Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta hadawa aydarh hannu yasa ya amsa ya juya ya fita daga dakin hajajju ma takama hannun aydarh tace tau asiya nima daga can gidan habibu zan koma kinsan nabaro kano har abada tun ina can watse ba dangin uwa ba na uba, tunda wanda ya kaini yabar duniar ma baki, ummi dai batace Komai ba domin wani zafi take ji a zuciyarta bazata iya jure ganin tafiyar tasu ba. Har suka shigo tashar babu wanda yayi ma wani magana cikin su yau ne karo na biyu data shiga keke a rayuwarta. Here is a piece of advice please 🙏🏼 For you to blackmail someone it will not take you a time? Idan ke kin zubar da mutuncinki or something like that dole sai kinyi ma wata sharri? Mi za ku samu ko mi zaku karo dashi a yi ma wani sharri dan girman Allah? Ai wance yar iska wance bin maza take! Baku da wani shaida ko hujja amma duk idan kika zauna sai kin kira sunan wata kince tayi kaza ai kaza take, and bara na dawo kan matan aure wasu daga cikin su kenan ba kowa ba 👌ke sarkin kishi ke masipapa ai mijina take bi ai mijina take dating to hell with you and your miji , wallahi billahi idan nice wata ke bi mun miji bazan ma bari asani ba tau that means nayi lacking wani abu da har zan bari a san mijina natare da wata awaje,Da wai har wannan darajar take da mutunci igiyar auranki zaki tari yarinya a titi ki nemeta da fada da hayagaga .Bara kiji yar uwa ke daraja da mutuncin auranki zai bare a titi wata kila mijin ma yaji haushi kin fito kamar karya kina hauka a titi da auranshi kanki kinga duk matakin da ya dauka kanki ke kika sani,Dan Allah muji tsoron Allah mu daina blackmailing mutane saboda wani dalili namu na daba,Allah ya shiryamu yashirya manah zuri’a Ameen❤ Yaune karo na biyu a rayuwarta da tashiga keke, har sai da mai keken ya juyo yace“malan ko ba nan tashar ba? Sai sannan malik yasauka tare da maida duban shi kanta, idonta lumshe yake bakinta yayi pink yarr ya tattare wuri daya kamar bata da lapia, girgiza kai yayi sannan cikin wannan muryar tashi kamar boss yace sauko, bata bude idonta ba kuma bata sauko ba kallonta yake ko kiftawa babu baya son raini kowa yasan shi da wannan halin amma ya lura ita kamar girman kai gareta da raini ,bai sake maimaita mata ba har yagama daukar jikkarta da ummi tahada mata da tashi back bag din daya zuba kayanshi basu fi kala shidda ba, sallamar mai keken yayi sannan ya zagayo side dinta yasa hannu ya rike soft hand dinta da sauri ta bude idonta ta watsa su tarr a kanshi shima ita yake kallo ko kiftawa babu kaifin idonshi da kwarjinin shi yasa ta dauke nata idon tare da kokarin janye hannunta daga nashi ,duk da ba rokon kirki yayi mata ba amma tasaka kwarta hannun nata shima bai saki bah, har sai da suka zo gaban motar kano sannan ya rabu da hannun nata, wanda ke lodin motar malik yayi ma magana ya gaya masu garin dazasu ,washe baki yayi yace tau masha Allahu daman wajan mutun biyu kawai ya rage ku shiga sai a dau hanya, kallonta malik yayi sai bin tashar da dakallo take she never come across suchs place ko commercial market bata taba zuwa ba ,in taje super market ma tau wani karamin abu taje purchasing yawanci komai nata na order ne daga wani kasa, Bai ce mata komai ba still hannunta yakama suka shiga motar. Hajajju na kallon rufaidarh tace tau daman wannan kuturun gida na ibrahin ai bazan iya zama ba Allah na tuba, rufaidarh tayi murmushi tace hajajju ai gaki nan yanzu a nan din ko, hajajju tace niba wannan ba cikina babu komai kawo man kalaci nayi, fita rufaidarh tayi ta shiga kitchen oum na tsaye tana slicing fruits da murmushi rufaidarh tayi takalli oum tace,”yan mata ba zama miji nagari yau sai wani jin kanki kike oum tace shin ba dole ba sai kuma ta marairaice fuska tace har yanzu fa abun na damunshi wallahi ban san yarda zanyi ba rufaidarh ta dafa kafadar oum tace ki kwantar da hankalinki uktiee kiyi kokarin sa shi manta komai mu ma kanmu uktiee mu daina tunanin abun a ranmu, in sha Allah uktiee zanyi duk yanda kikace in sha Allah, few minutes suka dauke ta shirya komai a kan wani hadaddan tray komai na abba oum tsaye take kanshi. Cup din shayi rufaidarh tahadawa hajajju ga irish plate guda tayi mata fraying 5 eggs da uban bread hajajju dai sai zufa take hadawa can ta kalli rufaidarh tace yaran nan fa ko waya wannan babu ahannunsu bamu ma san idan zasu sauka a kano ba nikaina lambar wanda na bashi bansan ko mutumin na nan ba ko ya mutu daman dai ya jima yana jinya, tunda tafara magana rufaidarh ta zuba mata ido tana kallo, rufaidarh tace hajajju daman baki san mutunmin ba kika ce kin san sa? Hajajju tayi mitsi mitsi da ido tace tau nan dakika zuba man waennan idanun naki kina kallona Kamar wadda tayi ma sarki karya fa, daga taimako sai abu yazama jafa’I ina nan naga saboda hankalin yaron ya kwanta yasa nace mashi akwai wanda zai tarar a can kanon koh? Rufaidarh dai tayi shiru batace komai domin so take baki daya su yakice tunanin aransu su bar addua da rokon Allahn dasukayi yayi aiki. Wani irin numfashi ya shaka ya fesar sauyin yanayi sauyin rayuwa da rubutaciyar kaddarar dake kudin littafinsu komai ya fara daga yanzu , babu abunda ke mashi amsa kuwa a kunne irin maganar oum ta karshe, amanaci nabaka idan kaci ka manta dacewa kana da wata mahaifiya a duniyar nan. Nan take yaji wani irin kwarin gwiwa da karfin zuciya yayi tawakalli yayi imani da kaddararshi kuma yasa ma ranshi daukar wannan kaddarar,zuwa yanzu jikinta yayi weak da yawa ahankali take tafiya jiri taji yana kokarin debar ta kasan bishiyar dasu ke tsaye tayi luu zata fada cikin zafin nama ya taro ta,tafada jikinshi wuri ya nema yazauna Still tana jikin shi cikin wata irin raunannar murya tace sanyi nake ji , dasauri ya cire rigan sanyin jikinshi ya yafa mata,baisan ta inda zai fara ba baisan yarda zayi ba yana jin duk yanda take kankame jikinta saboda . Saboda tsananin sanyin da take ji , yarasa makama da abunyi, cigaba da zuba mata ido yayi yana kallonta har sannan idonta na rufe bata ma san a jikin da take ba, Assalam matar tace cikin dan yin kasa da murya amsa mata sallaman malik yayi cikin wannan muryar tashi, cike da barikanci matar tace am tun cikin mota nake lura daku kamar batada lapia koh? Tunda tafara magana malik bai dago balle tasa ran zai kalleta har ya amsa, kara gyara tsayuwar ta tayi tace naga kuma Kamar baqi ne ko? wace anguwar zaku, ganin maganar nata yayi yawa yasa malik ce mata “ina zan samu chemists? Indai kemis ne bakada matsala akwai wani babban kilinik nan baya dan anguwarmu ne mai kilinik din, “ kallon aydarh yayi yaga yarda fuskar ta tayi wani sharr kamar batada jini lashes dinta sun tattare waje daya he can’t express how he feels on her shidai yasan baya jin haushin ta kuma shi dai yasan bata burgeshi rainin yarinya yayi yawa and the worst part ma taje tayi abun kunya an laqa masa sharrin da ma yakasa fassara abun sam karamin tsaki yayi azuciyarshi ahankali ya furta I will put common sense into your head idiot(miye abun zagi kuma 🤭😂) gajiya tayi da tsayuwa can tace yallabai ko dai bakaji mi na fada ba? Sai sannan ya tuno da wanzuwar ta a gun, can yace ina ne clinic din? Washe baki tayi tace can babu nisa zata iya tafiya ko na kama ta, Ahankali yace bara na dauke jikkar sai ki taimaka ki kamatan mu je “ ahankali ta bude ido wani irin banzan kallo tayi masa shi da matar dayake cewa ta daga ta su tafi ai ko mutuwa zatayi sai dai ta mutu da dai wannan ta kama ta baisan iya adadin dauriyar da take kenan ba bai san iya adadin karfin zuciyar datakeyi ba wajan duk abubunwa dake faruwa ba tasan babu yarda zatayi ,tasan bata da wani sauran gata a duniya shiyasa ta yarda da ummi lokaci daya taji wani irin kaunar ummin aranta,,”dasauri ta dauke idonta ganin shima ya zuba mata ido yana mata more than kallon datake masu shi da matar dake tsaye a kansu “ this is the second time da tayi abun da ya mugun bata masa rai a tafiyarsu baya son raini bai raina kanshi and yatsani mutun mai irin wannan halin “ cikin isa izza dakuma kwarjini irin nashi da dakakiyar muryar sa yace mata stand up and follow her! Wani irin abun ya tsarga mata a rai kamar tsoro shakka ko mai kenan batasan ya akai ba batasan mi akai ba samun kanta tayi da kokarin mikewa tsaye amma takasa kwata kwata jikinta kamar ba nata ba still kokarin ganin ma ta saisaita numfashin ta take amma ta gaza yin hakan, kamar jira matar take tayi karaf ta kamata, shi kuma malik ya dauki jikkar shi data ta yayi gaba, kamshin jikinta kawai matar ke shaka duk da ba normal turaranta ta fesa ba kuma ba ma kayan ta bane amma pefume din da skin scent din ta nan a jikinta. Wani karamin building suka shiga babu hayaniyar komai sai wasu few mutane dake zaune kan wasu rubber chairs da alama dai wajan reception ne wata nurse ce zaune kan kujera tana attending wani patient, tunda suka shigo ake binsu da kallo duk da wurin bai wuce mutun biyar ba amma hakan ba karamin damun malik yayi basai karamin tsaki yake saki, kowa kallonsu yake da mamaki basu saba ganin mutane irin su ba tau ko daga wata kasar suke oho “malik ya kalli matar ya dauke ido yace ina zan ga doctor? Kallon nurse din da ta saki baki ta maida hankalinta wajan kallon aydarh matar tayi tace ina dr ibrahin din yake marar lapia ce dashi baqi ne naga matar bata da lapia nace masa yazo mu kawo ta nan, murmushi nurse din tayi tace Allah sarki yana ciki yana duba wasu amma ku jira shi kadan, kallonta malik yayi yace it’s emergency asthma ke kokarin tashi ga jikinta is very weak can you talk to him? Tashi nurse din tayi ta nufi office din Doctor,:shiga tayi office din da sallama a bakinta wani matashi ne da bazai wuce shekarun malik ba ya amsa mata dogo ne baki da ka ganshi kaga very decent mutun, kallonta yayi yace is there any problem saratu? Yes sir wani ne ya kawo matarshi and it’s emergency shiyasa nashigo, okay muje “” fita sukayi lokacin malik na zaune yasaukar da kanshi kasa, aydarh dake zaune kan daya daga cikinsu kujerun itama nata idon a lumshe yake,matar da tarako su mai su na’ima itama zaune take tana ta kallon malik shi bai masan tanayi ba, taba shi doctor yayi sannan ya dago kanshi ya mike tsaye gaisawa sukayi “Doctor yace kai ka kawo patient din? Malik yace eh “Doctor yace wacece a cikinsu malik yanuna aydarh, nurse din tashiga da aydarh dakin da Doctor yana nuna mata, kusan 30 minutes kafin doctor yafito da murmushi ya kalli malik yace bismillah muje office yallabai “Doctor ya kalli malik yace matar kace yallabai? Gyada kai malik yayi duk da yaji abun wani kala haka ya daure yace masa ehhh, Doctor yace bawani serious sickness bane kawai damuwa ce dakuma kamar akwai abunda yasa ta shock saboda yanayin ta ya nuna hakan ‘’shidai malik kallon Doctor yake yayi shiru Doctor yace nayi mata allurar bacci saboda mu samu tasamu nutsuwa tana bukatar hutu sosai ,malik yayi masa godiya kafin ya mike zai fita “har yakai bakin kofar Doctor yace yallabai idan badamuwa inda tambaya, malik yadawo ya zauna , Doctor yace amma yallabai ku baqi ne ko? AJiyar zuciya malik yayi ahankali cikin kamala yafara magana yace masa eh mu baki ne cus ban masan kowa a garin nan ba, Doctor yace Allah sarki , ina ne masaukin ku? Malik ya girgiza kai yace daga tasha sai nan kawai muka yo bamu kai da samun masauki ba, Doctor yace oh Allah ya bata lapia Ameen malik yace sannan ya mike yace ma Doctor zaiyi excusing kansa yayi sallarh akwain masallaci a kusa, tare da Doctor suka tafi har masallacin sai jan shi da fira Doctor yake shidai daga eh sai aa idan abun dariya ne yayi wannan miskilin murmushin nasa. Sannu ya jikin? Na’ima tace mata , bata kaunar kallo ta lura kuma tun bayan farkawar ta daga bacci na’ima ke zuba ido tana kallonta duk sai taji ta uncomfortable pad din dake jikinta duk yabace batasan kuma yarda zatayi bak o wanda zata tambaya ba, ga wanka tana son kawa isai ji tayi hawaye na bin kuncinta, har yanzu gani take kamar a mafarki komai ke faruwa, har yanzu bata amsar tambayar na’ima ba kuma Still idon na’ima na kanta kamar tasamu t.v ganin tana hawaye yasa na’ima cewa asha kam sannu wallahi indai taipot ne haka yake mugun ciwo ne taipot wllh daurewa zakiyi ko maigidan naki zan kira maki ko kina bukatar wani abun bata jira amsar aydarh ba ta tashi tafita.”a office ta tarar da malik da Doctor ibrahim zuwa yanzu malik ya dan sake dashi suna fira akan abunda yashafi halin da kasar ke ciki , washe baki tayi tace sannunku yallabai ta farka naga kamar tana bukatar wani abu shiyasa nace bara nayi maka magana, Doctor ibrahim yace oh ta farka kenan, Bayan san son san halin da suke ciki hakan yasa shi daukar bags dinsu ya nufi dakin data ke ciki, can kasa yayi sallamar ko da hankalinta wajan yake ba lallai taji sa ba balle sam hankalinta baya tareda ita, cikin few seconds yakare mata kallo shekarun ta kwata kwata bazasu wuce na maryam autarsu ba amma sam yarda yanayi jikin su ba daya ba, jin alamar tsayuwar mutun akanta yasata dago idonta ta sace kallon shi batace mashi komai ba shima bai ce mata ba, kusan 10 minutes sunyi shiru babu mai magana sai celling fan dake nata aikin kawai ka ke jin sautin, duk ta takura ga wani irin fitsari da take ji kamar zai fito, ganin ba tada mafita ga kunya takeji ta ce mashi tana son pad ko zatayi wanka, sai taji daman tayi ma na’ima maganar, kwata kwata tasan bakinta bama zai iya furta ma mutun kamar na’ima ko da kalma daya ce ba,duk ta zama abun tausai kallo daya zakayi mata kasan batada lapia ba karamin gayu da hutu suka samu muhalli da waje a jikinta ba real definition of beauty classy ce aydarh “kallonta kawai ya ishe ka jin wani abun a rai, still kanshi nakasa idonshi na rufe , kamar zatayi kuka muryar ta tamkar sarewa zallar shagwabar hallita da kuma gata dasuka samu mazauni a murya game da rashin sabo da kuka sanin ta yarda zata furta maganar, tace tau ai ummi ta hada mun kaya ,shiru tayi kuma kamar wace aka daka ta fashe da kuka, wallahi shi mamaki ma tabashi baisan ma mi zai ce mata ba amma ya jinjina zallar yarintar ta sai yanzu ma yakara fahimtar wannan tamkar raino ne ma aka bashi, bai ce mata komai kamar yarda itama ba tasake magana sai kukan da tacigaba dayi kasa kasa, daukar bag din yayi ya dire a gabanta sannan ya juya yafita, nurse din yayi ma magana ta shiga ta taimaka mata ta shirya. Ahankali take shafa masa oily rublet hair din a kai kamar wacce ke shafa ma jariri abu haka take bi ahankali tana tafiyar da hannunta a sumar gently take rubbing mashi man, sanye take cikin wata mad dubai abaya yellow mai haske tayi matukar karbar jikinta sosai kanta babu kallabi sai wani hadaddan hair style da tayi akan,, kamshin jikinta dana jikinshi dana dakin baki daya hadin gwiwa da a.c dake fitar da kwantacan sanyi yahade wajan bada kamshi na musamman mai kwantar da hankali dasa nutsuwa, ahankali ya fesar da iska a bakin shi tareda tashi zaune ya maido ta zauna sosai kan cinyarshi, yadan fada kadan domin har yanzu da sauran tunani abun a ranshi duk da oum tana son mantar dashi komai amma yakasa ,cikin salihar murya cike da tausai kauna dakuma soyayya yace. Yace zarah ina son mu bar Nigeria cus zamana a Nigeria zai haifar man da mumunan ciwo a zuciya na yakarasa maganar yana zuba mata idonshi, ajiyar zuciya oum ta sauke tareda yi ma kanta masauki a kirjin shi tace, babu damuwa abba “duk yarda kace haka zaayi bani da fahimta ni kaina duk abunda yafaru bada son raina ba,bansan ta yarda komai yafaru ba “Amma hakan na nuni da wani iko ne na ubangiji, wani darasi ne na rayuwar dakuma bayanar da gaskia da na shekara sama da 22 ina kokarin nuna ma,amma kayi watsi da hakan, shiru tayi tana sauraron yarda bugun zuciyarshi ke fita, kusan 3mins bai ce komai ba ahankali ta dago kanta tace Abba nasan bayan mu dasu yayah babu wanda yasan abunda yafaru mi zai hana ka fahimce gaskia mai zai hana ka gyara laifin da ka aikata baka ganin Allah ne yaso ka da rahama a faruwar wannan alamarin, tun anan dunia yabaka damar gyara abunda ka aikata! Still Abba was quite sauraron ta kawai yake amma har cikin ranshi sam duk da faruwar wannan alamarin babu abunda ya chanza a zuciyar shi game da yayah ibrahim din da ahalin shi baki day abaya son duk wani labari ko tarihin da zai nuna tsohon asalin shi baya son alaqar da kuma zumunci da zai nuna yan’uwartakar su da abby sam yasa kafa yayi kwallo da alaqar dake tsakanin su yasa cleaner yayi cleaning tarihin da zai nuna asalin ko shi waye, tuni dunia tayi naam da shaharar shi a matsayin mai kudi dan mai kudi jikkan mai kudi kuma jinin mai kudi, tau taya suke tunanin zai iya fallasa gaskiyar tarihin sa?its unbelievable! Ita kanta oum shaida ce baya son abunda yashafi talauci baya kaunar sunan baya kaunar talaka duk abunda aydarh key i akan talaka duk hudubar shi ce duk tarbiyyar sa ce babu yarda oum ta iya said ai kallon ikon Allah, Kamar tasan abunda ke mashi yawo a kai kamar tasan abunda yake rayawa a zuciyarshi yasa ta cewa ABBANARH lokaci yayi dazaka…… da dan karfi ya kira sunanta zarahhhh bygone should be bygone please ! Daga karki sake yi man magana kalar wannan and get ready we are leaving tomorrow ! Bai jira amsarta ba yayi hanyar fita “oum ta bishi da kallo tana jin wani iri a zuciyarta , mike shirin faruwa?ta tambaye kanta duk wani efforts dinsu ita da rufaidarh yatafi a banza kenan? Inalilahi waina illahil rajiun shine kalmar da ta ambata a fili, wannan kuma wata sabuwar kaddarar ce ko mai? Wata zuciya ta gargadeta “ lumshe ido tayi ta bude kafin tace yah rabbil alameen kace man burina yah rahaman kasa nayi nasara kan abunda na shirya yah arrahamar rahimin kasa malik yazamo garkuwa haske da kuma madubi a rayuwar aydarh ya rabbi ka bashi iko da juriyar daukar duk wani kuruciya da shirme nata, yah azeez kasan yarda nake son gyaruwar komai yah rabbil arshi kasa komai ya gyaru cikin hikima da dabarar ka yah Allah. Nurse din ta sake kallon aydarh wannan karon kanta a kasa yake idonta rufe amma ba bacci take ba tayi wanka duk a takure take jin ta har wani kyankyanmin jikinta take ji ( ah🙄abun naki yayi yawa aydarh) asalin abayar ta ce da tafito daga gida tun farko ta mayar domin tak’I mayarda wanda ta cire, ta fada sosai sai asalin kyauwun fuskarta yafito tarr gashin gabanta kanta yayi luff luff kasancewar veil din abayar da ta daure kanta yayi baya “ can nurse din tace please can I asked you ma’am? Bude idonta tayi kamar bata taba kuka dasu ba wani irin haske da kyau garesu mai matukar daukar hankali da fizga, washe baki nurse Saratu tayi tace dan Allah daga Qatar kuke ko Egypt ni nakasa gane da yan wace kasar larabawan kukayi kama wallahi kunada mugun kyau ke da mijinki kai har kama ma kukeyi auran zumunci ne hala? Aydarh dai tayi shiru domin surutun nurse saratu ya dameta ko gane abunda take fada ma batayi,ganin aydarh bata amsa bay asa nurse saratu tace ko dai ke bakya jin hausa amma naji shi mijin naki hausa raddam a bakinsa wallahi daman baya son yawan magana, still aydarh was quite ganin bazata amsa ta bay asa nurse saratu kama kanta tayi shiru tace mata zan fita idan kina bukatar wani abu sai ki kirawo ni bara nayi ma maigidan naki magana yasamu maki abunda zaki ci, daga haka ta juya ta fita, sai sannan aydarh ta bude ido tana bin dakin da kallo. Dr ibrahim yayi murmushi yace kai kam baka son magana sam sai muna labari sai ka fada tunani, ko dai duk halin da mai dakin naka ke ciki ke damun ka nagaya maka babu wani damu ko zuwa gobe ma zamuyi iya sallaman ku, dan murmushi malik yayi yace tau Allah yakaimu “nurse saratu ce tashigo da sallama office din cikin girmamawa takalli malik tace yallabai asamo ma madam abunda zata ci zuwa yanzu alluran sun sake ta nasan ta isa tafara jin yunwa, kallonta yay isai kuma yace tau a ina zan samu wurin siyarda abinci? Da sauri dr ibrahim yace aa abokina bara nayi waya yanzu a ba yaro yakawo muku daga gida “ kallonshi malik yayi zaiyi magana dr ibrahim ya girgiza kai yace aaa babu komai gidan ai babu nisa kuma ance bakon ka annabin ka duk da ba wajena kazo ba amma ai garin mu kazo, murmushi malik yayi tareda shafa sumar kansa yayi kasa da murya yace tau angode Allah yasaka, Ameen dr ibrahim yace tareda fido android phone dinshi yayi dialing contact din da yayi Saving da iya, bugu biyu aka daga cikin nutsuwa yayi sallama daga can bangaran aka amsa mashi yace iya idan rabi’ah na nan a bata abinci takawo mun yanzu, amsa mashi akayi sannan yayi godiya ya katse wayar, Ko 12mins ba ayi bas ai ga wata matashiyar yarinya kamar aysharsu tashigo da warmer abinci kwara biyu cikin leda sai jug da cups biyu a hannu, tana tsananin kama da dr ibrahim koba a fada maka bak asan sister shi ce ta kalli malik ta gaishe sa ya amsa ta, tace yaya ga abinci amsa yayi yace mata sannu, yauwa tace tana satar kallon malik dayayi kamar bai office din dan ko motsi bayayi, duk abunda take dr ibrahim na kallonta. Kallon malik yayi yace gashi sai kaje ku ci don kaima tunda kuka zo banga ka kai komai bakin ka bah, hannu yasa ya dauki kayan abinci yafita zuwa dakin da take. Bayan fitar malik rabi’ah takalli dr ibrahim tace yaya a ina kasan shi please? Wannan ba balarabe bane kam? Ibrahim ya kalleta yace aaa ba indiye ne karewa! Wait miye hadinki da shi? Girgiza kai tayi ta mike tace ni natafi sai ka taso “:bata jira amsar shi ba ta phecee daga office din yaraka bayanta da harara, bayan sun dawo sallarh malik ya kalli dr yace dan Allah a ina ake samun gidajan haya? Shiru Doctor yayi sai can yace idan ba damuwa akwai wani gida can kasan anguwar nan babu nisa gidan mai clinic din ne da a ciki yake zaune kafin a mayar dashi kaduna aiki compound ne sauran parts din akwai mutane wannan ne kawai babu idan ya tashi da yace nashiga na zauna baya son barin shi

Chapter 7 of 83