Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
84 / 121
mana ta ishe ni. Wataran ana tsaka da bamu training, na fizgi bindigar wani, nayi yinƙurin kashe kaina, suka riƙe ni, aka ɗauke ni aka kai ni wani ɗaki, da ban zaci zan fito da rai ba. Sai da na kwana bakwai a ɗakin, ko class bana zuwa. Ranar na takwas, ogansu ya zo ya same ni, yake tambayata meye matsalata na yi yinƙurin kashe kaina. Na ce masa su mayar da ni garinmu, ina son ganin matata. Ya ce mini muddin ina son komawa gida, sai na basu haɗin kai, na yi wa ƙasata aiki, sun san ni yaron dodo ne, kuma akwai amfanin da zan yi musu, dan haka dole na mayar da hankali a kan training da kuma karatun da nake yi, kuɗi aka ware masu nauyi, saboda mu yi wannan karatun. Na ce ni ba zan yi ba, su kasheni kawai su daina wahalar da rayuwata. Ya ce ba zasu kashe ni ba, in yi abin da suka umarceni, idan ina son na ga matata. Sai na tambaye shi, matata na raye? Ya ce tana raye, zan ganta idan na daina taurin kai, nayi abin da ake so. Kuma ko ina so ko bana so, ubangidana ne ya nema mini wannan aikin, tun kan ya mutu, dan haka sai dai na mutu a process ɗin, tun da na san sirruka masu muhimmanci da zasu taimaki ƙasa. Na din ga tunanin, wane irin laifi na yi wa dodo, zai zaɓa mini wannan azabar, sai dai tsananin ɗoki, da daɗin bakin zan ga matata, ya sanya na saduda, gashi suka saka mini ido sosai da sosai, saboda suna iƙirarin bani da lafiyar ƙwaƙwalwa, kuma bana ji. Wata makaranta muke yi a russia, ilimin na'ura mai ƙwaƙwalwa kawai ake bamu, duk da na san abubuwa da yawa ni, ta online muke makarantar, a training ɗin nan aka koya mana duk wani nau'i na haɗawa da wargaza bindiga, ilimin makamai, leƙen asiri, da duk wani nau'i na abin da ya shafi harkar tsaro. Suka ce mini ƙwazona, shi zai bayar da damar komawata garinmu, har naga matata, na roƙe su ko a waya, a haɗani da matata tun da sun ce tana raye, suka ce ba zasu haɗamu ba, zan ɓata musu aiki. Na zage damtse, lokutan jarrabawa, ina cikin overollers, ina tashi da points masu kyau, na fara sabawa da wahalar training, jikina duk ya murɗe, sai dai babbar matsalata bana cikakken bacci, bana iya bacci, da na rufe idona, zan ganni a falo, tare da jauhar madaki zai kasheta, gaba ɗaya sai na tubure musu, na hau ihu. Ko abincin da nake ci, bana cin sa ta daɗin rai, saboda damuwa da tunani. Abokan karatuna a kan basu damar shan giya, har mata a kan kawo musu, amma ni duk ba wannan a gabana. Tun ina lissafi da sanya ran ƙarewar wannan wahala, naga babu rana babu wata, na zauna nayi tunani, babu yadda za ayi, jauhar na raye a gurfanar da ni a gaban kotu, a tuhume ni da laifin kisan kai, naga kawai raina mini hankali suke yi, sai kuma wata zuciyar ta ce mini ai mafarki nake yi, sai dai na rasa wanne ne mafarkin wanne ne zahirin?. A haka na shafe shekaru a wurin nan, ban taɓa barin kewayen in da muke ba, na rayu da matsanancin ƙunci da damuwa a zuciyata, wasu lokutan sai an yi mini allurar bacci nake iyawa. A haka muka kammala karatu, sauran ukun aka ce, za ayi posting ɗin su, in da ake son su gabatar da ayyukansu, ni kuma sai an yi settling issue ɗina. Mun zama sojojin leƙen asiri. Ni dai jinsu kawai na din ga yi, sauran suka din ga murna, aka shirya mana walima, sauran duk sun saba da su, ni duk yadda aka so ja na a jiki, a yi raha da ni, a saba ban yadda ba, dan ni kaina na san rabi mai hankali rabi mahaukaci nake. Abokan karatuna kuwa, basa shiga harkata, dan duk lokacin da ƙwaƙwalwa ta ta haska mini fuskar madaki, a jikin ɗaya, sai na kusa kashe shi, dan duk da training ɗin da aka bamu, na fi su ƙarfi nesa ba kusa ba, kuma ba addinmu ɗaya ba, ba ƙabilarmu ɗaya ba. Sai da na ji haushin dodo, duk da baya raye, na ji ya sakani a masifa, duk da ina fatan sanya indabo, biyan bashin abin da ya aikata ciki har da kisan dodo. Ana gobe za a mayar da ni kano, ina ta murna zan koma naga jauhar, naga ɗana, dan na san a lokacin ya yi wayo, ban san meyafaru ba, ko me suka yi mini ba, sai farkawa nayi, na ganni a prison. Hakan ya ƙara burkita ƙwaƙwalwa ta, na fara tunanin wani mafarkin na kuma yi, na din ga kiran sunayen shugabbaninmu da suka bamu training, ina cewa su zo su cika mini alƙawarin da suka yi mini, su haɗa ni da jauhar ɗina da ɗana kamar yadda suka yi mini alƙawari, gashi ko za a kashe ni, ban san sunan garin da aka kaini ba. Gandirobobi, suka yi mini dukan tsiya, wai na cika musu kunne da hauka, matar da na kashe da hannuna, bayan na sha na bugu, na amsa hakan a kotu, yanzu kuma na zo na ishe su da shirme. Suka yi mini dukan tsiya, amma na kasa daina kururuwar kiran sunaye da magiyar su haɗani da jauhar, gaba ɗaya na zama mahaukaci, ni kaina a lokacin na yadda ni mahaukaci ne. Wasu lokutan idan na buɗe jikina, ina ganin tabon raunuka da wahalar da na sha a wancan garin, amma fafur aka nuna hauka nake yi, da sambatun ƙarya. Tun da suka tabattar mini ni na kashe jauhar, na ƙara rasa tunanina, damuwa da tashin hankali suka koma sabbi fil. Kusan watanni uku, cikin dare ina kwance, dama ɗakina daban, aka tashe ni aka ce na fito, na fita na bi bayan wanda suka kira ni, aka fitar da ni wajen gate, wai an karɓi court order na tafi. Na tsaya ina kallonsu, ina mamakin wane mafarkin kuma na sake shigowa, suka rufe gate ɗin prsion ɗin, suka bar ni a tsaye. Zuciyata ta raya mini maza kafin na farka daga baccin, na je na ga jauhar, ko zan farka dai na ganta. Na fara tafiya a duhun nan, har garin Allah ya waye. rana ta ɗaga, na isa unguwar mu, ban manta hanya ba. Sai dai Abbu ya tabattar mini da jauhar ta mutu, ni na kasheta, na tafi na bar masa gida. Mutanen unguwa suka din ga kallona, har da masu gudu. Babu tunanin komai ko tsoro, bayan na je dabarmu, su Walid suka karɓe ni, suka kuma tabattar mini da cewar na rasa Jauhar. Na burkice musu, amma suka riƙe ni suna kula da ni, kawai sai ga sanarwa daga hukumar 'yan sanda, wai a kamo ni, a raye ko a mace, da fari suka ce na gudu daga prsion, daga baya kuma wai an sake ni ba bisa ƙa'ida ba. Walid ya ce "Kome za ayi, ba zasu yadda a sake mayar da ni a kulle ba, sun san ba zan taɓa kashe 'yar madara ba. Na tarar da su da ɗan mama, na san shi tun da na taɓa yi masa rauni, shi ne ya bayar da gidan da muke zaune muke ɓoye. Idan nayi kamar na gaya musu, rayuwar da nayi ana bani training, sai na tuna aikin sirri ne, an gargaɗemu a kan haka, kuma bani da evidence ni kaina bani da tabbacin cewa a gaske nayi wannan rayuwar. Bana iya bacci, bana iya cin abinci, ga azababben ciwon kai, ga nauyin ƙirji, kawai na koma shaye-shaye fiye da da, duk da a wurin training ina shan sigari da wiwi, sai dai bana shan miyagun ƙwayoyi, ko giya. Amma bayan tabattar da mutuwar jauhar, na cigaba da shaye-shaye ina fatan ko haukacewa nayi, na manta da duk wata rayuwa, wadda nake tunanin gaske ce ko mafarki, amma kayan cajin basa ɗaukata. Ganin ɗan mama na din ga yi tamkar Nura, dan ba zai fi sa'ansa ba, ya din ga yi mini biyayya, hakan ya sanya nake son sa sosai, saboda su Walid kullum cikin faɗa muke, suna hana ni shaye-shaye. Shi kuwa samowa yake yi ya kawo mini, a hakan idan na bushi iska, sai na tafi gidana na dura ta katanga, na kan yi iya ƙoƙarina nayi kuka, amma bana iyawa, sai dai na yi ta jin ƙunar rai da bugun zuciya. Na kan yi yinƙurin zuwa na ɗauki fansar abin da madaki yayi mini, amma su Walid su hana ni, suka samo mini waya keypad suka bani incase ina buƙatar wani abu, basa nan, ɗan mama shi yake yi mini duk wata hidima, kawai wannan mutumin ya fara kirana, yana ƙara dagula mini lissafi. Kayan shaye-shayen ya zama basa ɗaukata, sai dai nayi ta tamɓele, suna iya ƙoƙarin su a kaina, amma ba sa yi mini abin da nake so. Damuwa shaye-shaye suka ƙara tsunduma ni a wani hali, har nake yinƙurin kashe kaina. Ashe duk wannan abun, mutanen nan suna bibiye da ni, da duk wani motsina, na din ga ƙoƙarin jami'an tsaron kawai su kamani, su yi duk yadda za su yi da ni, amma da nayi laifi, dan goge hanyar da za abi a kama ni. Walid ya zo ya bani labarinki, na ce ƙarya yake yi, cutata zai yi. Bai haƙur ba, ya kawo mini ke, kawai ƙwaƙwalwata ta bani cewar, an haɗa baki da ke an shirya wani abun ne, dan a kuma yi mini wani mugun abun, hakan ya saka na sanya miki ƙarfe ko zan ga ainihin wacece ke, dan na san jauhar ba ta kaiki girma ba, ba ta kaiki waye ba, kuma babu yadda za ayi ta ganni ta kasa gane ni. Amma da ki ka faɗi, ciwonki ya tashi, sai na ga kin koma ita sak, duk da ina jin haushin mata wasu lokutan, amma a sanadinta nake tausayin su, saboda tunawa da ita, na sai kayan treatment ɗin ta na asma, nake ajiyewa ina kallo, ina ganin kamar zata dawo. Shigowar ki rayuwata, ya ƙara rikita mini lissafi, Walid ya ce na sanar miki irin kamannin da ki ke yi da matata, na baki labarina, amma naƙi. Na cigaba da barazanar kashe ki, saboda na kasa tantance jauhar ce ke ko ba ita ba ce, nayi ta ƙoƙarin avoiding ɗinki, kar na aikata ɓarna, saboda babu in da ki ka bar ta, sai kuma daga baya na ga zuwanki wurina, yana rage mini damuwa, kamar ke kin fahimci halin da nake ciki. Rigar da ake ta bibiyata da ita, ta wancan aikin ce, dan an tura mini saƙon zasu tafi da ni, na ƙi kulawa, sai daga baya da na amince da ke, na ga dole ina buƙatar security ko dan lafiyar ki, na amince zan tafi nayi aikin, amma sai na samu nasara a kotu. Aka ce za a ɗaukar mini lauyoyi da zasu kare ni, zasu nemi a basu ni, su suyi na su binciken, su yi mini hukunci na ce ban yarda ba, ina da lauya, tsaro kawai nake buƙata a tsare mini lafiyarki. Suka yarda da hakan, amma da zimmar zan fara yi musu aiki. Daga nan barrack ɗin kano, suka zo suka tafi da ni, aka bani kayan aiki, ciki har da tab ɗin hannuna, da rigar aiki da ki ke ganina da ita, sai dai ba kowa ya san ma'narta ba, ciki har da su Walid. A yanzu haka ina karɓar salary, kuma ina aiki da NIA, ƙoƙarin ki ne zai sanya, na yi free na cigaba da aikina, akasin haka kuma, zan iya komawa prison ne, babu ranar fitowata, duk da ba zan ce ma ban yi shekarun nan a prison ba, tun da kauwwame ni aka yi, aka hanani dukkanin walwala. Nabila tayi ƙuri da ido tana kallonsa, cike da tsantsar mamakin duk wannan rashin mutunci, da cin mutuncin doka, a Nigeria ake aikata shi. Wani abun idan bai zo kanka ya faru ba, sai ka rantse da Allah ƙarya ne ba zai faru ba. Har gara shi, da aka fitar da shi daga prison ɗin, taimakon sa aka yi ta wani fannin, wasu kuwa canza musu gari ake yi gaba ɗaya, suje su yi rayuwarsu, saboda tsabar masifa, a prsion ɗin ma bin sa aka yi za a kashe. Gaba ɗaya rayuwar Viper gaba a baya take, sai dai ita ma tata rayuwar kusan haka. "Abla, talk please, jami'an tsaro na nemana, zan je a ɗauki statement, kuma dole sai da ke zamu tafi, dan Allah ki daidaita nutsuwar ki, yanzu rayuwata tana hannun Allah, tana hannunki, nayi rejecting support ɗin da za a bani a hukumance, na zaɓi cika miki alƙawarin da nayi miki, ba zan ja da baya na barki ba" Ta ɗago idanunta da suke tsiyayar da hawaye ta ce "Wacece ni? Kuma wacece jauhar?" "Ki na ji na? Shiyasa tuntuni nake jinjina yadda zan yi miki bayanin nan, ki nutsu ki karɓi ƙaddara a duk yadda zata zo miki" Nabila ta ware masa manyan idanunta, da suka yi jawur, ta ce "Ba ni ce jauhar ba, to ni wacece? Ko jauhar 'yar uwata ce? Dan girman Allah ka kaini gidansu na ga ko iyayenta ne, wataƙila muna da alaƙa" Ya girgiza mata kai ya ce "Babu tabbacin kina da alaƙa da ita, bata taɓa gaya mini cewar tana da wata 'yar uwa ba, ce mini tayi itakaɗai mahaifiyar ta ta haifa a gidan, ta fita. Amma ke babu abin da ki ka sani game da mahaifiyarki, da ahalinta?" Ta ja wata irin ajiyar zuciya ta ce "Idan ya kasance jauhar yar uwata ce, kenan ina da 'yar uwa ban taɓa ganinta ba, ban rayu da ita ba? An cutar da ni, wallahi an zalunce ni" Viper ya ce "Kar ki ce haka, ki bari sai mun tabattar tukuna, kuma wannan amsar dole 'yan gidanku ne za su bayar da ita, amma mu fara gamawa da wannan case ɗin, kiyi haƙuri" Tari ta fara yi, tana kuka ta ce "Ni gaba ɗaya baka yi mini adalci ba, ka ɓoye mini abubuwa da yawa, da yakamata na sani, sai yanzu zaka gaya mini. Ni ka rabu da ni ma ka ƙyale ni, ina ga nima haukacewar zan yi" Duk yadda Viper ya sauke jin kansa, yake rarrashinta, ta burkice masa, ta ce idan an ga dama a ɗaure shi da igiya, case ɗin nasa ma ta fasa, ƙarshe haka ya tashi ya rabu da ita. *** "Badi'a, anya ba zan gudu na bar ƙasar nan ba, ina daf da yin faɗuwar baƙar tasa, wannan yarinyar ta dage sai ta ga bayana ta kaini ƙasa, ya zan yi ne?" Badi'a ta ce "Naja, wallahi ki ka bari yarinyar nan ta ga bayanki, kin ɗuma asara" "Badi'a, kowace hanya ta toshe ta ko ina, duk masu goya mini bayan, sun ce wannan karon lamarin yafi ƙarfin su, shi kansa Indabo yana can Abuja, yana fuskantar tuhuma, EFCC sun dakatar da wasu daga cikin kadarorinsa, yana cikin tashin hankali, na rasa yadda zan yi". "Wallahi kina guduwa asirinki zai tonu, ki jira kiga iya gudun ruwansu, tun da haryanzu ba su ce komai ba, ba su tona miki asirin ba" Kamar ta fasa ihu ta ce "Yanzu jira zan yi sai sun fito sun tona ɗin? Ke kin san ba zasu bar ni ba, lallai ɗan hakin da ka raina, shi ke tsole maka ido, babu ƙoƙarin da ban yi na kawar da yarinyar nan ba, amma abu ya gagara, amma duk da haka ba zan zuba ido ba, sai na san abun yi". *** Abdul kuwa ya yi sintiri tsakanin Kano da Abuja, babu adadi, amma ya kasa ganin Indabo, hakan ya sanya ya tabattar wa da kansa cewar Indabon ne ya ɗauke ramma. Duk yadda mahaifiyar ramma, ta bugi cikinta, ramma ta nuna mata babu abin da ya faru, Abdul ajieta kawai yayi, duk da ya ce ya aureta. Maman ramma ta ce "Har na ji sanyi, dole a zo a raba auren nan, dama ba da yardata kawunki ya aurawa wannan tsohon mara mutunci ke ba, saboda kuɗi da tsinannen son abin duniya yayi mini haka. In sha Allah yaron nan sai Allah ya tozarta shi kamar yadda ya tozarta mu, sai Allah ya wulaƙanta shi, kamar yadda yayi mana" jin Addu'a ramma tayi har cikin zuciyarta, dan sai da cikinta ya motsa, tayi shiru bata amsa da Amin ba, ta san duk inda yake yana can hankali a tashe. "Amma ramma, kin tabattar ba abin da ya haɗaki da mutumin nan? Mutumin da yayi miki fyaɗe shi ne zai aure ki kawai ya ajiye ki?" Cikin tsoro da rashin gaskiy, ramma ta ce "Eh, ɓoye ni yayi saboda kar asirinsa ya tonu, cewa aka yi da ya kashe ni ma, shi ne bai kashe ni ba. Kuma wai ya biya mini kuɗin makaranta na cigaba har jami'a" "Allah ya kiyaye, ba ma buƙatar duk wani abu daga hannunsa, da haka zai yaudaremu, in sha Allah sai an hukunta shi, barrister nan tayi mini wannan alƙawarin, sai an gurfanar da shi, ya girbi abin da ya shuka, ga kisan kan da suka yi wa wannan tsohon, da suka ƙalawa sharri, Allah dai ya watsa shi, daga shi har wanda suke goya masa baya" Ramma ta kawar da zancen, ta hanyar cewa "Mama wai a nan zamu yi ta zama?" Ta ce "A'a, nima wannan Alhajin ne ya saka aka ɗaukko ni wai idan aka bar ni, nima za a iya cutar da ni, ban san zuwa yaushe zamu zauna a nan ɗin ba, amma ina ga da komai ya daidaita sai mu tafi" Ramma ta jinjina kai. Maman ramma ta bi ta da ido, ganin yadda duk jikinta yake a sanyaye, ta kalli fatar ramma yadda tayi haske take ta sheƙi. "Rahama" "Na'am mama" "Wai me ki ke ci ne a hannun nasa, na zata a wahale zan ganki, ki gaya mini tsakani da Allah idan akwai wani abu" "Mama babu komai fa, nifa tun da ya ajiye ni baya ƙasar, sai masu kula da ni" mama ta jinjina kai kawai, ba ta sake magana ba. Viper ya haƙura da azabar kishin da yake ɗawainiya da shi, aka yi zama na musamman da shi da Alhaji mu'zzam, da shugabannin sa, aka sake jaddadawa Al'amin, Alhaji mu'azzam tainakonsa yayi, kuma tare da haɗin kan Alhaji mu'azzam komai ya tafi daidai, kasancewar sa babban mutum a ɓangaren harkar tsaro. Sai kuma aka yi masa alƙawarin ba shi duk wata kariya, da shi da Nabila, tun da haka ya zaɓa, amma muddin suka yi failing a shari'a a kotu, babu wani abu da za a kuma sake yi masa. Ya ce ya amince, babu gudu babu ja da baya Nabila ce lauyar da zata tsaya masa. Sai dai Nabila gaba ɗaya ta hargitse, Viper ya kasa gane kanta, gashi an gayyace shi hukumar yan sanda, ya je ya bayar da bayani, amma Nabila fafur ta ce ba zata je ba. Sanarwa kuma ta fita, muddin Viper bai kai kansa ba, order kotu zata koma arrest order. Nabila na zaune, zuciyarta a cunkushe ta rasa abin da yake yi mata daɗi, lallai tana buƙatar ganin Abba, ko ta halin ƙaƙa Viper ba shi da niyyar yi mata bayanin abin da take son ji. Ta ga wayarta a gefen gadon da take kai, tayi sauri ta ɗauka, ta kunna tana dudduba saƙonni. A What's app ta tarar da message, wai gari ana ta yaɗa rumors, cewar Viper ya saceta, ba a san in da take ba, wasu suna Allah ya ƙara, wasu suna yi mata addu'a. Ta buɗe message ɗin Nasir, ta saurari voice message ɗin da ya turo mata. "Haryanzu wanda ki ke iƙrarin karewa, bai bayyana a gaban hukumar yan sanda ba, idan ya wuce wa'adin da muka bashi, order kotu zata sauya, ga shela da ake ta yi, na cewar ya sace ki, ba a san in da ki ke ba, ko a nan sunanki ya ɓaci, am did on you. Knocking aka yi, tayi shiru, dan ta zata Viper ne, ta ajiye wayar. Wani narkeken mutumi ne ya shigo, tare da barrister Habib, da sumayya, da kuma Walid. Zama tayi sosai tana kallonsu, sumayya ta ƙarasa ta zauna a kan gadon ta ce "Nabila, ya kike kina cikin ƙoshin lafiya?" Nabila ta jinjina mata kai. Mutumin ya ce "I salute you barrister, kallabi tsakanin rawuna" yayi maganar cikin gurɓatacciyar hauss, amma da alama ya ji hausa. Ta ɗan yi murmushi yaƙe, ta kalli Walid ta ce "Oga walid" "Na'am barrister, ya ki ke ya ƙoƙari?" "Alhamdilillah" ta din ga bin su da ido, dan bata san dalilin zuwan su duka ba. Walid ya ce "Barrister, na san mun yi miki laifi, tun da fari na so Viper yayi miki bayani, amma yaƙi, kin san shi wasu lokutan da taurin kai, kuma na san kin yi haƙuri da shi, amma dan Allah ki janye batun cewar ba zaki tsaya masa ba, ki yi haƙuri dan Allah, ba zamu iya jure ganinsa ya koma prison ba, kiyi wani abu a kai, wanda kuke ƙalubalanta, suma ba zasu zauna haka ba, dole zasu yi ƙoƙarin yin wani abu suma, ki taimaka" Ɗaya mutumin ya ce "Duk wani support da zamu ba shi a hukumance, yaƙi yarda, ke kaɗai ce hope ɗin sa, kar ki ce a'a, kiyi haƙuri, a ƙarasa wannan case ɗin, sai koma menene ya biyo baya" "Meyasa ya ɓoye mini abubuwa irin wannan?" "Tsarin aikinmu ne a haka, haryanzu ke kaɗaice lauyar sa, ke ki ka sani, su kansu yanzu da muka zo tare ba komai suka sani ba, ga abokin aikinki, dole kina buƙatar sa, ga ƙawarki kina buƙatar ta, ga abokansa da sun san komai" Barrister Habib ya ce "Ga case ɗin ramma ma" Mutumin ya ce "Yess, ke fa yanzu idon duniya yana kanki, ba laifinsa bane, kin san ba mai yawan magana bane ba, kuma tsarin aikinmu ne, yanzu abin nan da ya gaya miki, zai iya zama da hukuncin kisa a kansa, banda mun san a situation ɗin da yake" Walid ya ce "Yana asibiti ma, ciwon cikin nan da yayi kwanaki ya kuma tayar masa, hantarsa ta kumbura, yana asibitin sojojin nan da aka ɗaukko ki" Nabila ta numfasa, ta ce "Muje zan ganshi, kuma ina son zuwa office ɗina, zan koma aiki" Mutumin nan ya ce "Is ok, zaki koma bakin aikinki, amma a ƙarƙashin kulawar mu, ƙasarmu na san rayuwar Viper" "Amma ku ka bari ya kusa haukacewa, aka ɓata masa suna" mutumin yayi murmushi ya ce "We are trying our best now" Sumayya ta ce "Nabila ina son magana da ke fa" "Ni da nake kare ɗan ta'adda, me ki ke so a wurina?" Sumayya ta yi murmushi ta ce "Arfan Abbanta, an buga dake an barki, batutuwa ne masu muhimmanci, amma sai kin saukko tukuna" A cikin wata rantsatsiyar mota, aka ɗauki Nabila da sumayya, da barrister Habib, suka tafi. Liti ya ƙarewa ɗan mama kallo ya ce "Ɗan mama, ni haryanzu mamaki nake yi, yaushe Viper ya san wannan mutanen bamu da labari ne? Wai naga sojoji ne suke kula da shi, duk ka munafunce mu" "Nima ban san meyasa ba" "Ƙarya kake yi munafiki, ka san komai, meye haɗin Viper da sojoji? Ko ka gaya mini ko na ɓulaka da wuƙa" Ɗan mama ya ce "Wallahi oga liti muka yi misbehaving, zanemu za ayi daga ni har kai a barikin nan, dan Allah kayi haƙuri ka rufa mana asiri" "Ni haryanzu tsoro nake ji, idan ba haɗa kai aka yi da kai, ake son a kashe mu ba, ko a haɗamu a cikin yan boko haram ace duk su ne ba, gaba ɗaya baka da imani ɗan mama, tsawon lokaci kana jakadancin munafunci" Suna cikin maganar, su Nabila suka shigo wurin, ba wanda ake bari ya shiga wurin Viper, su liti ma a waje suke. Aka ce Nabila ce kawai zata shiga wurin Viper. Ta taka a hankali ta shiga, ta tarar yana kwance, likita yana yi masa allura ta cikin cannula. Suka gaisa da likitan, ya gama yi masa ya fice, ta zauna ta kalleshi ta ce "Effect na shaye-shaye yana ta bibiyarka" ya yi shiru yana kallonta. "Idan ɓoye mini waye kai, ba laifinka bane tsarin aikinka ne, ni kuma ɓoye mini wacece ni, laifinka ne da wasa da hankalina. Ba zan watsar da alƙawarin da nayi maka ba, gobe in Allah ya kaimu zamu je station, zamu bayar da statement, amma bisa ga sharaɗi ɗaya da sai ka yadda da shi" Ya lumshe idanunsa ya buɗe

Chapter 84 of 121