Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
36 / 121
ne, na lallai sai ta nuna wa mutane tana cikin kwanciyar hankali, sai dai suna tsaka da gulmar, ta sake saka hotonsu riƙe da dadduma a filin idi, wanda hakan ba ƙaramin girgiza su yayi ba da ba su mamaki. Master ya kai mintuna goma sha biyar yana zaune, ta fito sanye da leshinta da ta saka ranar ɗaurin aure, ta shafa powder da jambaki, ta saka kwalli, ta kwantar da gashin gaban kanta, da gel, ta yi ɗauri mai kyan gaske, gashi ta kaiwa Suwaiba tela ta gyara mata ɗinkin, dai-dai jikinta. Har ya tashi zai shiga ɗakinsa, ya waiwayo ya ganta ta fito, mp ce a hannunta, tana bin waƙar da aka saka, a cikin nishaɗin barka da salla. Cikin waƙar m sharif *Farin gani kai ne tauraro, ko a cikin samari, mai ji da ni ba ka yin ƙwauro ka sa na wuce gori, na ɗau takarda na riƙe biro, kai na saka a fari, kai zan ba dawakai, kowanne da silkai, matsayinka ya kai ba zan yi ma kishiya ba....... Da haka ta ƙaraso gabansa tana rawa, tana yi masa fari da ido. Tsayawa yayi yana kallonta yana murmushi, sai dai bai tsinke da lamarin na ta ba, sai da ta ƙaraso gabansa ta riƙe hannunsa wai sai ya yi rawa. Karo na farko da ya buɗe haƙoransa talatin da shida yayi dariya. "Ba dariya zaka yi ba, ka yi mini liƙi ko ka yi mini rawa" ya buɗe baki ya ce "You are not serious" "Am serious mana, rawa ko liƙi, biyani ɗari shida ta ma da ka korar mini coustomer's" ya saka hannu a aljihunsa ya ciro dubu biyu da ɗari uku ya ce "Suke nan nake da su, uwar son kuɗi" "Ungo dubu ɗaya, sauran bari na bayar da ayata a markaɗo mini, na haɗa da snacks da tuwon salla na raba. Ba ka ce ma na yi kyau ba, ka taɓa ganin mace da tayi kwalliya tayi kyau kamar yadda na yi yau?" Yayi murmushi ya ce "Ni da ba kallon mata nake yi ba, ya za ayi na sani, ni dai ba ki yi mini kyau ba, kamar babyn roba haka ki ka zama" yayi maganar yana matsa kumatunta. "Daga Angela zuwa 'yar madara, yanzu kuma babyn roba?" "Eh, irin na wasan nan ba" Jauhar ta ce "Kyau nayi maka ne" Ta fice tsakat gida, tabbas tayi kyau kam, tayi fresh farar fatarta ta karɓi baƙin leshin sosai da sosai, kwalliyar ta yi mata kyau. Tana tsakar gida, wasila ta shigo ta kawo mata tuwon salla, suka gaisa tare da yi wa juna barka da salla. Wasila ta ce "Jauhar iyayen soyayya, mu matan layin nan, tare muka haɗa kai muka tafi idi, a hanya muka hango ku, an maƙalƙale hannun master ana yashe baki, kai jauhar a ji tsoron Allah" Jauhar ta ce "Anty wasila kina saka mini ido wallahi, ki sa ka in ta jin kunya" "Ke ba wata kunya, riƙe abunki wallahi, abunku gwanin sha'awa, kafin lokacin ya wuce, ba kowane namiji ne yake jure ayi ta soyayya ba". Al'amin ne ya fito, Wasila tayi tsit dan ba ta san yana nan ba, ta gaishe shi ya amsa ciki-ciki. "Master ina zaka? Kunun aya ka san baya daɗewa" "Nura ne a waje ya kirani, ba nisa zan yi ba" Ta ce "Ok to" Daga jikin gate guduma ya ce "Antynmu barka da salla". Jauhar ta ce "Yauwwa malam nura, ina fatan ka je idi?" "Eh na je, na biyo mu gaisa sannan ki bani tuwon salla". Jauhar ta ce "Aikuwa ka samu, amma sai ka kai mini markaɗen aya, ka sayo ƙanƙara sai na haɗa maka da tuwon" Ya ce "Ba case matar babban yaya" Al'amin bai sani ba, har gidansu jauhar ta aika da abincin salla, guduma ne ya kai ya kai na gidan su ita ma. Ta zuba wa Al'amin, ya tafi da shi, tun da ya shiga wurin na su, Liti da sauran yaran suke bin sa da kallo. Liti ya ce "Maza, wannan shuɗiyar audugar ruwan sararin samaniya fa, waye ya sayeka cikinta?" "Ban sani ba" Walid ya ce "Abun a tambaya ne, ni fa tun da na sanka sau ɗaya na ga ka saka manyan kaya, ranar da aka zarga maka uku, ina nufin igiyar sunnar ma'aiki da bint laban ɗin ka, wato madam 'yar madara" Ya tsuke fuska ya ce "Mai laya" Walid ya ɗaga masa hannu ya ce "Tuba nake, na kiyaya wannan ma'adanar abincin fa?" Al'amin ya ajiye musu kwanuka, suka dirarwa abincin nan da ci babu ji babu gani. Baba kuwa yaya saifu ya aiko, aka kawo mata fulasanta, da kuɗi dubu goma, kasancewar ba ta tura account number da ya ce ba a matsayin barka da sallar ta. Da daddare da ya dawo, yana shigowa ta ji warin sigari, dan da alama ma a cake yake, bai kulata ba, ya tafi ɗakinsa ya baje a kan katifa, ta bi bayansa har cikin ɗakin, cikin matsananciyar damuwa ta ce "Haba master, shi ne ka je ka sha da yawa, kalli a yadda ka dawo fa, gaba ɗaya ka ɓata mini ɗan farincikin da na tsinci kaina a ciki yau" yayi shiru yana sauke numfashi. Ta ƙaras ta ce "Tashi a cire kayan to, sai ka saka wasu" "Get out" "Ai zan tafi amma...... "I said get out" yayi maganar cikin tsawa. Ta tashi a razane, ta bar masa ɗakin, cikin azumi dai Allah ya taimaketa ya ɗan nutsu, saboda baki a rufe yake, ba ya shaye-shaye sosai, yau da ga sallacewa ya koma ruwa. Saboda tsabar takaici, ko baccin kirki ba ta yi ba. Da safe kamar ba shi ba, ya tashi ya fito abun sa, ya sayo abun karyawa, sai share shi take yi, amma ya nuna ko a jikinsa. Kasancewarta mai matukar raunin zuciya, sai kuma ta sake. Suna karyawa, Hafsa ta kira ta a waya, jauhar ta ɗaga tayi mata sallama ta ce "Amarya ba kya laifi" "Mhmm, dama anko ne mama ta ce sai an nuna miki, shi 'yan gida za su yi da bikina, zan turo miki ta what's app lace ne dubu goma sha biyar sai atamfar kamu dubu tara, na san ba lallai ma ki yi" Jauhar ta yi murmushi ta ce "Anty hafsa kenan, aikam dai kun san mijina talaka ne, zan sako dai abun da Allah ya hore mini na zo, in sha Allah" "Dama na sani ai, mama ce ta takura a turo miki kar abun ya zama surutu, a ga kin fita daban. Allah ya sauwwaƙe tisya" "Ba tsiya ba ce anty hafsa, idan ruwanka bai isa alwala bane sai ka yi taimama Allah ya kaimu bikin lafiya" ba shi aka gaya wa ba, amma sai ya ji maganganun hafsan tamkar direct da shi take, wani irin haushi da takaici ya kama shi. Sai dai ya basar ya cigaba da karyawa abun sa. Ya kammala ci, ta tashi ta yi aikace-aikacenta, yau ma wata kwaliyyar ta yi da abun da Allah ya yassare mata. Ya ce "Babyn roba" Ba ta kalle shi ba ta ce "Saura ta rodi" "Zaki gama kumbure-kumburen naki ki sace" Ta share shi, tana shafa muzurunta d take cewa boti. "Ina magana ki ka share ni, kina wasa da wannan abun da nake dana sanin kawo shi?" "To me zan ce maka? Kawai ka je ka sha abun da ka sha, daga yi maka magana ka hantare ni" tayi maganar idonta na cika da hawaye, saboda takaici. Maimakon ya damu, sai yayi murmushi ya saka hannu ya matsa kumatunta a hankali ya ce "Abun wasa na, you are like a toy to me, wani abu mai ɗan bani nishaɗi wasu lokutan" Galala take bin sa da kallo, ita ce ma abun wasan. "Kin daɗe kina yi mini abubuwa, abun da ki ka yi mini jiya ya tsaya mini a rai, ki ka ɗinka sutura sukutum ki ka bani, Allah ya suturtaki ranar da bayi za su tsaya a gabansa babu sutura. Na gode Allah ya baki miji nagari" Da sauri ta sake kallonsa, sakamon abun da ya faɗa na Allah ya ba ta miji nagari. "I still mean it, haryanzu ina kan bakana na rabuwa da ke a duk lokacin da ya dace, kina takura mini da yawa" A fusace ta saka hannu, ta buge hannunsa da ya riƙe kumatunta, ta waiwaya tana kallon gefenta. Ya ce "Idan ki ka kuskura ki ka jefe ni, yau ni da ke ne" tashi ta yi tana kuka, ta nufi ɗakinta. Ayshercool 08081012143 35 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??     Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??     Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??     Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.      Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾 Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽 08093932955 Ba ta ƙara kula shi ba wunin ranar, dama kuma ficewa yayi ya bar gidan, ta rasa sai zuwa yaushe Al'amin zai yadda ya karɓeta su yi rayuwa, kullum ba shi da magana, sai maganar da zata tayar mata da hankali na zai rabu da ita, gaba Al'amin yayi hannun riga da duk wani nau'i na  tausayi. Abun da zuciyarsa ta raya masa kawai yake yi, ko ya yi maka daɗi, ko akasin haka ba damuwarsa bane ba. 'yan yaran da suka din ga shigo mata yawon salla, su ne suka din ga ɗebe mata kewa da rage mata damuwa. Sai bayan sallar magariba sannan ta sake ganinsa, tun da ta yi masa sannu da zuwa, ta ajiye masa abinci, ta koma gefe ta na danna wayarta. Sai da ya ci ya ƙoshi, ya samu wuri a kusa da ita ya zauna, ya ce "Abun wasan, ya dai?" Ta ɗaga kai ta kalleshi ta sunkuyar, ta hau wasa da yastun ƙafarta. Hannunsa ya saka shi ma a yatsun ƙafarta yana tayata wasan da take yi da su. "Master" "Mmm" "Meyasa ka ke son lallai sai ka sake ni ne? Saboda ka ga bani da makoma ko? Ban taɓa burgeka, duk ƙoƙarin da nake yi, ba ka appreciating kullum cikin tsorata ni ka ke, kana gaya mini abun da zai ɗaga mini hankali, me nayi maka ne?" "Baki dace da ni ba, da salihin mutum nagari ki ka dace. Da zan iya samun mutum mai amana da zai riƙe ki, zan iya rabuwa da ke ya aura, you  have an innocent soul, that doesn't deserve someone like me, shiyasa nake yawan gaya miki haka. Ko jiya a fusace nake, na yi miki tsawa sai da ki ka yi kuka, ina ɗaukar hakkinki" "To ni na ce maka bana son zama da kai ne? Ina yi maka addu'a, wataran zaka daina ai ko?" Tayi maganar tana kallonsa. Yayi shiru bai yi magana ba, "Dan Allah ka yi magana, zamu iya rayuwa tare, irin damuwar mu ɗaya, matsalar iyalan da muka tashi a tsakanin su, ba sai mu zama familyn junanmu ba, mu rayu cikin aminci da walwala. Amma master meyasa ka ke shaye-shaye bayan ka san yana da illa ga lafiyarka? Yana saka aikata abubuwan da bai kamata ba, kayi faɗa da mutane a zubar maka da jini, ko ka zubarwa wani, har kisan kai fa yake saka". "Wa na kashe?" Ta ce "Ranar da na fara ganinka, a unguwarmu, gawar wani na ganka da ita ka soka masa wuƙa" Yayi murmushi, ya haɗiyi wani abu mai ɗacin gaske. "Ban taɓa kisan kai ba, ranar ce haɗuwarmu ta farko ko? Ban kashe kowa ba" Cikin damuwa ta ce "Amma wuƙa fa na gani a gefen cikinsa, kuma meyasa ka ke shaye-shaye?" "Bana son silly question, rabu da ni" ta gyaɗa kai kawai ta ƙyale shi. Ranar hawan salla kuwa,  Jauhar ba ta san me ake yi ba, Al'amin ya haɗa yaransa, da miyagun makamai, da sunan tsaro kar wasu daga wani wurin su zo su fake da kallon hawan salla, su kawo musu farmaki su cutar da wani. Sai dai sun yi ba ta kashi da wasu marasa jin sosai da sosai, ciki kuwa har da yaran madaki. Sai da 'yan sanda suka yi kame sosai da sosai, daga wurin hawan Al'amin bai koma gida ba, ya wuce cikin gari, saboda kar jauhar ta ganshi da makami, da jini. A cikin garin ma, sai da suka yi wata fitinar, aka yi sare-sare da faɗace-faɗace. Sai bayan kwana biyu, jauhar take jin labarin abun da ya faru a wurin hawa, ganin Al'amin lafiya ƙalau ya sanya ta kwantar da hankalinta, tare da bawa kanta yaƙinin cewar babu shi a rigimar. Kwana na huɗu, tana kitchen tana girki, tana shirin kaɗa miyar cin tuwo, maman halimatu ta shigo gidan a gigice. Jauhar ta ce "Maman halimatu lafiya kuwa?" "Ke kina nan baki san abun da yake faruwa ba?" Cikin rashin fahimta ta ce "A ina?" "Wani ɗan daba ne wai madaki, daga can unguwar ku ya zo unguwar nan wai neman mijinki, wai ya illata masa yara, sai tarwatsa mutane suke yi, suna sara kan mai uwa da wabi a guje na ƙaraso" Cikin tashin hankali ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" take kanta ya sara, jikinta ya hau rawa, ta ɗauki wayarta ta kira lambar sa, sai dai tayi ta ringing baya ɗagawa. Hijjabinta ta ɗauka, maman halimatu ta ce "Ina zaki? Saran mutane fa suke yi, duk wanda suka samu duka ko sara". Ai ba ta ko tsaya bata amsa ba, ta fita cikin matsanancin sauri da tashin hankali. Ba ta san in da za ta nufa ba, addu'a kawai take yi da roƙon Allah, Allah ya tsare mata mijinta. Mutane na guje-guje ita kuwa kutsawa take tana duba ina zata ganshi tana kuka. A wani layi ta hango shi, ya riƙe wani matashi, idon Al'amin kawai ta kalla ta san a buge yake, babu alamar mutunci a idonsa, idanun sun yi jawur sai gumi yake yi, yanayin sa ya tabattar mata da ya tafka ɓarna, kafin ta ƙarasa, ya fito da harshen sa waje, kamar yadda yake yi, idan ya ƙudirci aniyar yin wani abu, ya ɗaga sweazland ɗin sa, babu tsammani ya ganta a gabansa, ta riƙe rigarsa tana girgiza masa kai cikin tsananin tashin hankali. "Idan ka kashe shi, rufe mini kai za ayi, ba lallai na sake ganinka, ka yi haƙuri kar ka yi kisan kai dan Allah" Jikinsa tsuma kawai yake yi, ya aiwatar da abun da zuciyar sa take raya masa, saboda yadda haɗin da yayi amfani da shi, yake fizgar kansa yake jin sa tamkar jinjirin doki, zuciyarsa kuma kamar an kunna wuta. Ta rirriƙe hannun da ya riƙe wuƙar da shi, da hannu ɗaya ya yi jifa da matashin gefe, shi kuma ya saki wuƙar, sai tangaɗi yake yi, ya kasa tsayuwa, sai gumi da yake tsatsafo masa ya furta "Madaki" kawai ya yanke jiki ya faɗi, sai a lokacin ta ga uban saran da yake gadon bayansa, ashe duk abun nan an sare shi a baya, rigarsa ta rine da jini ta baya. Wani irin gigitaccen kuka ta saki, ta ce "Na shiga uku, dan Allah ku taimaka mini a kai shi asibiti" tayi maganar tana girgiza shi. Ya kalleta da idanunsa, suka yi jawur, jikinsa ya fara rawa ga gumi ya jiƙa masa fuska. Ragowar mutanen da suke wurin, suka dare suka bar ta da shi, a wurin. "Master dan Allah kar ka rufe idonka, yanzu zamu tafi asibiti, Allah ka kawo mini ɗauki, Allah ka duba lamarin nan". Guduma ne ya shigo cikin layin da gudu, ya jefar da makamin hannunsa ya ƙaraso, wata irin ajiyar zuciya ta saki, yana zuwa ya jijjiga Al'amin ya ce "Master" sai dai idanunsa sun lumshe, saboda jinin da ya zubar. Yayi ƙoƙarin ɗaga Al'amin, ya saɓa shi a kafaɗarsa, amma abu ya gagara, ba ƙiba ce da shi ba, sai dai akwai nauyi. Ya kalli Jauhar da ta rikice, take ta kuka ya ce "Anty ki kwantar da hankalinki, in sha Allah yanzu zamu kai shi asibiti". Ya din ga wani irin fito, kan ka ce kwabo, wasu matasa suka din ga ɓullowa da ɗaya ɗaya, su ma suna fiton wasu suna fitowa. Suna zuwa suka yi tara-tara suka sunkuci Al'amin, guduma ya saɓa shi da ƙyar, suka nufi titi. Da ƙarfin tsiya suka ƙwaci 'yar ƙurƙura a titi, suka ce mai ita ya bi su Asibiti ya karɓa. Sai dai da suka je, ma'aikatan lafiya, suka ce ba za su karɓe shi su duba shi ba, sai da jami'an tsaro. Cikin kuka ta ce "Dan girman Allah kar ku yi mini haka, ku ceto ransa kar ya rasa ransa, dan Allah ku fara duba shi, kan a kawo 'yan sandan" ma'aikatan suka ƙeƙashe ƙasa suka ce, sai fa jami'an tsaro sun zo". Ta din ga rusa kuka a cikin emergency, guduma sai bata haƙuri yake yi. Ta kasa jurewa, ta tashi ta bi wani likita, ta riƙe rigarsa tana kuka ya ce "Dan girman Allah ka ceto rayuwar mijina, kar a rasa ransa dan Allah" Ya ce "Ba laifina bane ba, dole mu san meyafaru kafin mu taɓa shi". Kan kace kwabo, sashen emergency ya cika da 'yan daba, saboda an kawo al'amin. Babu tsammani ta ga shigowar liti tare da Walid, da wasu tawagar marasa jin suna take musu baya. Suka ƙaraso, in da jauhar ke zaune, da Al'amin a gabanta. Walid ya ce "Madam, ya aka yi haka ta same shi?" Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, kawai ce mini aka yi ana faɗa, na je na tarar da shi, da zai cakawa wani wuƙa amma ya fasa, kawai dai ya ce madaki ya faɗi ashe an sare shi, kuma sun ƙi duba shi wai sai ƴan sanda sun zo, dan Allah ka saka baki yaya Walid. Ya kalli liti ya ce "Zan ɓallo ruwa, a toshe magudanan daga waje" liti ya jinjina kai, ya ja guduma suka fita. Wasu daga cikin matasan suka shigo, suka koro wasu daga cikin majinyata waje, suka ritsa likitoci da makamai, sai sun duba Al'amin. Aka ce su kai shi kan gado, Walid ne ya ɗauke shi, suka kai shi kan gado, saran da aka yi masa ba ƙarami bane, yayi zurfi, hakan ya ƙara razana Jauhar. Liti ya ce "Wannan yankan madaki ne yayi masa shi, wannan shegiyar wuƙar da aka ce ta tsafi ce, da ita yayi masa saran". Jauhar ta ce "Na shiga uku, ba zai tashi ba kenan?" Walid ya ce "Zai tashi ki kwantar da hankalinki" Aka yi wa Al'amin ɗinki, kamar ƙwarya aka ɗinke bayansa, sai dai walid ba su bari an yi a gaban jauhar ba, aka ɗibi jininsa, dan dubawa idan sai an ƙara masa jini, sai dai baya buƙatar ƙarin jini, sai dai an saka masa ruwa saboda jirin da yake yi ya hana shi tashi. Ana tsaka da duba shin, jami'an tsaro suka iso, Walid ya ce kar matasan nan su bar su su shigo, sai an gama yi masa komai. Aka din ga artabu da 'yan sanda da dandazon, yaran da suka yi wa harbar emergency ƙawanya, da kyar 'yan sandan suka shiga. Da ƙyar aka tarwtsa tarin matasan nan, tana zaune ta ƙurawa fuskarsa ido, ƴan sanda suka ɗauki statement ɗin abun da ya faru. Jauhar sai addu'a take yi, tana fatan Allah ya sa ya farfaɗo. Ta riƙe hannunsa, tana shafawa a hankali ta ce "Allah ya shirya mini kai, ya baka lafiya master, inuwarka ce kawai nake tsaye a ciki nake saka ran samun farin ciki, dan Allah ka daina zuwa ana cutar mini da kai" Idonsa a rufe, ya ɗaga hannunsa a hankali, ya shafi fuskarta sannan ya buɗe idon a hankali ya kalleta sai dai bai yi magana ba. "Sannu master, an yi maka ɗinki a bayanka, akwai abun da yake yi maka ciwo ne?" Ya girgiza kai almar a'a. Ta shafi sumar kansa ta ce "Allah ya baka lafiya" Juyi yayi a hankali, ya kwanta a kan cinyarta, muryarsa ƙasa-ƙasa ya ce "Idan kina kuka ciwon ƙara zafi yake yi" ta goge hawayenta ta ce "To na daina, amma idan aka ji maka ciwo, zuciyata ce take kuka ba na so master" tayi maganar hawaye na kwarara daga idanunta. A hankali yake matsa hannunta, yana jin wata nutsuwa ta mussaman, da sassaucin zafin da zuciyar sa take yi masa. Zuwa magariba, ya miƙe ya ce sai sun tafi gida, Jami'an tsaro suka ce za su tafi da shi, sakamakon tayar da tarzoma a unguwa. Walid ya ce "Saboda hauka ake yi, master ku ware gida, ni ku tafi da ni mu muka je muka tayar da tarzomar" Ana fito da Al'amin, guduma ma ya taso, da sauri, Al'amin daga shi sai dogon wando, suka tari napep suka tafi gida. A wurin maman halimatu jauhar ta karɓi mukulli, ta buɗe musu gidan suka shiga. Ta saka yayi wanka, yayi alwala ya rama sallolin da ake bin sa, ta kawo masa abinci ya ci. "Master" ya kalleta "Dan Allah ka fita daga shirgin madakin nan, ba shi da imani, kar ya hallaka ka dan Allah" Ya girgiza kai ya ce "Sai dai ɗaya yayi ajalin ɗaya ko ni ko shi, shari'ata da shi, Allah ne kawai zai rabata" Cikin rauni ta ce "Ina haɗaka da girman zatin Allah" "Shhhh, ki daina haɗa ni da Allah, kin san nauyin abun da aya aikata mini?" "Ban sani ba, amma ina da yaƙinin koma me zaka yi masa, ba zaka huce ba, ka yi haƙuri ka bar wa Allah mana, idan wani abun ya same ka ya zan yi ne? Yanzu kalli halin da ka sakamu a ciki, na san yanzu haka a cikin pain ka ke, ciwon a jikinka yake, amma a zuciyata nake jin raɗaɗin, haba master, haba dan Allah" tayi maganar wasu zafafan hawaye na gangarowa daga cikin idanunta. Ya miƙa hannunsa ɗaya da ba a side ɗin ciwon yake ba, ya janyota jikinsa, ba ta musa ba ko yi masa gardama, ta kwanta sosai ta cigaba da kukan, tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa sosai, kasancewar babu riga a jikin sa. "Ba zan ɓoye miki ba, ban taɓa tunanin zan yi wata alaƙa da wata 'ya mace ba, saboda ina yi musu kallon azzalumai, ke ki ka fara canza tunanina". Al'amin Ibrahim shi ne cikakken sunan Al'amin, mahaifinsa haifaffen garin kano ne, gidansu gidan yawa ne, baban Al'amin shikaɗai ne a wurin mahafiyarsa da ta daɗe da rasuwa, sai tarin 'yan uba da galibinsu mata ne. Yayi karatu daga primary zuwa sakandare har yayi diploma, sai dai aikin yi ya gagara samuwa, akwai abokinsa sammani da suka yi karatu tare, tare suke yawon neman aiki, ya ja shi garin su tofa, aka samo musu gona, suka fara noma. A can ya haɗu da Zahra'u, ya ce yayi mata, da fari tsokanarta yake yi, saboda kwalliyar da take yi ta 'yan ƙauye ce take bashi dariya, daga baya soyayya ta ƙullu a tsakaninsu. Abu kamar wasa, har ta kai ga aure, duk da bashi da wata ƙwaƙƙwarar sana'a, sai kame-kame. Sun sha gwagwarmayar rayuwa tare, sun yi faɗi tashi, sun yi fama da yanayin rayuwa, kafin Allah ya buɗa masa ya fara samu. Lokacin da suke cikin wahala babu mai taimakonsa, daga shi sai ita suke wahalar su, ta samu ciki a lokacin ta haifi ɗan ta na fari, aka saka masa Abubakar Assidiƙ, sai lokacin da Allah ya fara buɗa masa, 'yan uwansa suka saka musu ido, da surutun yana zaƙewa da yawa a kanta. Komai ya samu ita, ya tashi daga tsakiyar cikin garin kano, ya koma gwauron dutse yayi mata gida mai kyau. 'yan uwansa suka fara tsangwamar ta, da cewa ta shanye musu ɗan uwa, Ibrahim ya mayar da ita makaranta ya samo mata admission a FCE, ta ke karantar English islamic. Kasancewar ta mace mai kyauta, da fara'a da sakin fuska ga mutane, ya sanya take da masoya sosai. Sai dai duk da kyautarta, da son mutane dangin mijinta ba sa ƙaunarta. A can gwauron dutsen, ta haɗu da wata mata rahila, maƙwabciyarta ce, tana yawan zuwa ta kawo mata complain a kan mijinta ba ya kula da ita da yaranta, hakan ya sanya tausayin rahila ɗarsuwa a zuciyar Zahra'au, kusan kullum cikin yi wa rahila aike take, na abun da zata kula da yaranta, kuɗi, sutura, abinci kayan masarufi, saboda Ibrahim yana sakar mata sosai baya yi mata iyaka da komai. Tana NCE 2, Sadik ya shekara biyar, ta samu ciki, tayi ta fama ga laulayi ga karatu, rahila take barwa Abubakar ta tafi makaranta, ƙarshen wata, take biyanta da kuɗi mai kauri saboda ita ma ta samu. Ta haifi ɗanta na biyu, aka saka masa Muhammad Al'amin, saboda haihuwar maza da take yi, dangin miji, suka ƙara yi mata caaa wai tana ta haifar maza, dan ta kwashe komai na gado idan ya mutu. Tana iya ƙoƙarin ta wurin saka Ibrahim ya yi kyautata musu su ma, amma ba sa gani sam. An

Chapter 36 of 121