Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kwanta mun a rai tun kafin nasanki aydarh naji ina wani irin kaunanki duk da a rai nayi tunanin har na koma ga Allah bazan taba ganinki a fili ba domin sama tayiwa yaro nisa aydarh sai gashi yau gani gaki,dr hafsa tayi murmushi tace kinga ikon Allah ba? Still aydarh kanta nakasa batace komai ba saboda tasan datayi magana kuka zai biyo baya bata son kuma tayi kuka gaban dr hafsa din,dr hafsa tasake rike hannun aydarh tace kiyi hakuri aydarh ki mance da komai ki dubi rayuwar auranki kawai da mijinki har lokacin da komai zai wuce ku koma wajan familyn ku sai sannan aydarh taji wani irin kuka, dr hafsa tajawo ta jikin tana patting bayanta har kukan ya lafa. Duk gajiyan dasukayi na mota basu zauna ba har sai dasuka gama da duk wani abu a ranan, garin fulani ne sosai can cikin lafiya, Sosai aka karama su,dr ibrahim kau yasha tsiya wajan malik shidai bai biye masa ba, saboda yau gashi ga hibba,bazata wuce shekarun aydarh ba,fara ce marar jiki mai kyau da ita masha Allah, sai da suka gaisa da malik tana tambayar sa ya aydarh ai tayi tunani tare zasu taho dr ibrahim yakalle su yayi kasa da murya yace kema dai kingani dakyar fa nasamu yabiyo ni fa yace garin yayi nisa bazai taho da ita bs kar ta wahala, kuma gashi yakasa barin tunaninta shidai malik bai ce masu komai ba saboda ya lura duk halinsu guda, tashi yayi yace dare yayi fa ka rabu da ita, tawuce ciki muma muje mu kwanta nagaji,dr ibrahim yakalli malik yace naga dai babu wanda ya tsayar da kai anan “malik yace au haka kace tau shknn kafin ya kalli hibba dake dariya kasa kasa yace Amarya sai dasafe hibba tayi murmushi tace tau yah Malik Allah ya huta gajiya idan kunyi waya kace mata bayi fushi malik yayi murmushi yashafa kansa kafin yace in sha Allah. Daki daya aka basu shida dr ibrahim kan katifan ya kwanta bayan ya dauro alwalla yasaka jallabiyan sa ya kwanta, hakan nan yaji ransa na bashi kamar dr hafsa bata zo,duk da yasan kawai maybe tunaninta ne dayayi masa yawa amma sai yaji hankalinsa bai kwanta ba, wayar sa ya fiddo yashiga contacts yayi dialing number dr hafsa anan parlor ta kwanta bayan aydarh tayi tayi da ita su shiga bedroom tace bazata shiga ta kwanta a inda suke kwanciya da malik din ba sai dai tabata bedsheets da pillow ta kwanta anan kan carpet babu yarda aydarh ta iya haka ta dauko mata din, suna nan zaune parlor suna fira sama sama wayar dr hafsa din tafara ringing tana dubawa taga sunan yallabai murmushi tayi kafin ta turawa aydarh wayar tac eke ake nema “aydarh ta dinga bin wayar da kallo kafin tayi tayi accept, Assalam alaikum aydarh murya can kasa ta amsa ma yanajin itace yakoma yayi resting kanshi a pillow, bai sake cewa komai ba itama bata sake magana ba tayi shiru can yace hala baki iya gaisuwa ba?kaman yana gabanta ta wani bude ido kafin ta hade rai murya can cikin throat tace ina wuni “bai amsa ba sai cewa yayi have you eaten? Ta gyada masa kai kaman yana gabanta kafin ahankali tace yes “yace mi kika ci ,tayi shiru sai can tace fruit salad,yace only fruit salad? Yafada kaman irin tayi laifin nan,ta girgiza kai tace ah’ah fa naci abinci bai ce komai bayace sai dasafe ya kashe wayar ta dinga bin wayar da kallo kafin ta ajiye gefen dr hafsa da har tafara bacci, aydarh tamike tace auntie sai dasafe dr hafsa Allah yabamu alkhairi aydarh. Tunda dugu dugu dr hafsa tawuce bayan tashare parlor tayi mopping tass ko da aydarh ta tashi tagama gyara parlor,aydarh tayi mata sannu dr hafsa ta amsa ta,kafin tace bara taje ta gyara gida tayi shirin wucewa clinic,sharp sharp aydarh tagama dafa musu indomie kafin tayi frying egg dr hafsa tashigo yimata sallama zata wuce clinic “aydarh tace nagama breakfast ai bara na kawo kamar ko yaushe kadan taci dr hafsa tayi break dinta kafin ta wuce clinic din, sai da tagyara bedroom ta wanke two toilets din ta gyara kitchen ta wanke plates da warmer din dasuka bata already tana tashi tayi wanka kafin ta dauko books dinta tana dubawa.sai yamma dr hafsa tadawo aydarh na zaune parlor bayan tagama girki, bude mata kofan tayi kafin dr hafsa tayi murmushi tace mrs malik aydarh ta saukan da kanta kasa kafin tace sannu da dawowa dr hafsa tace yauwa y gida? Aydarh tace Alhamdulilah, abinci takawo mata suka ci tare dr hafsa tace aydarh baki son abinci ke kam aydarh ta girgiza kai tace ai nashs fruit,dr hafsa tace fruits ai ba abinci bane, aydarh dai tayi shiru kafin dr hafsa tace wata friend dina ta bude babban salon hadda su spa da lalle baki daya Aydarh tace masha Allah “dr hafsa tace kinga tunda su yallabai ranan Saturday zasu dawo sai muje ranan Friday ayi manah lalle,aydarh tayi shiru kafin tace lalle henna? Dr hafsa tace eh sai muje ayi manah kinga yallabai idan yadawo yaga kafan nan masha Allah yasha lalle ai bazai ganeki ba “aydarh tayi murmushi,dr hafsa ta kalli wayar ta dake ringing kafin tace gashi mai gidan ne bara naje gida na dauko abu sai nadawo. Malik yayi shiru bayan ya amsa gaisuwan datayi masa,kafin yace ina dr hafsa din aydarh tace taje gida yanzu, yace wake yin girki,Kaman tana jiran tambayar tace ni fa “malik yayi murmushi yace dagaske ta gyada kai kaman yana gabanta tace erh. Yace tau yau din mikaka girka? Tace fruits salad nayi sai nayi jallof din shape pasta (macaroni) ,yace inyee tau yayi dadi? Tace yayi fa auntie ma tace yayi dadi sosai yace wacece auntie? Tace auntie hafsa yayi murmushi yace kinyi kokari, littafin ki fa kin duba? Ta gyada kai tace erh naduba, Yace tau sai anjima “tace “to” kashe wayan yayi kafin ta ajiye wayan ta mike tsaye tadawo parlor tana jiran dawowan dr hafsa, knocking akayi aydarh tabude tasan dr hafsa ce shiyasa bata ma tsaya tambayar waye din ba, tana budewa taga inna tsaye tasha mayafi ga uban jikka ta rataya aydarh na ganin inna tayi murmushi kafin tace oyoyo inna “andawo lapia ya hanya? Inna tayi shiru bata amsa Aydarh ba kafin aydarh ta bata hanya tace shigo inna “anan parlor suka zauna kafin tace ina wuni sai sannan inna tace lahiya lau asiya, ya gidan? Aydarh tace Alhamdulilah inna dai tayi shiru ta tsuke baki ta zubawa waje daya ido aydarh ta mike tashiga kitchen ta kawo mata ruwa da abinci ta ajiye, inna ta kalli abincin kafin ta dauke ido,aydarh tace inna lapia? Inna tace duniya tazo karshe asiya aydarh tayi shiru tana kallon inna kafin inna tayi kasa da murya tace fisabillahi yanzu ita hafsa miye ruwanta dazuwa na wajan dangi na sabga? Aydarh tayi shiru bata ce komai ba kafin inna tace tau nida yanzu idan audu na nan ki shiga ki kira man shi nakai kararta wajan shi gaskiya,aydarh tace kiyi hakuri inna ita auntie mi tayi maki? Inna tace rashin mutunci da wulakanci sai wanda ta manta kawai ke batayi mun ba ,ina cikin fameli kawai ta kirani wai nataho ruwa zai mun banna, dayake ita kowa yayi shaidar bata kaunar Allah “ina dawowa gidan babu abunda yafaru “Aydarh tace gaskia ba dadi “ inna tayi kasa da murya tace shiyasa kingani bana shiga abunda yashafeta babu ruwana da ita “yanzu tashi ki shiga ki kira mun audu ya bige Mata wonin,babu ruwanta da rayuwata tunda nima bana shiga rayuwarta “Aydarh takalli “inna” tace ki yiakuri baya nan ma “inna tayi shiru kafin tace yana ina shi audun? Aydarh tace sun tafi auran Doctor ibraheem “ inna tace wanene haka kuma?aydarh tace wanda suke aiki clinic daya da auntie hafsa inna tayi shiru tace ibrahin wai? Aydarh tace erh shi, inna bata sake magana ba ta cigaba da cin abinci ta, har tagama kafin ta kalli Aydarh tace hafsa din tazo nan?aydarh tace erh amma yanzu ta tafi zata dawo anjima inna ta tabe fuska tayi yi shiru.malik yace tau ai baki daya zamu tafi ba?dr ibrahim yayi shiru kafin yace eh ai an riga da anyi jere so babu need din kuma ace hadda wasu yan rakiyan amarya,kawai da ita kawai zamu tafi malik yace tau Allah yakaimu asabar din “dr ibrahim yace Ameen “ , da sallama yaron yashigo hannu shi rike da jug da cups ya ajiye kafin yace ina wunin ku? Dr ibrahim yace lafiya lau malik ma ya amsa, can dr ibrahim yakalli malik yace naji baka kira, ta ba yau malik yayi wani murmushin gefan baki kafin yace ai nasan yanzu safiya ce dr hafsa na clinic ita babu waya hannunta “ dr ibrahim yace eh haka ne dazu nurse saratu ma takirani malik yace ohh, ringing wayar malik tayi number ce ke ta kiransa tun jiya baiyi niyyar dagawa bas ai kuma yadaga yayi sallama daga can aka amsa cike da yanga tace ina wuni ranka dade bai gane mai magana ba hakan yasa shi cewa lafiya, kafin tace ya nasarawan? Yace Alhamdulilah “kafin tace sunana rabi’ah kanwar dr ibrahim abokinka malik ya dage giranshi kafin babu yabo babu fallasa yace oh Allah sarki ykuke? Tace Lafiya lau alhamdulilah kafin yace ga ibrahim din,dasauri rabiah tace aa bashi nake nema ba kai nake nema daman nakiraka naji ko ranar daurin auran dawuri zaku taso saboda ayi muku girki dawuri saboda abokanan ku kamar bai gane tambayar datayi masa ba “ yace okay “ tasake cewa dawurin zaku taso? Ehhh kawai yace mata kafin yakashe wayan tacigaba dacewa hello hello taji shiru takalli bilki tace yafa kashe wayan bilki tace ai Alhamdulilah tunda wahalar mu bata tashi abanza ba daman malan yace ko sau dayane kukayi magana dashi shikenan aikinmu yaci,rabiah tayi wani irin tsalle kafin tace Wayyo dadi waya ga rabiah a matsayin matar bawan Allahn nan kafin ta mike tsaye tayi wani juye tana fari da ido, sai kuma ta zauna tana kallon bilki tace bilki matarsa fa?bilki ta tabe baki tace tau ke miyayi ruwanki da ita? Rabiah tawani zaro ido kafin tace baki da hankali bilki baki da kan gado kin kau san yarda take wannan yarinyar? Wllh ganin kanki zaki dinga yi biri idan kina kallonsa shida matarsa wallahi,kinga duk kyau yayah ibrahim dashi yabiyo iya ko?tau komawa yake wani kwa’do kwa’do bilki ta babake da dariya tace amma fa rabi baki da mutunci yayah ibrahim din?rabiah ta saukan da ajiyan zuciya tace bazaki gane bane bilki wallahi ko a mazan indian flim ban taba ganin mai irin haduwar shi ba kin ga tsawon sa kam?kinga fadin sa kam?ke Wallahi kalan fatar sa ma kawai ya isa ya ruda mutun bama kiran jiki ko kyaun fuska ba wand ani ban ma san yarda zan misilata miki kyaun sa ba, bilki ta saki baki tana zara ido tace kai haba ? Ita fa matar? Rabiah ta tabe baki,kafin tac eke wannan yarinyar fa tsoro zata dinga baki ban taba ganin abu mai kyau irin taba ke billahillazi ban iya ma hada ido da it ani kwarjini take mun ga isa raini hankali da shegen girman kai wai kinji muryarta da yarda take tafiya bala’In nan “bilki dai sai binta takeyi da kallo tace Allah natuba rabiah kuma shine kike son kai kanki inda Allah bai kaiki ba?kiji yanzu fa tsabar girman kai da isa ko sallama bai maki ba ya katse kira ke ko amsar kirki bai baki ba ‘anya rabiah bazakiyi ma kanki fada ba? Ki fta harkan su kiji yarda kika bani labarin abayan jikinta fa kika ce hannunta hadda diamond rings biyu ga dayan English gold kin kau san ko a can kasar wajan sai babban mai kudi ke siya?rabiah ta mike tsaye tayi ma bilki wani kallo tac eke Wallahi ko ma mi zai faru sai dai yafaru amma idan kika ga baayi auranmu dashi ba sai dai idan mutuwa nayi ko shi ya mutu, bilki ta rike baki tace tauuuuuuuu ban taba sanin abun har yakai haka ba yanzu ki tashi mu wuce kasuwan yarda zamuyu cefanan da wuri har mu hadu ma iya danata wanda zasuyi na wuni,rabiah tace tau shknn mutafi sai mu siyo kayan sobon ma baki daya tunda malan yace a zuba masa maganin a sobo bilki ta dau mayafin ta tace tau mu wuce kinga daga nan ma sai muyi wankin kan a daura man bakin lalle tunda munyi jaa rabiah tace tau shknn mu tafi. Dr hafsa tace kinga yau nace mata zamu zo,aydarh tace erh ‘dr hafsa tace idan muka je can aka saka miki lallan sai na warware miki calaban a wanke maki gashin right?aydarh ta gyada kai kafin dr hafsa tace tau ki shirya tunda munyi breakfast basai munyi lunch a gida ba a can munyi nima bara na shirya nadawo yanzu inna ta wuce gidan iya,aydarh tace ina ne haka?dr hafsat ace ohh gidansu dr ibrahim wajan biki sai angama biki tadawo nidai sai gobe in sha Allah wuni kawai zanje aydarh tace Allah yakaimu dr hafsa tace Amin kafin ta mike tace sai nadawo kiyi sauri ki shirya kema,aydarh tayi murmushi tace right now auntie dr hafsa tayi murmushi, dr hafsa na fita tashiga tayi wanka kafin ta fito ta shafa vaseline da powder kadan sai kajal a idonta tasaka lipstick kadan shima kafin ta dawo dinki da tabaro gida sanye dashi a jiki yarda fitted gown din ya zauna a jikinta sai taga kamar na yau yafi na kullun kafin ta shafa perfume ta fito da well iron baby pink din hijab dinta ta ajiye kan katifan dan kwallin kayan ta dauka ta daura shi akai masha Allah “ knocking kofan akeyi tayi tunanin dr hafsa ce tafito bata ce waye ba kawai ta bude kofan, tunda ta bude suka zuba mata ido kamar sun samu cartoon kallon su tayi kafin tace ku shigo Wallahi bilki duk tunanin aydarh bata kai kyaun haka ba duk sai taji sun muzanta duk yarda suka taho suna wani yauki, bilki dai takasa dauke idonta akan aydarh ta dinga kallonta ko kiftawa babu ga wani masifan kamshi dake neman zauta su,Rabiah tace sannu kin gane ni ai ko tafada tawani irin fizga kaman irin yan local champions dinnan (yan ghetto idan zasuyi abun yan gayu lol🤭) aydarh tayi wani irin abun da ido cike da isa ta tsaya bakin kofan ta rike Handle din ta girgiza kai bata ce komai ba kafin rabiah tace sunana rabiah kanwar dr ibrahim abokin yayah malik ,aydarh tace ohh ku shigo ta basu wuri takalmin su suka cire suka shiga yarda aydarh ke tafiya bilki ta dinga bin da kallo duk ta sha jinin jikinta da niyyarsu sai sunyi abunda zai ma aydarh ciwo tun yanzu tasan rabiah naso malik, kitchen aydarh tashiga zata kawo musu ruwan rabiah nata wani tabe baki bilki ta dafe kirji tace rabiah see shape dan Allah wai kinga yarda take tafiya kiji maganar ta fisabillahi,rabiah ta bangawa bilki harara ta dauke kai,fitowa tayi hannunta rike da plate din ruwa sai fruits da tayi musu slicing bilki ta washe baki tace ina wuni bamu gaisa ba babu yabo babu fallasa aydarh tace Alhamdulilah “ rabiah dai kamar zata mutu dan bakin ciki,kamar zai kasheta, aydarh tawuce bedroom tayi zamanta,kusan ten minutes suna zaune bilki nat asha kankana ita dai rabiah ko abu daya bata dauka ba, knocking akayi aydarh naji adduan ta daya dr hafsa ce domin haka nan taji batasan zaman su a gidan,fitowa tayi walking slowly ta isa bakin kofan kafin tace waye? Dr hafsa tace nice budewa aydarh tayi kafin tace auntie tun dazu nashirya fa, dr hafsa tace sorry sai danayi ma babyn neighbor din mu allura aydarh tace eyyerh kafin ta bata hanya suka shiga parlor dr hafsa ta dinga bin rabiah da kallo kafin tace rabiah ,rabiah ta kalli dr hafsa kafin tace na’am ina wuni dr hafsa tace lafiya bilki ma ta gaisheta ta amsa ranta fal mamakin abunda yakawo rabiah gidan aydarh tace mutafi? Dr hafsa ta gyada kai kafin Aydarh ta koma bedroom ta dauko hijab din tabude wardrobe ta fiddo da 5k din da malik ya saka mata,Still basu tafi ba suna gani aydarh ta fito rabiah ta mike bilki ma haka rabiah tace sai anjima idan munyi waya da yayah malik din na fada masa nazo, dr hafsa najinta tayi shiru aydarh ma haka kafin tace sai anjima suka fita, suna fita bilki tace wai Allah billahi kawata banyi tunani aie ta kai haka ba rabiah tace hmm nima sai naga Wallahi kaman ta kara wani abu bilki tace ko ciki gareta?rabiah tace nima shi nake tunani kiji structure dinta Kamar cikin ta kamar bata sa masa abinci amma ji kugu tafiyan nan maybe ba da biyu takeyin ta Wallahi bilki tace bawani da biyu haka take ajin ta har yayi yawa ma wallahi ahh. Dr hafsa tace tau muna ta shiri baki tambayi yallabai ba, aydarh ta zaro ido tace ah’ah fa,dr hafsa takalleta tace aa fa mi?tayi kasa da kai tace zai hana ne,dr hafsa tayi murmushi tace ohhni aydarh kullun ke kaman yarinya idan yahana ai sai a hakura amma kin taba ganin inda mata tafita ba da izinin mijinta ba? Aydarh tayi shiru kafin dr hafsa ta fito wayarta daga cikin handbag dinta tace bara nakira maki shi sai ki tambaye sa, dialing number malik tayi har ya kusa katsewa kafin yadaga batayi magana ba ta mikawa aydarh wayar, sallama yayi aydarh ta amsa yana jin itace yanemi guri yazauna yayi shiru yana jiran tayi magana itama shiru tayi kafin takama gefen hijab dinta tana wasa da shi kafin tace ina wuni voice dinta very slow and innocent yace lafiya lau,tayi shiru kafin yace talk,ta tura baki kaman irin yana gabanta tace henna “jin abunda tace yasa shi maimaitawa dan ba wai yagane bane yace henna? Sai sannan ta gyada kai tayi kasa da murya gabanta na faduwa kar yace bazata je ba kaman waccan ranan tace salon zamuje nida auntie daga nan ayi manah lalle takarasa maganan kamar mai shirin kukan murmushi yayi kafin ya girgiza kai yace tau ba auntie ta mikawa dr hafsa wayan da tun dazu take kallon ikon Allah wannan shagwaba har ina su yan gayu masu kudi komai nasu daban ne,wayan ta karba tayi sallama kafin ta gaishe bata ji abunda yace ma dr hafsa ba kafin tace aa yallabai abarshi wallahi babu damuwa,sai kuma tayi shiru tace tau shknn Allah ya amfana,sai datayi dialing acct digits dinta kafin ta tura masa,ta kalli aydarh tace cewa yayi na tura masa acct number yasaka kudin salon din Aydarh tayi shiru kafin tace to 10k yasa dr ibrahim yatura masu saboda shi bai da acct number yanzu suna shigowa dr hafsa tace masha Allah ya tura 10k aydarh tace to mutafi kafin kuma ta mikawa dr hafsa kudin hannunta tace gashi ai nasa 15k ma bazai isa ba dr hafsa tawara ido tace kai ai 3k ma ya isa aydarh da mamaki tace 3k kuma?dr hafsa tace aaa ai mu daku ba daya bane mu na mu babu tsada kai ta girgiza kai batasan lokacin da tace 35k ne henna kadan a nails sai salon hakane bill din,dr hafsa tayi murmushi tace ina gani a ig aydarh ai ba daya bane da namu aydarh tayi shiru kafin su fita sai da suka rufe kofan part din kafin suka fita,sai dasuka shiga keke kafin dr hafsa tace daman kinsan rabiah ne? Aydarh ta girgiza kai kafin tace sister dr ibraheem ne right?dr hafsa ta gyada kai kafin tace mi yakawo ta? Aydarh tabude hannu alaman batasani ba shiru dr hafsa tayi kafin tace datace idan sunyi waya da yallabai zatace masa sun zo shi ya aiko su? Aydarh tace I didn’t even know kawai ganin su nayi sun shigo, dr hafsa tace basu da hankali yaran nan at all bansan abunda ke damun su ba, aydarh dai tayi shiru har bakin babban plaza mai keken yayi Parking suka sauka dr hafsa ta biyasa kudin kafin suka wuce cikin plaza suka shiga wani irin faduwa. Wuri suka samu bayan Sadyyyy tayi welcoming dinsu cike da mutunci,tight friend din dr hafsa ce shagon babba ne mai kyau akwai komai a shagon, sadyy tayi murmushi kafin tace kawata ina aka samu balarabiya ne?dr hafsa ta girgiza kai tace gata nan dai kina gani she is my sister sadyyy tace Allah sarki kafin ta kalli aydarh da fara’a a fuskanta tace sannu fa aydarh ta mayar mata da murmushin tace sannu “dr hafsa takalli sadyyy tace jaa da baki zaayi mata lallan ni black kawai nakeso sadyyy tace tau shknn salon fa? Dr hafsa tace shima za’ayi afara yin lallan shi keda wahala,cikin few minutes aka hada komai kafin aka fara zanawa aydarh hadaddan flower a kafa, mai azaban kyau simple style ana farawa dr hafsa tafara warware mata calaban there are experts shiyasa ba awani wahala ba aka gama jan yayi kyau sosai sai daya fara sha kafin sadyyy ta dinga bin rings din hannu aydarh da kallo aydarh na lura da ita batace komai badai dr hafsa na janta da fira sama sama, kafin sadyy tace ki cire zoben sai ayi black din aydarh ta gyada kai kafin tasa hannu tafara cire rings tana gama cirewa ta hadda duk three din ta mikawa dr hafsa karba tayi tasaka cikin handbag dinta kafin tace cigaba da labarin datakeyi, sadyyy tayi murmushi tace kawata ban taba wa wani lalle yayi kyaun haka ba Wallahi dr hafsa tace dan Allah fa masha Allah aydarh dai murmushi kawai take,sadyyy tasaki baki tana kallon dr hafsa bayan tagama warware ma aydarh calaban gently tasa hannu ta shafa gashin aydarh kafin tayi kasa da murya tace Allahumma bareek” yanzu nan wai gashin nan salon yake bukata? Dr hafsa tace haka yake wannan gashi sai ki dinga ganinsa kamar a gyare kullun “ sadyy tace amma baki jima dayin salon ba right? Aydarh ta girgiza kai kafin tace yajima,sadyyy dai tayi shiru tana kallon ikon Allah, tun shigowar su taso tagane aydarh sai dai tayi shiru tarasa ina ta taba ganinta, can takalli dr hafsa tace kawata kina shiga page din salmerh malami right? Dr hafsa tayi murmushi saboda tama san abunda sadyy zata fadi kafin tace ehh ina shiga sadyyy ta rage murya tace dan Allah ba suna kama da wannan yarinyar datake posting ba dan dai wannan tafi waccan haske da giba yarinya dana nuna maki hillis din nace miki a million kadan ke babu did you remember? Dr hafsa tayi saurin cewa ehhh natuna sadyyy “ sadyyy tace Wallahi kaman ita, dr hafsa ta kalli aydarh da kanta ke kasa bata son labarin yayi tsawo saboda ta fahimce labarin kaman irin rauni aydarh ne kar abunda yafaru jiya yafaru yau kar daga wannan labarin su sake taso mata inda yake mata ciwo, ta dinga irin kukan datayi jiya,dr hafsat ace ehhh itace kawata sadyyy tawani gwallo ido tasaki hannun aydarh tace ki rantse da martabar Allah dr hafsa tace ai bama wannan wasan, sadyyy tayi shiru tana mamakin abunda yakawo nan din ‘shiru tayi kafin tace Allah sarki “tana kallon aydarh kafin tayi kasa da murya tace ki godewa Allah you are more than fine you are more than beautiful kinfi kyawu kyau , dr hafsa tayi murmushi tace awwww sadyyy kice masha Allah yanzu dai ayi sauri agama lallan Saboda mu koma dawuri let her makes some preparation for her husband a gida “sadyyy tace miji? Is she married dr hafsa ta gyada kai tace sure “sadyy da bakinta yak’I rufuwa saboda murmushi tace masha Allah congratulations dear Allah yabaku zaman lafiya da yara nagari aydarh tace Ameen ahankali Still bata dago kanta ba, sadyyy tace kawata amma bata haihu bako? Dr hafsa tace ehh sadyyy tace daga waje zai dawo mijin saboda na lura kamar itama tafi zama waje, dr hafsa

Chapter 20 of 83