ya kalleta a matuƙar fusace ya ce "Saboda kin ga ina ɗaga miki ƙafa shi ne zaki tsallake gona da iri, zaki wuce makaɗi da rawa? Bari na koma miki ainihin Abdul ɗina, kuma wannan huakan da ki ka yi, dai-dai yake da sake nesanta kanki da iskar 'yanci. Kuma bari na sake gaya miki, babu wani mahaluki da ya isa ya rabani da ke a duniyar nan ko waye shi, idan kin ga dama ki cigaba da ƙoƙarin lallai sai kin bar gidan nan, zaki ga yadda zan yi da ke"ya fice daga kitchen ɗin ya bar a zaune, hannunta riƙe da kuncinta, hancinta har ya fara zubar da jini, saboda azaba.
Ta rasa me ma yakamata tayi, saboda zuwa yanzu zuciyarta ta ƙeƙashe, kukan ma ba iya yin sa take yi ba.
Ta ja wuri ta zauna sosai saboda jirin da take ji.
***
Sallama take yi a tsakar gida, ta ce "Na shigo ko na koma?"
Umma da take ƙofar kitchen ta ce "Idonki kenan arfa? Yaushe rabonki da gidan nan?"
"Tuba nake umma, ayyuka ne sun yi mini yawa sosai, amma ayi mini afuwa dan Allah"
Umma ta ce "To Allah ya yi jagora"
"Amin umma, ina sumayya?"
"Tana ɗakinta"
Nabila ta nufi ɗakin sumayya, ta sameta tana ta aiki a cikin computer, sallamarta kawai ta amsa, ta mayar da hankali ta cigaba da abun da take yi.
"Sumy, dan Allah ki kalleni mana"
Sumayya ta ɗago ta kalleta ta ce "Idan na kalleki mai zai amfana miki, ni da nake munafuka?"
Jiki a sanyaye ta ce "Dan Allah ki yi haƙuri, nayi kuskure abun ne ya bani mamaki ya ɗaure mini kai"
Tuni hawaye ya cika idon sumayya ta ce "A yadda muke da ke, ban taɓa tunanin wani zai kawo miki aibuna ki yadda ba, ba tare da kin yi bincike ba, amma kai tsaye ki ka danganta ni da kalmar munafunci, baki san wahalar da nake ta yi dan kare rayuwarki ba"
Nabila ma sai ta saka kuka ta ce "Dan Allah masoyiyya kiyi haƙuri ki yafe mini, ɓacin rai ne, kin ga sam baki yi mini bayanin komai ba, na samu labarin an saka ki kina bibiyata, dole na shiga damuwa kuma ke baki gaya mini ba"
Sumayya ta dubeta ta ce "Waye ya gaya miki ana bibiyarki ta hanyata?"
"Ba shi da amfani faɗar, amma dan Allah waye ya saka ki bibiyeni, ki din ga kai masa rahotona?"
Sumayya ta kalli Nabila da take ta share mata hawaye, Nabila cikin jin kunya da sanyin jiki, take ta ƙara bawa Sumayya haƙuri.
Sumayya ta numfasa ta ce "Honorable indabo ne"
Nabila ta waro ido ta ce "Indabo kuma? Meye alaƙata da shi? Me na yi masa?"
Nan Sumayya ta warware wa Nabila yadda suka yi da Indabo, lokacin da ya ce taje gidansa su yi program.
Hankali a tashe Nabila ta ce "Amma meyasa baki gaya mini ba Sumayya?"
"Ya za ayi na gaya miki? Ya ce muddin ki ka sani, zaki iya rasa ranki, kuma na san dole zaki iya aikata wani abu, da zai sanya su yi miki illa, babban abun da ya bani mamaki bai wuce lokacin da muka yi waya da ke ba, ki ka ce kin haɗu da Viper, ya ƙara rikicewa gaba ɗaya, amma na tabattar masa da ƙarya ki ke yi, baki haɗu da shi ba, ina tunanin akwai wani abu a tsakanin sa da Viper, dan cewa yayi, zai yi wa Viper tarko da ke, ya kama shi"
Gaban Nabila ya faɗi, gaba ɗaya sai kanta ya kulle.
"To tayaya zan zama tarkon da za a kama Viper? Meye alaƙata da shi?"
Sumayya ta ce "Ban sani ba, amma dan Allah ki nutsu, kar ki aikata wani abu da zai saka ya cutar da ke, wallahi rashin imanin mutumin nan ya wuce tunaninki, ke hatta a wurin aikina akwai masu saka mana ido, da kin zo sai su kirani, su ce me muka tattauna, har wayar da nake yi da ke suke bibiya shiyasa nake kiranki da wasu lambobin"
"Na shiga uku, to ni uban me na yi masa? Sumayya da wace lambar suke kiranki?"
"Private number ce, ba sa kirana da lamba" zumbur Nabila ta tashi.
Sumayya ta ce "Ina zaki je?"
Tayi waje da sauri ta ce "Zamu yi qaya kawai" a tsakar gida ta yi wa Umman Sumayya sallama ta fice.
Ƙaramar wayarta ta ɗauko, ta kira Viper, ya ɗaga a rikice ta ce "Kana nan ne, gani nan zuwa"
"Ke tsaya mana, ki zo ina?"
"In zo wurinka mana ina cikin ruɗani da rashin fahimta"
"Koma menene ki nutsu, ki yi mini bayani ina jinki"
"Ni ba wani bayani da zan yi maka, kawai zan zo gani nan".
Ya ce "Hanya babu kyau, na gaya miki kar ki zo fa"
"To a ina zamu haɗu? Rayuwata tana cikin hatsari, ni kawai kana ina, na shga uku"
Viper da yake zaune ya tashi tsaye ya ce "Malama ki nutusu ki yi mini magana, kina cikin hatsari kamar yaya?"
A fusace ya ce "Na gaya miki hanya babu kyau, ana bibiyarki ko kin manta? Za a fara tracking wuraren da ki ke zuwa yanzu haka. Ki tsaya ki saurare ni.
"To ina jinka"
"Zan tura miki adress ɗin da zaki same ni, idan kuma ni in zo shikenan"
Ta ce "A'a kar ka zo"
"Ki samu wuri ki ajiye motarki, zan turo miki adress ɗin in da zaki same ni".
"To ka yi sauri" ta cigaba da tafiya a motar, tana waige-waige ko zata ga wani yana bin ta.
Ya turo mata adress ɗin da zata same shi, ta ajiye motarta, ta bi adress ɗin.
Wurin kamar garden haka yake, ba kowa a wurin, sai manyan bishiyu, ga wurin sanyi mai daɗi.
Tana tsaye tana waige-waige, ta ciro wayarta, tana ƙoƙarin kiransa, kawai ta ganshi unexpected a bayanta, sakin wayar tayi ta hau ihu.
"Menene?"
"Ba tsorata ni ka yi ba, sai ka zo kana wani sanɗa da na zura da gudu fa, ka daina wannan sanɗar".
Ya kalleta ya ce "Idan ban yi sanɗa ba, ban amsa sunan Viper ba, sai da aji hucina, ko bayan nayi ɓarna a ankare da na zo wuri, gani menene?"
Ta ƙare masa kallo ta ce "Ɗan beauty"
Ya tsuke fuska ya ce "Neman me ki ke yi mini?"
Cikin damuwa ta ce "Mu zauna, na gaji da tsayuwa"
Suka samu wuri suka zauna, ta ce "Dan Allah Viper meye haɗina da Indabo? Shi ya saka sumayya take bibiyata. Ta gaya masa yadda suka yi da sumayya.
Ya numfasa ya ce "To me zan yi miki?"
"Ban gane ba, ka gaya mini meyasa Indabo yake bibiyata, me nayi masa?"
Cikin ko in kula ya ce "Ya za ayi in sani?"
"Dan Allah ka gaya mini, kai ma fa ka tambayeni ko na haɗu da shi, me kake ɓoye mini ne? Dan Allah ka gaya mini mana"
"Meyasa liti ya rikice ranar farko da ya ganki, ya amince ya kawo ki maɓoyata?"
Ta ce "To ya za ayi in sani, ina tambayarka kana tambayata? Ka gaya mini mana"
Ya ɗago ya tsura mata ido.
"Ka yi magana mana, dan Allah meyasa yake bibiyata, ta ce ya rikice lokacin da ya ji na ce na haɗu da kai" still bai yi magana ba.
"Talk please"
Zuciyarsa ya ji tana harbawa da sauri, ya girgiza kai ya ce "Kamar na ji kin ce mamanki ta rasu ko?"
Turɓune fuska ta yi ta ce "wai ina ta rayuwata, kana tambayata wani abun daban".
"Nan gaba zaki so jin dalilin da ya sa na tambaye ki, bana surutun banza ni"
Kamar za ta yi kuka ta ce "To ni yanzu ya zan yi da wannan indabon?"
Viper ya ce "Ba ruwanki da shi, ni ne dai-dai shi, ki ji da bunkure karki manta, sati biyu kawai na baki ki yi mini aikina"
Ta narke murya ta ce "Nawa zaka bani ne da ka sakani aikin, ka san dai ba lawyer gwamanti ce ni ba"
"Nawa ki ke so?"
"Kai nake so" gabansa ya faɗi, da ya tuna Jauhar sararta ce faɗar haka.
"Kina wuce gona da iri" yayi maganar yana kallon in da yake facing.
"Daga zuwanka, ka saka DSP ya haɗa ni da Abba, an ce sai na duba samarina na fito da miji, sai ka aureni, tun da duk kai ka janyo koma menene"
"Are you serious? Ɗan ta'addan zaki aura kina gidan masu kaki?"
Ta ce "Eh mana, ka bani dama na zama yar suganka"
Ya ɗora hannunsa a kan ƙirjinsa, ya ce "Ki daina wannan wasan ba na son sa ko kaɗan, haryanzu ina jin motsin jauhar a cikin zuciyata. Idan ki na irin wannan maganganun ji nake tamkar na aikata zunubi mai girman gaske, babu wani abu da zan iya haɗawa da soyayyar jauhar a zuciyata, ki kiyaye wannan ki daina wannan wasan, kar ya zama gaske".
"Ba ka son yar sugar kenan sai madara ko?"
"Ke ki ka san sugan, ni ba na ta'amalli da shi ma"
"To zuma fa ko mazarƙwaila" ya yi mata shiru.
Ta tashi ta ce "Kar ka so ni ɗin, amma to ni ya zan yi da wannan indabon bashi da imani, kar ya kashe maka ni"
Viper ya ce 'Idan ya kashe ki ya hutar da ni"
Murguɗa masa baki tayi, ta kama hanyar tafiya. Sai da tai nisa sannan ya waiwaya yana kallonta.
Ita kanta murmushi ta yi, saboda yau ya sake, babu wannan alamar ƙuncin da damuwa a tare da shi.
***
Da daddare Nabila tana kan social media, taga wani dogon rubutu, da aka yi, na jinjinawa Naja bunkure, a kan ayyukan ta na jin ƙai. Sumayya na ganin posting ɗin, tayi tagging ɗin Nabila.
A take Nabila tayi reposting ɗin post ɗin, tare da caption kamar haka *Lokaci yayi da yakamata mu san haƙiƙanin ayyukan da Bunkure foundation ke gabatarwa, shin da gaske dan talaka take yi, ko kuwa dan rufe ɓarnar masu ido da kwalli kawai take yi?.
Mu duba case ɗin yarinya zulaiha, da ya faru shekarun baya, wadda ta fuskanci cin zarafi, daga wani ɗan mai kuɗi, bunkure foundation sun shiga case ɗin domin su tsaya mata, a hukunta shi, amma ƙarshe sai labarin mutuwar zulaiha muka ji, ta kashe kanta ta hanyar shan fiya-fiya, shi kuma wanda ya aikata, yana shekarar ƙarshe na kammala karatun degree a ƙasar Amurika.
Bana ƙwaina sai da zakara, akwai tarin hujjoji da nake da su a kan maganata.
Jikinta na tsuma, ta yi posting ɗin, ta rufe data.
Tayi addu'oin kwanciya bacci, ta kashe wayarta, har ta rufe ido maganganun ta da Viper suka faɗo mata.
Lumshe idanunta ta yi, amma maganar sa ta din ga kai komo a zuciyarta.
*Ba zan iya haɗa soyayyar jauhar da komai ba, dan haka ki ma daina wannan wasan*
Dafe ƙirjinta ta yi, ta ce "Na shiga uku, tausayin sa kawai nake ji, da wasa nake yi, me nake ji a raina ne?' ta tambayi kanta.
Wasi-wasi ne kawai, ta bawa kanta amsa tare da kwanciya.
Washegari da safe bayan sallar asuba, ta kwanta ta sha bacci, kasancewar lahadi ce, babu aiki.
Sai wajen ƙarfe goma ta tashi, ta yi wanka ta fito ta shirya ta ɗauki wayarta ta kunna.
Jerin saƙonni ne suka din ga rige-rigen shigowa wayarta, bayan ta kunna data.
Messages kuwa, ga na barrister Habib, ga na summaya.
Ƙarƙashin post ɗin ta kuwa, comment ya kusa dubu, da masu kare Bunkure da masu zagin Nabila, kasancewar alherin bunkure galibi mutane suka sani.
Ta ɗaga kiran wayar sumayya da yake shigowa, ta ce "Ya ne?"
"Nabila daga tagging ɗin ki a post, kin rikita media"
Nabila ta ce "Ai makaho ba ya sanin ana kallonshi sai an taɓa shi, bar su su gama haukan da kare ta, ina nan zan saki maganar ramma bayan an kuma zaman kotu".
"Amma Arfa kar fa ta yi miki wani abu"
"Ba abun da ta isa ta yi, ai ina da hujjoji "
"Allah ya ƙara tsare ki, zan cigaba da nemo miki sahihan bayanai a kan ta"
Naja ta kalli posting ɗin ta yi murmushi ta ce "Bari na nuna wa yarinyar nan ainihin kalata da take son gani.
Kira Nabila ta gani da private number, babu tsoro ko fargaba ta ɗaga.
"Wane irin move ne haka, kin san mutanen nan ba za su barki ba ko?"
Nabila ta ce "Kai ka bani aiki ka ce nan da sati biyu, aka yi sara a kan gaɓa, sumayya ta yi tagging ɗina a kan post ɗin, na ga ya dace na tofa wani abu".
Viper ya ce "Shikenan, amma ki shirya matakin da za su ɗauka a kanki"
Nabila ta ce "Ina da kai ai, idan na je aiki zan kiraka"
Nasir ne ya faɗo ɗakin ta ya ce "Nabila, wai meyasa baki da hankali ne"
Ta kalleshi ta ce "Me nayi kuma?"
"Ban ja miki kunne a kan Naja'atu Bunkure ba? Kin je kin tsokanota, gashi an fitar da sanarwa hukumar DSS suna nemanki, an shigar da ƙararki for defomation of character".
Ayshercool
08081012143
62
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Ta ce "Ban gane ba, su DSS ɗin uban me na yi musu suke nema na, kamar wata 'yar ta'adda".
"Shut up, ina magana kina yi mini gatsali, abun da nake ta ankarar da ke kenan ai, matar nan tafi ƙarfin ki, ba sa'ar yinki ba ce ba, amma saboda zunzurutun taurin kai, da zigar da ki ke ɗauka, kin cigaba da abun da ki ka ga dama, da yake ba kya son zaman lafiya"
"Ina son zaman lafiya DSP, kuma duk abun da nake yi da hujja nake yin sa, dan haka a gaban kotu yakamata ta ƙalubalance ni, ba wurin DSS ba, uban me nayi mata?"
"Look arfa, matar nan ba zata bi abun da doka ta tanada ba, dan tana tsoronki, koma menene za ta yi shi ne, dan kawai ta tozarta ki, ta nuna miki ke ɗin ba kowa ba ce ba, kuma babu abun da wani ya isa yayi. Ko hurumin DSS ne su kama ki, ko ba hurumin su ba ne, za su yi abun da ta ce ne, kuma babu mai ƙwatarki"
Kawai Nabila ta saki murmushi ta ce "Ai DSP duk wanda ya ce ayi wasan jifa, ya san me ya taka ne? Dss ai ba lahira bane ba, a yadda nake ji na yanzu, hukuncin Allah shi ne abu mai razanarwa da firgitarwa a gare ni. Ban fara wasan ba, sai da na tabattar da ingancin ƴan wasa na. Ita taƙamarta tana da manya a sama, da zasu tsaya mata, abun da ta manta da ita da manyan banzan nata shi ne, ƙanan na ƙasa su suka zama tsaninsu wurin zuwa ƙololuwar in da suke tafka tsiyar, daga zarar na ƙasan sun yi bore, na saman dolennsu su shiga hankalinsu, ita ta iya Black market ni ta hanyar shari'a zan nuna mata kuskurenta legally"
"Shut up a beg, uban me ki ka taka, mara hankali kawai, zaki tayar wa da mutane zaune tsaye" tayi masa shiru ya fice yana sababi.
Nan fa yan gidan, suka samu topic of discussion, ko a jikinta, ta gama shirinta tsaf, Baba magajiya ta iske a falo, ta ce "Yauwwa arfa, dama ke zan zo na kira, babanki na nemanki yanzu da gaggawa".
Duk da sauri take yi, amma ta nufi ɗakin Abba, ta iske shi da shi da Nasir, hankalinsa a tashe.
"Arfa, me ki ka je ki ka aikata? Yayanki ya ce kin yi posting a social media kin tayar da tarzoma jami'an tsaro suna nemanki"
Nabila ta ce "Wallahi Abba ban tayar da tarzoma ba, gaskiya kawai na faɗa, kuma haryanzu a hukumance ni ban ga cewar DSS su kama ni ba"
"Ƙaniyarki da ke da hukumar, amma dai kin san ni yanzu ba da bane ba da zaki je ki tsokano mutane ko, tsokanar taki ma, ki ka kasa yin dai-dai da ke, sai in da zaki sha wahala, haka kurum ki tayar mana da zaune tsaye, muna zaman lafiya a ga DSs sun yi mana dirar mikiya a gida, kamar wasu yan ta'adda".
"Abba ba su da hurumin kama ni, ban ɓata wa kowa suna ba, gaskiya kawai na faɗa"
"Rufe mini baki, ko na saka ki tsallen kwaɗo yanzun nan, mara kunya fitsararirriya".
Wayarta ce take ringing, ta ce "Bari na ɗaga waya"
"Hello yaya Habib"
"Nabila kina ina ne?"
"Ina gida, yanzu zan fito wurin aiki"
"Maza ki hanzarta ki ƙaraso, na ga wani rumors yana yawo, a kan posting ɗin da ki ka yi jiya, wai Dss suna nemanki, duk da ba officially na ga sanarwar ba, magoya bayanta ne suke ta zuzuta maganar, maza ki ƙaraso mu riga su ɗaukar mataki"
"To Barrister, gani nan in sha Allah" ta sauke wayar ta ce "Abba daga law firm ɗinmu ne, bari na tafi"
"Ki tafi ina, an ce ana nemanki?"
"Eh zan je in ji me za su ce ne"
Abba ya kalli Nasir ya ce "Ka kai ta law firm ɗin na su, duk yadda ake ciki, ka kirani, zan je na ga likita sai na biyo"
Sam Nasir ba haka ya so Abba ya yi wa Nabila ba, ya so ya ja mata kunne sosai, ya taka mata burki a kan abun da take yi, amma bai yi hakan ba.
Suna tafe a mota, ba ta kula shi ba, sai waya take yi da sumayya da murtala, sumayya ta ce zata ƙarasa law firm ɗin su Nabila.
Tana sauke wayar sumayya, kira ya shigo, an rubuta Confidential a kan lambar.
Ya kalli Nabila, ya kalli wayar, kasancewar Bluetooth ne a kunnenta, ya sanya ta amsa dan kaucewa zargin sa.
"Hello boss"
Viper ya ce "Ya ake ciki? Sun kama kin ne?"
"So ka ke su kamanin kenan?"
"Am asking? Ya ake ciki?"
"Eh, ba su da hurumin kama ni, yanzu ina hanyar law firm ɗin mu ne, Oga na a wurin aiki ya ce maza naje, a riga su ɗaukar mataki".
"Ok, amma you over react, na so ace a sannu ki ka bi abun, amma yanzu zamu raba hankalinsu biyu, zan yi wa Indabo aike, hakan zai sanya su kasa tsayar da hankalinsu wuri guda"
Ta kashingiɗa da jikin seat ɗin mota ta ce "Aiken me?"
"Ke da waye a motar nan?"
"Meyasa ka tambaya?"
"Akwai rashin sukuni da tsoro a cikin maganarki, ke da wayar"
Nabila ta waro ido ta ce "Kai ya aka yi ka gane, vi.... Saurin katse maganar tayi, da tuna katoɓarar da kusa tafkawa.
Tayi gyaran murya ta ce "Zamu yi magana anjima, yanzu ina cikin zullumi jami'an tsaro za su kama ni, ka bari na yi salati na nemi agajin Allah"
Viper ya ce "Ok" ya kaste kiran.
"Da wa ki ka yi waya?"
Ba tare da ta kalli Nasir ba, ta bashi amsa da abokin aikina ne.
***
Ramma ta takure kanta sosai da sosai, tun da Abdul ya dake ta, ya fice daga gidan ba ta sake ganinsa ba, itakaɗai take kwana take tashi, kuma ya ɗauke wayar da ya bata, da take kiransa a ita, hatta system ɗin sa guda ɗaya da yake ajiye mata, yana koya mata computer ko tayi kallo, dan har fina-finai na hausa, yake yi mata downloading dan su din ga ɗebe mata kewa, gaba ɗaya ya haɗa ya kwashe, ƙofar da zata fito da ita, ta sauka daga kan bene ma zuwa falon ƙasa, duk ya haɗa ya rufe.
Sam ba ta ko iya cin abinci, damuwa ta dawo mata sabuwa fil, ta rasa abun da yake yi mata daɗi baki ɗaya.
Tana zaune bayan sallar isha'i a bedroom, ta ji ya buɗe ƙofa ya shigo, a razane ta waiwaya ta ɗan ja da baya.
Ya ɗan tsura mata ido, sannan ya mayar da ƙofar ya rufe, ya nufi in da take hannunsa da leda.
Ya ajiye ledar, sannan ya zauna a kusa da ita, amma ta sake ja da baya.
"Guduna kuma ki ke yi yau?" Da ya motsa sai ta zabura, dan gani take dukanta zai kuma yi.
Shammatarta yayi, ya janyota jikinsa, ya rungumeta a ƙirjinsa ya ce "Am sorry please, ki yi haƙuri dan Allah" ta yi shiru ba ta ce masa komai ba.
"Ki yi haƙuri, tsantsar tashin hankali da na shiga ne, ya sanya na aikata miki abun da nayi, bana son gardama da taurin kai, tun da ki ka ga na ajiyeki, duk da irin son da nake yi miki, da magiyar da ki ke yi mini, ban mayar da ke gida ba, akwai matsala ne, mamanki ina zuwa wurinta, na tabattar mata da kina cikin ƙoshin lafiya, abin da ki ka yi shirin yi, barazana ne ga rayuwarki. Wallahi regret ne ya hanani dawowa tun da na fita na nutsu, gaba ɗaya nake cikin damuwa, amma ki yi haƙuri dan Allah"
Tayi lamo a jikinsa, amma taƙi magana.
"Rahama talk dan Allah, ki yi mini magana mana ko na ji daɗi dan Allah ki yi haƙuri ki yafe mini, son da nake yi miki ne ya sanya na ga abun da ki ka aikata barazana ne ga cigaba da kasancewarmu tare, ki yafe mini" ai kamar gunki, taƙi cewa uffan.
Ya ɗago fuskarta, yana kallonta, amma ta sunkuyar da kanta ƙasa.
Ya janyo ledar gabansa, ya buɗe tsire ne fal a ciki, ya ce "Ki ci abinci, duk kin faɗa kwana biyu, dan Allah ki yafewa Abdul ɗinki, ba zan ƙara dukanki ba"
Ta saka hannu ta share hawayenta ya ce "Yauwwa babyna, ai na zaki yafe mini, kina da yafiya shiyasa nake ƙara ƙaunarki Rahama, Allah ya yi miki albarka ya shirya miki ni" da ƙyar ya din ga bata abincin a baki, ta ci kaɗan ta tashi, sam taƙi sakar masa fuska.
***
Nabila suna zuwa law firm ɗin su, Barrister Kabir ya balbaleta da faɗa, Nasir ma ya taya shi, akan kasadar da ta yi.
Duk da Nabila ba ta son faɗa a rayuwarta, amma ko a jikinta, ta maze tana cunkusa baki.
Barrister Habib ya ce "Dan Allah ku yi haƙuri haka, aikin gama fa ya riga ya gama, ta riga ta aikata, sai a san abun yi, kuma wannan duk ba abu ne na tayar da hankali ba, in dai mutum yana da gaskiya, ai faɗa ba nasa bane ba.
Nabila shigo office mu yi magana.
Barrister Kabir ya ce "Naga kamar goya mata baya kake yi Habib, idan kuka janyo abun da ba zaku iya ba, to ku tsaya can, kar ku raɓa ni a ciki"
"To barrister idan ba a goya mata baya ba, kware mata baya zamu yi, ma'aikaciyarmu ce, tayi abun da wani bai yi yinƙurin yi ba, ai kamata yayi a duba, idan akan gaskiya take, a ƙarfafeta, shigo mu yi magana"
Nabila ta shiga cikin office ɗin sa, ya ce "Good girl, i like your confident, a lady of her words, kin dage sai kin cimma burinki a kan matar nan"
Ta ce "Yanzu dai ba wannan ba, meye abun yi, kafin a zo a kamani, nima su saka a kaini prison a ajiyeni babu Shari'a kamar yadda suka yi wa Viper"
"Suka yi wa Viper ita da wa?"
Nabila ta ce "Oho mata, shi ma wannan case ɗin ina nan zuwa kansa, zata gane bata da wayo ai"
Yayi murmushi ya ce "Ba wannan ba, na yi wa Bashir ma magana, yana hanya, zamu yi maza mu shigar da ƙara, a kan lallai kotu ta dakatar da kamun da aka ce Dss su yi miki idan ma da gaske zasu kamakin, ba su da wannan hurumin, sannan su daina yi miki barazana dan kin faɗi albarkacin bakinki"
"To ayi sauri ayi, dan wani update ɗin zan saki, da ni take zancen"
Duk da hantarar da Barrister Kabir ya yi wa Nabila, tare da shi, da sauran lawyoyin law firm ɗin, suka haɗu suka tattara bayanai, da hujjoji da za su kai kotu, dan hana kama Nabila.
Suna can suna ta ƙoƙari, Nabila suka keɓe da Sumayya, ta tura mata videon yaron da ya ketawa zulaiha haddi, a cikin abokansa a ƙasar amurka.
*Wannan shi ne Najib, wanda ya keta wa yarinya zulaiha haddi, har ta kaita ga rasa ranta, a shekarun baya, shin ina shari'ar ta tsaya? Ko ya fi ƙarfin doka ne, dokar a kan talaka kawai take aiki?
Kwana kwanan nan, mun ga yadda labarin wani matashi ya cika dandalin sada zumunta, a kan yadda aka tsare wani matashi shekara goma sha biyu, a gidan gyaran hali, bisa zargin sa da aikata fyaɗe, sai bayan shekaru goman nan, a ziyarar da wani bawan Allah ya kai gidan, ya tausaya masa, ya tsaya masa aka cigaba da yi masa shari'a har aka gano ba shi da laifi, saboda shi talaka ne ya sanya Bunkure foundation ba ta shiga ire-iren cases ɗin nan, sai dai na mata kawai? Me zai saka ace mata kawai foundation ɗin take tsayawa ban da maza? Anya babu wata maganar a ƙasa?.
Wannan ra'ayina ne a matsayina na ƴar ƙasa, wanda yake da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 65 Chapter of 121