Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
94 / 121
ma 'ya ta ce ai, na gode Aminullahi, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi" Viper ya ce "Baba da ka yi haƙuri da kukan nan haka, saboda su ma su samu ƙwarin gwiwar yin haƙuri, mu gode wa Allah kawai" Ya jinjina kai yana maimaita Alhamdilillah. Baba ya din ga shafa kan Nabila, amma hawayensa suka kasa tsayawa. Zakiyya tare da maman hafsa su ka shigo ɗakin da sallama, su na kallon yadda ya saka su Nabila a gaba yana kuka. Viper ya na ganin Zakiyya ya haɗe rai, tamkar ya ga abin ƙyama. Su ka zauna su ka din ga surutai marasa ma'ana, marasa tushe balle makama. Tare da taya su kukan cike da makirci. "Baba ina hafsa?" Nabila ta tambaya da kyar. "Ta je gidan kakaninta da su ka haifi mahaifiyarta". "Baba shikenan ban san jauhar ba, ba kuma zan ganta ba, ban san mama ba, ita ma kuma ban santa ba, mun rayu a wurare daban-daban, ba mu san juna ba" tayi maganar tana sake fashewa da kuka. Cikin sigar rarrashi ya ce "Hakan hukuncin Allah ne, ki yi haƙuri, mu masu tarin laifi ne a wurinki, mussaman ni, na san ni ne baban mai laifi, duk da major ma mai laifi ne, bai kamata ƙiyayyar da yake yi mini ya sanya, ya nesanta ni da ke ba, ya kawo mini yarinya amma bai kuma waiwaiyarta ba, amma Alhamdilillah na ji dadin yadda ya kula mini da ke" Viper ya numfasa ya ce "Baba yakamata mu koma haka, da su" Baba ya ce "Aminullahi, dan girman Allah ka bar mini ita" "Ka yi haƙuri, ai aikin gama ya riga ya gama, tun da har komai ya riga ya bayyana, sai da na saka hannu na ɗauki excuse sannan na fito da ita, shi ma bisa uzurin aiki za ta yi, kuma ka ga a hannun Abba aka yi yarjejeniya a ka ɗauketa, da niyyar ba ta kariya, har a kammala shari'ata, addu'ar ka muke fata". "Yanzu ka na nufin mijin 'yar uwatta take karewa, Allah al-hakimu, Allah ya bayar da nasara, yayi muku jagora dukkaninku" Su ka amsa da Amin gaba ɗaya. Baba ya ce ya bari su ci abinci, Viper ya ce "Lokacinsu a ƙididdige yake, idan su ka saɓa akwai matsala" Har gaban mota ya rako su, yana rungume da Nabila kamar zai mayar da ita cikin sa. Su ka je bakin motar, ya riƙe hannun sumayya, ya riƙe na Nabila, ya kasa tsayar da hawayensa, ya kalle su ya sake fashewa da kuka ya ce "Ku yafe mini dan Allah, ku ci gaba da haɗa kanku, Allah ya yi muku albarka, Allah ya jiƙan mahaifinki ke kuma Allah ya jiƙan mahaifiyarki da jauhar" Su na kuka su ka shiga motar, su ka ja, su na tafe a hanya, Viper bai rarrashe su ba, dan ba wani ƙwarewa ya yi a hakan ba, ya yi musu shiru, su ka yi ta kukan, ya ce a fara kai sumayya gida, sannan su koma barrack washegari sai su je wurin su ramma. *** Major ya sha mamakin yadda Nabila ta nuna fushi take yi da shi, taƙi saurarsa. Mama kuwa sai ziga shi take yi, ta ce "Dama ga ubanta yaushe za ta saurare ka, ai kai ka gama yi mata amfani kuma, shiyasa tuntuni da yaranka ka kama, da ya fiye maka" shi dai bai furta komai ba, amma abin ya din ga cin zuciyarsa. Rahila ma aka sallameta daga asibiti, bayan an yi mata ɗorin karayar hannunta, sai da Abbu ya dage ya ce sai Abba ya bar masa gidansa, aka kaɗa aka raya ya ce ba zai ci gaba da riƙe shi ba, idan kuma ta dage sai ya zauna, to sai dai ta bi shi su bar gidan. Shahida ma ta dage a kan raba aurenta, da fari Abbu bai sani ba, amma bayan ya takurata, da ta gaya masa bai tausayawa halin da rahila take ciki ba, yayi mata tas, ya ce sai an raba auren, ba za a saka masa 'ya a halaka ba. *** Sumayya ta labartawa ummanta abin da yake faruwa, sumayya na ce mata jalingo, ummanta ta ce ta san mahaifin Nabila, amma ba wani sani ba, ta dai san abokin aikinsa ne. Madam halima ta gaya wa Nabila Viper ya zo, yana jiranta su fita. Kallo ɗaya ya yi mata, ya san ba ta samu isasshen bacci ba, fuskar nan babu walwala. "Ina kwana" tayi maganar a hankali. Ya tsura mata ido, ita kuma ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Akwai sauran damuwa ne? Kin haɗu da mahaifinki ba shi ne fatanki ba?" Yayi maganar yana kallon ta. Ta girgiza masa kai. Ya ce "To me ya yi saura kuma?" "Kewar yar uwata, da tunanin yadda zan daidaita Baba da Abba, kowanne ya na da muhimmanci a gare ni, amma Abba ba zai saurare ni ba, saboda Nasir ba zai daina ziga shi ba, saboda haushin tsaya maka da na yi, zai ta ziga shi a kan lallai ya yadda kai ka kashe jauhar, ba ni da gaskiya ina tsaya maka" "Ƙalubale ne ma hakan, amma yakamata tun ba yanzu ba ki san kuka ba magani bane ba, na san duk ni ne silar komai, shigowa ta rayuwarki, ki yi haƙuri" "Ba kai ka shigo rayuwata ba, ni na shiga taka, ko in ce ƙaddara ce, amma in sha Allah zan yi iya yi na, sai an hukunta wanda su ka kashe 'yar uwata, ku ma na tabattar da an kwance sarƙar da aka sanya wa mijinta alƙawari ne na yi wa kaina" ta yi maganar tana share hawayenta. Ya jinjina kai ya ce "Allah ya ba da sa'a" "Amin" har ya yi gaba zai fita, ta ce "Viper" ya tsaya ya waiwayo. Ta ƙarasa gabansa ta ce "Ina son ka ji abin da na ji a lokacin da na rungumi mahaifina, ina son ka yi amfani da nasihar da ka yi mini, a kan kanka. Mahaifinka yana da muhimmanci a rayuwarka" "Wannan ni ya shafa, ba ke ba, dan haka babu ruwanki a ciki" Ta ɗan yi murmushi ta ce "Ina roƙonka ne a matsayina na ƙanwarka, ba lauyar ka ba, ina fatan ka kasance cikin rahamar Allah kamar yadda nima ka ankarar da ni nawa kuskuren" Ajiyar zuciya ya yi, ya fice ta bi bayansa. Haka kurum su na tafe a mota, yake tunanin da gaske yanzu Nabila a matsayin yaya ta ɗauke shi kawai?. Harabar wurin 'yan sandan cike da motoci. A can su ka tarar da sumayya, mahaifiyar ramma ma ta je wurin ita da ramma, Alhaji mu'azzam ya saka an kai su. Nabila tana matuƙar jinjinawa gudunmuwar da Alhaji mu'zzam ya ba su, ya cancanci yabo da godiya, amma goga Viper hakan ko a jikinsa, balle ya nuna masa yabawar sa da jin daɗin sa. Suka gaggaisa, ramma da ƙyar ta iya gaida Viper, saboda matsanancin tsoronsa da take ji. Su liti tuni sun je wurin, dan sun kai wa ɗan mama abinci. Sumayya ta zauna su ka sake tattauna wa da ramma, kasancewar su na jiran ƙarasowar su Abdul da lauyoyin sa a ɗauki statement ɗin su duka. Sumayya ta naɗi wani sashi mai muhimmanci, na tattaunawar su da ramman, wanda zai yi wa Sumayya amfani haka Nabila, mussman ta ɓangaren Naja'atu Bunkure. Viper kuwa cikin isa yake yawonsa a headquarter yan sandan, ya je ganin ɗan mama da kansa. Sumayya ta dubi Nabila ta ce "Nabila, haryanzu ina mamakin yadda aka yi ki ka haɗu da Viper, ikon Allah ashe duk wannan haƙilon a kan sister ɗinki ki ke yin sa, amma Nabila idan ba shi ne ya kashe Jauhar ba, wanene?" Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Mu haɗu a kotu kawai sumayya, abubuwan su na da girma da faɗi sosai" "Meye wani sai mun haɗu a kotu, ki ƙarasa mini, kin bar ni a cikin duhu da zullumi Abla, kamar yadda na ji ana kiran ki, Nabila gayen nan kuwa ba son ki yake yi ba?" Nabila ta numfasa ta ce "Sumayya, ba ki yi ƙarya ba, ni ina son Viper, na kamu da sonsa ba tare da na shirya hakan ba, dan da farko dan na taimaki rayuwarsa ya dawo hayyacinsa ya sanya na ce ina son sa, sai dai ban yi aune ba, na faɗa son shi da gaske. Saboda Viper mutum ne na musamman ya kai a so shi, kin san meya ƙara jefani cikin ƙaunar sa da gaske?" Sumayya ta ce "Sai kin faɗa" "Zamantakewar sa da ya yi da jauhar" Nan Nabila ta fara ba wa sumayya labarin abin da ba ta sani ba, matakan da ta bi wurin haɗuwa da shi, zuwa labarin sa da Walid ya bata. Ramma ta yi shiru ta na sauraron su, kawai ta din ga jin, idan jauhar tayi haƙuri da Viper mutum mai ban tsoro ta zauna da shi, ta yi wannan gwagwarmayar lallai idan aka yi haƙuri Abdul ma zai iya shiryuwa. Wani ɗan sanda ne ya leƙo, ya ce su shiga, sun ƙaraso. Gaban ramma ya faɗi, maman ramma na can ta na shan hantsi, Nabila ta yi mata magana ta ce ta taso. Gaban ramma ya tsananta faɗuwa, aka yi musu jagora zuwa ofishin da za a ɗauki statement ɗin. A ciki su ka tarar da Viper a zaune, har da manyan mutane abokan Indabo da su ka zo, ga mahaifiyar Abdul yasar a wurin ita ma. Ai su na shiga office ɗin, Abdul ya miƙe, kallonsa ramma ta yi, ya rame sosai da sosai, ba wai rama ta damuwa ba, rama ta ciwo. "Rahama" ya kira sunanta a raunane. Mugun kallon da Viper ya yi mata ne,ya sanya ba shiri ta nemi wuri ta zauna. Tashi ya yi ya nufi in da take, wani ɗan sanda ya daka masa tsawa, amma bai saurare shi, ba ya nufi ramma. Ƙafa Viper ya saka masa, abin ka da mara lafiya, ya tafi luu zai faɗi, Viper ya riƙe rigarsa ya hana shi kai wa ƙasa. Aka saka ɗan sanda ya janyo shi, ya zaunar da shi, tuni ramma ta fara kuka. Kawai ya zuba mata ido ko ƙiftawa ba ya yi. "Abdul da ma wannan ce yarinyar da ka ke ta wannan haukan a kanta, duk matan garin nan? Wallahi ka bani kunya" mahaifiyarsa tayi maganar a ƙule. Aka tambayi ramma sunanta ta faɗa, aka nuna mata Abdul aka ce "Kin san wannan?" Ta jinjina kai alamar eh. "Waye shi?" "Mijina ne" ta faɗa kai tsaye. Gaba ɗaya su ka Kalle ta, cikin takaici mamanta ta ce "A gidan uban wa ya zama mijin naki?" Nabila ta tashi ta je gaban ramma, cikin raɗa ta ce "Dan Allah ki nutsu rahama, ki yi bayanin komai, saboda a ƙwatar miki hakkinki" Aka sake tambayar ramma "Meye alaƙarki da shi, me ya yi miki?" Tayi shiru ta na kuka taƙi magana. Abokin Indabo ya ce "Ni fa ina ga wannan abun duk da masalaha aka yi, aka sasanta abun nan, dan gudun ɓacin sunan yarinyar nan, tun da akwai aure kuma abin nan ya wu.... "Shut up, ba rikicin jam'iyya ba ne ba ko na siyasa, a ƙwatarwa yarinya hakkinta mu ke buƙata" Viper ya yi maganar cikin tsawa. "Aminu Viper, mai bunu a ƙugu ba ya kai gudunmuwar gobara, ka bari ka fara kashe wutar gabanka, kafin ka zage ka na ɗaga jijiyoyin wuya, haryanzu ɗa na ya na da gatan da za a iya shafe ko ma me ya aikata, mu ka zaɓi ayi masalaha". "Gobarar da nake ƙoƙarin kai gudunmuwar kasheta, ai ku ne gobarar, dan kun fi ni shiga matsala da hatsari, a ɗauki statement a gabatar da ƙararmu a gaban kotu " "Ya isa haka, nan fa gaban hukuma ne, ba teburin caca ba. Ke ki yi magana mu na jiranki" Ɗan sandan yayi maganar yana kallon ramma. Da ta ɗaga kai ta kalli Abdul, sai ta ji ta karaya. "Talk" Viper ya daka mata tsawa, ta zabura ta rirriƙe Nabila ta na kuka. A hankali Abdul ya ce "Ku daina yi mata tsawa, yes i rape her, na amsa laifina" "Ba ka da hankali, lauyoyin ka ba su gargaɗeka a kan kar kayi magana ba?" Nabila cikin rarrashi, ta ce "Rahama ki yi magana, dan Allah kar ki bari tausayi ya yi tasiri a zuciyarki, ki yi magana" Cikin kuka ramma ta ce "Ai ya nemi yafiyata, kuma da gani ba shi da lafiya, dan Allah a sassauta masa, ko a bari wataran idan ya warke sai na yi magana". Ayshercool 08081012143 Abu na farko da zamu buk’ata daga wajenka shine mahaifar matarka, Ma’ana ba zaku haihu da matarka ba.” Imaam ya ‘dago yana kallonsa Ya ji kansa ya wani sarà masa, amma sam ya kasa masa musu… Alwan yana murmushi ya ce “Ka kirata ku yi shawara…” Ya fice ya bar masa wajen. Da sauri Imaam Ya kira Safna. Tana d’agawa ta ce “Yaya? Imaam Allah yasa dai baka musu taurin kai ba?” Ya saki huci ka’dan ya furta “Ba zan iya abinda suke so ba….” “Zaka iya Imaam, ka yi koma me suke so? Yanzu fa ba abinda baa yi saboda ku’di, ana ya Kai Kai, mutum yana kwanciyar da y’ar cikinsa, da Uwar data haifeshi ma saboda ku’di, ana luwa’di da ma’digo saboda ku’di, ana bada Uwa ko y’a Yaya ko k’anwa, K’ani ko wa? Duk saboda ku’di, don haka ka yi ko me suke so Moddi Saboda ku’di… bana son musu…” ta fa’da tana zame kanta a duk sunayen da ta ambata, bata k’i ya yi komai ba in dai zai samar musu da ku’di, bata damu ta ji shara’din da suka bashi ba. Imaam Ya saki ajiyar zuciya, sai ya ji ya samu k’warin gwiwar bayar da mahaifarta tunda ita ta jawowa kanta ta ce ya yi komai saboda ku’di. A zuciyarsa Ya dinga jin baya so, amma harshensa ya kasa amince masa ya furta baya so d’in. Ya kalli Alwan da Ya shigo d’akin idanunsa a kansa shima ya ce “Yaya Aboki? Ka yarda ko a’a? Abu guda dana sani baka isa ka San sirrinmu sannan ka bijire mana ba….. Cab’di kin fara bibiya ko har yanzu… Hadarin gabas dai da zafinsa yazo akwai cakwakiya anan gaba… Za’a yi kuka za’a yi dariya za’a sha soyayya a cikin littafin nan. Hanzarta ki fara Ina Imaam Muhammad Moddibo Ya kai kansa? 89 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Sake kallon wayarsa ya yi, ya ga location ɗin wayarta ya na harba hanyar gidan mahaifinta. Kasa nutsuwa ya yi da hakan, kawai ya tashi ya sanya kaya ya fita. Saifu ya riga su Nabila ƙarasawa, Allah ya sa Baba bai kai ga fita ba. Saifu na sanar masa, Nabila ta na hanya, bakinsa ya ƙi rufuwa, ya fasa fita, ya ce a haɗa mata kayan abinci. Ya ce "Saifullahi ita da wa za ta zo nan ɗin?" Saifu ya ce "Itakaɗai ce, kai take son gani" Cike da fara'a ya ce "To Allah ya kawo mini ita lafiya cikin aminci" Ana haka Nabila ta yi sallama, hafsa ta fito da gudu daga ɗaki, ta rungumeta ta na "Oyoyo ga jauhar" Nabila ta yi murmushi ta ce "Nabila dai, ba jauhar ba" ta yi shiru ta na kallon Nabila. "Kin ƙi yadda haryanzu ko?" Ba ta sake cewa komai ba, ta ci gaba da kallon Nabila, ta na ƙoƙarin gano dalilin da ya sanya za ace mata ba jauhar ba ce ba. Baba da kansa ya fito ya tari Nabila, har zuwa ƙaton falonsa, ta zauna su ka sake gaisawa, babu kunya Zakiyya da maman saifu su ka biyo bayanta har ɗakin su ma. Su ma ta gaishe su, su ka amsa su na kallon ta kamar baƙuwar halitta. "Ya ki ke aikin naki?" "Lafiya ƙalau Alhamdilillah" "Ina ɗaya 'yar ta wa?" Nabila ta ce "Ta na wurin aiki, ni ma zuwa nan ɗin faɗo mini kawai ya yi na taho" Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, yaushe za ki kammala aikin ne, ki dawo ki zauna tare da ni, in dinga kallonki ina jin daɗi tare da ɗebe mini kewar jauhar" "Baba ko na kammala, zan zo dai na ɗan yauta maka amma ba zan iya dawowa gidan nan na zauna ba, idan na dawo nan gaba ɗaya Abba fa?. Na zo ne na nemi bakin zaren saita tarwatsatsiyar alaƙar da cikinku babu wanda yayi tunanin gyarata duk a sanadiyyar hawa dokin zuciya da ku ka yi. Baba, kai mahaifina ne, major kuma rayuwata ne, kuma ka san waye shi, a fannin tsatstsauran ra'ayi da kafiya, a wannan karon ya sake ɗaukar zafi da yin fushin da har ya nemi ko dai na rabu da kai, da shari'ar mijin jauhar, ko kuma babu ni babu shi, saboda ya na ganin jauhar ba ta samu kyakywar rayuwa daga gareka ba, ka aurar da ita ga ɗan daba, wanda ya yi ajalinta. Tabbas na rayu dogon zamani, cike da muradin son sanin waye mahaifina, sai dai gaba ɗaya na sare, gwiwata ta yi sanyi, tun bayan da na saurari labarin abin da ya faru. Sai dai hakan ba zai hanani sauke hakkina a matsayina na 'ya ba, yanzu warware mini wasu abubuwan, zai taimaka mini a kan shari'ar nan, kuma ya taimaka mini wurin wanke ka a wurin Abba. Dan Allah ka fahimce ni, ba wai ina fatan na ƙure ke ba ne ba, mafita nake nema, saboda ni ce a tsakiya muddin aka ci gaba da tafiya a haka, rayuwata aka saka a tsakiya dukkaninku kuna da muhimmanci a gare ni, kuma babu wanda zan iya zaɓa na bar ɗaya. Dan Allah baba ka warware mini abubuwan da su ka shige mini duhu. Me mahaifiyarmu ta yi maka, ka barota a garin da ba ta da kowa sai Allah sai kai, meye dalilin da ya sanya ka aura wa jauhar mai zamani, duk da ka san waye shi?" Baba yayi shiru, sai hawaye da yake gangarowa daga cikin idanunsa. Zakiyya ta ce "Ke kuwa abin da ya riga ya wuce, menene na gutsura magana, abin da ya faru ya riga ya faru, sai fatan Allah ya kiyaye gaba". Nabila ba ta kulata ba ta ce "Talk please" Ya numfasa ya ce "Nabila, na ga ƙoƙarin ki da ki ka yi saurin saukkowa daga fushin da ki ka yi, ki ka saurareni, kawunki ya yi mini laifi, amma zan iya cewa koma menene ni na janyo. Kuma na so na yi magana da shi ta fahimtar juna, sai dai tsawon wannan shekarun, major bai canza a yadda na san shi ba, yanayin sa ya tabattar mini da ba zai taɓa ba ni dama ya saurare ni ba, tun da amana ce ya bani na ci. Haƙiƙa na so chubaɗo, so na gaskiya, ga ta 'yar ƙauye ba ta da wayewa sosai, amma ina samun nutsuwa da kwanciyar hankali a tare da ita, babu hayaniya ba ta da tashin hankali da kan ƙara, ta na da matuƙar haƙuri da biyayya. Ita kuma zuciya na son mai kyautata mata, hakan ya sanya ko a cikin dangina, ba na ɓoye son da nake yi mata, da na zauna hirarta kawai nake yi na ji daɗi. Ba a iya cikin gidana ba, hatta a yan uwana, sun fara nuna mini cewar ina zaƙewa a kanta, dan sai da aka fara haɗa ni da mariƙiyata a lokacin nan, cewa na tattarare a wurinta, ta yi mini asiri. So da tausayinta ya sanya na ɗauke ta, na tafi da ita garin da nake aiki, saboda ta haihu a tare da ni, na ba ta dukkanin kulawat da ta dace, sai dai daga zuwa hutu, ban san meyafaru ba na manta da chubaɗo gaba ɗaya a cikin kaina ba, na kan yi mafarki da ita, amma da na tashi sai na manta me na gani. Ina yawan ƙoƙarin tuna wani abu mai muhimmanci a tare da ni, amma sai na kasa. Na karɓi transfer ta, na cigaba da aikina, sai watarana da na je azare, ƙanwata ta yi mini maganarta, sannan na tuna da ita, sai dai a lokacin sunanta kawai da ta kira, na ji kamar na kurma ihu, na ji a duniya babu abin fa na tsana sama da chubaɗo, ko kiran sunanta ba na son na ji an yi. Har zuwa lokacin da major ya kawo mini Jauhar, na furta masa sakin chubaɗo ƙasan zuciyata na ƙuna saboda takaici, amma a zahiri ko a jikina. Sai dai na ɗauki soyayyar duniya, na ɗorawa Jauhar, saboda babu in da ta bar chubaɗo a kamanni da kuma haƙuri. Bayan dogon lokaci, kamar wanda ya farka daga bacci haka na tashi cikin tashin hankali, na tariyo abubuwan da su ka faru, na shirya na tafi Jalingo ba tare da sanin kowa

Chapter 94 of 121