Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mata ta girgiza kai kadan batace komai ba ummi tayi shiru itama tausan yarinyar taji bana wasa ba Wallahi dagani tasha wahala ahannunsa tasan halin malik tasan yanayin larurin sa dole ta wahala gashi ba lallai ma tasha wani magani ba kafin yaje kusa da ita tunda a can babu wani wanda ke gareta sai shi sai Allah kuma daga shi har ita ba lallai bane su san dawani maganin mata “ganin yarda take tafiya kawai yasa ummi tunanin ma ya riga yayi mata duk abunda yadace tunda tasan sa da tausayi “mikewa tayi ahankali takalli aydarh for few seconds kafin tajuya ta fita yarinya takai mace barakallah tana da kyau tunda biyu yahade mata uwarta balarabiya ubanta kuma fulanin usuli “kallo daya zakayi ma yarinya kaga tsantsar kamun kai dakuma nutsuwa tareda ita irin yaran nan marar sa girman kai da shegen surutu “bakaramin godiya take ma Allah ba a duk lokacin da tuna malik yanada yarinyar a matsayin mata duk da basu zauna tare ba,tana fita taga abby da malik sai halime da aysha hadda Maryam sun hade waje daya duk sun rungume abby din kallonsu take baki bude watau ya yafe ma yaronsa kenan dauke kai tayi daga kallonsu ta wuce kitchen sharp sharp ta daura jallof din taliyan hausa ‘tasan malik naso da kuma batayi niyyar dafawa dashi ba aydarh kawai zatayi ma wa amma takasa kawai ta daura musu locus beans ta dauko mai kyau wacce aka kawo mata daga kauye sai manya fresh attarugu da pepper masu kyau ta wanke ta jajjaga ta zuba pure groundnut oil “ta yanka onion tasaka tabare maggi tasaka kafin ta rufe ta sauke ruwan zafin tasaka pure zuma mai kyau a ciki da cloves and ginger Lipton “ ta motsa tafito zuwa yanzu su aysha suna zaune gefe malik kuma na kwance jikin babansa “hankalinsa na kanta amma yanda yaga ummi nayi masa yasa shi kama kansa “kallonsu ta sakeyi suma duk suka kalleta tayi shigewanta “dakin ta ajiye cup din shayin zuman hannunta “kafin ta saka pillow ta gefe da gefen aydarh kafin tasa hannu ta zare mata veil din kanta tabarta da inner cap din murmushi ummi tayi jikin kamshin aydarh tun farkon zuwanta gidan ummi tayi experiencing kamshin kamata tayi tace tashi ki sha shayin zai taimaka maki “ahankali aydarh tace zan sha anjima “ummi tace aa asiya daure ki tashi kinji daurewa ake sannu kinji aydarh ta gyada masifan kunyan ummi take kaman kasa tabude tashige shknn ummi tasan abunda sir yayi mata ita kam tabani!kokarin mikewa take amma ta kasa batayi niyyar kuka ba amma kawai tafashe da kuka kasa kasa azaban yayi yawa zafin ya isheta Allah ummi takama ta dasauri duk sai taji ta damu kodai yaron nan yaji ma yarinyar nan ciwo wai taga yanayinta is very worst she looks very pale Allah ummi tayi kasa da murya tace ko dai zakiyi wanka asiya aydarh tace ah’ah sanyi nake ji ummi tace sannu “Aydarh tayi shiru kawai ummi tace kunje asibiti ne???aydarh tace ah’ah ummi tace shi ya duba kine ?aydarh ta gyada kai kawai ummi ta lura zafin ciwo ne take ji da kuma kunya zama tayi kusa da aydarh kafin tasa hannu tajawo ta ahankali cike da lallashi “Aydarh ji tayi she feels very safe a jikin ummi “sai ta dinga tunuwa da moment dinsu da oum dakuma auntie rufaidarh she surely missed her family ji take kaman ta bude ido taganta cikinsu yanzu tayi lamo jikin ummi tana saukan da numfashin ahankali ita ummi sai taji kaman malik din ne ta rike har cikin ranta takejin aydarh cup din ta dauko tadinga bata shayin kadan kadan yanda ummi ke feeding dinta cike da so da lallashi Wallahi yasa aydarh shanye shayin tass kafin ummi takomar da ita kwance “tana shafa kanta “ummi ta fita rike da kofin shayin a hannu, labari kawai sisters dinsa ke basa abby na rike dashi yahana sa zuwa wajan ummi yanzu sai ta huce zuwa anjima shima abbyn har ransa yake jin diyar dan uwan nasa so yake suyi magana amma yabar ma ummi ita ganin kaman son yarinyar yayi mata yawa “kitchen ummi tashiga ta sauke girkin lafiyayan taliyan hausan datayi musu ga chicken daya dahu luff wanda abby yasiyo musu jiya tacire bones din ta zuba a cikin lafiyayan flat ta daura fork “tafito ta wuce da plate din dakinta inda aydarh take shidai malik sai kallon ummin tasa yake ganin yanda tawani share sa duk da abby da sauran sisters dinsa sun karbesa saboda dayayi niyyar bawa abby hakuri abbyn ma rufe masa baki yayi yace anjima kadan zasuje inda maganan ya dace sai ayi a can am as far as now baya son wani magana bayan bayanin yanda rayuwarsu ta kasance lokacin da malik yagama ma abby bayanin tun daga farkon zuwansu kano har samun aikinsa da zuwansu adamawa a yau duk da yayi shorting stories din kaman abunda yashafi shi shida aydarh amma kama daga saukansu kano basu gida da dr ibrahim yayi samun masa aiki under alhaji musa da duk wani abubuwan alkhairin dasuka faru dashi a kano da su inna da zuwansa Washington dakuma matsayin sa a can sujjud kawai abby yayi yakai ten minutes yana jero adduar godiyan Allah su aysha tana amsawa malik farin ciki har bayayi bayani ba saboda tsaban dadin ganin yanda su abby suka ji,halime tace Alhamdulilah yayah ubangiji Allah yabada sa’a yayah daman base uni nake so abuja pleaseeeeee malik ya gyada kai kawai yana jan hancinta “Wallahi he really loved his sisters his sisters are his world yana son yaran nan Allah “duk abun nan hankalinsa na can wajan aydarh “ummi dake kitchen kaf taji labarin da malik ke basu tsayawa tayi kawai bayan kofan kitchen din tasa hannu tana rufe baki tafashe dawani irin kukan dadi Allah Alhamdulilah hakika bata da bakin yiwa Allah godiya ganin abunda bai fi shekara ba adduarta ta amsu abubuwa dayawa datake mafarki ya tabbata wai ABDOOLMALIK dinta ne keda aikin yi babba kaman wannan shine yazama cikaken Likita burinsa ya cika danata da kuma na abby basu da wani buri daya wuce zamowar malik likita Allahu akbar wasu hawaye suka sake wanke fuskan ummi malik ne keda mata yaronta ne yazama babban mutun haka “wanke fuskan tayi ta window kitchen din kafin ta dauko fura mai kyau sauran wanda ta ajiye ma abby ta dauko fresh kindirmon mai kyau na adamawa ta zuba dayawa tasaka madara sai honey a ciki tafasa block kadan ta zuba kafin ta fita dashi a hannu kan ummi kasa takira sunan aysha cike da respect cus sun samu cikaken tarbiyya “tace na’am ummi “ummi tacigaba da tafiyanta tace ki shiga akwai abinci ki ba wanda yadace “aysha tace tau ummi saboda ta fahimce abunda take nufi abby ma murmushi yayi yana girgiza kai yasan halin matar shi daza’a bude zuciyanta murna ce dankare amma miskilanci yahanata sakar masa fuska “shiga tayi dakin tasake zama kusa da aydarh kaman dazu haka ma yanzu ta dinga bata taliyan bata wani ci dayawa ba ta dauke kai ummi tace da kin daure kinci asiya saboda kisamu karfin jikinki kinji ko?aydarh ta goge hawayenta tace no koshi “ummi batace komai ba ta dauko cup din fura takafa ma aydarh a baki bata janye ba sai data tabbatar da ta koshi “ kafin tace tasa hannu tana gyara mata inda yabace kafin ta ciro paracetamol din tabata da ruwa so take taji ko tana drugs amma bata shirya magana dashi yanzu ba,maida ita tayi ta kwantar kafin ta gyaramata bedsheet din data yafa mata “ tace sannu kinji asiya aydarh ta gyada kai kafin ta maida idonta ta rufe “tarasa yazatayi taji dadi ta daina jin zafin ko dai shknn haka zata cigaba da zama yaci aci zuwa yanzu ta rage amma Wallahi babu abunda ya ragu “.malik yayi shiru yana kallon abby kafin yace tau abby amma shi abban nata yana nan?abby yace tau bana ce ba malik “amma dai baza ‘a kwana yau ba sai munje munji ma tsayar su suma tunda kace hutun naka na kwana bakwai ne malik ya gyada kai abby yamike yace bara naje na sanar ma umminku da fito tare da matar taka “suma su aysha su shirya sai a rufe gidan malik yayi shiru abby yayi murmushin su na manya cikin kwantar da murya yace ka kwantar da hankalinka duk abunda Allah yayi mai kyau ne kuma daidaine nasan kana tunani zai sa kasakar masa y’a indai hakan yafaru daman Allah yayi zamanku ba mai tsawo bane ka cigaba da ba kanka kwarin gwiwa “kaji in sha Allah babu abunda zai faru ba sai alkhairi “malik yamike kawai ya rungume abby yace dan Allah abby ka taimaka mun kayi masa magana nidai bazan iya sakinta ba ko yace “abby yayi dariya kace kaji ja’iri watau ni kake fadawa haka malik yashafa kansa yace abby ku shirya bara nasamu keke tau kwara biyu “abby yace hala ko dakashigo baka lura da mota kofan gida ba?malik yayi shiru kafin yace eh abby “abby yace tau malan aminu ya chanza nasa shine yayi mun kyautan tsohowan nasa malik yayi murmushi yace masha Allah “Allah yasa albarka angode sosai wannan abota haka abby yayi murmushi kawai. Ahankali abby ke magana bayan ya dage curtain din kofan yace malama ku fito zamuje wani wuri yanzu “ummi tace da anhakura sai zuwa gobe yarinyar nan bata jin dadi,abby yace ta dai daure yau ya kamata muje wurin shiyasa ta daure Allah ya sawwake yace yana sauke curtain ya wuce “ummi dai tai shiru tana kallon aydarh da idonta ke rufe kaman irin baccin nan ya dauketa amma kuma ba bacci take ba idonta biyu “mikewa ummi tayi tabude wardrobe tafito da hijab din da zata hau da atamphar jikinta tasaka ta fesa perfume sama sama “sai karantse kace a hutu ummi take saboda jikinta babu inda ya nuna wani tsofa ko talauci ‘matsawa tayi kusa da aydarh tace BABY “aydarh tabude idonta tana kallon ummi kafin ahankali tayi kasa da idonta “ummi dake kallonta cike da tausayi tace ya jikin naki? Aydarh ta gyada kai kafin tace da sauki “muryanta yakarasa dishewa very weak and slow “dayasa ummi jin wani kala anya basai ta ajiye Komai wannan yaron yayi mata bayani karfa ace babu abunda yayi ma yarinyar nan duk wannan aika aikar dayayi? Ummi tace sannu zaki iya tashi yanzu Wallahi aydarh bata ma fahimta kawai ta gyadawa ummi kai ummi tace tau taso ahankali kinji abbynku yazo yace mu shirya zamu fita “Aydarh da kwalla suka ciko idonta tace To”ummi dai na kallonta tayi yunkurin tashi ahankali dasauri ta ririke katifa wani kalan emotionl kuka na kufce mata bata ma da energy yinsa da karfi ummi tayi saurin kamata tana yi mata sannu cike da lallashi da dubara ummi tafito da ita bayan ta yagyara yafa mata veil “suna fitowa da malik ummi tafara hadda ido sai kallon aydarh yake ba kunya balle tsoron Allah tunda tare suke da ummin,Wallahi duk wani kala yake ji yadauki hakkin ta ne dayawa Allah bai masan kalman dazai amfani wajan ba yarinyar nan hakuri ba zuwa yanzu banda bugawa da sauri babu abunda zuciyarsa keyi tsaban fargabar abunda zai tarar a gidansu aydarh ‘ummi ta banga masa wani shegen harara yayi saurin dauke idonsa shidai abby tuni ya fita followed by malik sisters “ahankali ummi ke tafiya da aydarh da hawaye sun ki tsayawa a fuskan ta har suka zo ta gaban malik dasauri yace bara na tayaki ummi ‘ummi tayi masa wani kallo tace karka sake ka taba mun yarinya kaji ni?kafin fuskan ta a daure tace fita kaba mutane wuri marar kunya kawai “kasa yayi da kanshi “ya juya yafita.shine gaba sai su baya abby kuma na driving yar Peugeot din shi ‘aydarh ta kwantar da kanta bisa shoulder din ummi the journey was silent ummi bata fahimce inda zasuje bas ai data ga hanyar wani irin yankewa gabanta yayi yafadi badai abby na nufin mayar da yarinyar nan zaiyi ba tama rasa kalar tunanin da zatayi sai kawai ta hau addua a cikin ranta,malik dai daka gansa kasan yana cikin damuwa yama rasa inda zai kamo komai yayi mashi chak aydarh kami don rufe bata masan wainar da ake soyawa ba “suna isa bakin mad gate din da this time ma ba kalan waccan bane wannan karon ansake gyara gidan yakarasa zama kaman white house na american ma “ga security’s kala da iri a bakin gate din Sai da abby ya saita hancin motan ta wajan gate din kafin ya tsaya security’s biyu suka karaso wajan sanye da uniform din civil defense “abby yakara sauke glass din window gefansa yana kallon su kafin suka ce mr where are heading to? Kafin su rufe baki aydarh ta bude ido dawani speed tana kallon inda suke kawa isai tasake lafewa a jikin ummi gabanta yayi wani irin faduwa itama zasuyi mata hakuri kaman shi?yaxata idan iyayanta suka cigaba da fushi da ita?inalilahi waina illahil rajiun shine kalmar dakawai take nanatawa “su aysha kam kallon gidan suke da mamaki ina ne nan din “Abby yayi ma security’s din pointing aydarh Wallahi arnan mutanan da ba musulmai bak asa rufe baki suka ganin small hajiya a cikin kalan wannan motor kai this is very unbelievable “kaiiiiiiii sanin halinta kawai yasa dayan kamo hannun dayan suka bude domin sun san halin aydarh bawani abu bane tasaka a kore su Ko second baza’a kara ba “wangale gate din akayi malik dai kaman anzare masa wata lakka a jikinsa haka ma ita maman tasu “su aysha dai kallon white house din kawai suke ko flim basa tunanin su taba ganin irin gini haka ba ga parking lots din motoci kaca kaca kaman irin ana siyarwa duk wacce aka mutun yana iya karasa rayuwarsa ta duniya tsaban kudi aka saka kana gani wajan siyan motocin “shima abby waje yasamu yafaka tashi sai dayayi jim kafin yakarasa adduar neman sa’a shima malik yayi wacce abby yace yayi,itama ummi ta ta adduar tayi “ahankali abby yace duk ku sauko su aysha ne suka fara fita kafin abby ummi ma ahankali tafito tana rike da aydarh bazaka iya ma misilta yanayin datake ciki ita kadai tasan abunda take ji a ranta wani kalan yanayi take ciki ‘ummi takama ta kaman dazu cikin dabara ake tafiyar su aysha suka bisu baya abby yace sauko malik babu abunda zai faru sai alkhairi kafada wa zuciyar ka haka, malik ya jinjina kai yana ba kansa kwarin gwiwa yafito “abby yayi gaba suka bisabaya har main entrance din gidan aydarh tarufe ido tana iya jin yanda zuciyanta ke dawata cikin riga duk steps din tafiyan dasukeyi “ sai taji wani irin abu abby da kansa ya taba door bell din duk suna tsaye sai dayayi kusan sau biyu kafin security kofan tabude tana kallonsu sai taga wani kaman yallabai Wallahi kallonsu dai kawai takeyi har idonta yasauka kan aydarh dasauri taja baya tana basu hanyar wucewa “abby yayi sallama yashiga kafin malik sai su aysha ummi dake rike da aydarh sune a baya sudai su aysha na ganin ikon Allah irin wannan gida haka tau wai ina ne nan din?basu da mai basu amsa kawai yasa su yin shiru “oum dake dinner ita da rufaidarh fruits ne gabansu kaca kaca “oum ta sake wani irin kyau da haske tana sanye da cotton lace mai kyau da tsada anyi mata A -line gashinta tayi parking a kasa tayi wani ture kaga tsiya karamin kama suke da aydarh said ai aydarh har taso ta fita kyau ma Wallahi rufaidarh ma masha Allah kana ganinta kaga balarabiya tana sanye da normal hijab kalan na yan makka “hankalinsu yakoma kan alaman shigowan mutane tunda tasan yau bata da bak’o kuma ko ma akwai sai security ta tambaya kafin ta bude amma yau batambaya sai shigowan mutane da ta ganin “ahankali cike gayu aji dakuma kamewan oum ta kalli rufaidarh tace uktiee kaman shigo nake ji rufaidarh dake slicing peach din hannunta tace zakiyi baki ne yau? Oum ta tace ah’ah bamuyi dakowa zai zo ba tunda jiya nadawo “rufaidarh tace to muje mugani maybe bakin babyn kine oum tayi ma rufaidarh hararan wasa tace na lura tunda nadawo jiya kin chanza wa bawan Allahn can suna “rufaidarh tace to karya nayi oum na murmushi exactly yanda aydarh keyi tace noooo gaskiyar kenan “mikewa sukayi suna shiga cikin parlor billahil azim oum ji tayi wani hajijiya mai kaman jiri na niyyar kayarda ita “da kyar tanemi wuri ta zauna kasan stages din tana ganin abun kaman a flim aydarh aydarh yarinyarta is back she cannot believe all this ta rantse “rufaidarh kau kasa karasa stepping tayi cikin parlor sai kallon abunda take ganin kawai take takasa gazgata hakan Wallahi! Abby yayi murmushi yace bismillah hajiya ku karaso fatan dai Habib din na nan rufaidarh datayi gathering courage dinta ta ja numfashi ta fesar kafin Still kuma ta tsaya nan inda take tsayi “da alama dai abun yashige su dayawa tunda oum ta zauna bata bude idonta ba tayi shiru tana jiran sauyawan abunda tayi noticing just now “daga kan stairs dake saukowa tasha riga da zane na lace ga mayafi ansha irin flower lace din sai flat shoe dinta masu shima kalan lace din (too match kenan)sauko take tana fama sababi “tana cewa tau Wallah ini sai nakama kaina tunda mutunan duniya duk sun karasa zama watsatsu banda ma rashin kan gado ace katuwar arniya tunda safe zata tasheka wai zatayi gyaran safe “shi habib din haka ake masa ko sa ini uwarsa eyi? Abby yayi murmushi daman baba kulu ta sanar dashi hajajju na gidan kuma hakan bakaramin dadi yayi masa ba itama babar na kan hanya zata zo “ hajajju takarasa sauko sam bata lura das uba har sai data shigo parlor wani irin kwana datayi tana shigewa corridor din nan parlor dake well decorated kaman dai wani showroom tsaban haduwa “ ta dafe kirji ta lafe a bango kaman zata shige bangon tana zara ido duk ta gigice “shidai abby dariya ma tabasa “malik ma duk halin dayake ciki shan kwanar da hajajju tayi bakaramin dariya ya basa ba har Sai dayayi murmushi “ yana girgiza kai “su halime dai are all speechless what is all this hajajju anan gidan kuma?kuma kowa yashiga shock a gidan tau kodai nan ne gidansu auntie aydarh? Tabbas ma nan ne saboda oum dasuka gani daka ganta ka ga aydarh “Abby yayi gyaran murya yace hajiya da dai kun daure an kira shi habib din munyi magana zafi kaddarar muce ahaka yara dai gasu suna dawo cikin koshin lafiya ba cuta ba cutarwa “ tau Alhamdulilah,sai lokacin rufaidarh tayi wani ajiyan zuciya takarasa shigowa cikin parlors malik yasauka daga kujera yana gaisheta kallonsa tayi ganin kaman ya chanza yazama wani babba kudi tabarakallah amsa masa tayi kafin suka gaisa da abby da ummi su aysha ma duk suka gaishe ta “wurin Aydarh kawai ta nufa tana zama kusa da ita takamo ta tasaka ta ajikinta aydarh kaman tana jira tafashe dawani kalan kuka wanda yasa oum dawowa daga duniyar data tafi hakika aydarh ce yarinyar tace dagaske ba wai wasa ba aydarta “Allah is great!!ashe shiyasa duk kwana biyun nan mafarkan datake da aydarh duk da gaske ne zai faru itama mi zatace ma Allah yama zatayi yanzu tukun Allah akbar “tunda ga kasan zuciyarta taji wani irin sanyi kaman an yayi mata wata cutar dake damunta na tsawon shekara dari “hajajju dake corridor tafito tana wara ido sai kawai tafashe da kuka tana nufar malik tace wala hauli wala kuwwata ina billahi “Allahu akbar audul Allahu akbar “anki Allah yaso wayyo Allahna “jama’a mukam bamu da bakin godiya ga Allah said ai muyi shiru “abby yayi kasa yace ina wuni baba ? Hajajju tafice majina tace lahiya lau ibrahim kunga yarda Allah ke nashi ikon ko ga yara nan sun dawo ummi ma dai tayi karfin halin cewa ina wuni hajiya mun same ku lafiya “hajajju tace lahiya lau asiya sai kuka ga abunda kuka kora koh? Ummi dai tayi kasa da kai duk su halime suka gaisheta kafin suka gaishe da rufaidarh “Wallahi oum ji take kaman taje ta rungume yarinyarta ji take kaman ta rike da hannunta yanzu nan “batasan iya adadin soyayyar dake kwance cikin zuciyarta ba na yarinyar ta “har bata masan iyakan yanda zata fadi bako ta bayana mikewa tayi ahankali tana gyara mayafin ta takarasa cikin parlor “walking in a righteous way “irin na mata yan gayu masu nutsuwa da kamun kai matan masu kudi yan boka “kan one sitter ta zauna ta dan dukar da kanta wajan gaishe da abby ya amsa mata da fara,a kafin suka gaisa da ummi cike da girmama juna saboda a iya rayuwar dasukayi daaa tare oum taso su kaman ranta bata wani nuna bambaci yanda take girmama nata yan uwan haka take girmama nasa amma sam shi abba ko ajikinsa “malik ya durkusa har kasa “ya sunkuyan da kanshi cike dawani irin ladabi da biyayya dakuma girma da darajar oum dayake gani ya gaishe ta itama oum wani irin nauyi taji tarasa miyasa har kasan zuciyanta kawai jinsa tayi a matsayin siriki “itama cikin alkunya ta amsa tana satar kallon aydarh dake jikin rufaidarh tana kuka idonta kano um din tana son zuwa wajanta amma Wallahi tsoron yanda zatayi mata take ji saboda zuciyanta zata iya buguwa a yanzu batasan iya adadin yanda take jiba yanzu data ga oum din sai taji duk duniya babu abunda yafiye mata nutsuwa irin ganinsu din “hajajju tayi gyaran murya kafin tace wani abu sai ga sallaman baba kulu “hajajju tayi mitsi mitsi da ido kafin tayi kasa da murya tace ma malik kaji wani bala’In kuma tau irin ruwan kulu kuma anan duk fa bata tashi zuwa bas ai yanzu dazata zo ta nuna isa wai ita ala dole babba Wallahi kar sakar mata fuska saboda yanzu ta daure tace kasar musu y’a ahtau shawara nabaka nidai bakina alaikum tunda ga ma iya nan sun karaso “bara kaga nasa ita fatimar ta fiddo da Habibu yana can sama uwa duniya “malik ya gyada kai kawai shi kawai yasan abunda ke damunsa amma hajajju ta cika sa da surutun ta baki daya kowa ya gaishe da baba kulu banda hajajju datayi kaman tana wani abu bayan kujerar dake zaune “itama baba kulun wuri tasamu ta zauna tana bin daga malik din har aydarh da kallo kaman yanda oum takeyi said ai ita kuma ta kasan ido kallon yanda suka sauya lokaci gudu suka chanza dagani kasan basu ma san wani abu wahala ba kaman yanda oum tayi expecting “ ganin tayi skin din aydarh ya linka uku kan yarda take da kyaunta ya isa isa yake fitowa darrr a fuska saidai a ido data dan fada kadan wanda a jiki bata fada basai ma karawa datayi “daga yarda take masha Allah kallo daya zakayi mata kasan banda kuka hadda rashin lafiya ma dagani bata da lafiya yarinyar rufaidarh ma taji saboda yanda temperature dinta is high, hajajju ta juyo da kalli oum tace kije ki kira habib din yazo “oum tace to “tafada tana mikewa tabi tawani hanyar daban aydarh dai ta bita da kallo ko kiftawa babu har tashige hanyar dazata kai ka side din abba “tana shiga bayan pillow dinsa wanda yagaji da kyau bedroom tawuce yafito wanda kenan yana shafa cream tana shiga yakalleta “take murmushi yabayana a fuskan shi yace pardon me mai kyau yanzu nake kokarin kiranki tayi masa hararan wasa tana turo baki tace bawani nan naki “abba yace okay I should kneel down before I beg yafada yana shirin yin kneel down dasauri ta tareshi tace no kasan bana fushi da kai duk yanda oum taso boyewa abba damuwanta sai daya lura yace what is wrong wife?ta girgiza masa kai tace baki kayi a parlor abba yace baki kuma ni?ta gyada masa kai zai kara magana ta rufe masa baki tace noo “muje nataimaka ka shirya idan ka fita zaka ga waye

Chapter 45 of 83