Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
89 / 121
ba, me zan sayo miki ki ci?" Ta girgiza masa kai alamar babu. Ya kwantar da murya ya ce "Tashi na baki abincin a baki, ai za ki ci ko fulanina" Fafur taƙi sai ma ta saka masa kuka wai gida, ya mayar da ita gida. ya tashi ya fita ya sayo mata tsire fal, da fanta ya kawo mata. Ya din ga rarrashinta, da ƙyar ta daina kukan, ai ba ta saurari nama ba, ta din ga ɗaɗɗakar fanta. Yayi murmushi ya ce "Ka ga bafulatanar Bashir, da ga yanzu na gano lagonki, fanta ce maganinki" sai kuma ta sunkuyar da kai tana murmushi. Sai da ya shafe wata guda a Bauchi, ya kaita can garinsu azare, da yake shi ba a can yake zaune ba, a can ya samu ya ɗan sake da ita sosai, dan sai da suka kwana uku, sosai danginsa da yan uwansa suka karramata. Mamaki take yi yadda yake salihi, a gaban mutane, ake yi masa kallon mutumin kirki, yake sunkuyar da kai, amma ida suka keɓe yayi ta yi mata fitsara da rashin kunya. Wata irin soyayya yake yi mata, wadda bai iya nuna mata a waje ba, dan da gaske yake jin sonta a cikin ransa, chubaɗo akwai haƙuri da biyayya, ya samu har ta ɗan fara sakewa da shi, yayi kamar ya ce zai tafi da ita in da yake aiki, dan dab da za ayi bikin su, aka mayar da shi Naija state. Da ya fara yi mata wani abu dan soyayya da kyautatawa, sai ta ce ya bari, saboda tana son ta shiga aljanna. Ya dubeta ya ce "Waye ya ce idan na yi miki tausa, ko dafa miki ruwan wanka, ba zaki shiga aljanna ba? Jin dadin biyayyar da ki ke yi mini, ya sanya nake yi miki abin da zaki ji daɗi kema" "To zan shiga aljanna?" "In sha Allah, hannuna a naki zamu shiga" Ta rausayar da kai ta ce "Wataƙila babar saifu ta hanaka, ta ce na ta hannun zaka riƙe ita da amarya, ku tafi ku barni" tayi maganar cikin kishi da yarinta. Yayi dariya ya ce "Kowaccenku, zan riƙe hannunta mu shiga tare in sha Allah" Mairamu bata aikin komai, gidan ma kusan ba wanda yake wani aiki a gidan, saboda suna da masu yi musu aiki. Da fari tana so ta ɗan sake da matan gidan, amma suka nuna mata bata isa ba, hatta masu aikin ma wani gani-gani suke yi mata. Sai dai saifullahi ne mutuminta, shi ne ya kan shigo ɗakinta, har su ci abinci tare da shi. Tun da Bashir ya koma aiki, suka mayar da mairamu tamkar baiwarsu, suka din ga sakata ayyuka na wahala, suka dakatar da mai aikinsu, ita ce wanke-wanke, shara raino wankin yara da kuma girki. Gashi har a lokacin da ƙauyanci da ƙuruciya a kanta. Maƙwabta suka din ga ziga su, wai ƴar aiki kawai aka kawo musu, ban da haka ina wannan bagidajiyar zata iya kula da miji. Ranar da zai dawo, duk sun sha ado da kwalliya, mairamu kuwa futu-futu dan wuni tayi tana aiki. Duk zumuɗin ya zo ya ganta, bai ji daɗin ganinta a haka ba, da ya shiga ɗakinta sai da ya ce mata ƙazama. Haƙuri kawai ta bashi ta yi shiru. Ranar da ya dawo ɗakinta, ta yi kwalliya, hakan yayi masa daɗi sosai da sosai, babban abin da ya basu mamaki, bai wuce jiyo dariyar Bashir da mairamu ba, suna yi mata kallon sokuwa, amma ta saka miji a ɗaki suna ɓaɓɓaka dariya. Tambayarta yake yi "Da a baki fanta, da nagge wanne ki ka fi so?" Ta ce "Kai Nagge mana" Ya ciro check, ya rubuta Naira dubu ashirin irin ta da a jiki, ya ce "Nan dubu ashirin ne, da na baki wannan, da na baki nagge wanne ki ka fi so?" Tayi dariya ta ce "Aradu na fi son nagge" suka tuntsure da dariya ya ce "Baki da wayo, wannan kuɗin sai ya sai miki nagge biyar" "Wannan ɗin, takadda ce fa kawai gaskiya na fi son nagge" Bashir ya ce "To da ni da nagge wanne ki ka zaɓa?" Ta waro ido. Ya ce "Sai kin zaɓa fa" Ta faki idonsa ta ce "Nagge"ya riƙeta yana yi mata cakulkuli ya ce "Me ki ka ce?" "Kai na zaɓa" tayi maganar tana dariya. Mairamu ba ta taɓa kai ƙarar wani wurinsa ba, su kuwa ba sa rasa Sharrin da zasu yi mata, wani ya yadda wani ya rabu da su. Ba ta taɓa cewa ya sai mata wani abu ba, duk da yana jaddada mata, duk abin da take so, ta tambaye shi. Maitama ya zo gidanta bayan auren, sai dai yayi farinciki da yadda ya tarar da mairamu, babu yunwa babu ƙishirwa, akwai kulawa sosai da sosai. Duk da kashedin da Bashir yayi musu a kan mairamu ba ta da cikakkiyar lafiya, bai hana idan baya nan su azabtar da ita ba su tura ta gaban hayaƙi ba. A gidan Bashir ta fara al'ada, shi ma sai da matan suka yi ta ƙanan maganganu, dan sun zata ciki ne da ita. Ana haka Allah ya yi wa baffa rasuwa, babu wanda ya sani, dan sai da yayi watanni uku, sannan maitama ya sani, ya saka aka gaya wa Bashir. Chubaɗo ta sha kuka, kamar babu gobe, ta shiga matsananciyar damuwa da tashin hankali. A haka ta shafe shekara guda cif, dada ta zo mata, ta ji daɗin hakan, sai dai sai da suka kuma yin kukan rashin baffa. Dada ta din ga rarrashin mairamu, dan ta fuskanci yanayin zamanta da abokan zamanta babu daɗi, amma gidan akwai kulawa komai na buƙata akwai. Sai da ta shekara biyu, ko ɓatan wata ba ta taɓa yi ba, ko a jikinsa, ita dai tana ta addu'a, Allah ya sa ita ma ta haihu, dan yar da aka haifa hafsa kamar ta ce a bar mata, duk da idan ta  ɗauka ayi ta yi mata habaici. Aka kuma canzawa Bashir wurin aiki, ya samu ƙarin matsayi, ga aiki ga kaswuanci, ya sai wuri a kano, ya fara gini, saboda yana ƙaunar garin kano, yana son idan ya gama, su koma can, ya nemi transfer ya dawo arewa gaba ɗaya, dan a kano ya auri matarsa ta biyu, kuma garin ya burge shi. Watarana da safe, ana shirin karyawa, jaririya hafsa ta fara rarrafe, mairamu ta ce "Ki kula kar hafsa ta ɓaro kunu a jikinta" aikuwa tana rufe baki, hafsa ta sheƙo kunu a jikinta, ta ƙone, tun a ranar suka laƙaya mata maita. Haka kurum ta fara rashin lafiya, abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, ga Bashir ba ya gari, aka rasa mai kaita Asibiti, abu har da suma, ciwonta kuma ya tashi, sai masu aiki ne suka kaita Asibiti, a tsukin lokacin Bashir ya dawo, ya sha baƙin ciki da ɓacin ran abin da suka aikata. Duk ta rame ta yi duhu, ya mayar da ita Asibiti da kansa, aka tabattar masa da tana da juna biyu. Ya din ga murna kamar ba a taɓa yi masa haihuwa ba, sai dai yayi shiru da bakinsa, da ya tashi komawa aiki, ya ce da ita zai tafi. Suka yi surutansu da masifarsu, suka gama. In da aka mayar da shi aiki, can wani gari ne a kudancin Najeriya, a lokacin rabonta da hammanta, kusan shekara duk ta damu tana son zuwa ganin gida, ya ce ta bari idan ta kusa haihuwa, zai mayar da ita gida ta haihu ta yi arba'in. Lokacin maitama shi ma babu zama, daga wannan gari zuwa wancan gari, har ƙasashen da ake yaƙe-yaƙe a Afrika ake tura su aiki, dan haka bai samu sukunin sake zuwa wurin mairamu ba, sai dai kullum tana zuciyarsa. Tana yawan yi wa Bashir zancen makaranta, ya ce zai mayar da ita, yana sane, dama target ɗin sa, ta haihu ko ɗa ɗaya ne, sai ya sakata a makarantar. Ashe matansa sun ƙwafe tafiyar da ya yi da ita a ransu, sun ƙullace su, dama a hakan a rashin wayon nata, da azabar da suke yi mata, gani suke yi ta mallake shi abin da take so kawai yake yi. A can garin kuwa, yana bata kulawa iya yin sa, amma laulayi ya sakata a gaba, ciwonta kuma kusan kullum cikin tashi yake, shi yake yi mata komai yake kula da ita, cike da ƙauna da tausayawa, bai taɓa gajiyawa da ita ba, sosai yake tausayinta, ba ta da wasu dangi, da za ace su zo su kula da ita, ko ya kaita tayi rainon cikin a can, dan har ga Allah ba zai iya kaita rigar nan tayi rainon cikin a can ba. Idan ya samu lokaci, yana zuwa can gidan, ya yi kwanaki ya dawo, cike da addu'a da fatan Allah ya sauketa lafiya. Cikinta na da wata takwas, ya je gida, tun da ya je, gaba ɗaya tamkar an shafe masa duk wani tunani da ya shafi mairamu, yazo da kwanaki biyu, aka turo masa da takardar transfer, an mayar da shi aiki jigawa. Bai ko sake komawa garin da ya baro marainiyar Allah ba, ya je yayi reporting a wurin aikinsa na Jigawa. "Abba, ina ga canza hanya zamu yi, akwai go slow sosai a nan, maganar Nasir ta dawo da Abba daga tunanin da yake yi. Ayshercool 08081012143 85 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Major yayi wata irin nannauyar ajiyar zuciya, ba tare da ya ce komai ba. Nasir ya ce "Abba" "Nasir, ko ma ta ina ne ka bi, fatana kawai na cimmusu, shi kansa yaron na ji dalilin sa na shiga sha'anin iyalina ba tare da izinina ba". Nasir ya ce "Ina ga hakan baya rasa nasaba, da ta jikin hoton da na kawo maka" Abba yayi shiru bai sake cewa komai ba. Viper kuwa muryar Abbu ce ta cigaba da amsa kuwwa a cikin kunnuwansa, ya din ga jin muryarsa har cikin ƙirjinsa. Gefensa Nabila ta na ta kuka, ba yadda ya iya, ya ji zuciyarsa babu daɗi sam. Ya matsa murya ƙasa-ƙasa ya ce "Ki daina yi mini wannan kukan, na gaya miki ba na so ko?" Shiru tayi masa ta cigaba. "Babu buƙatar mu je in da zamu je, kina kuka a haka, idan kuma mu koma ne shikenan" Cikin kukan ta ce "Ni ku tsaya ku sauke ni, koma ina ne ba zan je ba" Ya ce "Saboda me?" "Yanzu ku ka gama ci mini mutunci da kai da abokanka, bani da kamun kai, ina yawo a cikin maza, kai kuma dan na haɗaka da mahaifinka, ya zama tashin hankali, har ka manta har da fushin iyaye ya jefa ka a musibar da ka ke ciki, daga ƙoƙarin sasanta ku, wataƙila komai ya zo mana ma da sauƙi a dalilin hakan, amma kalli yadda ku ke cin fuskata, wallahi ƙaddara ce ta kawo ni in da ku ke, har gaban iyayena na bari nayi karatu, ban lalace ba, kuma ban saki jiki da maza ba, duk aikin ƙaddara ne, da ƙoƙarin ceto rai, amma bakomai na gode" Sai kuma jikin liti yayi sanyi, Walid kansa bai ji daɗin abin da suka yi wa Nabilan ba. Walid ya ce "Yi haƙuri Nabila, dan Allah ki ke yi ba dan halin su ba, kuma Allahn yana gani, shi ne zai biya ki, idan ki ka gama shari'ar nan, duk ki watsar da su ki yi ta kanki, kar wanda ki ka sake nema. Wallahi ni ina gani, kuma ina yabawa abin da ki ka yi" Liti ya ce "Walid ba a haka, wannan ai ziga ce, ke yi haƙuri haushi ki ka bani ne" Zazzage jakarta ta fara yi, saboda numfashinta baya sauka cikin ƙirjinta sosai, saboda kukan da ta yi. Viper ya taimaka mata, ya ɗaukko mata inhaler ya saka a bakinta, sau biyu ya fesa mata, ta saka hannu ta karɓa ta mayar ta saka a cikin jakarta, tana share hawaye. Message ya rubuta mata a wayarsa, ya tura ta ta, ya miƙa mata ta karanta, ɗagowa ta yi ta kalle shi, suka haɗa ido, ta galla masa harara ta gyara zamanta, tana kallon taga. *** Asibiti kuwa sai da aka je da 'yan sanda, sannan suka karɓi rahila, shi kuma Abba aka je aka kamo shi. Tuni labari ya karaɗe gari, yaro ya yi wa uwassa duka, a kan tayi masa faɗan daina ta'amalli da kayan maye. Hannunta na hagu ta samu karaya, har guda biyu, ga gefen wuyanta da ya kumbura yayi suntum saboda duka. Abbu ya ce "Daga hannun yan sanda sai dai su san yadda za su yi da shi, dan ba zai sake zamar masa a gida ba, ya koma hannun ubansa. Abun takaici sai dangin rahila suka fara ƙananan maganganu wai da ɗansa ne, ba zai ce zai kore shi ba, tun da abin ƙaddara ne, bai wuce kan ɗan kowa ba. Abbu ya ce "Ai ba ɗan nawa bane, nawa ɗan ma da ya ƙi ji bai ƙi gani ba, dan haka ba zai yi mini kisan kai a gida ba, tun da ya iya dukan uwarsa wataran ai ni zai daka" "Yo Allah na tuba kisan kan, ai kai ba ka yi wa wani gorinsa ba, tun da dai kai ma naka ɗan yayi, kuma in sha Allah, Allah ba zai nuna mana wani yayi kisan kai a zuriyar mu ba" Abbu ya ji zafin maganar da ƙanwar uwar rahila ta gaya masa, amma ya haɗiye yayi shiru, bai ce uffan ba ya fice ya bar su. *** Ramma abin duniya ya isheta, wata irin kewar Abdul take yi kamar babu gobe, Abdul ɗan gayu ne kuma ɗan hutu, tun da ta ji an ce an kama shi, sai ta ji gabanta na tsananta faɗuwa, da zata yi masa adalci roƙonta da ya din ga yi, ta yafe masa yakamata ta yafe masa, da fari ta zata idan aka kama shi, aka hukunta shi zata huce, amma sai ta ji ba haka ba, tausayin sa ma take ji. Gashi mahaifiyarta, ta saka ta a gaba, ko saurararta ma ba ta yi yanzu, ta kuma dage a kan lallai idan tana son su zauna lafiya, to sai an zubar da cikin nan, da ba zata taɓa yarda ta haɗa zuriya da marasa mutuncin mutane irin su Abdul ba. Gaba ɗaya dauɗa ce take bin zuriyarsa babu na Allah cikin su, mussaman zaluncin da aka yi wa ɗan ta Nura, wanda hakan yake ƙara tunzurata ta ji tamkar ta yi wa ramma shegen duk ko zata huce. *** A nesa kaɗan da ƙofar gidan suka yi parking, Viper ya ce "Bari na je tukuna na dawo, ku jira ni ina zuwa" Walid ya ce "To shikenan, babu matsala" "'yar sugar am talking fa" yayi maganar yana kallon ta. Haɗe rai ta yi ta share shi, tana ta tura baki, tana son tayi masa tsiwa, amma ta kasa sai harararsa da take ta gefen ido. A zuciyarsa ya ce "Allah ya bamu ikon cin wannan jarrabawa" ya sauka daga motar, ya nufi gate ɗin gidan, yana yaba cigaban da suka samu, dan wannan gidan na su ya fi na cikin gari kyau da suka baro, nesa ba kusa ba. Ya tsaya a bakin gate ya fara bubbugawa. Wani yaro ne ya buɗe, yana cewa waye, Viper ya ce "Ka je ka ce ana sallama" yaron ya ce "To" ya koma cikin gidan, mintuna kaɗan Tijjani ya fito, kawai suka yi arba da Viper, ya kalle shi, shi ma ya kalle shi. "Me ka zo yi mana gida kuma?" "Wurin Baba na zo" "Zai fi kyau ka kira shi da sunansa kawai, ba sai ka yi masa kara ba, bayan ka kashe masa 'ya" Kai tsaye maganar ta soki, tsokar da ke tsakanin ƙirjin Viper wato zuciya, amma ya dake ya ce "Ina son ganin Baba, ka yi mini iso wurinsa" "Ba zan yi ba, baka da abin da zaka gaya masa.... "Shhh Viper ya faɗa, a lokacin da ya ɗaga wa Tijjani, rigarsa. Ya hangi ƙyallin iraƙi a ƙugun Viper "Haryanzu ina nan a yadda ka sanni, in saka maka ƙarfe, in tsallake ka, na shige gidan nan, ba zai zama sabon abu ba, a abin da na saba aikatawa ba, ka shiga ka yi mini iso da mai gidan" gummm tijjani ya rufe bakinsa. Baba kuwa ya san da zai yi baƙo, sai dai bai san wanene ba, dan an kira an tambaye shi ne kawai yaushe za a same shi a gida, ya bayar da wannan lokacin. Yana zaune a falonsa, yana karanta jarida, Tijjani ya shigo yana zazzare ido. Mama ta ce "Lafiya kai da waye a wajen ne?" Wata irin zazzafar ajiyar zuciya ya sauke, ya ce "Mijin jauhar ne a waje, wai yake son ganin Baba" gaba suka yi sak suna bin sa da kallo, a gigice Abba ya tashi ya ce "Wace jauhar ɗin? Waliyiyya dai? Kana nufin Al'amin?" Ya jero masa dukkanin tambayoyin lokaci guda. Zakiyya ta ce "Ya zo yayi mana me, ko kuma ya ce me? Shi har yana da kunyar sake tunkaro mana gida, alhalin ya kashe mana 'ya? Kenan da gasken dai sakinsa aka yi, yake yawonsa a gari yadda yake so?" Hanyar fita Baba ya tunkara, Tijjani ya riƙe shi, ya ce "Dan girman Allah baba kar ka fita, yanzun ma da makami a jikinsa, kar yayi maka illa, ba fa mun san meya kawo shi ba. Can waje kuwa, Saifu ne ya dawo, ya ajiye motarsa ya fito ya nufo shiga gida, kawai ya ga Al'amin a tsaye. Kamar mai mafarki, haka ya ƙarasa gaban gidan, yana kallon Al'amin. Ya ce "Kamar mai zamani mijin jauhar?" Viper ya kalle shi, bai ce komai ba. "Me ka zo yi mana gida, saboda rashin kunya da rashin ta ido, sai yanzu bayan shekaru shida, ka zo ka kalli fuskokinmu, kaga wani hali ka sanya mu a ciki, bayan sakayyar da ka yi mana, aka ɗauki 'ya mafi haƙuri da tarbiyya a gidanmu a ka baka, duk tausayinta da soyayyarta gare ka bai hana kashe ta ba, ka zo ka yi mana gadarar iyayen gidanka sun sanya an sake ka ne kamar yadda ka saba?" Yayi maganar idanunsa na cika da hawaye. "Har duniya ta naɗe, ka bar mana mummunan tabo a zukatanmu, tabon da ba zamu taɓa yafe maka ba, babu yadda ban yi da ita a kashe auren nan ba, amma taƙi ta dage, ita na rabu da ita tana son aurenta, ta san zaka shiryi, zaka daina duk abin da ka ke yi, amma kalli irin ƙarshen da tayi duk a dalilin rashin imaninka, wallahi ba zamu yafe ba" Viper ya ƙurasa masa ido, ya rasa abin da zai ce masa, duk da a baya ba wani shiri suke yi ba, amma yana ɗagawa saifu ƙafa, saboda yadda jauhar take yin sa, take yawan zancensa da shi da hafsa, mussaman ma shi. Tabbas ya cancanci ya shanye duk wani abu da za a gaya masa yau, komai ya samu shamuwa watan bakwai ne ya janyo mata. Cike da ƙosawa Nabila ta ce "Ni fa gaskiya na gaji, wai me yake faruwa ne?" Walid ya ce "Ki ɗan ƙara haƙuri kaɗan, za ki ga koma menene" Babu yadda Tijjani bai yi ba, amma fafur baba yaƙi tsayawa, yayi waje a sukwane. Viper yana ido huɗu da mahaifin jauhar, kawai sai ya karaya, gabansa yayi mummunan faɗuwa, bugun zuciyarsa ya ƙaru, jikinsa yayi sanyi ƙalau, ji yake yi kamar ƙafafuwansa na neman gazawa da ɗaukarsa, bai san ma da wane idon zai kalli baba ba, bai san me zai ce masa ba, rabonsa da shi tun kan mutuwar jauhar, da ya kawo musu ziyara da daddare, har Viper ya kusa abun kunya, bai san baba yana gidan ba, ya shigo yana mitar "To uwar son kuɗi, yau ba oyoyon babu ɗan karairayar, Allah ya sa ba neman kuɗin ki ka ƙule a ɗaki ki na yi ba" tana gaban baba, amma kamar ta nutse, sai da ya shiga falon ya ga baba, kamar ya juya ya koma saboda nauyinsa da ya ji. Baba yayi murmushi ya ce "Ka sanya a ranka ban ji komai ba, ni babu abin da na ji" Da kyar ya iya shiga suka gaisa, sun jima suna hira, har baban ya ba wa jauhar ruwan tofi da ya karɓo mata, wai saboda haihuwa. Ya na ta murna da ɗokin, zai ɗauki jika ta wurin jauhar. Da Baba zai tafi, Viper ya raka shi, ya cigaba da yi masa nasihar ya nutsu, ya zama mutumin kirki, saboda yana daf da zama uba, yayi ƙoƙarin zama uba nagari ga abin da za a haifa masa. Viper yayi masa alƙawarin hakan, tare da tabattar masa, duk wani abu

Chapter 89 of 121