,malik ya kankance ido yace wayace?dr ibrahim na dariya ya nuna aydarh dake zaune kanta a kasa, karfasa dake saitin kafanta yasa ya taketa da dan karfi taji sare amma ta daure duk dataji zafi, kafin ya kalli side din inna dake bacci yace ni kayi discharging dina idan yaso ita sai ka bata gadon dana sauka tunda zaman bai ishe ta ba,dr ibrahim yace auu haba?naga time din dabata lafiya ko nan da bakin clinic kasa fita kayi saidai ,kaga idan nabata gado kaima zaman ba isheka ba,aydarh dai najin su still kanta na kasa bata dago ba.Kasancewan gidan koi na very neat yake babu wani dirty suna shigo malik yawuce bedroom so yake ya kwanta tunda alright anyi isha’I dr hafsa takalli aydarh tace tau sai dasafe Allah yabashi lafiya Aydarh tace Ameen har bakin kofa ta raka dr hafsa din kafin ta rufe kofan da key tadawo kitchen ta shiga ta dinga bin kayan girkin da kallo bata iya kuna camping gas din bahakan yasata matsawa sosai kusa dashi ta dinga bin rubutun jiki da kallo open/close ashanan data gani nan aje ta dauka tana murda wajan open din ta qasta ashana sai kau wuta tagama murmushi tayi kafin ta tari tukunya ta daura ruwan zafi, parlor tadawo ta zauna few minutes kafin ta koma kitchen din yatafasa yasa takashe gas din successfully wani hadaddan simile tayi kafin ta fita ahankali without making any sound,ta bude kofan bedroom din bacci yake sosai kanshi a waje while ya rufe jikinsa da duvet toilet ta wuce ta dauki bucket kafin ta fito ta koma kitchen din juye ruwan, wanka take son yi amma tana tunanin yarda zatayi wanka gashi a cikin dakin towel da dauka da duk abunda zata bukata tashiga toilet din sai datayi wanka tass kafin ta sake kayan jikinta tafito,zama tayi can karshan dakin kusa ta wardrobe tana shafa Vaseline gently ,tun dazu yafarka yana lura da duk abunda take sai bai nuna ba ,duk da duk bayan seconds sai ta kallesa taga ko ya farka ita yake kallo,dayaga zata juyu din sai yayi maza ya rufe idonshi kamar yana bacci saida tagama komai kafin tasaka hijab ta takure kanta waje har bacci ya dauketa ahaka, yabar jin motsinta hakan yasa shi gane cewa tayi bacci,tashi yayi daga kan katifar,daf ya dauketa kamar baby ji yayi kaman ya dauke paper, baccin ta yayi nisa shiyasa sam bata ji sa ba har ya kwantar da ita kan katifan ahankali yasa hannu ya zare mata hijab din jikinta bin ta yadinga yi da kallo ko dauke ido babu yarda tawani hade fuska duk da bacci take yabashi dariya ya girgiza kai yace troublemaker,bargonsa ya fiddo da pillow sai bedsheet din dayake rufa ya shimfida nan kan carpet ya kwanta.kiran sallarh farko yasa shi bude ido kallon katifan kafin ya dauke ido ,toilet dinta yashiga har kamshin ta ya kama toilet din,yadinga bin pants dinta da brassieres da kallo sai dayasa soap dinta ya wanke fuska kafin ya dauro alwalla yafito, yana shigo sallan asuba har yanzu bacci take bata farka ba,hannu yasa yataba pillow datake kai, ahankali tabude idonta dasuka koshi da bacci,yace wake up its time subhi batace komai ba ta lumshe ido shi kuma yajuya yafita daga dakin ya koma parlor ya zauna ,ta dinga bin katifan da kallo ta dai san ba nan ta kwanta ba amma ya akayi ta dawo nan din?tabe baki tayi kafin tashiga toilet tayi alwalla tafito sallarh tayi ta koma kan katifan ta rufe ido still da bacci a idonta, 8:00am daidai yafarka daga baccin dayasake daukar sa anan parlor kitchen yashiga ya daura ruwan shayi kasancewar yasiya kayan tea yana saukewa ya mayarda ruwan dazai dafa masu indomie zuwa yanzu yagama jin sauki tass daman haka ciwon yake masa, yajuye ruwan a flask indomie ma yajuye musu a warmer kafin ya wanke few plates din daaka bata baa wanke da tun kafin ya kwanta ciwo sai daya gyara kitchen din tass kafin yadawo parlor nan babu wani dirty shiyasa bai dauke shi long time ba kafin ya karasa yashiga toilet din nan parlor ya wanke shi kal bedroom din yashiga Still tana bacci incense sticks kawai yadauko yazo nan kitchen ya kunna yasaka a parlor kafin nan ruwan zafin daya daura sun tafasa ya shiga yayi wanka ,har sai da yashirya yaci abinci kafin yaji motsinta alaman ta farka, bai shiga bedroom din ba yayi zamansa anan parlor, Tana tashi ta kwashe bargon daya kwana aka isai data ajiye komai a inda yake Kamar yarda taga yanayi kafin ta yaye bedsheet din ta gyara katifan tanaji yaune second time a rayuwanta data gyara gado da kanta yayi kyau babu laifi dan har tafisa iyawa murmushi tayi ganin ta gyara dakin yayi kyau sai taji wani irin dadi,shara ya rage sai mopping shima bara taje ta dauko tayi tasan zata iya,tana buda kofar ta ganshi zaune kan carpet yana kallon satin kofar har zata koma sai kuma tafito kanta a kasa ta nufi hanyar kitchen din mopper day agama goge kitchen da parlor na nan bakin kofan kitchen din bai zuban da ruwan ba hannun tasa ta dauki bucket din da tsintsiya sai Parker yadinga bin ta da kallo tau mi zatayi? Ya dai dinga binta da kallo baice komai ba har tashige daki,yana nan zaune yanata tunanin abunda zatayi da mopper tau ko dai tafara gyaran gidane hakan da zuciyarsa taraya masa bakaramin dadi yaji ba,Ahankali ya furta Alhamdulilah ,komai yafara zuwan mun cikin sauki Allah nagode ma, mikewa yayi tsaye yanufi bedroom din kawai dan ya tabattar yana shiga yaga ta zage tana ta mopping, kafa yasa zai taka tace “hey wait”kafin tawani yi kincin kincin da fuska tace karka takamun, daure fuska yayi yace tau idan ban shigo bai na kike son naje na dauki abunda zan dauka? Tayi kasa da murya tace to basai kajira ya bushe ba kafin ‘ malik yadai dinga bin dakin dake nan gyare tsaf yayi kyau kamar daman tasaba da gyaran aransa yake tambayar kansa daman ta iya ne? Bai dai ce mata komai ba yaja bakinsa yayi shiru domin yasan halinta koya tambayeta baza mata tanka sa ba, juyawa yayi ya koma parlor Alhamdulilah yake ta furtawa saura girki kenan yanzu islamiyya a can ne yake tunanin kawai zai saka ta a koya mata komai na addini dakuma zamantake ta yau da kullun,da wannan tunani yayi tazama parlor har sai data gama kafin ta fito hannunta rike dasu mopper,kitchen ta shiga ta kunna gas kamar yarda tayi jiya ta daura ruwan dazatayi wanka ,tana fita yashigo kitchen din zuwa yanzu mamaki yakarasa kashe sa how talented she is wai duk a cikin kwana biyu ta iya abubuwa haka? Auu tau daman can rashin koya matan dabayayi ne yasa bata iya ba, kusan 5mins yana nan tsaye a kitchen din kafin yajuya ya koma parlor,fitowa tayi da bucket a hannu tashiga kitchen din, ko da tafito wanka nan ta tarar da plate din indomie da cup din tea sharp sharp tashirya kafin ta zauna tayi breakfast din. Dr ibrahim dayagama sauraron malik ,yayi shiru yace tau badamuwa ai babu ma nisa daga nan zuwa can iskamiyyan matan aura ina ma da aboki a waja inaga kamar shine headmaster gaskia,malik yace tau yaushe zamuje can din? Dr ibrahim yashafa kansa kafin yace aa bara na tura maka number sa sai ka kirasa kayi masa bayani idan yaso sai yayi muku fixing time kuje can din,Malik yace tau shknn ngd, tura masa number yayi anan take malik yakira mutunmin waya suka gaisa yayi masa bayani mutunmin yace tau shknn idan Allah yakaimu gobe sai ku shigo waja tara nasafe in sha Allah malik yace tau Allah yakaimu, bayan malik yagama wayar dr ibrahim yakalli sa yace maganar tafiya nasarawan fa saura kwana tara yau,malik yayi shiru can kuma yace tau Allah yakaimu yau ina son zuwa wajan aiki bara nashiga gida nashirya,dr yace tau shknn nima clinic zan tafi,idan angama magrib mu hadu a can wajan kallon wasan basai na biyo ta nan ba,malik yace tau shknn. Yana shiga gidan ya tarar da Ramlah nan tsaye kofan part dinsu bai ce mata komai ba yayi wucewar sa da sarsarfa tabi bayansa har wajan kofan shiga parlor bai ko kalle taba yafara knocking ahankali almost 10seconds yana nan tsaye kafin a bude,yana shiga itama Ramlah ta shiga, wani irin banza kallo aydarh dake tsaye tabita dashi kafin ta kalli malik ahankali cikin wannan hadaddan innocent voice dinta tace tell her to walk out I want to shut the door tana fadin haka ta tsare sa da ido fuskanta babu alaman murmushi,wallahi malik kamar wani yaro ko mai jiran umarninta haka yasa shi kallon Ramlah yace mata out, Ramlah kau kamar zata fashe da kuka gawani irin shakkan su,su biyun duk dataji ya diran mata lokaci daya tayi maza tafice kafin aydarh tamaida kofan ta rufe da karfi,har sai da yabita da kallo. Kallo har sai da tashige daki kafin yabar bakin kofan shima yashigo, tura kofan bedroom din yayi ya sameta tsaye gaban wardrobe tana mayar da kayanta daya wanke ranar,ahankali yace wai miye ruwanki da yarinyar nan? Dawani irin speed aydarh ta juyu har ta manta ma bata ajiye bra din dake hannunta ba, cike da masifa tace kai ma miye ruwanka da ita? Malik ya daure fuska yace mind you she is my gurl,aydarh tawani wara ido ta tabe baki tace your gurl bata masan tayi wani dariya ba,da har saidai ta malik yakasa dauke ido kanta kafin ta wani tabe baki tace ashe mace ce wannan din,ai ni bansani ba, Malik bai sake ce mata komai ba ya juya ya fita, kamar kullun yauma haka suka wuni aiki ‘ wani big mansion suke ginawa a nan anguwarsu Alhaji musan, sai yamma lis ya koma gida ya gaji sosai yau shiyasa ya tsaya wani café ya musu takeway yawuce, yanzu ma kamar dazu ita ta bude masa kofan yayi sallama ta amsa masa kamar an mata dole, kafin ta dinga binsa da kallo har yashiga kitchen yarda jikinsa ya bace da cement yak bata mamaki accident yayi ko faduwa yayi? Tayi shiru tana tunanin abunda yasa mesa,jin takunsa yasa ta saurin dauke idonta ta shige bedroom bin ta yayi da kallo ya girgiza kai yashige bathroom din nan parlor, sai dayayi wanka tass kafin ya mayar da kayan jikinsa ya shiga dakin tana nan zaune kan katifa idonta a rufe duk da ba bacci take ba saboda dayayi sallama ta amsa sa Still kuma Idonta na a rufe,bude wardrobe yayi ya dauki kayansa da Vaseline da perfume sai comb ya dawo parlor sai da yashirya tsaf kafin ya shiga,kitchen yajuye masu chips din a plate kafin yadauki pure watar yatafi bedroom din ya kai mata, bata wani chips din dayawa ba ta ture,sai ana kiran magrib dr ibrahim yakirasa yace yataho kawai bazai biyo ta gidansa ba su hadu kawai a can tau malik yace ya katse kiran,bai dawo ta gidan ba can ya wuce kawai. Sai wajan ten ya shigo gidan kamar ko da yaushe yau din ma akwai nepa koi na tsaf tsaf har parlor yakama kamshinta saboda yawan zaman da take yawan yi a yanzu,ledan da yashigo da shi yawuce kitchen ya wanke fruits din dake ciki yayi slicing kan plate kafin ya debe nasa ya zuba mata nata a plate da fork, da sallama yashiga bedroom din yaji shiru bata amsa ba,bacci take takure waje daya cikin duvet kamar yar baby hulan kanta ya cire manyan calaban da dr hafsa tayi mata yafara warwarewa duk ya baje kan pillow, sai da ya ajiye plate din hannunsa kafin yazauna can nisa da ita yana binta da kallo kamar mai irga numfashin ta, kusan 5mins yana ahaka sai yau ya lura da kunnata bula ne har uku kowani a jiki akwai hadaddan barima gold bakaramin kyau bariman yake dashi bad uk duniya ya matukan son bula shiyasa a gida ma yake yawan ba su aysha kudi yace su siya earring su

Chapter 15 of 83