kula da shi sosai. Zan zo in ga jikin nasa in sha Allah"
"Shikenan, Allah ya kawo ki" ya kaste wayar, yana kallon in da Viper yake kwance, hannunsa ɗaya a kan ƙirjinsa, yana ta sauke numfashi.
***
Duk wasu kalamai da Abdul yake tunanin idan yayi amfani da su, zai shawo kan ramma, yayi amma fafur taƙi saurarsa, ya kaɗa ya raya, amma taƙi saurarsa. Da ya addaba mata cikin tsawa ta ce "Wai me kake so ne Abdul, ai ban yi zaton mugun zaluncinka ya kai haka ba, ka yi mini fyaɗe an ɗora wa mutanen da suka taimaka mini sharri, wannan wace irin rayuwa ce?"
Ya sake kwantar murya ya ce "Ki fahimce ni dan Allah, zan yi duk iya ƙoƙarina a kan mutumin nan ya fita a sake shi, dan Allah ki daina ɗaga hankalinki"
"Dama dole ka ce haka mana, tun da kana ganin ko ta halin ƙaƙa, kuɗi zasu ƙwatar maka komai, baka tunanin mawuyacin halin da zaka jefa zukata, baka yi dacen hali ba ko kaɗan" taƙi sauraronsa, sai uban miyagun maganganu da ta din ga yaɓa masa.
***
Bacci ya gagari idanun Nabila, ta ga tamkar an ƙara wa daren tsawo, gashi ta kasa bacci, ƙarshe ta tashi tayi alwala ta tayar da nafila.
A gaggauce ta hana baba magajiya aikinta, ana idar da sallar asuba, ta shiga kitchen ta dafa abun da take buƙata, da duku-duku, ta ɗauki motarta ta fita.
Jin ƙarar mota ya sanya Nasir ɗaga labulensa ya duba, ya ga babu motarta, ya kalli agogo, hari sam bai gama waye ba, ya fara tambayar kansa ina tafi da wannan duku-dukun?.
Gudu ta din ga yi a titi, gani take yi tamkar kafin taje, wani abun ya same shi.
Gari yayi haske sosai tana hanya, ta ajiye motarta a wani wuri, ta fito ta tsaya ko zata samu abun hawa, amma bata samu ba, dan haka ta cigaba da tafiya da ƙafa, gabanta na ta tsananta faɗuwa sai addu'a take yi.
Ta sha tafiya sosai, sannan ta samu abun hawa ta hau, ya ƙarasa da ita.
Kasancewar da tafiya daga titi zuwa gidan da yake, haka ta din ga haɗawa har da gudu, har ta ƙarasa tana ta haki, ta shiga da sallama, ta ƙarasa ƙofar ɗakin, ɗan mama ta hango zaune a gaban Viper, yana ta rarraba ido, daga shi sai shi a gidan.
Ƙwayoyi ne a hannun Al'amin, gefe ga allura a cikin sirinji, amma sai haki yake yi mai ban tsoro.
Da sauri ta ƙarasa ɗakin, tana cewa "Wannan ƙwayoyin na menene?"
Kafin ta ƙarasa ya watsa su a bakinsa, babu ruwa yake ƙoƙarin haɗiyewa, ba ta san lokacin da cikin tsawa ta ce "Viper meye haka? Ƙwayoyin meye wannan kashe kanka ka ke son ka yi?"
Bai kulata ba, ya cigaba da ƙoƙarin haɗiyewa, sai dai ya kasa saboda abun da yake ji ya tokare masa a wuyansa zuwa ƙirjinsa.
Matse bakinsa tayi iya ƙarfinta, tana girgiza masa kai "Kar ka haɗiye, wallahi hakan ba mafita ba ce ba, dan girman Allah ka zubo su daga bakinka" hankaɗeta yayi yana ta huci.
Ɗan mama ya ce "Ki daina zuwa in da yake, zai yi miki illa, wallahi aiken su Walid yayi, ni kuma yayi mini barazana da wuƙa, na samo masa kuma wanda ya watsa a bakinsa sun yi yawa, sun yi masa ƙarfi"
"To waye ce ka kawo masa, ba sai ka gaya wa Oga walid ba, ai ka san ba zai taɓa iya kisan kai ba"
Ta sake tunkarar Viper, sai haki yake yi mai haɗe da huci, tamkar kumurcin, yana motsa bakinsa a hankali, yana son haɗiye ƙwayoyin.
Bakinsa ta sake matsewa, idanunsa sai buɗewa suke yi suna lumshewa, wanda suka fara narkewa a bakinsa, sun fara rikita masa lissafi.
"Kalleni nan, ka fito da su na ce" tayi maganar tana zare masa ido.
Ya ɗago a hankali ya kalleta, ta ce "Ka zubo da su, kar ka haɗiye. So kake ka kashe kanka, idan ka kashe kanka, ɗan wuta zaka mutu, kuma ko ka je lahira ka mutu ɗan wuta, yar madara kuwa muna saka mata ran tana aljanna, kaga ba zaka ganta ba"
A galabice, ya buɗe bakinsa, yana zubo da ƙwayoyin da suka rage a bakinsa, yana ta haki.
Shammatarta yayi, ya ɗauki sirinjin da yake gefensa, ya caka mata a hannunta, wata irin ƙara tayi, cikin razani, dan ba ta yi tsammanin hakan ba.
Ɗan mama ya rikice, ya nufo su da sauri, Viper ya kalli in da ya caka mata sirinjin, ya kalli fuskarta yadda ta fara kuka, sai kuma ya ankare da abun da yayi.
Sai ya rikice, ya zare sirinjin ya jefar ya riƙeta ya ce "Zahra, me nayi miki? Yi haƙuri, na daina shan komai, ai nayi miki alƙawari" yayi maganar yana ƙoƙarin kai hannunsa fuskarta, ya share mata hawaye.
Walid ne suka shigo tare da liti, suka nufo su, liti ce wa yake "Me ki ka yi masa?"
Viper ya yinƙura ya tashi, amma ya yanke jiki ya faɗi.
Suka rufu a kansa, suka ɗaga shi da kyar, Nabila ta gaya wa Walid a halin da ta zo ta same shi.
Walid ya kalli ɗan mama, cikin tsananin ɓacin rai, ɗan mama ya ce "Nifa bani na kawo masa ba, wallahi ɗaukko masa kawai ya saka nayi, ban san a ina ya samo abun sa ba"
Suka mayar da hankali a kan Viper, sai dai ba maye kawai yake yi ba, suma yayi, ga numfashinsa iya ƙirjinsa yake.
Nabila ta ce "Dole fa a kai shi asibiti, ko da hakan yana nufin a kama mu ne baki ɗaya, lafiyar sa ita ce mafi muhimmanci a wannan lokacin"
Walid ya ce "Haka ne, amma wani asibiti zamu kai shi?"
Liti ya ce "Akwai wani asibiti a can bayan gari sosai, sai dai na kuɗi ne, ina ga kamar can zai fi zama safe"
Nabila ta basu mukullin motarta, ta gaya musu a in da take.
Liti ya karɓa ya tashi ya fita.
Nabila kallonsa take cike da tausayawa, namijin gaske ne, sai dai ta wata fuskar yana da raunin zuciya sosai.
Da liti ya kawo motar, suka yi kama kama, suka ɗauke shi, suka shafo tafiyar nan da shi, suka fito titi.
Liti ne yake jan su a motar, ɗan mama da Viper da walid suna baya.
Asibiti ne mai kyau, sai dai ya yi nisa da gari sosai da sosai.
Ganin halin da yake ciki yasa suka karɓe shi da gaggawa, Nabila ta tambayi ya tsarin Asibitin yake, da payment ɗin, aka ce su bari, a fara ceto ransa tukuna.
Da aka tambayi sunan Al'amin, sai Walid ya ce "A saka masa Muhammad Nura"
Liti ya ce "Meyasa baka bayar da normal sunansa ba"
Ya bashi amsa da "Saboda tsaro"
A kan oxygen aka fara ɗora shi, saboda numfashinsa, sannan aka fara sauran ƙoƙari a kansa.
Walid kallonta kawai yake yi, yadda take a rikice cike da tashin hankali, babu ma alamar tana fargabar a kamata ko wani ya ganshi, ta uzzurawa likita da tambayoyi.
Likitan yayi mata bayanin yadda Jinin Al'amin ya hau, ga bugun da zuciyar sa take yi, fiye da kima kamar yadda ECG ɗin sa ya nuna, he's at very risk of having heart attack.
"Subhanallah, dan Allah doctor kayi ƙoƙarin ka, na san Allah ne mai komai, amma dan Allah ka taimaka"
"In sha Allah zamu yi iya a ƙoƙarin mu a kai"
Tayi masa godiya, ta tafi reception ita da litu, suka gaisa da cashier ta tambayi, me za su yi depositing, na patient ɗin su da aka yi admitting?.
Ya tambayi sunan mara lafiyan, liti ya gaya masa, ya duba cikin system ɗin gabansa ya kalle su ya ce "Ai an biya"
Suka kalli juna da ita da liti, liti ya ce "Malam ka duba sosai, ɗazu muka shigo fa, aka ce mu bari a fara bashi taimakon gaggawa, ka duba ko masu irin sunan biyu ne".
"Shikaɗai ne me irin sunan da aka yi admitting yau, Al'amin Ibrahim"
Suka kalli juna da Nabila, liti ya ce "Mu sunan mara lafiyanmu Muhammad Nura"
"Wanda ya biya kuɗin, sunan da ya bamu kenan, ba shi ne na ɗaki mai lamba 2 ba? Al'amin Ibrahim ya ce mana, ya turo kuɗi ya ce ayi masa duk abun da yakamata".
Ayshercool
08081012143
59
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Nabila ta ce "Malam ya za ayi mu kawo mara lafiya, mu zo kuma ace mana wani ya biya kuɗinmu, dama haka ake yi, wannan wane irin abu ne, ka gaya mana bills ɗinmu mu biya, mu bamu san kowa ba"
Ya girgiza mata kai ya ce "No ma, ba zan karɓi kuɗinku ba, na gaya miki an riga an biya"
"Waye ya biya?"
Liti ya ce "Kai bana son nuƙu-nuƙu, wanene ya biya kuɗin?"
"Nima ban sani ba, management ne suka turo mini receipt, aka ce kar mu karɓi kuɗinku, an yi settling bills ɗin"
Nabila ta ce "Suwaye management ɗin?" Yayi shiru yana kallonta.
"Malam kayi mini magana, ka tsare ni da ido, suwaye management ɗin? Suwaye suka biya kuɗin?"
Liti ya ce "Ki yi magana a hankali, kar ki janyo hankalin mutane kanmu"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ana bibiyarmu, wanda yake wannan abubuwan ya san duk wani motsi da muke yi"
Liti ya jinjina kai ya ce "Nima nayi wannan tunanin"
Nabila ta ce "Mu koma wurinsa, kafin mu san abun yi" suka koma in da suka baro Al'amin da walid da ɗan mama.
Walid na ganin su ya ce "Yaya? Nawa ne kuɗin?"
Nabila ta ce "Kar ka damu, an biya"
Tayi maganar tana zama a gefen Viper, ta tsurawa fuskarsa ido, kawai tuno yadda ya din ga kuka ta din ga yi, gaba ɗaya jikinta ya ƙara sanyi.
Walid ya ce "Ba zaki ga likita ba, wurin da ya caka miki allura?"
Ta girgiza kai ta ce "Bakomai, ni yanzu ta lafiyarsa nake yi"
"Amma yakamata ki koma wurin aiki fa, ai muna tare muna kula da shi"
"No, ko na tafi hankalina ba zai kwanta ba, ba zan iya aikin ba, bari na jira naga abun da hali zai yi"
Likita ya sake shigowa, yana duba Al'amin.
Ya ce "Alhamdilillah, ina ga ya samu bacci, dan ya farfaɗo daga suman"
Nabila ta ce "Masha Allah" ji tayi ya taɓa hannunta, ta kalli hannunsa, ya yi mata alama ta matso.
Ta matsa ta kai kunnenta saitin bakinsa, a hankali ya ce "Ki gaya masa a cire mini wannan abun na hancina bana so".
"Haba master, baka ga yadda kake numfashi da kyar bane ba? Dan ya taimaka maka aka saka maka shi, dan Allah ka yi haƙuri ka ji, Allah ya baka lafiya"
Ya sake cewa "Ki ce musu bana iya bacci, yayi mini abun da zan yi bacci, kaina zai tarwatse"ta ɗago ta kalli likitan ta ce "Doctor, ya ce dan Allah ayi masa allurar bacci, so yake yayi bacci baya iya bacci"
Likitan ya ce "Ai mun yi masa, kuma da jinin ya sauka zak yi bacci mai yawa mai daɗi in sha Allah"
Ta sake sunkuyawa, zata yi masa magana ya ce "Bana son baccin, ba na son jinin ya sauka, bani da rabon sake yin su, Allah ya nuna mini ranar da zan bi matata"
Babu wanda yake iya jin abun da yake faɗa, sai ita, muryarta na rawa take yi masa magana a hankali cikin nutsuwa.
"Haba Al'amin, mai babban suna, shikenan bawa ba zai yi imani da ƙaddara ba, tun da ka fuskanci kurakuran da ka yi a baya, ba sai mu nutsu mu nemi mafita ba, yanzu idan ka mutu maƙiyanka sun ci galaba a kanka kenan fa.
Dan Allah ina roƙonka ka janye wannan fatan da ka ke yi, kuma in dai muna tare in sha Allah zaka yi bacci mai daɗi mai cike da nutsuwa da kwanciyar hankali trust me.
Wallahi i feel your pain, bani na tsinci kaina a halin da ka ke ciki ba, but ina jin zafi a zuciyata, in sha Allah you won't cry alone, an cutar da kai, in sha Allah kuma sai in da ƙarfina ya ƙare a kan ƙwato maka hakkinka, in sha Allah sai nayi sanadin dawo da farincikin ka.
Amma sai ka yi haƙuri, ka yi haƙuri, kayi haƙuri na san da wahala, da ciwo, an yi maka illa, amma ina roƙonka a wannan karon kar ka jinkirta tuba, mu yi ta addu'a, Allah ya taimake mu, ka kwantar da hankalinka ka yi haƙuri, Allah da kansa ya rarrashi masu haƙuri a cikin Alqur'ani"
Yayi shiru yana sauraren Nabila, hawaye yana bin gefen fuskarsa.
"Madam ya kuma kike kuka, mu da muke son hankalinsa ya kwanta, jininsa ya sauka?"
Liti ya ce "Rabu da shi doctor, kukan shi ne samun afuwarsa, mun gode sosai da ƙoƙarin ku.
Cikin kalaman hikima, da tausasawa, ta cigaba da yi wa Viper nasiha, tare da bashi ƙwarin gwiwa, a kan cigaba da haƙuri, da kuma Addu'a.
Har bayan azahar, Viper bai gama frafaɗowa ba, haka Nabila ta haƙura ta tafi gida, bayan ta ajiye musu abincin da ta zo da shi.
Sai magariba ta isa gida, Allah ya sa Abba baya nan, balle ta sha tuhuma.
Message ne ya shigo wayarta, ta ɗauka ta duba.
"Arfa dan Allah kar ki yi mini mummunar fassara, ki tsaya ki saurare ni mu yi magana, kin ƙi ɗaga wayata, hankalina a tashe yake, amma ki bani dama nayi miki bayani, dan girman Allah"
Har jikin Nabila yayi sanyi, kamar ta yarda da maganar Sumayya, sai kuma ta fasa, tayi mata reply da "No peace for wicked person, kar ki sake tunanin zan yarda da maganarki" ta saka lambar a busy, ta cigaba da sabgar gabanta.
Ta idar da sallar isha'i, tana zaune tana cin abinci, kawai Nasir ya faɗo ɗakin, babu ko sallama. Ta ɗaga kai ta kalle shi, amma bata ce masa uffan ba.
"Arfa"
"Na'am yaya"
"Ina ki ka je yau?" Ta ɗaga ido ta kalleshi ta ce "Meyasa kake tambayata?"
"Ki bani amsa kawai"
Cikin ko in kula ta ce "Wurin aiki"
"Ƙarya ki ke yi, me ya kai motarki hanyar ungoggo?"
Ta ajiye cokalin ta ce "Haba DSP, mutum nawa ne suke da vibe a birnin kano?"
"Ya ina magana kina nema ki raina mini hankali, wurin aikinki an ce baki je ba"
"Amma yaya ka san aikina ba na zama wuri ɗaya bane ba, yaya ka ke yi mini tmbaya kamar ka ritsa ƴar ta'adda ne? Wataƙila harkar aiki ne ta kaini wurin, bibiyata kake yi kenan? Ko kuwa meyafaru ko rashin yadda ya shiga tsakaninmu ne?"
Ya sauke numfashi ya ce "Gaba ɗaya kwanan nan kin canza Arfa, na je Division ɗin ungoggo kan wani case, a hanya na ga motarki, dan lambar motarki ce"
"Abokin aikina ne ya ari motar, suka fita, ta sa ta samu matsala. Sannan kuma ni ban canza ba, kai ne dai ka canza mini kwanan nan, ni ban san me nayi maka ba, duk ka tsane ni, ka daina goyon bayan gaskiya, ni na fara tsoron ko kaima ka fara karɓar cin hanci" tayi maganar tana ƙaƙalo kukan kissa.
Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "No ki fahimce ni, ke ɗin ce yanzu dole sai ana saka miki ido, kar wani abun cutarwa ya samar mini ke, ki yi haƙuri ki daina kuka" a haka ya ɓuge da rarrashin ta, ta nuna masa komai ya wuce, yana fita tayi masa gwalo, tare da ajiyar zuciya.
Ta ɗaukko wayarta ta ce "Bari na kira na ji ya jikin ɗan marayan zakina" sai dai wayarsa a kashe, haka ta haƙura.
***
Gaba ɗaya ramma ta fita daga harkar Abdul, abun duniya ya addabe shi, gashi ya kasa gano in da mahaifiyar ta take, babban tashin hankalinsa kar ta gano cewar mahafiyarta ta ɓata. Dan bai san wane irin kalar bori zata yi masa ba.
Ga Indabo ya uzzura masa, dan har an kai masa kuɗin aure, ga shirye shiryen takararsa na ta ƙara yin nisa, amma gaba ɗaya hankalinsa baya kan takarar. Abokansa sai mita suke yi masa a kan duk ya canza, ga aurensa an saka su fara shiri, amma ya kasa mayar da hankali a kai, sun kasa gane kansa gaba ɗaya.
Babu wanda ya tsaya saurara da bashi amsa a kan surutun da yake yi.
Yana zaune yana kallo, amma hankalinsa ba a kan kallon yake ba, tunani kawai yake yi.
Ramma ta ƙaraso kansa ta tsaya, ya ɗaga kai ya kalleta, ya tashi zaune sosai ya ce "Rahama, ya aka yi ne?"
Ta ƙaraso ta durƙusa a kan gwiwoyinta, hawaye na bin fuskarta ta ce "Abdul yasar, dan son da kake yi wa Allah da annabinsa, ka mayar da ni gaban mahaifiyata, naga message a notification ɗin ka, wai aure zaka yi, dan girman Allah ka mayar da ni wurin uwata da ɗan uwana, na yadda zan ƙarasa rayuwata, a rushen zan tattara ta na rayu, ba ma na saka ran zan zan yi aure, na yarda na rayu a haka"
Ya kalli ramma ya ce "Daga ganin message sai ki ce aure zan yi? Bincike ki ke yi mini kenan? To ni ba wani aure da zan yi ".
Cikin kuka ta ce "Ka daina yaudarata Abdul, ka rabu da ni, idan kana son iyayenka, na gaji, na gaji na gaji da haƙuri, da fatan zaka mayar da ni gida, ka ƙyaleni dan girman Allah, ai ka gama morar abun da kake so zuwa yanzu, kowace irin ƙishirwa ce ka kasheta zuwa yanzu ka rabu da ni dan Allah " tayi maganar cikin ɗaga murya.
Abdul ya kalleta a tsanake ya ce "Kin manta alƙawarin da ki ka yi mini ne?"
"Babu wani alƙawari da nayi maka, ni ban san wani alƙawari ba, ka mayar da ni gida"
"Wallahi ƙarya ki ke yi ki rusa maganar da muka yi da ke, da alƙawarin da ki ka yi mini"
"Ka yi mini duk abun da ka ga dama, amma ni dai ka sakeni na koma gida, idan duk matan duniya ne ka je ka aura, ban damu ba, amma a yanzu tun da dai ka gama da rayuwata dan Allah ka rabu da ni"
Abdul ya tsura mata ido, yadda take kuka wiwi har da majina.
Ya saukko daga kan kujerar, ya zauna a gabanta ya ce "Rahama kishina fa ki ke yi"
Kamar zata kai masa mari ta ce "Ƙarya ne, Allah ya kiyayeni ya tsare ni da kishin ƙazamar halitta mara tsoron Allah kamar ka, ni kishin rayuwata nake yi"
Ya sauke numfashi ya ce "Zan mayar da ke, amma sai kin cika mini alƙawarina, sannan kin haifa mini ɗa sannan zaki koma gida, kin ga idan kika haihu duk duniya babu wanda ya isa ya raba ni da ke" yayi maganar yana share mata hawaye.
"Abdul ba zan taɓa yafe maka ba, na bar ka da Allah"
"Duk cikin kishina ne, matsayin matar da zan aura daban, naki ma daban, you are like my guest house, wurin hutawa ta da nishaɗina"
Jiki a sanyaye ta ce "Ka cuce ni Abdul, duk saboda ina 'yar talakan ƙauye, mara gata mara galihu"
Ya girgiza mata kai, ya haɗe bakinsa sa nata, wata irin ajiyar zuciya take yi, a hankali ya cire bakinsa daga nata, ya kalli idanunta ya ce "Iya wuya rahama, ina tare da ke, ban ga wanda ya isa ya raba ni da ke ba. A lokacin da maza da yawa suke gudun matan da suka lalata, ni a dai-dai lokacin soyayyar yarinyar da na lalatawa rayuwa ta yi mini kamun kazar kuku".
Jiki babu ƙwari ta cw "A hakan? Wace irin soyyaya ce zaka yanke mini farincikina ba tare da wani dalili ba, bana sonka Abdul ko kaɗan"
"Ki saurari zuciyarki, kina jin zafin abun da nayi miki ne kawai, amma kina so na rahama, nima kuma ina matuƙar sonki"
"Da ban yi wa kaina, da mahaifiyata adalci ba, idan na fara sonka Abdul yasar"
"Zuciyar ki, cike da ƙuruciya, kina ƙoƙarin sakawa kanki ƙiyayyata ne ta ƙarfin tsiya ne".
"Wallahi wannan ba so bane, ka gama lalata ni, ka samu abun da kake so, kuma ka ce sona kake, me yayi saura?"
"Kin san abun da na ɗauko ki ki yi mini, kuma na daina kamar yadda ki ka buƙata. Wuri ɗaya nake kwana da ke nake tashi, amma na daure, ban sake yi miki ba, kuma na lazumci istigfari kamar yadda ki ka gaya mini. Kar ki saɓa alƙawarinmu mana. Wa ki ka taɓa ganin ya lalata yarinya ya bita kuma yana so? Ke kin san waye ni a garin nan da ƙasar nan. Na fiki shekaru, da ilimi da tarin dukiya, amma gaba ɗaya na bar abun da yake gabana na tattara hankalina a kanki, ki yafe mini mana sweetheart, ki yarda ki so ni, zan goge laifukana zan kuma mayar da ke wurin mama in sha Allah"
"To yaushe?"
"Very soon, da zarar kin yafe mini, kuma kin cika mini alƙawari"
Ramma ta share hawayenta ta ce "Abdul ta yaya zan haihu da kai, in kalli duniya in ce musu me? Baga mata nan zaka aura ba, ba sai ku haihu ba?"
"Naki nake so please" yayi maganar yana sumbatar goshinta, cikin tsananin so da shauƙinta.
***
Yau ma uban sammako Nabila ta yi, ta tafi asibitin da Viper yake, sai dai ba ta ɗauki motarta ba.
Yanzu ma ɗan mama ta tarar, yana ta sharar uban bacci, babu liti babu Walid.
Viper kuma yana zaune, ya jingina da bango idanunsa a lumshe.
Murmushi tayi, tare da farin cikin ganinsa a zaune.
Ta ƙarasa ta zauna ta ce "Yallaɓai, good morning, ya jiki? Alhamdilillah na ji daɗin ganinka a zaune" sai dai kamar mai bacci, bai buɗe idonsa ba.
Hannunsa ta kalla, ɗaya da drip, ɗaya kuma kamar lazumi yake yi. Wani irin farinciki ya kama Nabila.
Wani baƙin abu ta hanga, a gefen pillown sa, ta saka hannu ta janyo, ta ce "Menene wannan, ko kayan da zaka canza ne?" Tayi maganar tana buɗewa.
"Wannan rigarka ce?" Buɗe idonsa yayi ya kalleta, cikin wani irin zafin nama ya fizge rigar daga hannunta, ya hau waige-waige.
Ta ce "Menene? Meyafaru?"
Ya kalli in da ɗan mama ya saki baki yana bacci, ya kalli taga babu hanyar shiga ko fita ta tagar, ya sake ɗaga rigar.
Baƙar riga ce shirt, mai ɗauke da hoton tambarin dragon a gefen rigar, bayanta kuma an rubuta wasu alphabets, da bai bar Nabila ta karanta ba. Duk da jikinsa babu ƙwari haka ya saka ƙarfin sa, ya yayyaga rigar, yana cigaba da waige-waige.
Cikin rashin fahimta ta ce "Wai me yake faruwa ne?" Ya girgiza mata kai, ya sake jingina.
Nabila ta kalle shi ta ce "Akwai damuwa fa, jiya an yi settling bills ɗin ka, sai dai bamu san waye ba, an ƙi gaya mana ko wanene" ya ƙura mata ido, ta jinjina masa kai, alamar da gaske take.
"Dan Allah ka gaya mini, menene yake faruwa ne, bai kamata ka ɓoye mini komai ba, tare fa zamu yi gwagwarmayar nan" Sai ya lumshe idanunsa ma, yaƙi kulata.
"Haba master, yar suganka ce fa, talk mana" a hankali ya fara kaɗa ƙafa, amma bai yi magana ba.
"Sweetheart" ta faɗa tana dariya ƙasa-ƙasa.
"Sweetheart magana nake fa" sai ya kwanta ya juya mata baya baki ɗaya.
"Am sorry wasa fa nake yi maka, ya ƙarfin jikinka to, ina fatan akwai progress, kana samun sauƙi?"
Ya girgiza kansa alamar "A'a"
Ta ce "Ohh ni Nabila ina ganin mulki yau, Allah dai ya jaddada rahama da Fatima jauhar, ta yi ƙoƙari sosai"
Ya ce "Amin" tausayin sa ne ya sake kama ta, ta ce "To tashi ka karya, na san yanzu za a zo yi maka allurai, kuma na san kana jin yunwa"
Bai yi magana ba liti ya shigo da leda a hannunsa, ya kalli ɗan mama da yake ta bacci, ya dake shi da ƙafarsa ya ce "Tashi, ɗan asara, idan ma sace shi za ayi, kana kwance ka shanya baki kamar fatarin mata kana bacci" ɗan mama ya tashi yana mutsutsuka ido.
Jauhar ta kalleshi ta ce "Ina kwana?"
Ciki ciki ya amsa, ya dafa Viper ya ce "Maza ya ne, ya jikin?"
"Alhamdilillah"
"To masha Allah, ga brush ɗin da toothpaste, ka wanke bakin, yanzu Walid zai kawo abinci, sai ka yi wanka ka canza kaya"
Ya yinƙura ya tashi zaune, ya ƙurawa ɗan mama ido, sannan ya ce "Kai waye ya shigo ɗakin nan jiya da daddare?"
"Likita ne, sai mai bada magani Nurse, sukenan"
"Ƙarya kake yi"
Ɗan mama ya ce "Wallahi sukaɗai na gani"
Liti ya ce "Dama ya kwanta yana ta uban bacci, ya za ayi ya san me ake yi? Ina fatan ba wani abun ne ya faru ba?"
"Babu komai"
Da Al'amin ya shiga banɗaki, sai Nabila ta fita tana waya da barrister Habib, ya ce lallai yana son ganinta, Sumayya T ladan ta turo wasu mata, kuma zasu taimakawa aikinta a kan bunkure.
Nabila
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 62 Chapter of 121