Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
93 / 121
ba kowa ne zai iya fahimtar bayanin ba sama-sama. Ko da sumayya ta je, ba wanda ya hanata shiga, da ta tambayi in da Nabila take, Nabila na ganinta ta miƙe tsaye, fuskarta ta kumbura suntum saboda kuka. Ta rungume sumayya ta ci gaba da kuka, Sumayya ta ce "Subhanallah, Nabila waye ya mutu? Kin ga yadda ki ka rame fuskarki ta kumbura kuwa?" Cikin kuka ta ce "Sumayya na ga babana jiya" waro ido sumayyan tayi ta ce "A ina?" "Viper ne ya kai ni, Sumayya ashe yar biyuna ya aura aka kashe, duk wannan haƙilon da nake yi, 'yar uwata aka kashe" Sumayya ta ƙurawa Nabila ido, ta ce "Anya kanki ɗaya?" "Kai na ɗaya Sumayya, amma ai kin san lokacin da nake ce miki ina mafarki da mai kama da ni, ki ke yi mini dariya, wallahi sumayya ina da 'yar uwa da ban taɓa ganinta ba, a kanta nake shari'ar Viper" "Nabila, gaba ɗaya kin rikita ni, ban gane in da ki ka dosa ba wallahi, gaba ɗaya na rikice" Viper ne ya turo ƙofar ɗakin ya shigo. Jiki na rawa sumayya ta gaishe shi ya amsa, ta kalli Viper ta ce "Vi ka yi wa sumayya bayani, ta ƙi yadda ta kuma kasa gane bayanin da na yi mata" "Wa zai fuskanci wannan bayanin naki at once dama, ki ƙwarara jikinki, ki yi haƙuri ki daina wannan kukan, yana daga dalilin da ya sanya tun farko ban gaya miki ba" Sumayya za ta yi magana, Abba ya turo ƙofa ya shigo da sallama, suka amsa masa. Sumayya ta gaida Abba ya amsa mata, suka gaisa da Nasir ma. Viper ya yi masa barka da zuwa, amma ya yi masa shiru. "Arfa, kin ji sauƙi ina son a sallame ki, mu koma gida ne" kawar da kanta gefe ta yi, ba ta kalle shi ba. Sumayya ta ce "Nabila Abba ne fa" Ta ɗaga kai ta kalli Sumayya ta ce "Abba disappointed me, meyasa ya ɓoye mini ina da 'yar uwa, gashi ta mutu ban taɓa ganinta ba... "Wai mahaifiyarki ma ba rasuwa ta yi baki taɓa ganinta ba?" Viper ya yi maganar a kausashe. "Amma jauhar ta yi tsawon rai ai, meyasa aka hukunta mu da laifin babanmu" Nasir ya ce "Nabila Abban ki ke gaya wa haka?" Major ya yi shiru, kawai ya tashi ya fita. Sumayya ta ce "Nabila meyasa ki ka yi haka? Baki kyauta ba, duk ɗawainiyar da ya yi da mu, hakan da ki ka yi ba dai-dai ba ne ba. Idan aka sallame ki, dole mu je ki ba shi haƙuri. Kiran gaggawa aka yi wa sumayya, ta tashi ta tafi, cike da mamaki da tunani daban-daban a cikin zuciyarta. Bayan tafiyar major, sai ga Bashir, har da kayan abinci niƙi-niƙi sun zo duba Nabila. Tana zaune, a kan gado, Viper yana gefe yana waya, yana ganinsu ya kashe wayar, ya risuna suka gaisa da Baba. Ƙarasawa yayi gaban gadon Nabila ya zauna ya ce "Sannu ya jikin naki?" Ƙura masa ido ta yi, amma ta kasa masa uffan. Ya zauna ya dafa hannunta, amma ta janye ta sunkuyar da kai. Bashir jiki a sanyaye ya tsaya yana ci gaba da kallon Nabila. Viper ya ce "Ina ga ko zaka ɗan bata lokaci, kafin Nabila ta ganka, tana ɗokin da muradin ganinka, abin da ta ji ne dole za ta ji wani iri, amma in sha Allah za ta maye maka gurbin jauhar. "Na san ni mai laifi ne, amma ƙaddara ta riga fata, wallahi tamkar an shafe ni tunanina a cikin kaina, haka na manta da mairamu. Yaya za ayi ace ka auri mace ka manta da ita, ban san meyafaru ba a lokacin. Kuma ni maitama bai gaya mini ku biyu ba ne, amma ki yi haƙuri ki yafe mini dan Allah" ya kalli Viper ya ce "Bari na je, hafsa ma za su zo dubata yanzun nan in sha Allah" Viper ya tashi ya raka shi har harabar Asibitin. Nabila ta jingina da jikin bango ta lumshe idanunta, hawaye na bin gefen idonta, Viper ya dawo ya tarar da ita. "Ba ki kyauta ba abin da ki ka yi? Duk ɗokin ganin mahaifin naki, abin da ki ka yi kin kyauta kenan?" "Ba ka san me nake ji ba ne?" "Ko ma me ki ke ji ba ki kai ni ba, abin da ki ke yi ba ki kyauta ba, ke zaki jajirce ki daidaita wannan rashin jituwar da yake tsakaninsu, ki rungumi mahaifinki" Ta zuba masa ido hawaye na bin idonta. "Menene kuma? Kukan be isa ba haka?" "Vi" tayi maganar muryarta na rawa. "Abla" "Ka ga abin ƙaddara ko? Ƙaddara ce ta sanya na din ga bibiyarka" Ya ce "Haka ne" "Kwatsam na fara sonka daga wasa, na yarda da maganarka, ba zan taɓa jauhar ba, kuma idan na ci gaba da sonka ban yi zumunci ba na ci amanar 'yar uwata. Zan fara jin kunyrka a matsayin ka na mijin yayata, ba soyayya tsakanin mu yanzu, zan yi iya ƙoƙarina na ga an ƙwatarwa 'yar uwata hakkinta, kuma na ga an wanke ka daga zargin da ake yi maka. Na gode sosai da sosai da ƙoƙarin da ka yi mini". Ayshercool 08081012143 88 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa *BRIGHT PENS SECOND BATCH* Ku kasance da littatafan bright pens, second batch. *ƘARFE A WUTA (AYSHERCOOL)* *MUTALLAB (NIMCYLUV)* HADARIN GABAS (NAZEEFA NASHE)* *ZAYTOON (ZEE KUMURYA)* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾   *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327  Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327  sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 Abin da Nabila ta faɗa ya sanya Viper jin ƙirjinsa ya tsananta bugawa. Ta sake cewa "mu yi zumunci kawai, zumuncinmu ya ɗore, amma yanzu na fahimce ka, da ka yi ta jaddada mini, ba zan taɓa zamo wa jauhar ba" zai yi magana. Hafsa ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da sallama, hannunta riƙe da leda cike da kayan marmari, ta ƙarasa tana murmushi. Bayanta saifu ne yake biye da ita, tana zuwa ta dungurar da ledar ta zauna a kusa da Nabila ta ce "Waliyiyya kin warke ya jikin?" Nabila ta yi murmushi, ta fuskanci Hafsa 'yar uwatta ce, dan tana kama da ita kaɗan, ta ce "Jiki Alhamdilillah". Ta kalli Viper ta risuna ta ce "Ina wuni" "Lafiya ƙalau yaya hafsa" ya kirata da yadda jauhar take kiranta. Sai ta yi murmushi ta sake kallon Nabila ta ɗora hannunta a goshin Nabila ta ce "Ba kya zazzaɓi ma, kin warke sai mu tafi da ke gida ko? Ko gidanku zaki koma ke da shi? Har gidan naku nake zuwa ba a sani ba, baba ya ce idan na kuma zuwa Yaya tijjani ya zane ni" Saifu ya kalli Nabila ya ce "Yaya jikin naki?" Nabila ta ce "Na ji sauƙi Alhamdilillah" "Allah ya sauwwaƙe, ga hafsa nan ita ma yar uwammu ce, yakamata ace duk an gabatar miki da yan uwanki, amma sai Allah ya sa kin warware, zan je duba wani abokina, idan na dawo zan zo na ɗauke ta. Ina amfani da wannan damar wurin baki haƙuri, da nema wa mahaifinmu afuwarki ki yi haƙuri dan Allah. Sannan ku yi haƙuri da abubuwan da za ta yi, tana misbehaving wasu lokutan, tana fama da matsalar ƙwaƙwalwa ne, ta damu a kawota wurin ki ne" "Baba ya ce kar ka sake ce mini mahaukaciya, ni da hankalina dan Allah jauhar na yi kama da mahaukaciya?" Hafsa tayi maganar kamar zata yi kuka. Nabila ta girgiza kai ta ce "Ko kaɗan" Saifu ya juya ya tafi, ba tare da wani ya kula wani tsakanin sa da Viper ba. Bayan ya fita Hafsa ta ce "Jauhar ina jaririnki ne?" Viper ya ce "Ba jauhar ba ce ba" ta kalli Nabila ta kalle shi ta ce "Ita ce mana" Ya ce "Kalle ta da kyau dai" ta sake ƙurawa Nabila ido, ta kalleshi ta ce "Jauhar ce mana, ina ɗan naku to?" Ya ce "Tambayeta" Nabila ta ce "Ta tambaye ka dai" Viper a hankali ya ce "Ya rasu" Ta ɗan yi shiru ta ce "Shi ba zai dawo ba kenan kamar yadda ita ta dawo, to yaushe zata samu wani cikin, ina son na ga ta haihu wallahi, ka san baba cewa yake yi, idan ku yi aure ku haihu da ƙuruciyarku, sai su zama kamar ƙannenku" gum Nabila tayi jin katoɓarar da Hafsan tayi. Gaba ɗaya suka yi mata shiru, ta kalli Nabila ta kalli Viper ta ce "Baku gaya mini ba" Viper ya kalli Nabila ya ce "Abla tana magana, yaushe zaki sake samun wani cikin ki haihu?" Nabila ta ce "Na shiga uku"ta yi maganar tana sunkuyar da kai, sai ya faɗi magana ya wani maze kamar ba shi baz wannan nannauyar maganar tayi masa sauƙin faɗa haka yana kallonta. Ya basar ya ce "Ina mijinki ne?" "Ni bani da aure, rabuwa muka yi, uwargidansa ta hana shi kula ni, sai dai ya ɗauketa su tafi yawo su bar ni a gida. Nayi ta kuka na gaya wa Anty, amma wai na yi haƙuri, na zo na daina bacci, na je asibiti aka bani wani magani na kwana biyu, tun daga ranar da nayi bacci na ji daɗi, na din ga kai wa wani mai chemist yana bani ina sha, har ya fara ƙara mini da wasu ina sha. Gaba ɗaya baya yi mini irin yadda ka ke yi wa jauhar, idan na zo gidanku naga yadda ku ke yi, in yi ta kuka, kuma fa anty ce ta din ga bani magani dan ya aure ni, amma wallahi ina son shi, na din ga shaye-shaye da ban san shi nake yi ba sai daga baya. Zama yaƙi daɗi ya sake ni. Bayan ya sake ni fa sai da ya auri wata kuma ta zauna ita ba ayi mata irin yadda aka yi mini ba. Na cigaba da shaye-shaye damuwa ta yi mini yawa, mai chemist yayi mini haɗin wata ƙwaya ya ce zan manta da damuwata ashe ƙwaƙwalwa ta ya taɓa mini sai aka ce wai na zama mahaukaciya. Amma nima na san alhakin ki ne ya kama ni, ki yafe mini dan Allah ƙanwata" Nabila da tausayin Hafsa ya sanya ta fara hawaye, ta kalle ta ta ce Jauhar zuciyarta daban ce, ta musamman ce. Ita ai kusan kun gama yi mata komai da ku ka aura mata sanyin idaniyarta. Turo ƙofar ɗakin aka yi hafsa ba ta waiwaya ba, amma ta tsorata gabanta ya faɗi, jin ƙamshin turaren Alhaji mu'azzam ya cika ɗakin. Sallama ya yi suka amsa masa, ta ɗaga kai a hankali, suka yi ido huɗu da shi, gabanta ya sake faɗuwa, zai iya cewa tun da ya saketa bai sake ganinta ba sai yanzu. Jan jikinta tayi, ta haye gadon da Nabila take. Ya miƙa wa Viper hannu, amma Viper ya tsaya yana kallon sa, Nabila ce ta ɗan gyaɗa masa kai, a hankali ya miƙa masa hannu, suka yi musabaha. Ya ja wata kujerar ya zauna. Ya ce "Barrister ya jikin?" "Alhamdilillah" ta amsa a hankali. Ya kalli Viper ya ce "Ashe ka kawo ƙarshen labarin da kanka?" Viper fuskarsa babu yabo ba fallasa ya ce "Eh na kawo" "Na san kan labarin ya ƙarƙare da sauran rina a kaba, ina yi muku fatan alkhairi. Nabila zuwa yanzu kin san wanene ni, da dalilin da ya sanya na din ga bibiyarki, ta tabbata jauhar Sister ɗinki ce ko? Duk na san mahaifinki, ban yi garajen sanar da shi komai ba, saboda binciken da nayi a kanki, babu ta in da ya nuna jauhar da ke akwai alaƙa, ashe akwai ɗin dai. Na tayaki murna" Nabila ta jinjina kai ta ce "Na gode sosai, Jauhar da ni twins ne, abubuwan ne da tsayi sosai amma bani da bakin yi maka godiya Allah ya saka da alkhairi. Ga wannan ita ma tana cikin 'yan uwana, sunanta hafsa" Ya kalli hafsa da tayi tsuru, yayi murmushi ya ce "Na santa ai, hafsa mun san juna ko?" Hafsa ta kalleshi, kawai ta dira ta ɗaya side ɗin, ta zari takalmanta za ta fita, Nabila ta ce "Ina zaki je?" Ba ta juyo ba ta ce "Waje zafi nake ji, kar ki da mu ina da hankali ba wani wurin zan je ba" ta kai bakin ƙofa walid ya turo ƙofa ya buge mata goshi. A rikice ya ce "Ya salam, yi haƙuri dan Allah, ban dan kin taho ba" ta yi murmushi ya ce "Bakomai ai babu zafi tayi waje. Suka shigo ɗakin, suka gaisa da Alhaji mu'zzam, ya tashi da hanzari ya ce "Bari na je waje na amsa waya, daga nan zan wuce, amma ina son zama da ku, a kan shari'ar nan amma ina zuwa dai" Alhaji mu'azzam ya fice daga ɗakin. Kawai suka ga Viper ya saka dariya, gaba ɗaya suka zuba masa ido, Nabila tunani take yi, anya ta taɓa ganin dariyar Viper haka. Walid ya ce "Mutumina meyafaru ne ka ke dariya, dariyar da rabonka da ita tun 'yar madara na raye" Ya ce "Muhsin, wani abu ne ya bani dariya" "Akhbirni mutumina, meyafaru ne?" Ya tsagaita ya mayar da dariyar murmushi ya ce "So mugun wasa ne, mai saka ma'abocinsa yi masa biyayyar dole ko bai shirya ba, babu wata waya fa da zai amsa, ya bi matarsa ne kawai, maybe yana kewarta" Nabila ta ce "Ita ce Hafsan da oga walid ya bani labari, dama zancen Alhaji mu'azzam take yi?" Viper ya jinjina mata kai alamar eh. "Ikon Allah, yanzu duk tsawon wannan lokacin kun san komai, ku ka rufe ni" Viper ya ce "Yanzu ai gashi kin sani". Can bayan ɗakin Nabila ta zagaya, hawaye na zubowa daga idanunta, ta tsaya tana ta share hawayenta, ta jima a tsaye tana share hawayen, sannan ta juyo da niyyar komawa, kawai ta ga Alhaji mu'azzam a bayanta a tsaye. Tsuru-tsuru ta yi kamar mara gaskiya. "Haba hafsa, ko gaisuwa babu, tamkar dodo daga ganina sai ki hau gudu? Ya goshin naki?" Cikin inda inda ta ce "Lafiya ƙalau, babu zafi" Alhaji mu'azzam ya ce "Ya kumbura fa, kuma ki ce babu zafi?" Ta ɗaga kai alamar eh. Ya taka a hankali zuwa gabanta, ya mamaye ta da ƙamshin turaren sa, ta kalleshi, yana sanye da yadi ash mai tsada riga da wando, Alhaji mu'azzam akwai kwalliya da ado. "Kin ga wata sabuwa daban mai kama da jauhar ko?" Ta girgiza kai ta ce "A'a jauhar ce". "Ba jauhar ba ce, wannan sunanta Nabila. Hafsat" ya kira sunanta a hankali. Tsigar jikinta ta tashi, taƙi kallonsa. "Meyake damunki ne? Kin rame kin yi duhu, ba gayunki kamar da, meyafaru haka?" Kawai kuka ya ƙwace mata, har da sheshsheƙa. Jauhar yake so ba hafsa ba, amma yana tausayin ta mussaman da ya ganta yanzu. Daga baya ya fuskanci ba wai kuɗinsa kawai take yi wa ba, tana matuƙar son sa. Amma shi kansa bai san ya aka yi ya din ga misbehaving ba, kuma a lokacin ƙanwar indabo tsohuwar budurwarsa jidda tana ta bibiyarsa ya aureta. Handkerchief ɗin sa ya ɗaukko, ya fara share mata hawayen. Ƙoƙarin rasa nutsuwar sa ya fara yi, ita ma ganin idan ta cigaba da tsayuwa, za su iya ɓarna, dan har wani tsuma take yi, soyayyar sa ƙamshin turaren sa, da maganganun da ya fara yi mata, narka mata zuciya yake yi, hakan ya sanya ta buge hannunsa daga fuskarta, ta raɓa shi ta bar wurin. *** Abdul yana kwance a gadon asibiti, hannunsa ɗaya da ankwa, mahaifiyarsa na gefe tana ta uban kuka, tamkar an ce mata gawar Abdul ce a gabanta. Ga Indabo can yana fuskantar hukunci. Jami'an tsaro na son ɗaukar statement dan a shiga kotu, amma ko magana ba ya iya yi, idan ya yinƙura sai aman jini. Bunkure ma kamar zata haukace, dan ko ta wani ɓangare tana samun suka, kuma babu sassauci. Mutane sun fara juya mata baya, tare da gazgata zancen Nabila da tayi a kanta a kwankin baya aka din ga attacking ɗin ta. Nabila ta bar Asibiti, ta koma gidan madam Halima. Viper ya dage da yi wa Nabila nasiha, tare da tausarta, a kan ta karɓi mahaifinta, tayi haƙuri sannan ta nemi gafarar major shi ma, dan bai cancanci abin da tayi masa ba. "Ni ka ƙyale ni dan Allah, in ji da raɗaɗin rashin 'yar uwata da hake addabar ruhi da gangangar jikina, koma menene ya faru laifinsu ne na kasa samun nutsuwar karɓar dukkaninsu". A fausace ya hau ta da faɗa "Are you out of your sense, rayuwata ba ta zama darasi a gare ki ba? Duk abin da ya faru a tsakaninsu, ke ina ruwanki ne a ciki? Could you imagine mahaifinki na yi mini kuka a kan na shawo masa kanki ko sau ɗaya ki yi masa kallon uba, ya riƙe ko da hannunki ne, ya ji daɗi? Ya rasa jauhar, babu tsammani kin bayyana a gare shi, ba tare da ya san ki na raye ba, amma kin ƙi saurarsa ina ruwanki da abin da ya riga ya wuce? Wallahi ko kaffara ba zan yi ba da yar uwakki ce ba zata yi haka ba, jauhar ta daban ce, mai tausayi da jin ƙai ce. Na san da ke aka yi wa abin da aka yi mata a kaina bijirewa zaki yi. Da haƙuri da siyasa ake cin ribar zaman duniya ba fushi da shirme ba. Kin nuna rashin jin dadin ki abin da aka yi miki da farko daga baya kuma sai ki saukko ki haƙura ai" Sumayya da tana wurin, ita kanta sai da ta tsorata da faɗan da Viper yake yi. Nabila kuwa kuka take yi wiwi, wasu lokutan gara faɗan Abba da na Viper, gaba ɗaya sai ya razanata ya saka ta rasa abin da yake yi mata daɗi. "Ki tashi ki shirya, zamu je ki nemi afuwarsa, sannan mu je mu ga ɗan mama, da su Rahama" Haka Nabila ta shirya, sumayya tana ta mamakin samun abin da zai iya tsorata Nabila ya sakata kuka, bayan Abba. Yau ma a ƙofar gidan su jauhar, aka yi parking, tare da sumayya suka zo, da sallama suka shiga. Baba yana gareji, yana ba wa saifu sallahun wanke masa mota, Nabila suka shiga. Cak ya tsaya yana kallon su, da sumayya da Nabila. Kallo ɗaya Sumayya ta yi wa Baba ta gane baban Nabila ne. Rikicewa yayi ya nufota duk da jikinsa a sanyaye ya nufeta, idanunsa cike da hawaye. Yana ƙarasowa ta faɗa jikinsa tana sakin wani irin kuka mai karya zuciya. A hankali ta ce "Baba" tana kuka yana kuka, kamar wani zai ƙwace masa ita, haka ya ƙanƙame Nabila, yana kuka har da majina. Sumayya da take tsaye ita ma fashewa ta yi da kukan, cikin matsanancin tausayin su, ta san irin artabu da ƙalubalen da Nabila ta din ga fuskanta a kan rashin uba, a gidan major yadda suke kiranta da tsintacciyar mage wai babu wanda ya san babanta, Nabila ba ta da wata magana da ta wuce fatan ganin mahaifinta, ta ji ina ma ita ma tana da rabon sake ganin mahaifinta a rayuwa. Viper yana hango su daga waje, ya sunkuyar da kansa hawaye na cika masa ido, cike da fatan ina ma shi ne ya sake ganin Jauhar ta bayyana a rayuwarsa ba tare da ya yi tsammanin hakan ba. Nabila ta ce "Sumayya ga babana, kin ga babana" "Na gan shi Nabilata, Ina tayamu murnar ganin Baba, burin da muka daɗe muna fatan Allah ya cika mana" "Ki yafe mini 'ya ta, abin da ya faru ba da son raina ba ne ba, wani abu ne da ba zan ce ga a yadda ya faru ba, na san mai laifi ne a gareku da mahaifiyarku, ke kaɗai ki ka rage mini a cikin su, dan Allah ki yi haƙuri ki yafe mini" yayi maganar cikin matsanancin kuka. Ya rungumi Nabila zuwa cikin gidan, sumayya na biye da su, yaran gidan duk su ka kewaye su, wasu na taya su kuka wasu na kallon su. Ya ce aje a ce wa Al'amin ya shiga. Nabila ta kwantar da kanta a kan cinyar baba, tana cigaba da kuka. Bayan Viper ya shigo su ka gaisa da Baba, ya kalli sumayya ya kalli Viper ya ce "Anya Aminullahi wannan ma ba tawa ba ce?" Viper ya yi murmushi ya ce "Duk naka ne Baba, an baka" "Na san fuskarta ne, ta na kama da wani wanda na sani, amma ba zan iya tuna waye ba? Ya sunan mahaifinki?" Sumayya ta share hawayenta ta ce ba ni da wayon sanin mahaifina, amma dai sunansa Tahir ladan. A take ya yi sak, ya ce "Wane Tahir ladan ɗin? Coustom ne?" Sumayya ta jinjina masa kai ta ce "Ka san shi?" Yayi shiru ya ce "Tare mu ka je ɗaurin aurena a jalingo, abokin aikina ne, lokacin da aka yi mini transfer daga in da na bar mairamu shi ne ya koma, ya je yayi reporting a wurin aiki, ya koma yayi hatsarin mota ya rasu. Viper ya ce "Kenan dai duk 'ya'yan naka na kawo maka" Kamar ƙaramin yaro ya kalli Sumayya ya ce "Ni babanki ne, ke

Chapter 93 of 121