tantance a ina take, dan ba ta taɓa ganin wurin ba.
Ji ta yi an rufe ƙofa, ta ɗaga kai ta kalli mai shigowar, take gabanta yayi mummunar faɗuwa, duk da idonta bai gama washewa ba, amma sarai ta gane shi.
"Kin tashi kenan? abun da aka shaƙa miki bai taka kara ya karya ba, amma ki ka yi wannan dogon zangon" yayi maganar lokacin da ya tsuguna a gabanta yana kallon idonta.
Ƙirjinta ya din ga bugawa da sauri da sauri.
Ganin ba ta ce komai ba, ya sanya ya tashi ya fita, babu jimawa ya dawo da plate a hannunsa, ɗauke da indomie da kifi a ciki, sai ruwan roba, hannunsa ɗaya kuma ledar magunguna ce.
Ya tura mata plate ɗin gabanta, sannan ya fara haɗa alluran.
Tayi shiru ta zuba masa ido, har sai da ya ce "Ki ci mana, allura zan yi miki"
Cikin kuka ta ce "Dan Allah kar ka kashe ni"
Abdul ya yi wani murmushi ya ce "Saboda me?"
"Ni dai kar ka kashe ni, dan Allah ka mayar da ni wurin babata"
Ya kalleta ya ce "Kashe ki fa sai na yi, ba dai ke taurin kai ba ke da babar taki, zan nuna muku cewa talaka ba komai bane illa bawa kuma takalmi ga masu kuɗi da dukiya, ba yanzu zan kashe ki ba, sai kin gama yi mini amfani tukuna.
Yanzu ki ci abincin nan, zan yi miki allurai na zazzaɓin da yake jikinki".
"Ni ba zan ci ba" ta yi maganar za ta tashi tsaye, amma ya daka mata tsawa ya ce "Wallahi idan ba ki ci ba, a yanzu zan kashe ki, ko gawarki babarki ba zata gani ba".
Babu shiri ta fara cin abincin, sai dai a loma ta uku, ta hau amai, ta amayar da duk abun da ta ci.
Cikin tsananin takaici ya ce "Ke mahaukaciyar ina ce zaki yi mini amai a nan? Nan yayi miki kama da wurin juye ƙazanta?.
Tayi shiru ta sunkuyar da kai.
"Tashi mu je in nuna miki in da duster da mopper suke ki gyara"
Cikin tsoro ta tashi, tana jiri tana bin bango, haka ya saka ta gyara wurin da ta yi aman.
Bayan ta gyara, ta shiga banɗakin tayi alwala, ta fito ta tayar da salla, ba tare da ta san ina ne gabas ba, da kuma adadin sallolin da ake bin ta ba, dan ba ta san adadin lokacin da ta shafe, ba a hayyacinta ba.
Ya dawo ya tarar da ita a zaune, a takure wuri guda, bai kulata ba, ya ƙarasa ya sanya hannun sa a goshinta, ya ji shi da zafi rai. ɗaga ta ya ja ta ya dungurar da ita a kan gadon.
Ya kama hannunta, ya saka sirinji, ya fara ɗaukar jininta.
Bayan ya gama ɗaukar jininta, ya yi mata wasu allaurai duk a jijiyar hannunta.
Ta zubawa saurautar Allah ido, dan kasa magana ta yi, tun yana allurar ta fara jiran jin alamar ciwonta ya ƙaru, dan ta sallama kashetan zai yi kamar yadda ya faɗa, amma bayan ya gama yi mata ya tashi ya fice, ya kulleta a ɗakin, ba tare da ta ji yanayinta ya sauya ba.
***
Abun duniya fa ya ishi Nabila, wayar Viper ta zame mata wahala, dan kuwa kashe ta tayi gabaki ɗaya, sai dai duk in da ta zauna, musamman da daddare, idan ta shiga cikin duhu, Viper ne yake yi mata gizo, har abun ya fara tasiri a yanayin mu'amalarta.
Tana toilet tana wanka, wayarta ta din ga ringing babu ƙaƙƙautawa, ta kammala wankan ta fito, ta ɗauki wayar tana dubawa.
Lambar Nasir ta fara kira, ta nemi wuri ta zauna a gefen gado, tana jiran ya ɗaga.
"Ina ki ka shiga ne? Ko kina wurin aiki ne?"
Ta ce "A'a, yanzun nan na dawo gida"
"Baki da lafiya ne?"
"No, gajiyar aiki ce kawai"
"To, aikin ki yayi kyau arfa, na yi waya da mu'azzam, gayen nan da ki ka faɗa mun kama shi, tare da tabar wiwi da ƙwayoyi"
Sassanyar ajiyar zuciya ta yi ta ce "Alhamdilillah ala kulli halin, Allah shi ne abun godiya, what next?"
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce "Na saka lallai su fara tuhumarsa, ya faɗi in da Viper yake".
Zuciyarta ta din ga raya mata ko ta sanar masa kai tsaye, abubuwan da suke gudana, ta bashi wayar hankalinta ya kwanta, amma zuciyarta ta gargaɗe ta a kan aikata hakan.
***
In da ya bar ta a kan gadon, nan ya je ya sake tarar da ita, ta tashi ta zauna ta dunƙule jikinta a wuri ɗaya tana bacci, sai ajiyar zuciya take yi.
Wani irin murmushi ya yi, yayi miƙa lokaci guda, ya fara rage kayan jikinsa.
Motsinsa ya sanya ta farka, fes ta buɗe idanunta, sai dai hankalinta ya yi mummunan tashi, ta ja da baya, ba ta ƙaunar ganinsa ko kaɗan.
Ya hawo kan gadon ya nufota, ta din ga ihu tana kiran sunan Allah, ta na yi masa magiyar ya ƙyaleta, ya mayar da ita gida.
Amma kamar ya kamo ƴar kaza, haka ya danƙota zai yi mata rashin mutunci, sai dai yana haɗa ta da jikinsa, ya ji kamar ana hura wuta a Jikinta, saboda zafin zazzaɓi, gashi sai wani irin ƙarni take yi, da warin man kaɗanya da take shafawa ya haɗe da ƙarnin koren sabulun da take wanka da wanki da shi.
Ba wannan ya fi damunsa ba, rashin saukar zazzaɓin jikinta ne bai so ba, dan ko a yanzu a galabaice take.
A ɓangaren ramma ma, warin giyar da yake yi, da ƙamshin turaren sa ya sanya ta fara yinƙurin amai, ba shiri ya cikata, ta sauka da gudu, ta tafi banɗakin da yake cikin ɗakin, ta din ga kwara aman, sai dai ruwa kawai take amayarwa, bayan shi babu komai a cikinta.
Ta gama aman tana ta sauke numfashi, ta lallaɓa ta fito, tana bin bango, sai dai ta tsaya cak tana kallon sa yadda ya zuba mata ido.
Cikin kuka ta haɗa hannayenta ta ce "Dan girman Allah ka yi haƙuri, ka mayar da ni in da ka ɗauko ni, hankalin mamana na san yana can a tashe, dan Allah ka yi mini rai ka yi haƙuri" ta ƙarasa maganar tana zubewa a kan gwiwoyinta tana bashi haƙuri".
Strip ɗin gwajin ciki ya ɗago da yake hannunsa, wanda ya gwada da jininta da ya ɗiba ɗazu ya ce "Ke ce mace ta farko da ta fara ɗaukar cikina, kin kafa tarihi, tun da ki ka ce ba za a zubar ba, nima na ji ya shiga raina, ina son abuna, zaki haife shi kafin na kashe ki, kuma ba zan kashe ki ba sai bayan kin haihu" ta yi shiru tana cigaba da zubar da hawaye, wai ita ce ɗauke da ɗan shege a cikinta, a wani keɓantaccen wuri tare da ɗan iska, saboda kawai ba su da kuɗi, sai yau ta ƙara tabattar da illar talauci.
Ya miƙe tsam daga kan gadon ya fice ya bar ta a ɗakin, ba tare da sanin makama ko abun yi ba.
Sumayya ce a office ɗin manager, fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa.
Ya kalleta ya ce "Sumayya yaya aka yi ne? Ko yayi miki wani abun ranar da ku ka yi program ɗin?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"To menene? Na ga kin yi editing ma kin tura mini, komai yayi normal, na ce a saka idan lokaci yayi kin yi ƙoƙari sosai, ina ga program ɗin hannunki zai dawo gaba ɗaya"
Ta sauke numfashi ta ce "Sir"
Ya amsa da "Yes ma"
Sai kuma ta yi shiru.
"Ki gaya mini mana idan da wani abu" ta girgiza kai ta tashi ta fita.
Addu'a ya din ga yi a zuciyarsa, tare da fatan Allah ya sa ba wani abun indabo yayi mata ba, dan ya san halinsa sarai.
Nabila tana office ɗin ta, tana aiki, barrister Habib ya buɗe ya shiga da sallama.
Miƙewa tayi tsaye ta ce "Sannu da zuwa, da ka kirawo ni ai"
Ya ƙarasa gaban teburinta ya ce "Babu damuwa, aikin da ki ka ba ni ne na yi"
Tayi murmushi ta ce "Taimakon da na nema dai aka yi mini"
Shi ma murmushin ya yi ya ce "Zan tura miki court ɗin da aka fara yi masa shari'a, da sunan wurin wanda za ki je ya binciko miki file ɗin, akwai dai wani abu a ɓoye".
Cikin sauri ta ce "Ok, ai daga nan ma kana tura mini sai na tafi"
Ya ce "Wait, ki tafi yanzu ba ki da aiki ne?"
"Ai na kusa kammalawa saura kaɗan ne"
Ya ce "shikenan, zan tura miki ta what's app, amma ki bi a hankali, fa kar ki je ki yi abun da ba shikenan ba"
"In sha Allah, na gode sosai"
Yana fita ta fara lissafi a ranta, tun kan viper ya je hannu, za ta bibiyi cases ɗin sa na baya, domin a shirye take da ta ƙalubalanci hukumar shari'a ciki har da alƙall da kuma hukumar gidan yari, kan sakin Viper ba tare da ƙa'ida ba, ta san ko ba ta yi nasara ba, za ta yi suna sosai.
Tattara jakarta ta yi, ta fita bayan da saƙon barrister Habib ya shiga wayarta.
Ba ta wani sha wahala ba zuwa kotun da ya bata adress ɗin, tun da dama sananniyar magistrate court ce a kano.
Ofishin rijistra ta je, suka gaisa da mutanen wurin, sannan ta tambayi office ɗin mutumin da barrister Habib ya gaya mata.
Aka yi mata iso, sannan ta gabatarwa da mutumin kanta, da wanda ya turo ta.
Ya karɓeta da mutuntawa sannan ya ce "Baiwar Allah, gaskiya ta in da ki ka biyo, babu yadda za ayi na kasa yi miki alfarma, amma riƙe file ɗin nan, tamkar saka hannu ne ki ɗaukko ƙarfen da yake cikin wuta ne, dan Allah kar ki je ki yi wani abu da bai kamata ba, tun kan ki zo aka yi waya, aka ce a baki idan kin zo"
Nabila ta ce "In sha Allah, babu wani abu da zan yi, ina ɗan yi wani bincike ne kawai".
Ya ja ta suka tafi wani wuri a cikin kotun, suka shiga can wani office, da ba zaka ce akwai mutane a wurin ba, sai da suka shiga can ciki, suka iske wani mutum yana ta aiki a computer.
Suka gaisa, wanda ya rakota ya ce "Oga, ga baƙuwa mun yi, Barrister Habib ne ya aikota, shi kuma daga top oga, ya ce a kawo ta file ɗin Al'amin viper zaka ɗaukko mata"
Shiru mutumin yayi yana kallon ta sannan ya ce "Ya sunanki?"
"Nabila yusuf maitama"
"Me za ki yi da file ɗin?"
Ta ɗan rausayar da kai ta ce "Wani bincike nake yi ne"
Ya mayar da hankalin sa kan mutumin da ya rakota ya ce "Ka gaya mata illar da ke cikin hakan?"
"Na gaya mata, ko ma dai menene na gaya maka wanda ya ce a ba ta ai"
Yayi ajiyar zuciya yana cigaba da yi wa Nabila kallon tuhuma, ya tashi ya shiga wani wuri.
Ta kalli mutumin da ya rakota ta ce "Yallaɓai, meyasa file ɗin yake da hatsari har haka?"
Yayi murmushi ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Yana da alaƙa da rashin gaskiya"
Mutumin ya fito ɗauke da file ɗin, duk ya yi ƙura, hannu na rawa ta karɓa ta ja kujera ta zauna, ta fara dubawa.
Sannu a hankali ta din ga bin bayanan ciki, da binciken rahoton ƴan sanda a kai, sai dai komai ba straight forward aka yi shi ba, gaba ɗaya kanta ya kulle, ba ta fuskanci wani abun kirki a ciki ba.
"Amma sir, ina ƙarshen shari'ar, ai wannan ba a yanke hukunci ba, ranar ƙarshe da aka ɗaga shari'ar an ce sati uku za a sake zama, yanzu kusan shekara biyar, ba a sake rubuta komai ba"
Mutumin ya ce "Eh yadda ki ka gani a haka yake"
Cike da mamaki ta ce "Dan Allah wane alƙalin ne ya yi masa shari'ar?"
"Yana abuja" suka bata amsa a taƙaice.
"Wannan documentation ɗin, sam ba a yi shi ma yadda za a fahimta ba, amma dan Allah....
Wanda ya ɗauko mata File ɗin ya ce "Mu fa babu abun da za mu iya sake gaya miki, ba wanda yake da damar zuwa wurin nan sai staff ɗinmu, dan haka ki tashi ki tafi".
Ta miƙe tsaye ta ce "Na gode sosai"
Ta fito daga office ɗin tana mamaki, ta ja ta tsaya tana kallon office ɗin, a abun da ta fuskanta wuri ne da ake ɓoye files na musamman.
"Yayi kisan kai!" Ta faɗa a fili.
"Ba abun mamaki bane ba, da gani zai aikata abun da ya fi kisan kai, amma menene dalilin ajiye shi shekara biyar, ba ayi masa shari'a ba, an ɓoye file ɗin sa a wuri na musamman, ya shekara biyar a prison, kuma kwatsam an sake shi, babu document na wanke shi aka yi daga laifin ko kuwa, duk da an rubuta ya amsa laifin, amma wane hukuncin aka yanke masa? Wayyo Allah kaina zai fashe" ta yi maganar tana dafe kanta, da ya yi mata nauyi.
***
A tsaye yake a kanta yana ƙare mata kallo, yanayin yadda take a kwance ya tabbatar masa da salla ta yi.
Ruwan robar hannunsa ya fara zuba mata a Jikinta, hakan ya razanata ta tashi a gigice.
Ya watsa mata sabulu da soso a jiki ya ce "Ki tashi ki je ki yi wanka, ba na son ƙazanta, kar ki haifar mini ɗa mai dauɗa"
Ta yinƙura ta tashi da kyar, tana jiri, ga yunwa ga zazzaɓi ga kwana da ta yi amai, ta din ga bin bango, har ta isa banɗaki.
Ta daɗe a banɗakin tana kuka, sannan ta yi wankan ta fito, ta tarar da shi a kan gado a zaune yana danna waya.
Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Dalla cire wannan kayan, ƙazamar banza da wofi, har amai ki ka yi a jikin kayan amma ki ka mayar da su jikinki" kallonsa take yi, to tsirara yake son ta zauna?
Ya buɗe wardrobe ɗin da ke ɗakin, duk kayansa ne a ciki, ya jefa mata wata shirt, ya ce ta ɗauka ta saka.
Banza ta yi masa, ta kawar da kanta gefe, wanda hakan ya hasala shi, yana zuwa gabanta ya kwasheta da mari, abunka da jiki babu ƙwari, take ta faɗi ƙasa, ta riƙe fuskarta.
"Ke kin isa ina magana ki yi mini banza, ƴar wahala mara amfani, ɗauki ki saka kan na tattakaki"
Ramma ba ta ƙaunar duk da abun da zai taɓa lafiyar jikinta, haka ta zura rigar nan, ta zo mata har gwiwa, sai rufe jikinta take yi.
Ya danƙota, ya fita falo da ita.
A falon ya haɗa mata baƙin shayi, sai soyayyen dankali da ketchup ya ce ta ci.
Gaba ɗaya a tsorace take, saboda kar ya kuma dukanta, haka ta din ga tsakura tana ci tana hawaye.
Ta gama ci, ya ɗaukko alluran zazzaɓi da yake yi mata yayi mata.
Ta lura yana da mai aiki a gidan namiji, har girki da gyaran gidan shi ne yake yi masa su.
Ya kashingiɗa yana kallon tv, ita kuma tana gefensa a ɗarare, sai mutsu-mustu take yi tana share hawaye.
Sahidar yatsunsa ya gani kwance a fuskarta, har ya ɗaga ya basar ya cigaba da kallonsa yana kaɗa ƙafa.
***
"Allah ya taimaki maigida"
"Menene labari?"
"Na samu kiran waya ɗazu, wata yarinya ta je an kaita har ofishin secret files, an ɗaukko mata file ɗin viper ta duba"
"Wacece ita?"
"Yarinyar da ka ce ayi amfani da ita a kama Viper"
Da sauri ya ce "What? Ya aka yi ta san da file ɗin ta je? Waye ya ce a bata?"
"Wallahi ban sani ba, amma an tabattar mini da ga sama su ma aka ba su umarnin ba ta"
"Sama ina, waye ya bayar da umarnin?"
"Ban sani ba wallahi, kuma da gaske lawyer ce, idan kuwa haka ne, za ta iya yiwuwa da gaske ta haɗu da Viper, ƴar jaridar nan raina mana hankali ta yi"
Indabo ya numfasa ya ce "Kar ku yi gaggawa, kar ta san mu na bibiyarta, ka bi ta hannun ƙawarta, ku samo me take son samu a kansa, idan ta ƙi, ku kamata ku azabtar da ita".
Ya amsa da "Ok sir".
Daga kotun, gida arfa ta tafi, tun daga shigarta, Sauda ta fara tsokanarta da faɗa, amma ba ta ita take ba, ɗakinta tafi ta cigaba da tunani da lissafi.
Kamar wadda aka zungura, ta ɗaukko wayarta ta kira Nasir.
Murya ƙasa-ƙasa ya ce "Arfa ya dai? Mun shiga meeting ne"
Kamar za ta yi kuka ta ce "Yaushe za ka dawo?"
"Zamu yi waya an jima, ki yi haƙuri"
"Kar ka kashe mana dan Allah, ni ina cikin damuwa magana nake son mu yi, wani abu zan baka"
Ya ce "Wani abu me?"
"Abu ne mai muhimmanci a kan viper, amma sai ka yi mini alƙawarin ba zaka yi mini faɗa ba ko ka gayawa abba ba"
Tattara nutsuwarsa ya yi ya ce "I hope, ba wata kasadar ki ka je ki ka aikata ba"
Ta girgiza kai ta ce "Ba wata kasada da na yi, ni dai ka yi ka dawo, kan na mutu"
A rikice ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, menene ki gaya mini"
"Ka kwantar da hankalinka, kawai dai ka yi ka dawo, abun yana da muhimmanci, na san yadda zaka same shi kai tsaye"
"Kin ga ba zan iya jira ba, gaya mini menene sai na aika su Mu'azzam, dama wanda aka kama ɗin nan ya ƙi magana"
"Sai ka dawo gaskiya" ta kashe wayar gaba ki ɗaya, dan kar ya biyo ta, ta sake dafe kanta.
Sumayya na news room, tana jiran lokaci ya cika, ta gabatar aka turo ƙofar aka shigo. Sak tayi tana kallon mai shigowar.
Mutumin da honorable ya saka ya karɓi wayarta ne, ranar da ta je gidansa.
Ya ja kujera yana kallonta, ya ce "Ya dai, kin yi mamakin ganina ne? Mintuna goma sha biyar suka rage miki, kan ki fara karanta labaran, zaki yi mini aiki".
Ta zuba masa ido, amma ba ta ce uffan ba.
"Meyasa ki ke yi mana ƙarya a aikinmu? Da gaske ƙawarki ta haɗu da Viper?"
Cikin ɓacin rai Sumayya ta ce "Na gaji da amsa wannan tambayar, idan ba ku yadda da ni ba, ku nemeta ta amsa muku mana"
Ya shafi sajensa ya ce "Zamu gani ai, yau ta je court ɗin da aka yi wa Viper shari'a, ta karɓi secret file ɗin sa ta duba, zaki kira ta, ki ji dalilin zuwan ta, da kuma abun da za ta yi da file ɗin"
Sumayya ta girgiza kai ta ce "Nabila ba wani abu da za ta amfana muku, kawai na san ƴar rigima ce, so take ta yi suna ta ɗaukaka ta taimakawa yayanta shikenan"
Yayi dariya ya ce "Za mu gani, daga yanzu zuwa azahar ɗin gobe, idan baki kawo rahoton dalilin bin diddigin shari'ar Viper da take yi ba, abun da ba kya zato zai faru" ya miƙe tsaye ya ce "lokaci ya cika, ki gabatar da aikinki"
Sumayya ta dafe kai cikin matsananciyar damuwa, tana tunanin wannan wace irin rayuwa ce.
Murtala ne ya shigo yana faɗin "Afuwan sisyna, mamager ya kira ni ne, na saita komai ki fara".
"Ba ka ga mutumin da ya fita yanzu ba?"
Ya kalli ƙofar ya ce "Ban ga kowa ba"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan mu fara".
***
Ƙaramar wayarta ce isheta da vibration a ƙasan pillow, ta ɗaga ta ce "Bacci fa nake ki ke ta kiran wayata".
"Haka dai, daga bacci sai kwalliya da cin abinci, ke har kin koma gida kin kwanta, ni tun 9 gani har 5 ban tashi ba"
Nabila ta ce "Ke ba na samun bacci a ƴan kwankin nan wallahi"
"Meyasa?"
"Wallahi a tsorace nake, ba na iya bacci, gani nake kowane lokaci viper zai kashe ni, cewa yayi fa sai ya kashe ni, sonake Yaya ya dawo na danƙa masa wayar nan, na huta, wai da wayar wa ki ka kira ni ne?"
Sumayya ta ce "Wayata ce ta ɗauke, ina ki ka je ne yau?"
"Wurin aiki mana, amma da labari sosai, mu haɗu gobe in Allah ya kaimu"
"Yakamata mu haɗu kam, dan na ga mutuniyarki bunkure, a gidan honorable Indabo"
Daga kan gadon da Nabila take ta miƙe tsaye ta ce "Amma ba ki gaya mini ba sai yau?"
"Na san halinki ne, uzzura mini zaki yi, ke bari na tafi gida ma yi magana"
Ta kashe wayar, ta kaiwa murtala wayarsa, dan ta fuskanci mutanen honorable na bibiyar kiran wayar da take yi.
Wuni guda ramma ba ta sake saka Abdul a idonta ba, sai dai kukunsa idan ya kammala girki, ya ƙwanƙwasa mata ƙofa ya ajiye mata abinci.
Tayi kuka har ta gaji, ta koma addu'a, tare da fatan Allah ya kuɓutar da ita daga sharrin zaluncin Abdul.
Tana zaune a ƙasan carfet, har wurin sha biyu na dare, ya shigo yana kokawa da ƙofar ɗakin, saboda a buge yake.
Ta tashi tsaye cikin tsoro, sai dai ba tare da ta yi masa laifin komai ba, ya hau ta duka, ya din ga ball da ita yana taka ta da ƙafarsa, tun tana kururwa har ta kasa sai ajiyar zuciya, ko ƙwaƙwƙwaran motsi ba ta iya yi.
Tamkar dabba haka ya afka mata, ba tare da la'akari da ƙarancin shekarunta ba, kodayeke ina tunani ga wanda hankalinsa ya gushe?.
Bai farka ba sai kusan tara na safe, yayi miƙa ya tashi yana kallon ɗakin, da sauri ya kalli gadon bai ganta ba, ya kalli jikinsa, ya tashi yana mayar da kayansa, kawai ya ga jini a gefensa, har zuwa banɗaki, cikin hanzari ya nufi banɗakin, ƙofar tana buɗe dan haka ya shiga, ya tarar da ita a zaune ta jingina da jikin bath jini yana ta zuba daga jikinta, ga jikinta duk a kumbure saboda duka, idonta a rufe.
Ya ƙarasa ya durƙusa ya ɗaga hannunta ya saki, ya ga ya koma babu alamar numfashi a tare da ita, rigarsa dake jikinta, tayi sharkaf da jini.
Dafe kansa yayi yana tuna abun da ya faru jiya, kamar mafarki.
16
🔞*PAID BOOK NE, ₦500 BOOK1-3 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143*
16
Shi gashi ko sunanta ma bai sani ba, ya sake ɗaga hannunta, amma hannun ya sake dawowa ƙasa.
Ya kai hannunsa hancinta, ya ji tana numfashi kaɗan-kaɗan.
Ya haɗa ruwa a bath ɗin mai ɗumi, ya cire rigar jikinta ya ajiye a gefe.
Ya ƙarewa jikinta kallo, ko ina shatin duka ne da ya yi mata, take wani abu mai kama da tausayinta ya ɗarsu a ransa, ya ɗaga ta, ya sakata a cikin bath ɗin, ga abun da ta yi ɓari nan daga cikinta a ƙarƙashin ta.
Duk da ƙyanƙyaminsa, da yadda ƙarnin jinin yake hawar masa ka, haka ya din ga tarar ruwa, yana kwarawa a banɗakin, ita kuma ya din ga canza ruwan da take ciki, saboda yadda yake ɓaci da jini.
Rigarta kuwa, wuri guda ya ware ta, dan kuwa yarwa zai yi, bai san yadda zai yi da ita ba.
Ya fita da sauri, ya kira mai aikinsa solomon, ya rubuta masa abubuwan da yake buƙata ya ce ya sayo masa.
Har solomon ya je ya dawo, yana ta ƙoƙarin ganin ya tsayar da jinin da take zubarwa.
Ya ɗauke ta zuwa kan gado ya kwantar da ita kamar gawa, ya sake ɗiban jininta, ya yi bawa solomon ya ce ya kai kowane lap ne, idan ya kai ya kira shi a waya.
Ya saka mata drip hannu biyu, ya sake su, yana yi yana duba vitals ɗin ta.
Ƙofar ɗakin ake ta bubbugawa, ya tashi ya buɗe, ya ga saif a tsaye.
Saif ya kalleshi ya ce "Ya na ganka kamar mara gaskiya? Lafiya kuwa?"
Ya girgiza kai ya ce "Ina fa lafiya, yarinyar nan ce tayi miscarriage"
Saif ya ce "Shi ne me to? Dama ba haka kake so ba, na ga ma fa kasheta za ka yi ka bar ta"
Abdul ya ce "Haka ne, jiya daka sauke ni bayan ka tafi, ka san a buge nake, na dake ta sosai"
"Lallai Abdul, yau ka fara yi wa mata haka to?"
Ya girgiza kai ya ce "No, kawai su sauran su ne suke kawo mini kansu, shiyasa ban taɓa jin komai ba a kan abun da nake aikatawa, sai ta ji sauƙi sosai, zan kasheta na huta"
Saif ya ce "Well mu je in ga jikin nata"
Abdul ya tsaya a gaban ƙofar ya ce "No, ba zaka shiga ba"
Cikin mamaki ya kalli Abdul ya ce "Lafiyarka kuwa?"
"Ras nake, ba zaka shiga bane kawai"
"Ka kashetan kenan?"
"Idan na kasheta, zan kasa gaya maka ne, ko tsoronka nake ji?"
Suna haka solomon ya kira shi, ya haɗa su da masu lap, ya gaya musu gwaje-gwajen da yake so a yi wa jinin ramma da ya bayar aka kai.
Ya koma ɗakin da take, ya rufe ya saka mumulli, ta ciki, ya sake nufar gadon, ya hau yana tattaɓata ya ga ko ta na da rai.
Ambaton Allah ya ji tana yi, tare da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 121