Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
daman sunyi da shi yayan formular zaa dinga bawa babyn ita dai ba nononta ba kwara ma yafada musu “dakyar ummi tasamu aydarh takarasa karban shayin “malik na zaune kan kujera yana kallonsa banda murmushi babu abunda malik keyi son da ummi take ma aydarh na daban ne wani kalan so take mata irin na uwa da diya “kwantar da ita tayi ta kalli malik tace ruwan zafi fa? Malik yace akwai a heater cikin toilet din ummi tace jeka can inda su hibba suke kace nace tabude karamin akwatina akwai kayan wankan dana zo dasu sai ka kawo mun “ malik yace tau fita yayi yaja dakin ummi tashiga bayin ruwan masu zafi daidai ayi wanka jego toilet din kaman baa taba amfani dashi ba da alama sabon building ne wurin babu wanda yataba shiga aydarh is the first person daaka fara kwantar da a dakin cikin bathtub ummi ta tara ruwan tafito daidai yashigo dakin rike dawani leda daakayi well packaging yamika ma ummi da hannu biyu “karba tayi tacire veil dinta ta ajiye tashiga toilet din kayan wankan tasaka ciki “dan jim tafito tace kayanta faa?malik yace duk suna can babies bar ummi tajuya tace naga da sabon towel nan jeka ka dauko kayan nata da pads yace tau ummi “tashi yayi yatafi ummi tamatsa kusa da gadon tace yi ahankali ki daure baby ki gwada tashi zaune mu gani aydarh ta lumshe ido ta gyada kaii kokarin tashi tafara ta cije baki ta dai daure din ta tashi zaune ummi tayi murmushi tace masha Allah yauwaa sannu baby ummi tace ko har tashi ma zaki iya?aydarh tagyada kai ummi tace Alhamdulilah tashi tau “kokarin tashin tafari y isai gashi tashi tsaye but kafanta nadan rawa narashin karfin jiki da taimakon ummi suka karasa toilet din “ummi taware sai data tabbatar tama aydarh pure wanka jego tazauna cikin ruwa ta gasa ta kafin tadaura mata towel suka fito duk da this is not the first time da ummi tamata wanka amma takasa hada ido da ummin tsaban kunya yana daya daga cikin abunda kesaka ummi jin kara son aydarh kunyar yarinyar nutsuwan ta dakuma kawaici sun taimaka sosai wajan daura ma ummi son aydarh fiye da yanda take son iyayan ta data haifa da cikinta kan gadon tazauna har malik yakawo kayan nata da uban pads kusan five bags ga pants kusan six sai inner cap hadda socks da sweater da perfume da cream dinta “ ummi taimaka mata tashafa cream din kafin tahada mata pad kwara biyu tasaka mata tabata pant din tasaka rigan dayakawo mata tasaka tasa hulan da sweater ummi ta duka tasaka mata socks din zata kwanta ummi tace tadaure tayi exercise ko dakin ta zagaya”so take tace ina babien tagansa amma kunya take ji hakan nan taji tana son ta gansa “ yayah yace mata kama yake dashi har yagama duk labaran sa dazun nan jin sa kawai take bata da bakin mayar masa “ shigowa dakin yayi hannunsa rike da leda har kwara biyu friuts ne kala da kala sai dayan ledan kuma abincin wani restaurants ne yasiyo suna dishes na all country yasamu mata pepper meat sai grilled meat sabon gashi “ ajiyewa yayi yakalli ummi yace sannun ummi ummi tace yauwa mom dinku fa? Malik yace suna can babies bar din yace aie ko ita da hibban ne sun tafi gida junior fa mura yake dasunyi wanka sun huta “ malik yace kwarai dagaske suma yaran zaa iya tafiya dasu gida tunda they are all fine ummi tace tau Alhamdulilah ita baby fa? Malik yace zuwa dare in sha Allah zamu iya tafi sai nakarasa mata sauran medications din a gida ummi tagyada kai tace tau ba damuwa maganar suna fa kun yanke shawaran suna ne yayi kasa dakai yana shafa suman sa yace eh ummi ansa musu suna ummi nakallonsa tace waya samu su?yayi murmushi yace nine ummi “ummi tayi smile tace inyee ita maman yaran fa?tare kukayi shawaran ko gaban kanka kayi Abdool? Aydarh najin abunda ummi tafada tanemi wuri tazauna kan kujeran dake kusa da ita tayi kasa dakai tana wasa da yatsun hannunta “ wai wasu yara itafa wannan kiran yaran yaran daake nasa ta jin wani kala wai yara har nawa kodai kwara ukun ne? Malik ya girgiza kai yace aie bata da damuwa ummi “ummi tayi shiru kafin ta gyada kai tace mika aka saka musu “malik yarage murya yace babban Muhamad adam sai tabiyun sunanku ne ummi sultana sai karamin shine abba naff ummi tayi wani kalan murmushi tace Allahu akbar ubangiji Allah yama su albarka Allah yaraya su Allah yasa su biyo masu halin Allah yasa duniya tayi alfahari dasu Allah yamuku albarka Allah yaba mamansu lafiyan shayarwa da kuma ikon tarbiyantar dasu Allahumma bareek malik na murmushi yace Ameen Ameen mamaarh Allah yasaka muku da alkhairi Aydarh tasakeyin kasa da kai tace Ameen “ amma lissafin yayi yanzu duk ya kwance mata tunani wallahi bakinta yayi nauyi sai yane take jin haushin wannan bakan masifan kunyan nata datakasa yin tambayar dake ranta in Ummi’s presents bakinta fal zuciyanta fal tambaya amma bakinta yakasa buduwa yayi su “ tayi shiru tana kallon kasa ummi takalli malik tace bude mata abincin tafara ci bara naje wajan mom dinku “har ummi tamike sai kuma ta tsaya tace wai ita baby taga yaran ankawo su wajanta ne? Malik ya girgiza kai ummi tace yau ga shirmen banza tau kan wani dalilin? Malik yace ummi aie baki daya datashinta da zuwanku babu tazara daman niyyana sai tafarka kafin ummi tace tau aie shknnn yanzu taci abinci sai tasha magani bara naje sai nazo dasu malik yajinjina kai ummi takalli Aydarh tayi kasa da muryanta cike da lallashi tace kidaure kici abinci kinji namesake sai ki sha magani sannu ahankali ahankali jikin zai karasa warwarewa ko dakika gan isai daaka sha wannan wahalar kafin yazo duniya said ai nawani yafi nawani “bakaman ke kinyi namijin kokarin nakudar da har uku “still kan Aydarh nakasa bata dago ba “ ficewa ummi tayi dasauri tadago takalli malik tayi raurau da ido yadage mata gira yace what?mike miki ciwo? Tace yanzu har kwara three ne yayah “ malik yatashi yamatso kusa da ita yajinjina mata kaii yace yes cuddle bug this is suchs a blessed Alhamdulilah Alhamdulilah Alhamdulilah mungode ma Allah dawannan kyautar daya manah mamana “a lokaci daya a rana daya yara dayday har kwara three this is very amazing Allah yamiki albarka nagode sosai Allah yasaka da alkhairi “tasa bayan hannunta mai cannula tagoge hawayen dake zubo mata ta jinjina masa kai muryanta narawa alaman zatayi kuka tace masa to yayah waye zai dinga basu nono?yanda tayi maganar har yaso yayi dariya ita da zuciya daya tafada wallahi yasani “daurewa yayi baiyi bay ace ke ai kinyi mai wuyar tunda kin haifa madara zamu cigaba dabasu tagyada mai kai dasauri kaman irin yan yaran nan daake so amma wayau “tayi kasa da murya tace daman aie kafada to yanzu ma kasake maimaitawa ko kasiyo formular ma? Malik yagyada kai yace erh tun ma jiya fa nasiyo har sun far asha but adam is not responding to the milk “Aydarh tayi shiru tace wanne cikinsu? Yace wanda kika fara haifa har bata so ta tuna wani kalan yankewa gabanta yake fadi tsaban yanda bata son tunawar daga ita sai Allahn daya halicce ta kawai suka san iyakar matukar masifan wahalan azabar datasha tasha wahalar da baki daya tayi tunanin fitar da rai daga rayuwa tasa mutuwa zatayi at that stage she even pray for her death da wahalan datasha “ ahankali tace why?malik yawara ido yabude hannu yace wallahi bandai sani ba kuma anduba sa he is fine amma ina ganin ko baya son madara sai natural breast milk “Aydarh tadan kallesa tadauke ido “ bude mata grilled meat din yayi yasan she will like it more than the pepper meat “ already anyi sliced din apple din da peach sai strawberry yamiko gabanta ahankali take ci kaman bata son ci sai dayayi kaman yanda ummi tace taci taci sosai tasha fruits din da maganin ta “ rufaidarh ce tafara yo gaba rike da naff a hannunta daaka musu wanka anchanza musu kayan zuwa wani baby set white da abun daukar dakomai off white ne “sai sulty dake hannun hibba tagoya junior abaya dake bacci ummi ce karshen shigowa rike da adam wanda yanzu ma dakyar tasamu yayi shiru “Aydarh tadinga binsu da kallo dasauri hibba tamikawa malik sulty taje taba Aydarh hug tace masha Allah Alhamdulilah sissa congratulations Allah yaraya manah triplet Alllah yabaki lafiya dakuma lafiyar shayarwa kinyi kokari gaskiya masha Allah Aydarh tayi murmushi tace yasu iya?where is my baby hibba tace wannan sarkin rigiman yayi bacci Aydarh tace erh zaman flight aie babu dadi “ ki kawosa hibba tace no aji da yan kannansa first bakaman sarkin kuka bawan Allah “rufaidarh tayi murmushi tace sannu baby Aydarh tace mom kinzo rufaidarh ta jinjina kai tace dolene aie baby “ sannu Aydarh tayi kasa da kai “ tace yauwa “ummi ta matso tace fara karban wannan bawan Allahn dan baby duk yafi matsowa dan Allah afara bashi muga in sha Allah zaya karba Aydarh data fahimce abunda ummi ke nufi dasauri ta kalli malik suka hada ido kasa yayi da kansa shi bai masan yanda zaiyi ba shifa wasa yakeyi all ce matan dayake ba ita zata shayar da yaran ba “kallonsa take ta yi kaman zatayi kuka so take yayi magana amma taga baida alaman yi don yama dauke kansa yamayar kan yarsa “ummi na kallonta bata gane abunda Aydarh ke nufi ba taga dai tana ta kallon malik kwalla yacika mata ido daura mata yaron tayi a cinya sai lokacin takalli yaron daya bude dan bakinsa ya tsala kuka “ whatttt aie malik tagani sak a fuskan yaron so take tasake kallonsa amma bara ubansa yayi shorting wannan case din first ummi taga Aydarh ko motsi batayi ba balle takama yaron taciro nono tabasa tace basa yasha manah baby kukan nasa yayi yawa kuma duk yunwar ke cinsa nasani “ dan motsi tayi da hannunta sai kuma tasauke kanta tana satar kallon yaron “tagefen ido “ idan ma maganar tayi feeding din yarone bazata iya ciro nono gaban su ba tabashi ai wallahi kunya takeji ita fa ansata tsaka mai wuya rufaidarh tagyara rikon naff a hannunta tace yau ga iskanci kewai ko bakiga yaron nan kukan dayake ba baby? Ummi tace ayi mata ahankali mom “mom tace ba maganar ahankali bane ummi ita komai sai tayi yarinta tau dan ubanta kar tabashi yasha tabarsa ya sike “malik dai kansa nakasa ummi takalli hibba tace daughter kije ki can dakin ki dauko mun feeders dinsu mom kawo mijin nawa kema kije ki huta mom talura ummi so take su fita bata son fadan dake ma Aydarh tamika mata naff din tace tau aie shknnn sai tayi “daga haka mom da hibba suka juya ummi tasamu ta lallaba Aydarh da hawaye yarr yafara mata zarya a kuncin ko fito da nonon wallahi bata iya ba baa tsoron miji yataba ko yasha sai dan bawan Allah dabai san abunda ke cikin duniyar ba “duk ummi ta taimaka mata ga uban hawaye ga yal banzar kunya har aka samu aka fito da right tit dinta “ ummi tanuna mata yanda zatayi tanayi yaron kaman yana jira yawani kama dasauri “dasauri tace ouchhhhh sai ga uban hawaye don wallahi wani kalan zafi taji a nipple din “haka ya dinga sha tana hawaye malik tashi yayi yakwantar da sulty gefen naff da ummi ta kwantar kan gado sadaf sadaf yafice daga dakin kaman wani munafuki Aydarh tafakaici idon ummi tabanka ma bayansa harara har yawuce daman damuwan adam bai wuce na yunwa ba kuma bai ya son formula saidai nono sai ummi tasa ta chanza masa har yasaki da kansa Aydarh tasauke ajiyan zuciya tana lumshe ido ga hawaye share share “ummi takarbe sa tashafa bayan sa da ko 2 mins baayi ba yayi bacci ummi taje ta kwantar dashi “ kusa da sauran wani kalan kyau suka mata sun burgeta sosai a kwancan wai duka yaranta ne ita ta haifesu dagaske “duk zasu dinga cema mama itama she is now a mother?waiii kaiii she cannot believes this ita din nan with 22 ko 23 ma ne yanzu she gave birth to triplets oh wow “su naff ma duk sai dasuka sha kaman zatayi hauka don haushi yanda ummi tasa ta feeding dinsu sukuma sai sha suke as if there lives depends on it (yoo it depends of it manah 🤣) .A ranar akayi sallama basu kwana ba suna karasawa gida sai ga mr joe yakawo su halime da malik yace yaje yadauko su suna shigowa suka rikita gidan da ihu da murna sai daukan yaran su wallahi duk suna ta murna sai jin dadi ake anata tabata yan uku masha Allah malik ma yaki fita dashi aketa zaman jegon ummi ce tsaye kan Aydarh komai ita kema ta , Jego mai kyau da tsafta Aydarh tayi kafin ranar kwana bakwai ta isa isa tazama wata iri har kashe ido take fatanta yayi fresh yasake daura haske kan nata tayi fari tass barakallah tayi kiba sosai masha Allah “ yau daran suna yau su iya zasu iso taron suna “har sun iso suna ciki yanda aka shiri kaman baa wata kasar ba kaman a nigeria sai hidima suke. Tun daga ran da aka haife su har yau idan zaa basu nono sai an shafa fama bata yarda tabada nono gaban kowa har kwara ummi itama tsayawa take don ta tabbatar ta basu din malik kam bawan Allah indai har zaayi feeding dinsu yana kusa sai ansace kallonsa an watsa masa harara “kwata kwata bata son raino ba iyaka a bata yaran tabasu nono a karbe har kwara adam ana barin shi wurinta duk yafi sauran yawan shan nono ga rigima yacika kuka kwata kwata idan dare yaraba zai tashi yadasa da ita da ummi sai triplet suke kwana a daki daya dayan dakin su mom da hibba dasu mariam ke kwana malik ya kwana a parlor yau dasu iya suka iso sai wurin kwanciyar yayi karanci yafara processing samar musu gidan inda yafi nan mom tahana sa tace su da zasu koma gobe in sha Allah ummi ce kawai zaa bari kar yakashe wannan uban kudin “ ko da rufaidarh tayi maganar ama mai lalle booking flight daga sudan Aydarh kwabe fuska tayi tace bata so rufaidarh tasaki baki tana kallonta tace hala kin taba ganin inda akayi mai jego babu lalle ran suna?aydarh ta girgiza kaii aysha tace kiyi hakuri manah auntie basai tazo tayi miki ba Aydarh tayi shiru batace komai ba malik dake can sofa yayi kaman baya jinsu yana dadana waya yadago gently suka hada ido yawani kashe mata ido ta danna mai harara shi dinnan ma bai san haushinsa takeji bane kawai yana cin arzikin su ummi batace masa komai ba gashi kila ma hutu ya dauka wajan aiki don baya fita fa idan ma yafita baya cika one hour yake dawowa ba kunya zai tsatsalaka yadauki yaransa “yanzu din ma naff ne a hannunsa shi aka fara gamawa wanka sauran na can wurin ummi ana musu mariam ce mai taya ta rikesu idan angama ko hibba ko mom ke shirya su “ yace mom ku duba ga kudin flight din nan rufaidarh takalli wayanta aikam ga alert nan tace haba son dandai kudin flight zan biya baice komai ba yayi murmushi yatashi da naff a hannu yawuce daki yace mamana bismillah kaman bashi yayi maganar ba yashige daki kallon bayansa ta danyi bata tashi ba “ rufaidarh tayi shiru tana kallonta taga iyakar gudun ruwanta ahankali tamike tana tafiya kadan kadan wanda tunda ta haihu haka take tafiya da zama ahankali dan ma ummi tsaye take kanta wajan sit bath shiyasa take jin wurin ahankali ahankali yana warwarewa kanta a kasa wai kunya tabude dakin tashiga yana tsaye da naff a shoulder yana jijiga sa tasamu wuri ta zauna kan gadon “ tace gani “yace aie naganki tayi kasa da kai yamika mata naff dake dan korafi yace feeds him first Aydarh tasace kallonsa taga fuskan nan babu wasa ta turo baki gently tafito da tit din yazauna kusa da ita yaron na kamawa ta dan cija lips “ malik yace maganar suna tunda aka saka musu suna baki ce komai bak o baiyi ba dasauri ta girgiza kai tace yayi yayah Allah yayi musu albarka yayi murmushi yace Ameen maman adam “Aydarh tasa hannu tarufe fuska tace lallai kam maman adam tarage murya tace kuma haka mutane zasu cigaba da fadamun? Malik ya jinjina kaii yace eh manah tazare naff tana mayarda nononta tace nidai Allah yayah ah’ah am shy ma self yar karama dani bana so malik yarage murya yace tunda mijinki yamiki ciki kuma kin haihu aie shknnn yanzu kema daidai kike dakowace mace “ tace umm yace kiyi magana manah tace ita oum bazata zo?yadan shafa giransa yace Allah sarki oum “kara take duk waennan mutane basu isa bas ai tazo zata zo definitely but sai after kowa yakoma “Aydarh tace sir kanajin hajiya bay ace wa wai hajajju tace erh ita dai fa kasan sometimes inna bata shiga abunda bai shafeta ba da dai kan auntie hafsa ne wannan malik yace nasani ita hajiyar mi ta maki Aydarh tace wai fa irin su huta dinnan sai nadauki hijab nasaka naje na gaishe su nayi musu ya hanya shine fa take cewa hala har nakoma wajanka nayi wani cikin shine nake fama da hijab ita dai ba ruwanta bazata gantale a hanyar zuwa wannan kasar ba suna “ baba ce ma tayi mata magana kuma ummi da iya duk suna dakin malik yayi dariya yace don’t worried about her kinsan halinta aie suma sun sani rabu da it ani rabon da ko dan kiss dinnan ma shiga tsakanin mu tun ran daran dazaa haifa su damsel ‘tace sulty ne damsel din?yace dawa tace ni manah yamata wani kala da ido yace oh really?tadaure fuska tace pretty sure yace tau madallah “tace kaga idan zaka karbi yaronka ko fita better idan kuma kuna nan ni bara nafita bazaka jamun abun magana ba ace wani abu ni ban son suchs maganganin su inna dan Allah yace babu inda zakije tace dan Allah fa yayah yace yaron nan bai gama sha ba kimayar dashi tamarairaice fuska tace ayyah sir kaga sauran dole nabasu kuma zafi nakeji gashi dana masu zanna tajin yunwa yunwa “kaman mi “ malik yace shiyasa naga ummi bata cika two hours bata maki something to eat bat ace nidai yanzu kadauka yaronka ku fita “yace Allah ko kibasa kona ciro nabasa “ Aydarh takallesa tadauke ido bata ciro din ba hannun yasa yarike ta ya kwantar da naff a laps dinta yasa hannu cikin riganta yafito da boobyn kallonsa take yana kokarin saita naff wurin taki taimaka masa sai ma dauke kai datayi mariam tayi knocking malik yace yes tayi tunanin zai bari ko ummi ce bai bari ba mariam ta turo tayi sallama “kallo daya tayi musu tawani kalan kasa da kaii “Aydarh tashiga shock ganin har mariam tashigo bai bari ba kwalla taji yazo mata dasauri mariam ta ajiye yaron ta kama gabanta tana fita tashige inda tabar halime da rabiah sauran duk suna parlor halime hutawa take rabiah kuma na waya da mijin ta “ rufe kofan tayi halime tabude ido kadan tace haba haba mariam don nahuta nazo nan see how you just bang the as if wani ya kora ki mariam tamatso tace yoo koroni akayi manah rabiah tace aie tsiyar ki kenan bakya magana kasa tsaye tace yanzu naje nakaiwa auntie Aydarh adam daaka gama masa wanka na tarar da yayah dakansa yaciro yana bawa naff halime tayi tsaki tace shine mi tau?rabiah tace bar banza tau wanda shi yayi cikin karewar yafito mata da nono yaba yaro “mariam tabude baki tace tau aie shknnn badamuwa “ ficewa tayi duk suka cigaba da abunda sukeyi wannan tacigaba da wayanta halime takoma tarufe idonta.Dr ibrahim da dr faisal da dr umar sai nr yasir da dazzy yau suka iso cikin daran nan hotel suka kama hadda “ malik acan zasu kwana “ bayan sun zo sun ga babies da matan su duk an gaisa triplet sun sha gifts bana wasa ba wurin kowa na familyn abby yabude musu share a account na kaf companies dinsa da sunan aydarh dakomai dakomai nata “godiya sukayi ma abby yana murmushi dayake vedio call ne yace sai ga uwargida da amarya sunyi anko din suna? Aydarh tayi kasa da kai tana murmushi ta jinjina kai yace gashi kuma naga kaman su sosai masha Allah malik yace saima a fili abby abby yace masha Allah nima in sha Allah bayan suna zan shigo sai mu taho tare da umminku ko zaka barta tabiyo sune Aydarh ta dan sace kallon malik ya girgiza kai dasauri yace aaaa abby daman tasan zaayi hakan shiyasa bata masa ma ranta ba “ Dr hafsa kusan kullun sai takira vedio call sau hudu tana ganin Aydarh da triplets dinta daga ita sai oum akabari har yanzu yanayin jikinta ummi tace tazauna “kafin masu tafi sai dayazo yaganta “yakawo mata wani set din boxes din da latest expensive atampha’s laceses dakuma dubai abayas har motar sai da ya chanza mata hadda car key din yasaka cikin box din motar na can lagos kaman zatayi masa kuka itama zataje yace aaaa tayi hakuri idan ma Aydarh bata zo ba tana jin sauki shi da kansa zaya kaita Washington din sannan fa kudi ya tura mata a account duk nunawa oum “oum tamasa godiya suka tafi ita har tarasa tsakanin ummi da oum wanda yafi kirki kowa yayi bakin kokarinsa da iyawar sa akanta “ . Mai lallan ta iso Aydarh ce first wacce aka fara mawa kalan dai waccan wanda take musu “yau hadda baki maakayi kadan kadan zo kaga kyau dan Allah kunshin yabi skin din yayi luf yayi wani kalan kyau ga gyaran kai anyi an kwance calaban dayayi mata sai tafito zallar asalin mai jegon ta tayi wani fresh kyau masha Allah “kullun sai ummi da malik sun tofe yaran da addua saboda bakin mutane nonon Aydarh nada kyau sun sake zama lukutaye “duk anma kowa lallen cikin su aysha” washe gari dasafe suka hau shirin suna wanda iyakar su ne sukayi sunan su sai few wanda malik yasani a garin suka zo da matan su suna yayi dadi don parlor kusan cika yayi da gifts din Aydarh da triplets kowa dayazo cikin turawannan sai dayayi musu presenting gifts “ Aydarh tayi kyau kyau irin kyau dinnan mai suna kyau wani kalan arna cotton lace tasaka coffee sai golden jikinsa hijab boubou aka mata da straight skirt dr nairobi tazo tare da yarinyar ta “ itama tama Aydarh makeup kwalliya aka mata kalan na turawa “ masha Allah tabarakallah kayan jikin yan uku abun kallo ned asu da maman su da babansu bazaka taba so ka dauke ido daga kallon su ba kowa yayi kyau duk sunji kudi “ kudi da hutu ya zauna masha Allah anyi pictures anci ansha saidai muce ubangiji Allah yaraya manah triplet yamusu albarka “ har dare mutane basu gama tafiya ba suma yan nigeria gobe zasu dau hanya wasu sai jibi rufaidarh ma yau dr usamanta ya iso acan nigeria akama yaran yanka abby cewa yayi bai yarda da dabbobin nan kasar ba shima kuma malik ya goyi da bayan hakan “company da abba keyi a jordan dakuma canada dasunan triplet aka budeshi saboda yace yabasu shi halak malak yasaka ma company komai duk wani profits dama komai yaware a account ana zuba musu “ malik bai san dawani baki zaiyi amfani dashi ba wajan godewa family din nasa ba amma yaga so yaga kauna said ai yace Alhamdulilah don wata kyautar ma tafi gaban nagode saidai na tuba “ yarage sune kawai inna tace azo abude kyaututukan bata fahimce abunda suke nufi ba dabasu

Chapter 81 of 83