bai ta san hanyoyin hukunta shi. Sakin guntuwar sigarin yayi, ya koma ɗaki ya kwanta ya cigaba da tunaninta.
Da haka wani nannauyan bacci ya ɗauke shi, sai dai kasancewar da ita ya kwanta a ransa, sai ya din ga mafarki da ita, mafarki mai cike da shauƙi da nishaɗi irin na ma'aurata.
"Master salla fa, zaka rasa sallar asuba." tayi maganar tana shafa sumar kansa.
Ƙanƙameta ya ƙara yi, yana tura kansa cikin wuyanta, da yake fitar da daddaɗan ƙamshin turaren da yake matuƙar son jin tashinsa daga jikinta.
"Viper wai ina zaka shiga a cikin pillown nan ne? Wai ko dai ka sha wani abu bamu lura ba, tun ɗazu fa muke tashinka, ka tashi mu yi salla dan Allah"
A hankali ya motsa, ya buɗe idonsa ya ga hasken fitilar solar, ya haske ɗakin, sai a lokacin ya lura da ya ƙanƙame pillow.
Yayi miƙa tare da yin salati, ya kalli liti da yake tsaye a kan sa ya ce "Akwai gas ne?"
"A'a ɗan kaɗan ne sosai, sai an yi refiiling ma zamu iya dafa karin kumallo".
"Ɗora mini ruwa, ku yi sallarku zan yi wanka"
"Wai Viper meyake faruwa ne kwana biyun nan, ko ka fara dawowa bil adama ne? Ni ina cewa ka yi wa addini hidima meyake faruwa"
Ashar Viper ya yi masa, ba shiri liti ya ce "Allah ya baka haƙuri, ya ƙara lafiya"
Walid kuwa dariya yayi, ya ce "Allah ya ƙara, uban son jin ƙwaƙwaf".
Bayan sun karya Baba ya kira Viper a waya, ya ɗaga suka gaisa, ya ce "Aminullahi, dan Allah idan baka komai zuwa azahar ina son ganinka"
"To Baba in sha Allah zan zo, nan gidan zan zo na same ka?"
"Eh dan Allah"
"Zan zo in sha Allah"
"Yauwwa Allah ya yi maka albarka"
Viper ya amsa da Amin.
Ɓangaren Nabila ita ma kwanaki bakwan nan da suka yi, ba sa magana da Viper, abin ya dameta, ƙishirwar son ganinsa ta addabeta, ga ayyuka sun fara yi mata yawa, 'yat shaharar da tayi ta kwanan nan, ya sanya take ta samun cases ko ta ina.
Ban da masu nuna suna sonta, manyan mutane da suke sonta da aure.
Yau da mafarkin da tayi ta tashi a zuciyarta, mafarki tayi da mai kama da ita, wadda take da tabbacin jauhar ce.
Tana nuna mata inuwar mutumin da yake ɗaure cikin sarƙa a baya, yanzu babu sarƙar, sai dai daga yanayin inuwar tasa, kamar a galabaice yake, duk da babu sarƙar sai tangaɗi yake yi.
Tana murmushi ta cigaba da nuna mata shi, ta nufi in da take nuna mata, sai dai da ta waiwaya ba ta ganta ba, tana ƙoƙarin ƙarasawa in da mutumin yake, kawai ta farka daga baccin.
A hankali ta furta Viper, a gurguje ta shirya, tayi ta trying lambarsa, amma yaƙi ɗagawa, ta din ga jin ko me zai yi mata, yakamata ta kira shi, ta ji ya yake.
****
Ko da Viper ya je gidan su Jauhar, ya tarar da motoci a ƙofar gidan, bai damu da ko me ake yi ba, ya kira Baba ya ce masa gashi nan yana ƙofar gida.
Baba ya ce ya shiga kawai, ya ƙarasa ya shiga, babu wanda ya kula a mutanen gidan, sai hafsa da suka gaisa ya shiga ɗakin Baba.
Alhaji mu'azzam ya tarar, da Abbu, da kuma shi kansa Baban.
Gefe ya samu ya zauna a ƙasa ya gaishe su, sai dai da ya zo kan Abbu kamar an yi masa dole, haka ya gaishe shi.
"Ya gida ya ƙoƙarin Kuma?" Baba ya tambayi Viper.
"Lafiya ƙalau Alhamdilillah"
"Ina yan uwan naka?"
Viper ya ce "Su na gida, nikaɗai na zo".
Baba ya ce "babu laifi, Al'amin"
"Na'am Baba"
"Na san zaka yi mamakin kiranka da muka yi, babu tsammani da wuri haka.
To bakomai bane ya janyo, Nabila ta same ni, tayi mini wata magana ne, kuma nima naga hakan yakamata, duba da yadda abubuwa suka wakana.
Al'amin su iyaye, ba a fushi da su, kuma duk lalacewarsu iyaye ne, balle babu lalacewa a cikin iyaye, yakamata ka sasanta da mahaifinka, yanzu ina jauhar, ina mahaifiyarka, ina ɗan uwanka, ko da kuɗi ba zaka sake ganinsu a gidan duniya ba. Dan haka ka yi haƙuri, mun san mu masu laifi ne a wurinku, amma ku yi haƙuri a yafe ya wuce dan Allah ba dan halinmu ba".
Viper ya yi shiru, kamar mai nazari amma bai ce komai ba.
Abbu ya ce "Al'amin, nauyinka da nake ji, ya sanya na kasa nemanka gaba da gaba na nemi afuwarka, na san in dai dan halina ne, da abin da na aikata maka, ba zaka sake kallona a matsayin mahaifi ba, amma ba dan halina ba domin Allah.
A ƙaddarar rayuwarmu, na ɗauki darasi da dama, daga illar da mutum zai yi wa rayuwarsa, shi ne auren mace domin buƙatarsa kawai, ba tare da tunanin abin da gobe ka iya haifarwa ba.
Duk da ni a zatona dan gobenku na auri Rahila, amma ta ci amanata, kuma nima na san da laifina na rashin bibiya da tantance abin da take ɗora ni a kai, amma dan Allah ka yi haƙuri Al'amin, ka yafe mini ka dawo gida mu yi rayuwa a ɗan abin da yayi mini saura na rayuwata"
Alhaji mu'azzam ya ce "Viper, ka yi haƙuri dan Allah, duk wani abu da ya faru, ya wuce tun da bawan Allah nan shi yayi silar zuwanka duniya, kuma wani abin idan bai yi maka ba, wani yayi maka, yana cikin tashin hankali da damuwa sosai"
Viper ya numfasa ya ce "Ko a baya ni ban ƙi Abbu ba, ina matuƙar ƙawazucinsa da son kasancewa tare da shi, Abbu shi ne ya ƙi ni ya kore ni, amma tun da yanzu ya nemi na dawo shikenan, ya riga ya wuce. Amma ni a yanzu na girmi zaman gida, ba zan iya rabuwa da su Walid ba, sai na tabattar da rayuwarsu ta inganta suma, kamar yadda suka rayu da ni lokacin da kowa yake mini kallon mara amfani.
Kuma idan na koma gidan nan, zai iya cigaba da haddasa husuma, wanda ni kuma bana fatan hakan".
Abbu ya ce "Hakan ma na gode Al'amin, Allah ya ƙara shirya mini kai, dan Allah idan ka samu dama, ko zuwa gobe in Allah ya kaimu ka zo gida, ina son mu yi wata muhimmiyar magana da kai"
Viper ya jinjina kai, Baba ya ce "Bari a kawo abinci mu ci baki ɗaya"
Al'amin ya ce "Baba ayi mini uzuri dan Allah, ana jirana ne, ayi mini afuwa" ya fita ya sanya takalmansa ya tafi.
Rarrashin Abbu suka din ga yi, saboda yadda jikinsa yayi sanyi, dan gani yake yi, kamar da wani abun a ran Al'amin haryanzu, duk da ya san halinsa farin sani, ba kowane lokaci ake iya gane yanayin sa ba.
***
Washegari Nabila ta kira Abbu a waya, domin ta ji ya ake ciki, ko Al'amin ɗin ya saukko?.
Abbu ya ce "Kin san ɗan nawa hukuma ne sai da rarrashi, ya ce dai ya wuce, amma bai tsaya mun ci abinci tare ba, yau dai ina jiransa, ina son ya zo zamu yi magana da shi, idan ya zo kin ga sai na ɗan ƙara saka ran ya saukko ko?"
Sai ya ba wa Nabila tausayi, ta ce "Abbu ka kwantar da hankalinka, Viper yana sonka haryanzu, shi ba abubuwan da ka yi masa ne suka dame shi ba, korar da ka yi masa ce kawai ta tsaya masa, amma tun da ya ce maka ya yafe, ya yafe ɗin ne, dan Allah ka kwantar da hankalinka Abbu, idan ma bai zo ba na yi maka alƙawarin kawo maka shi har gida in sha Allah"
Abbu ya ce "To shikenan, na kwantar da hankalina, Allah ya saka miki da alkhairi"
"Amin bakomai Abbu, sai anjima"
Shahida ita tayi girke-girken zuwan Al'amin, Rahila na gefe tana kallonsu, sai yan surutai take da ƙanan maganganu saboda ƙwaƙwalwarta ta riga ta taɓu, amma har aka yi sallar magariba Viper bai zo ba.
Hakan ya ƙara sanya Abbu karaya nesa ba kusa ba, domin kuwa yana da muhimmiyar magana da yake so su yi.
Shahida tayi ta ci gaba da bashi haƙuri, amma a washegari ma still babu Viper, babu dalilinsa, tun Abbu yana sanya ran ganinsa har ya sare.
****
Viper yana ganin kiran Nabila, amma ya shareta.
Message ta turo masa "Ka ɗaga wayata, is an emergency"
Sai da ta kusa katsewa, sannan ya ɗaga yana hura hanci.
"Vi wai dan Allah meyake damunka ne, kai mutum nawa ka yi wa laifi kai ko neman yafiyar ma baka yi, kai shikenan komai naka babu sauƙi, Abbu ya nemi afuwarka, amma ka yi burus, ya ka ke so yayi ne?.
Idan shi ma ya mutu sai ka huta, ni dai nayi iya yi na, sauran na bar wa Allah, ban san ya zan yi maka ba kuma, Abbu yana Asibiti ya yanke jiki ya faɗi, ana addu'a Allah ya sa ba ɓarin jikinsa ne ya taɓu ba, yana ta kirana a waya, yana gaya mini kamar baka yafe masa ba, ya nemi ka je ka ƙi zuwa, to yanzun ma Viper idan ka yi ra'ayi ka je, idan ba ka yi ra'ayi ba shikenan, ni fara gajiya da halinka"
Ba tare da ta kashe wayar ba, ya ajiye wayar, yana duba agogon hannunsa, sauran awa ɗaya ya shigo garin Kano, ranar da ya baro wurinsu, aka tura shi Jos, kuma yana sane da kiran da Abbun yayi masa, dajin da yaje ko network babu.
Sai dai ƙirjinsa ya din ga bugawa, hankalinsa yayi mummunan tashi, ya shiga fargaba da zullumin rasa abu mai muhimmanci a rayuwarsa karo na babu adadi.
Ayshercool
08081012143
98
Shiru yayi yana dubanta, domin ya tabattar idan da gaske take, sai dai yanayin fuskarta ya tabattar masa da gaske take yi ba wasa ba.
Basarwa yayi ya ce Shikenan su tafi, amma deep down ya ji zafin abin da ta yi masa nesa ba kusa ba, he wish 'yar madararsa tana raye, da ya san ita ba zata watsa masa ƙasa a ido ba, kamar yadda Nabila ta yi yanzu ba.
Dan rashin kunya, su na tafiya a hanya kuma, ta na yi masa hira da surutu, ganin ya yi mata banza, ya sanya ta ja bakinta ta tsuke, kuma ta tabattar fushi ya yi.
A hanya ya sauka, ya bar ta da Joseph, ya mayar da ita gida, shi kuma yayi nasa wuri.
****
Washegari da yamma, Abba yana gidan gonarsa, yana office ɗin sa, ana ta fitar da ƙwai na kaji, da na sauran tsuntsaye ƙaton gidan gona ne sosai da sosai, gidan gonarsa na cikin manyan gidajen gona da yake fitar da ƙwai, har maƙwabtan garuruwa. Da su kansu kajin da kifaye, ban da sauran dabbobi.
Masinja ya sanar da shi ya yi baƙo, Abba ya ce a shigo da shi.
Mintuna kaɗan aka buɗe ƙofar Office ɗin aka shigo, ajiye biron hannunsa ya yi yana kallon Viper.
Viper ya yi sallama, Abba ya amsa a hankali yana ci gaba da kallonsa.
Ya ƙaraso ya tsaya, ya gaida major cikin girmamawa kamar yadda suke yi a tsakaninsu masu ɗamara, hakan ya tabattar wa Major akwai wani abu tattare da baƙon nasa. Ya bashi dama ya zauna.
Viper ya ce "Duk mun taɓa haɗuwa ba na da tabbacin ko ka gane ni, amma bari na sake gabatar maka da kaina, sunana Al'amin Ibrahim, wanda 'yar ka Nabila ta tsayawa a kotu, kuma mijin 'yar uwar Nabila da Allah ya yi wa rasuwa"
"Mijin wadda ka kashe dai, da babanta bai san ciwonta ba ya ɗauketa ya aura maka. Ta yaya zan kasa ganeka, da ka ɓata mini shirina na shekara da shekaru ka ɗauki Nabila ka haɗata da babanta, mutumin da bai martaba rayuwar uwarta da ta 'yar uwatta ba har ya iya aura maka ita ka kasheta".
"Ba ni na kasheta ba, kamar yadda kotu ta tabattar kuma ta wanke ni, ina roƙonka saboda Allah, kar laifin da ba namu ba ya shafe ni da ni Nabila, mussman ma ita.
Makamancin abin da ya faru da Jauhar, irinsa ne a rayuwata, da ya jefa ni cikin ƙaddara. Duk wannan mummunar rayuwa da nayi, ta samo asali ne daga rashin samun ingantaccen bangon da zan jingina rayuwaya da shi, sai da ƙaddara ta saka aurena da Jauhar, ba zan taɓa mantawa da ita ba har duniya ta naɗe, kuma ban kashe jauhar ba.
Kamar yadda kotu ta tabattar, duk da na fuskanci mutum ne kai irina, muna amfani da ƙwaƙwƙwarar shaida da muka gani a zahiri ne, ba dan haka ba, ba zan so na baka wata gamshashshiyar hujja da shaida da zata tabattar maka da Nabila a kan dai-dai take, kamun da aka saka ɗanka yayi mini ba bisa ƙa'ida bane ba.
Da fari hukumar'yan sanda ce ta bashi umarnin, daga baya kuma an bashi maƙudan kuɗi dan ya kama ni, hakan ya sanya ya din ga ɓata Nabila a idonka. Duk ban gaya maka wannan abun da raba maka kan iyalinka ba, roƙonka kawai nake yi, ka daina fushi da Nabila, duk da ganin mahaifinta da ta yi, a duniya ba ta da wani wanda ta shaƙu da shi take ƙauna sama da kai. A madadinta ina mai ƙara baka haƙuri, domin kuwa na san duk ni ne silar komai, amma dan Allah na roƙe ka, ka yi haƙuri ka yafe wa Nabila da mahaifinta, ci gaba da fushi da ita, zai kua jefa rayuwarta a cikin damuwa"
"Ka gama?" Major ya yi maganar yana kallon Viper.
Viper ya yi shiru bai ce komai ba.
"Na ji na kuma gode, amma ka tashi ka tafi, ka ɓata ruwa ba domin ka sha ba, ka ɓata mini haɗin kan iyali"
"Abba ban ɓata maka kan iyali ba, son abin duniya ne ya rinjayi Nasir, ya ƙara ta'azarra al'amarin, ina sake baka haƙuri, saboda Nabila kar azo ta shiga wani halin" ya na gama maganar ya tashi tsaye ya fice daga ofishin.
Bayan fitarsa Major ya yi shiru yana kallon ƙofar da ya fita, da nazartar maganganun da ya yi.
Gaba ɗaya Viper ya daina kiran Nabila a waya, ita ma kuma ba ta neme shi ba, hakan ya ƙara tunzura shi, ganin yadda ta watsar da shi gaba ɗaya.
Major ya so ya yi wa Nabila maganar zuwan Viper in da yake, amma yayi mata shiru ya rabu da ita.
*****
Satin awon Ramma ya zagayo, Nabila ta je ta ɗauki ramma, suka je asibiti. Aka yi mata awo aka duddubata, komai nata lafiya ƙalau.
Su ka tsaya suka yi sayayya, suka tafi prison. Ramma sai murna take yi tana jin daɗi za ta ga Abdul.
Saboda yadda Nabila ta zama popular yanzu, duk in da ta shiga an santa, tana samun alfarma, yau ma har ciki aka shiga da su.
Aka je aka fito musu da Abdul, yana ganin ramma ya saki murmushi, ita ma murmushin ta sakar masa, ta miƙe tsaye ba tare da ta san ta miƙe ba.
Nabila ta ce "Bari na baku wuri, idan kun gama ma gaisa" ta fita waje, bai damu da gandiroban da yake wurin ba, ya rungume abar sa.
Ta ce "Doctor ya jikin ka warware?"
"Inyee an daina gantsara mini sunana, Abdul yasar"
Ta saki murmushi ta ce "Ko dan saboda wannan ai yakamata na fara saye sunan" tayi maganar tana nuna masa cikinta, da ya kai watanni shida ya fito sosai.
Murmushi yayi ya zira hannunsa cikin hijjabinta, ya shafa cikin nata.
"Ina fatan dai wurin awon babu wata matsala da babyn namu?"
Ta ce "Anty Nabila tana kula da ni sosai, tana kai ni awo"
"To ki na cin abincin da shan maganin dai ko?"
Ta jinjina kai ta ce "Eh, kawai dai ina son na ga ka fito ne, ina cikin damuwa tsareka a wurin nan"
Ya kalli wurin ya ce "Kar ki damu, ai na riga ma saba kuma ba wata wahala nake sha ba your excellency, kewarki nake tayi ne dai kawai, amma yaya zasu bar mu mu cigaba da zaman aurenmu?"
Ta rausayar da kai, ta ce "To gashi nan dai, ban san ya ake ciki ba, basu sake cewa komai ba. Ina son in roƙi Anty Nabila, ta ɗan ƙara lallaɓa mini su, amma nauyinta nake ji".
Ya ja hannunta suka zauna, ya ce "Ni zan roƙeta, ko sake durƙusawa zan yi a gabansu na basu haƙuri, ni dai su bar mini ke babyna, da ke jaririnmu mu rayu tare ko Rahamana?"
Ta jinjina masa kai, ta numfasa ta ce "To yaya yanayin abincin kana samu ka ci kuwa?"
"Eh mana, komai nawa normal kawai dai ina tsare ne, ki kwantar da hankalinki, ki rainar mana babynmu, ina fatan lokacin da zan fito yayi dai-dai da lokacin da zaki haihu, a karɓi haihuwar nan da ni. Na so ni zan kula da ke ayi rainon cikin nan da ni"
"To yaya zamu yi, kana naka Allah ya sa shi ne dai-dai, Allah ya fito mini da kai lafiya"
Abdul ya dafa kafaɗarta ya ce "Naki ne ni?" Ta jinjina masa kai cikin jin kunya tana murmushi.
"Naki ne ni rahama, ƙaddararmu ce ta zo mana a hagunce, amma mun gode masa Allah ya sassauta mana, ya sanya su barmu mu yi rayuwarmu ta aure"
Ta ce "Amin, bari ta zo ku gaisa, mu tafi, na san yanzu za su ce mu tafi"
Ya marairaice ya ce "Haba dai, kwata-kwata yaushe ku ka zo, ban gaji da ganinki ba, yayi maganar yana sumbatar goshinta.
Gandiroba ya ce "To sharokhan baban soyayya, lokaci yayi"
Abdul ya yi murmushi ya ce "Ai shi sharokhan na shi film ne, ni kuwa soyayya ce ta zahiri, dan haka ni na fi shi ma" yayi maganar yana dariya.
Nabila ce ta dawo, suka gaisa da Abdul, sai dai da ta ga farinciki a fuskokinsu, sai ta ji daɗi.
"Ina godiya sosai da sosai, rahama ta gaya mini yadda ki ke kula mini da ita da babyna, Allah ya saka miki da alkhairi"
Nabila ta ce "Amin, ai yi wa kai ne, rahama ƙanwata ce, ina jin daɗin ganinta cikin farinciki. Nayi mamakin yadda aka yi ka yi mata laifi kamar wannan kuma ka iya dasa soyayyarka a cikin zuciyarta. Meye sirrin ne?"
Yayi murmushi ya ce "Ita zaki tambaya ai"
Ramma ta harare shi ta ce "Ba wani sirri, ban da faɗa me ka iya?"
"Soyayya" ya bayar da amasa kai tsaye, da sai da ramma ta ji kamar ta nutse.
Suka yi dariya, ya sake cewa Nabila "Dan Allah na ga kamar ke kina tausaya mana, dan Allah ki rarrashi mama, ki ba ta haƙuri su bar mana aurenmu dan Allah"
Nabila ta sauke numfashi ta ce "To bani da ta cewa ne, idan na matsa yayanta hayayyaƙo mini zai yi, amma zan lallaɓa ta ɓangaren mama na cigaba da shawo kanta, in sha Allah komai zai wuce"
Ya ce "Na gode sosai da sosai, Allah ya saka da alkhairi. Idan da wani abu ko kuɗi sun yi kaɗan, ayi mini magana"
Nabila ta ce "Kai wane irin kuɗi sun ƙare, wannan maƙudan kuɗi har haka, akwai kuɗi sosai in sha Allah ba wani abu"
Ya ce "To shikenan, muna godiya sosai barrister, babyna sai yaushe kuma?" Ramma ta galla masa harara, amma bai fasa ba, ya riƙe hijjabinta, ta waiwayo ta fizge ta na murguɗa masa baki.
Shafar sumar kansa ya yi, yana dariya, suka fice ita da Nabila.
Suna tafe a hanya, Nabila ta ce "Ramma har mamaki ku ke bani da ke da Abdul, dan Allah me Abdul ya yi miki, har ki ka fara sonsa, duk da girman laifin da ya aikata miki?"
Ramma ta jinjina kai ta ce "Na san da yawa ba za su fahimce ni ba, za a zata ko kwaɗayin wani abu ne na hannunsa, ko kuma wani abu nake yi wa, wanda ni har muka rabu ban san menene auren ba, kawai dai ina jin daɗin shiryuwar sa a dalilina. Kuma yana da wasu nagarta, wanda shi kansa bai san yana da ita ba. Da ya samu isashshiyar tarbiyya, ba zai yi wasu abubuwan ba.
Ya nuna tsantsar nadamarsa, gani nake idan na rabu da shi, zai iya koma wa ruwa, duk da da gaske, yake tuba a kan abubuwan da yake aikatawa. A matsayin ya aureni, ya tabattar mini da ya aure ni, babu irin zagi da rashin mutuncin da ban yi masa ba, amma ko a jikinsa, bai taɓa damunsa ba, kawai zai yi abin da ya ga dace yayi domin ya kyautata mini, ko na yaba ko na kushe bai dame shi ba.
Sannan daga halayensa masu kyau, yana da tausayi da taimako, mutum ne mai kyauta ta ban mamaki, kuma ya san aikinsa sosai da sosai, ina duba wannan abubuwan ne, amma ni kaina na san ta wani ɓangare kamar ban kyauta wa kaina da mama ba"
Nabila ta ce "Kar ki ce haka, wannan shi muke kira da jarrabawa, Allah ya jarabce ka ya ga yaya zaka yi? Bar ganin Abdul ba ya ji, wallahi sai ki ga saboda yawan kyautarsa da taimakonsa, ya sanya Allah ya din ga ji da shi, maybe shiyasa ya sanya tsautsayin nan a tsakaninku, domin ya rabauta ya tuba, yadda ya daina zina within shot period of time da ku ka zauna, ya cancanci a yaba masa daga ke har shi, ina fatan Allah ya tabattar da alkhairi a zamanku, ya sanya sanadin shiriyar sa kenan, idan Allah ya tabattar da zamanku, ki yi ƙoƙari ki rufa masa asiri, ki zauna da shi da zuciya ɗaya, ki yafe masa".
Ramma ta ce "In sha Allah Anty, na gode sosai da sosai, Allah ya nuna mana aurenku ke ma, da Yaya Al'amin"
Nabila ta kalleta ta ce "Da wa? Wannan yayan naki ai sai Jauhar ɗin, Allah ya bashi mace ta gari dai ba Nabila ba" Cikin mamaki Ramma ta ce "Amma Anty Nabila saboda me? Wallahi yana da kirki, yana da faɗa ne dai kawai"
"Wasu dalilai rahama, ki manta kawai, ba soyayya muke yi ba dama, kawai dai nima yayananne"
Jiki a sanyaye ta ce "A'a shi sonki yake yi"
"Yaya aka yi ki ka sani, shi ya gaya miki?"
"Ni a wa zai gaya mini, bai gaya mini ba, amma wasu lokutan irin kallon da Abdul yake yi mini, yake yi miki. Idan mutane sun kai goma a wuri, duk wanda zai yi magana ba zai damu ba, amma da kin fara magana, zai tattara nutsuwar sa da hankalinsa a kanki. Ko wani abin ki ke yi daban, yana kallonki ta ƙasan idonsa"
Kwashewa da dariya Nabila ta yi, ta ce "Kai rahama, haka ki ke saka masa ido kina kallonsa, ke duk a ina ki ka san hakan shi ne so?"
"Wurin doctor, amma Wallahi yana sonki"
"Daina rantsewa rahama, Viper mace ɗaya tak yake so a duniya, kuma yanzu ba ta raye, babu kuma macen da za ta iya maye gurbinta, dan haka ki manta kawai"
Rahama ta ce "Shikenan, tun da kin ce haka, amma ai kamarku ɗaya ita, kema yana sonki, ina ga dai ke ca ba kya sonsa kawai" Rahama tayi maganar cikin sanyin jiki sosai, dan tana son ta ga sun yi aure, dan sun dace sosai.
****
Abubuwa suka din ga damun Major, game da maganganun da Viper ya gaya masa, sai ya kasa haƙuri, ya kira Nasir ɗakinsa.
Ya dube shi sosai sannan ya ce "Nasir tambayarka zan yi, kuma ina so ka ji tsoron Allah, ka gaya mini gaskiya"
Ya ce "To Abba in sha Allah"
"Waye ya saka neman yaron nan da Nabila ta kare?"
Ya numfasa ya ce "Abba maitaimakin CP ne"
Abba ya ce "Da kuma wa?"
"Shikaɗai ne Abba"
"Gaskiya na ce ka gaya mini, waye ya baka kuɗi a matsayin cin hanci, ya ce lallai ka nemo shi? Kar ka yi mini ƙarya, ka san nima tsohon ma'aikaci ne"
"Ba kuɗi aka bani ba, senator ma'aruf Indabo ne"
"A kan me zai saka ka nemo masa wani ɗan daba, menene alaƙarsa da ɗan daba yana sanata?"
Nasir ya girgiza kai ya ce "Nima ban sani ba Abba"
"Baka sani ba, kawai ka karɓa ka fara yi, Nasir idan baka ji tsoron Allah a kan aikinka ba, a tsiyace zaka shekara talatin kana wahala, ka gama aiki ka zama abin tausayi.
Na fara yadda wasu abubuwan kai ka ta'azzara su, kamar Nabila ta fika gaskiya".
"Abba mutumin fa ɗan daba ne, da yake zubar da jini, da aikata miyagun laifuka"
Major ya ce "To meyasa ba ku nemi kama shi a kan laifin da yake aikatawa ba, wani zai ja ka gefe ya kuma tunzuraka, ba tare da ka san abin da ya haɗa su ba, Nasir ka san aikinka kuwa? Kaga tashi ka je kawai jeka"
Ya buɗe baki zai yi magana major ya ce "Jeka ba zan sake magana da kai a yanzu ba,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 104 Chapter of 121