Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
masa amma inaa “ Hugging dinta yayi very tight kaman ya mayar da ita ciki “yana jin yanda take kuka” Alhamdulilah amare duk sun sauka kowa “gidan ta yayi kyau bana wasa kaf dinsu same furnitures aka musu dr hafsa da rabiah a compound daya suke wanda na dr usama ne doctors estate ne babba mai azaban kyau tacan ma su halime anguwa daban daban suke masha Allah kowa gidan yayi cus duk yaran masu Hali suka aura “Dr hafsa ta dinga nuku nuku a hijab shidai dr faisal yana sane da ita yanuna bai gani ba can yamike yace tau ki kwanta sai dasafe wani sanyi taji aranta ganin zai fita dan dariyan gefen baki kawai yayi yafita. Judge this case “tsakani ga Allah cikinsu waya ja wani aydarh tayi laifi data fada masa all abunda tace?irin mutanan masu masifan kishi daman haka suke “ance iya so iya kishi na yarda da haka nima nagani yau wajan malik da aydarh “nidai anawa tunanin malik shine bai kyauta ba yarinya nata maka biyyaya ba kalan halittar su daya ba amma duk da haka tana hakuri duk don tayi biyayya “duk saboda yan uwatanka”saboda soyayya mi zai saka yayi mata haka miyasa zaice zaiyi aura while yasan yanda take da this kishi “ malik zai yarda yasaki aydarh kam????lets seee! FADIMARH AROUND THE CORNER! Idan tabari asuban yayi lokacin tafiyarsu yayi bata bar masa gidansa ba bakinciki ne zai kasheta “wani kalan sake fashewa da kuka tayi tana sauka kasa daga kan gadon tahade kanta da gwiwa tana wani fixgar numfashi wallahi malik baki daya yazama kaman wani status har wani kala yayi kaman bashi ba yanemi wuri yazauna gefe daya tunda yazuba mata ido yaki janyewa “ganin kukan bayi zai mata ba kuma da asuban tayi tasake tabishi shknn angama da ita should at last bara ta nuna mashi itace macan in this aure gently tamike don ko gabanta bata gani idan tabar mashi gidan shi ko da wani wuri sai tasamu idan ake fitar da ciki a fitar mai da kayansa ko da salmarh ce tasan zata taimaka mata indai tafadi abunda yahada su amma taya zata fara fadawa salmarh sirrin su wanda baki daya familyn babu wanda yasani “ kafanta yayi tsami haka ma jikinta ga ciwon kai kaman kan zai fadi tsaban rashin samun bacci ne kuma wallahi da yabarta da laulayinta ma kawai ya isa bafa bata shan wahala ba kawai take daurewa saboda ganin yanda yake kula da ita bata son tacika complain “ amma duk bai gani ba saboda son zuciya da kai kalan namaza ‘yana ganin tamike shima ya tashi dasauri taja kafanta tabar mishi dakin ta rufe kofan da mugun karfi har sai da sound din yashiga brain dinsa “ bammmmm ji yayi hawaye sun kawo idonsa wallahi zuban su kawai yaji “yadafe kansa yana neman wuri yazauna “ yasa both two hands dinsa ya rufe fuskan shi “tana fitaa tashiga dakinta toilet tawuce ta tara ruwan zafi cikin bathtub kayan jikinta tacire tashiga cikin ruwan zafin ta zauna sai datayi sit bath don maranta ciwo yake mata da zafi wanka tayi tunda tazo duniya tana iya cewa baa taba mata abunda yamata ciwo ba kalan yau daman haka akeji idan wanda kake so yabata maka rai daman ciwo da radadin da zafin da zuciyanka yake maka wallahi ji take kaman ta mutu zai mi fita sauki wai har malik zai dube tsaban idonta “ yafada mata zaiyi aure babu Komai aie har yanzu tana tunanin baya sonta ne shiyasa shiga tayi cikin closet tafito da dogon rigan atampha da pant da bra sai normal hijab ash kalan atamphar ko cream bata shafa hawaye sun ki tsayawa a idonta “bra tasaka da pant ta saka rigan tashafa perfume sama sama tasaka hijab hand bag dinta ta dauka tabude bedside drawer akwai kudi yan 500h kusan guda ten zasu isheta kudin napep tasaka a hand bag din wayanta tadauka taga har karfe biyar na asuba ta jinginar da kanta a bango wallahi batasan yaganta cikin gidan nan idan yashigo duk abunda zai faru said ai yafaru amma dolene sai ta tafi yanzu takalma tasaka ahankali tabude kofan dakin takalli kofan nashi dakin tadauke kanta dasauri wani hawaye nasake fitowa a idonta tasa hannu tagoge dasauri “tasauka daga stairs din kofan main shigowa parlor a rufe take ga duk ankashe hasken ko’ina tanajin kiraye kirayen sallarh asuba without making any sound tabude kofan kusan dai kofan yan gayu bawani kara bane dashi gabanta na masifan faduwa kar ya fito ko tsayawa rufe kofan batayi ba tafice duk sanyin daake nagarin gashi asuba yayi bata dam uba gateman har yabude kofan yafita masallaci wanda ke hade da gidan daman haka yakeyi yabar ma malik idan malik din yafito sai yarufe su dawo tare daga masallacin har rufe idonta tayi taji wani dadi ganin kofan a bude ficewa tayi daga gidan anguwar shiru babu kowa sai kiran sallarh kawai da ake da alama takalmin mutane a kofan masallaci duk suna ciki tadinga waige waige ganin ta ina zata fara samu napep ma bata tsaya ba tafara tafiya daidai ana bude gate din makwabtan su wanda ke kusa da gidanta “fitowa akayi da mota wata matashiya ce wacce bazata wuce aydarh ba likita ce a asibitin bayan gari take aiki yanzu ma call tasamu yasata fita da asuban nan “ full light sai ta tsaya dasauri saboda tagane aydarh,aydarh naganin ta tsaya itama ta tsaya sauke glass tayi aydarh taganeta don sau biyu tana shigowa wajan aydarh tare da sister ta bata wani sakewa dasu sosai by nature haka take kuma hada karin ma malik ke bata son yanmata nashigo mata gida Farida tace lahh auntie cute good morning aydarh tace ina kwana “Farida tace Allah yasa dai lafiya naga kinfito a irin wannan lokacin aydarh tace muna da marar lapia Farida tace asha kam ina doctor faa ganin tambayar ya yi yawa ga daman ranta amugun bace yake aikam tama farida tsawa tace bayanan ganin haka farida yasa taja bakinta tayi shiru tace bismillah ki shigo bude front sit din tayi tashiga batace ma faridar komai ba tajuyan dakanta tarufe ido ita dai farida ta tayar da motar suka hau hanya “ ahankali Farida tace ina zamuje ko juyuwa aydarh batayi ba tafada ma farida anguwar “damugun speed suka hau hanya ita dai farida sai satar kallon aydarh take ta mudubi watau Allah yayi halitta nan “yarinyar idan kana neman real definition of beauriee tau gashi nan watau sai tasamu tashiga jikin matar nan tasan kalan product din skincare take amfani dashi don wallahi karya ne ace bata shafa komai haba daii “suna isa anguwar gaban aydarh ya yanke yafadi har bakin gate din shiga gidajen su takai sai farida ta tsaya tace amm auntie cute shiga zamuyi?aydarh tagyada kai farida tashiga gate din aydarh sai bin gidajan biyu take da kallo tasan idan tashiga cikin gidansu a wannan lokacin batasan iyakar yanda oum zatayi da ita ba gashi mom ma bata tafi ba da wallahi a hotel room zata zauna ayau tayi booking flight din can America Kwara tazauna wajan mom tasan koma miye ita zatayi backing dinta “ lumshe ido tayi ta bude tana tunanin ina zata shiga wata zuciya tace tashiga gidansu malik din kawai tasan ko ummi zatace takoma ba yanzu ba amma tasan oum ko zama bazata bari tayi ba zata komar da ita itakuma wallahi tagaji bazata sake auran bas ai dai idan so na kisa sonshi yakasheta she prefers ta mutu data koma gidan shi maganar ciki kuma dole mane zata samu wanda zai fitar mata dashi kofan gidan su malik tanunawa Farida tayi parking tace thank you feereedarh Farida tagyada kai tace ba damuwa auntie cute Allah yabasa lafiya amma shi doctor baya kasar ne aydarh batace komai farida ta dan tabe baki tace anyway bara na wuce inada patient a asibiti “aydarh tace ohk “tabude motar zata fita ko’ina da haske wuta a anguwar duk anata fitowa zuwa sallarh farida tace amm dan Allah neighbor idan babu damu was ina son number dan jim aydarh tayi takarbi wayan farida na faridar normal 16 ne itakuma 16pro max “Farida sai smile take tana kallon aydarh “aydarh tayi mata waving hannu kafin tajuya “itama aydarh hanyar gidansu Malik tabi tana dako daya gabanta sai ya yanke yafadi rasss tadinga labe labe kaman mai counting steps dinta haka takarasa bakin gate din “ bude kofan taji anayi gabanta yawani kalan fadi har ji tayi ta firgita hawaye sharr ta lafe jikin gate din duk ta rike jikinta takama hand bag dinta tarike kamm “abby ne yafito daga gidan yasha jallabiya white da irin hulan nan tabani kaji hadisi “ shima fari duk da akwai haske sai da yakunna torchlight din hannunsa yace kaii wanene a gun nan waye ne?daurewa tayi ga wani mugun kunya takamata daman wani masifan nauyin abbyn take ji wanda sam bataji na ummi haka “ sai ta fashe da kuka marar kara”abby dai yakarasa inda take yagane aydarh ce ahah salati ya hau yi wallahi sai da yakama kansa kafin ya kashe hasken torchlight din yace lafiya asiya kiyi mun magana miya faru haka ina shi Abdool din miyasamesa wani abu ya hada ku mi miki inalilahi waina illahil rajiun “ aydarh tayi shiru shima abby shiru yayi kafin ta durkusa kasa tadaure muryanta na rawa zata fashe da kuka “tace ina ..k.wa.na abby yace tashi tashi shiga ciki wajan mamanki ina zuwa shiga wajan umminki ina zuwa wallahi kaf abby yarasa nutsuwan shi hankalin shi duk a tashe shiga tayi cikin gidan zatayi knocking kofan ma taji shi a bude takai 5five mins tsaye a parlor “ kafin ta daga kafa tayi side din ummi knocking kofan parlor ummi tayi daga can ciki ummi tace wanene aydarh tace nice ummi jin muryar aydarh yasa dasauri ummi takarasu tabude kofan takamo aydarh ganin yanayin ta yasa ta kamata suka shiga bedroom ummi duk ta rude ta gigice “miya faru minene baby fadi naji ina mijin naki miya hadaku dashi mi yamaki baki da lafiya?ko shine bashi da lafiyar miya faru dake kiyi mun magana baby ‘aydarh ta girgiza kai ummi ta rungume ta ajiki aydarh kam tafashe da kuka tacigaba da kukanta ummi duk hankalinta yatashi “ ummi ta cigaba da shafa bayan aydarh tarasa mi zatayi mata tayi shiru ko kuma tasan abunda ya faru “ ganin kukan yasa yayi yauwaa tace baby aydarh tayi shiru ummi tace ya isa haka kinji aydarh ta gyada kai ta dinga sauke ajiyan zuciya “ ummi tace ki dauke ni matsayin kawarki kanwarki yayarki da kuma mahaifiyar ki “ki fadamun gaskiyar abunda yafaru ina mijin naki lafiyar shi lau?aydarh tasa hannu tashare hawayenta tace erh “ummi tace yana gida?tasake ce mata erh “ummi tace tau miyasa kika fito daga gidan ki a kalan wannan lokacin saboda nasan ba gidanku kika kwana ba tunda ban bar gidan naku ba jiya sai da karfe kusan sha dayan dare feel free and talks to me my baby kiyi magana dan Allah kuma kidaina wannan kukan bake kadai bace akwai ciki ajikinki baa son mai ciki da damuwa kifada mun koma yi zan saurare ki baby “bana son kina wannan kukan zuciyata zafi take baby aydarh tasa hannu tana goge hawayenta amma duk dahaka hawaye sun gagara tsayawa “dakyar dai tasamu tace babu komai ummi ummi tace ko ban shekara dari ba na kwana dari baby nasan ba lafiya zai saka ki zuwa a irin wannan lokacin ba kallo daya nayi miki nasan ba lafiya mi yahadaku har dazai ce ki tafi gida? Aydarh tayi shiru dai batace Komai can ummi ta mike tabude dakin tafita few seconds sai gata tashigo da bottle water a hannunta tabude taba aydarh sai data sha rabi kafin ta janye ta ajiye ummi tace fada kukayi gyada ta kai tanayin kasa da kai hawaye yaki tsaya mata “ganin aydarh bata son fadin abunda yafaru “yasata cigaba da shafa bayanta “tana sauke ajiyan zuciya ahankali ta kwantar da it akan gado tasata tacire hijab din tabude wardrobe tadauko mata inner cap tasaka ma aydarh a kai kafin tasa duvet ta rufe ta tamike ta kabbara sallarh tana idarwa bata tashi daga kan prayer mat din ba “ tazauna tana lazumi tana kallon aydarh hamdala tayi ganin kaman aydarh tasamu bacci wayanta yayi ringing ummi nadubawa taga abby ne dauka tayi yace ta iske shi parlor shi “ahankali ta tashi tafita daga dakin “part dinsa tawuce yana zaune a parlor zama ummi tayi suna facing juna abby yace kinga wani abu yau kuma ummi tasauke ajiyan zuciya tace wallahi kuwaa abby yace tamiki bayanin abunda yafaru ummi ta girgiza kai tace bata yi ba kuma bazan matsa mata ba nasan halinta koma miye tabbas laifinshi ne shi yayi mata wani abu abby yace mufara bincike dai ummi tace kiransa zakayi kaji dalilin dayasa koma mi yafaru zai barta tafito da asuban nan banda Allah yana tsarewa dakuma karfin adduar mu kansu miyake tunanin zai faru kuma ko yanzu ya kuka da kanshi saboda huguma ce kawai zata rabani dashi dan sai nayi karar shi nabarin mun yarinyar tafito a kalan wannan lokacin tamike tafita fuuuu abby yabita da kallo ganin wannan irin masifa watau ya lura yanzu kaf a rayuwan ummi tadauki son duniya da duk wani lokacin tada hankalinta ta mayar kan wannan yarinyar wani babban wuri yarinyar tasamu a zuciyar ummi tazauna Allah mai ikon yasan duk abunda zai faru malik bazai bari tafito kalan wannan lokacin ba saidai idan bai sani ba amma koma miye barin garin yawaye zai nemi shi yaji dalili yazauna aie babban abun kunya ne garesu abba dasu oum su ji wannan labarin banda ma yarinyar na da hankali instead of taje gidansu shine tazo nan tarufa ma mijinta asiri kenan “ .Babu kalan fada da masifan da malik baiyi ma security ba yau kaman zaiyi hauka wallahi daga mutumin har matarsa dolene su baka tausayi yanda malik keyi shi kansa malik din dole ka tausaya masa ganin ma baki daya aie baya cikin hayacinsa “neman wuri yayi yazauna wurin parking space din yahade kansa da gwiwa watau shi kadai yasan kalan halin dayake ciki ayau wallahi kuka ma rahama ne tau shi yanzu ta ina zai fara ina zaije nemanta gidansu ta tafi ko gidansu?duk ciki dawani baki zaiyi musu bayanin sun samu matsala har yayi sakacin barinta tafita akalan wannan lokacin??? Wata zuciya tace masa idan fa bataje gidan ba wani rasss yaji gabansa yayi mumunar faduwa zabur yayi yamike yabude mota yashiga dagudu mai gadi yabude mai yafita da motar mai san a iya speed din dayake tafiya ba shidai kawai Allah yakaishi lafiya shifa duk abunda zai faru yafaru idan ya tabbatar da eh gaskiya tana daya daga cikin gidajan biyu “kaman yasani gidansu yafara shiga “ ummi na daidai kofan shiga kitchen tayu baya dasauri tana masa wani shegen harara yayi saurin kasa da kansa yana shafa sumar kansa cikin tsawa ummi tace masa get out. Yayi baya baidai fita ba kuma bai shigo ba “ummi tace wallahi billahi kafin na bata maka rai kafice kabani wuri daman zan ci mutuncinka mutumin banza mutumin wofi komai yarinyar nan tamaka Abdool is she not your sister yar’uwarka ce fa ta jini idan aka tsaga jininta akwai naka kaima idan aka tsaga naka akwai nata kafada mun yarda kai zakaji idan har daya daga cikin dauda ko umar suka koru aysha ko halimatu cikin sanyin asuba lokacin da babu tsaro da duhun asuba ka ce ta taho gida dan baka da mutunci baka da tsoron Allah “wallahi billahi da wani abu yafaru da yarinyar nan da ban san hugumar daza su rabamu ba nida kai a fadin kasar nan “ko kafita ka kama gabanka ko na tona ma asiri nafadi abunda ka mata kowa yasani kowa yaji kunyatattace kawai “ malik dai kansa nakasa bai masan abunda zai fada ba wallahi wannan wani kalan ruwa ya kwaso ma kanshi”durkusawa yayi kan gwiwan shi yahade hannunsa yace ummi dan Allah ba dani baki tsaya ki saurareni ummi nayi miki bayani ummi tace baka da bakin yimun bayani duk abunda yafaru koma mi kayi mata ko ma mi tayi maka “kabar karamar yarinya da karamin ciki tafito daga gida a irin wannan lokacin saboda baka da tausayi baka da mutunci baka da imani abby dayaji abun yayi yawa ummi bata ma ji bata gani saboda ranta yagama bace gyaran murya yayi ya fito ummi ta kallesa ta dauke ido shi kuma abby yabi malik da kallo duk yayi wani kala shi yasan koma mi yafaru bakar zuciyar malik ce tajawo kuma duk alama da komai yanuna billahi zai iya rantsewa malik aka raba sa da yarinyar nan tau kaman an datse masa jin dadi da walwala na rayuwa ne “ abby ya zauna kan three sitter ya kalli malik “yace tashi malik yamike yataho gently kaman babu lakka jikinshi kaman mai counting steps dinsa yazauna kan carpet yayi kasa da kai “ abby yakalli ummi yace je ki kiramun asiya malama “ummi tayi dan jim tace tasamu bacci abby yagyada kai yakalli malik yace tashi kaje Part dinka ka samu ka kwanta zuwa gari ya karasa haske zamuyi magana “ gyada kai yayi yamike yafita ummi tashige kitchen “Mariam ta bunky dinsu suka taya ummi tahada breakfast yau zasu juya abuja ‘Koda mariam tashiga dakin ummi sai datayi shiru tana kallon aydarh dake kwance kan gadon ummi tarufe duk jikinta tabar iya fuskar ta abude tana bacci kitchen din takoma takarasa kusa da ummi ta rage murya tace lahhh ummi naga auntie aydarh fa a dakinki ummi tace tafarka ne?mariam ta girgiza kai tace aaa she is still sleepy ummi tace Alright suka cigaba da aikinsu “ kunun gyada sukayi sai kosai lafiyayye mai dan banzar kyau yaji kayan hadi sai sukayi frying eggs kawai a dining suka shirya komai mariam da bunky dinsu suka wuce dakin su wanka zasuyi kafin breakfast din don lokacin flight dinsu ma yakusa “ummi ma dakinta ta wuce lokacin aydarh tafarka har tayi sallarh ma tahade kanta da gado tana kan abun sallarh bata tashi ba “ummi tayi sallama aydarh tadago ahankali ta amsa mata “ ummi tazauna kan gadon wajan kanta tace kingama baby?aydarh tagyada kai tace erh ummi ina kwana?ummi tace ya jikinki?aydarh tayi kasa da kai tace Alhamdulilah “ummi tamike tashiga toilet tahada mata ruwan wanka tace shiga kiyi wanka sai kiyi brush tagyada ma ummi kai bata son ta mayar da kayan datacire duk da ko 4 hrs bata cika ba da yin wanka yanzu ahaka tashiga tayi wanka tashafa cream din datagani kan mirror tashafa perfume ta mayar da hijab dinta “ sai ga ummi tashigo da alaman tayi wanka wallahi kunyar ummin take ji matar na masifan kama da malik ta iya kwalliya na manyan mata yanzun ma atampha tasaka gold zani da riga da kallabi hadda mayafi kalan atampha da flat shoe masu dan burauban kyau da tsada “ ummi sai bin aydarh da kallo take har tafada a fuska tayi wani fresh kuma idonta ya dan kumbura duk da baiyi ja ba kana ganinta kasan she cried wallahi “wani kala ummi taji she is highly disappointed a malik data tuno at hours din da aydarh tashigo gidan sai taji wallahi idan bataci burauban malik ba bazata ji dadi ba “ummi tace taso muyi breakfast baby tare suka fita Mariam da bunky dinsu na nan zaune a dining din sai ga ummi da aydarh sun fito “mariam tamike zumbur tafita ummi tabita da kallo flat din malik tashiga yayi wanka yasaka blue din jallabiya sabo dal da a gidan yabarshi yana zaune parlor shi ya rufe ido kaman wanda ke bacci ita mariam ma data gansa she thinks he is sick tayi shiru kafin tasake yin sallama still idonsa a rufe ya amsata tace yayah ina kwana yagyada mata kai ita dai gabanta ma faduwa yake mike faruwa newai ?ahankali tace yayah ummi tace kafito muyi breakfast duk da karya take tadamu da yanayin da gansa dazu duk da bata san abunda yake faruwa ba “yana jin haka yabude idonsa yakalli mariam tasan Abunda yake nufi hakan yasan ta jinjina masa kai fita tayi yabiyota a baya “har sun fara kalacin ummi sai lallabar aydarh take tasamu tayi break din tsakura kawai take sai ga mariam da malik sun shigo kanta nakasa bata ga shigowar sa ba shi kam tunda yashigo idonsa na kanta wani kalan rawa zuciyarsa tafara “wani abubuwa yake ji from noway kanta dan tsayawa yayi bai damu da ummi da su mariam dake zaune wurin ba yakafa mata ido ummi naganin duk abunda yake yi ita fa har mamakinsa take ji wai wannan wani kalan sone tau wai mi ma yahadasu wallahi tausayi yaronta yake bata kaman mi tonuwa datayi tana fushi dashi yasa tunanin ma yabar zuciyarta aydarh kam bata dago kanta ba “ balle tasan da zuwan shi ma “kujera yaja ya zauna “ sai lokacin taji kamshin sa yakama wurin dago ido tayi bata yarda suka hada ido baa kaman wani mugun abu tamike dasauri ta dauki cup din kunun gyadan tajuya tayi hanyar dakin ummi duk suka bita da kallo bakaman malik da ko kiftawa babu mikewa yayi zai bita ummi tama sa wani harara yakoma yazauna jiki babu kwari plate din kosai da egg din da ummi ta zuba mata ummin tadauka ta bi bayanta dashi tana shiga dakin taga ta zauna kan sofa tacire hijab din tana shan kunun kaman bata son sha “ahankali ummi ta ajiye plate din ta zauna tace kiyi hakuri baby kiyi Breakfast din duk ma miya faru ina bayanki kinji kiyi hakuri dan Allah kidaina saka damuwa aranki shi namiji duk yanda kayi dashi sai yamaka ba daidai bah aka Allah yahallitace su tundaga kan kakanin mu har yau baa samu daya daya fita zakka ba “kiyi hakuri koma miye ki fidda shi daga zuciyarki hakanan nida shi zamu gauraya yasan bani da kyau aie aydarh tasa hannu ta goge hawayenta ta gyada kai tace in sha Allah ummi “ummi tayi murmushi tace tau kiyi kallacinki ina zuwa bara naje nakaiwa abbynku kalaci ina zuwa “aydarh tayi kasa da kai tace to ummi “ke banga kin ci abincin ba ummi tayi murmushi wallahi yarinyar babu ruwanta har yanzu zakaga she is still a kid baiwar Allah “tace zanci kinji namesake kifara cin naki dai murmushi kawai tayi jin ummi takirata da namesake “ hmmm!wallahi idan ma zata hakura saboda ummi da abby dasauran sisters dinsa kawai zata yafe masa “amma idan bahaka da saidai ya mutu tagama auran kuma! Ahankali tacigaba da cin kosan kwara four kawai taci taci fried egg din tasha kunun “zama tacigaba datayi tabasa time yafita bata ma son tafita ta hadu dashi ko hasken wayanta ta kunna sai ta bankawa hoton shi dasuke tare harara a bikin mom ne ranar dinner sunyi wani kalan kyau a tare yakwantar da jikinsa a bayanta kaman irin zata goyasa “ yasa both hannunsa holding her waist kaman zaa kwace masa ita “har sai data shiga wallpaper zata chanza pic din tafasa ta wurgar da wayar ta kwanta tayi lamo “ . Abby yace banda hauka tunda kasan bata so miye nayi mata wasan? Ummi tace rainin hankali kam banda rainin hankali wa ke wasa da zancan kishi banda ka mayarda mutane shashashai this is not a reason daza kace ta taho ka bude baki kayi magana my friend tunda aka fara aydarh datayi shiru ta kwantar da kanta a cinyar ummi baa ce tayi magana koda aka tambayi malik abunda yahadasu kawai yafada bai fadi abubuwan datace masa babu yanda abby baiyi ba malik yaki fada baya son yafada wallahi kawai dai yace ce mata yayi zaiyi aure kuma wallahi dawasa yakeyi shine suka dan samu matsala “abby yakalli aydarh yace asiya ta tashi zaune tana sake jawo hijab dinta tace na’am yace miya hadaku keda yayanki miya hadaku da mijinki?aydarh tayi shiru cike da nutsuwa dakuma tsantsar kunya

Chapter 77 of 83