da ita ku kula,
Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍
Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍
Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃
Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,
Mmn Yusuf likitar Mata💃😍
Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃
Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃
Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima
KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻
Kalolin gumba
Kalolin matsi
Kalolin gari
Kalolin tsumi
Zumar dabino
Zuma Mai rubutu
Zumar goron Tula
Zumar ridi
Dahuwar kaza
Dahuwar zabo
Dahuwar zuciya
Dahuwar ciccibi
Dahuwar tsoka Tara
Dahuwar Yan shila
Dahuwar kwai Mai rubutu
Turaren mallaka
Turaren Mara
Turaren tsugunno
Turaren k'irji
Shuumar humra
HATSABIBI turare
Hatsabibiyar humra
Matan gaske
Maltinat Mata
Shayin Mata
Tsumin kankana
Sirrin tafin k'afa
Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini
Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a
Akwai hadin farinjini na matar aure
Akwai kwallin mallaka
Zoben mallaka
Set na Jigidar mallaka
*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻
07069711327 Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍
Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊
Bakin Nabila ya cigaba da karkarwa, idanunta suka fara ƙoƙarin kakkafewa.
Liti ya na tsaye daga baya a jikin bishiyar umbrella da take tsakar gidan, wani irin tausayin Nabila da jauhar har ma da Viper ya mamaye shi, har gara ma Viper, shi yanzu idan da sabo ya riga ya saba, ita kuwa an rabata da 'yat uwatta, an nesanta su da juna, kuma ta rasu ba su haɗu ba, sosai ya ji nadamar abubuwan da ya din ga yi wa Nabila.
A hankali Viper yake ɗan girgizata, yana kiran sunanta "Nabila, me yake damunki?"
Su Zakiyya da suke ɗaki kuwa, gaba ɗaya suka yi sak, dan sun san su ne kanwa uwar gamin abin da ya faru.
Baba ya miƙe hannu zai taɓa Nabila, major ya riƙe hannunsa ya ce "Bashir, haryanzu ina nan a kan bakana, babu kai babu abin da mairamu ta bari, ba zan taɓa baka Nabila ba, kuma ka cire a ranka Nabila ba 'yar ka ba ce ba"
"Yanzu maitama abin da ka yi kana ganin daidai ne? Baka gaya mini yarana biyu ba, ka kawo mini ɗaya ka nesanta ni da ɗaya? Zan iya ƙararka fa a kan abin da ka yi mini"
"Shut up! Ko kuma ni na yi ƙararka ba, da ka kashe mini 'yar uwa, ai dai na kawo maka ɗayar ko, ka aura wa ɗan daba ya kasheta, kai ka sani" Viper ya yinƙura da Nabila a hannunsa, sai wata irin miƙa take yi, ya nufi waje da ita.
Bayansa suka biyo, Bashir sai share hawaye yake yana kiran "Aminu ina zaka kaita ka tsaya na ga 'ya ta".
Cikin ɗaga murya, major yake yi wa Viper magana, a kan ya tsaya, Nasir kuwa kasa shan gaban Viper ya yi, gaba ɗaya suka bi shi. Sojan da ya kawo su, yana ganin Viper ya fito, ya buɗe masa mota, ya saka Nabila a ciki.
Saifu ya riƙe shi ya ce "Ina zaka kaita, dole fa ka tsaya a gama wannan tarzomar"
"Cika ni" Viper ya yi maganar yana kallon saifu. Saifu ya cika shi ya ja da baya.
Viper ya kalle su ya ce "Zan mayar da ita asibitin barrack, idan na bar muku ita a nan, zan iya yin laifi tun da tana ƙarƙashin kulawar jami'an tsaro ne.
Walid taho mu yi gaba, su taho tare da liti"
"A'a shi dai su taho tare"
Zakiyya ta ce "To a tafi babu wata mace, mu tafi gaba ɗaya mana" kafin Viper ya bata amsa, Hafsa ta ture shi, ta shige cikin motar, yanayin yadda ta shiga kawai zaka gane kan babu daɗi.
Ya kalli saifu ya ce "Ka shiga ka riƙeta mu tafi"
Hafsa ta ƙanƙame Nabila, tana kuka ta ce "Yaya saifu, rannan ba ce muku naga Jauhar a asibiti ba, aka ce bani da hankali, to ai gashi yanzu ta dawo ba ta mutu ba"
Walid da Viper suna gaban mota, sai da Walid ya waiwayo gwanin ban tausayi, bai manta hafsa a da ba, yar gayu 'yar ƙwalisa, jawur da ita ta sha mai, amma yanzu duk ta koma baƙa ta firgice.
Har suka isa barrack, Nabila tana wannan miƙar bakinta yana rawa, viper ya ce a ƙarasa da su asibitin sojoji, saifu ya ce "Anya wannan abun ba aljanu ba ne?"
"Ba wani aljan" Viper ya faɗa a daƙile.
Sai dai suna isa, aka ɗauki Nabila aka shiga da ita, Viper ya yi wa ma'aikatan alama, da karba bari kowa ya shiga in da take.
Tafiya ce mai nisa sosai, daga gidan baban Nabila zuwa asibiti, amma har suka zo, jikinta a sandare yake, dai dai idan ta motsa tayi miƙa kawai.
Alluran bacci kawai aka yi mata, sai drip na babu gaira babu dalili, kusan ko ina a jijiyoyin hannunta akwai tabon hudar cannula.
Major ya fara tambayar ina aka kai masa 'ya, aka ce masa an hana kowa ya shiga in da take. Cikin hasala ya ce shi ma fa tsohon ma'aikaci ne kamar yadda yake gaya musu, dan me za ace ba zai shiga ba.
Aka ce masa ba bisa umarnin sojoji aka hana kowa shiga wurinta ba, bisa ga umarnin likitoci ne.
Baba ma ya ƙarasa tare da tijjani, yana kiran wayar saifu, dan ya gaya musu, a in da aka kwantar da Nabila, bayan su haɗu, saifu ya sanar masa an hana kowa shiga.
Baba bai damu da irin mugun kallon tsanar da major yake yi masa ba, babban burinsa kawai ya sake tozali da kyakywar fuskar 'yar sa, mai kama da jauhar Waliyiyya, kuma kamannin mairamu chubaɗo.
Walid ya kalli liti, da kamar ya koma kamar ɗan tsakon da ya faɗa ruwa, duk yayi tsuruu da shi, kamar mara gaskiya.
"Ya dai liti?"
"Walid zuciya da saurin fushi ba su yi ba"
"Meyafaru?"
"Yarinyar nan wani irin mugun tausayi ta bani, wallahi kamar na yi kuka, tabbas na daɗe da gane ba ita ce jauhar ba, tun da damu aka yi jana'izar ta, hausin abin da wancan banzan yayi mini mai ƙugu kamar an miƙo kare ta taga, da rashin kunyarta da shishishigi da take yi wa Viper, ya sanya na ji na tsaneta, haka kurum idan yana saurarenta, sai na ji kamar ya na cin amanar jauhar ne, ko bayan mutuwar ta, bai kamata ya kula wata mace ba"
"Abin da nayi ta nuna maka kenan liti, amma ka ƙi ganewa, kullum cikin yi mata rashin mutunci ka ke, ji maganganun da ka caɓa mata muna tafe a hanya. Ai a duniya idan zaka yi ƙiyayya ka yi ta sama-sama haka ma soyayya amma kawai ka je ka yi ta hantararta, ashe abin da yayi jauhar shi ya yi Nabila"
"Amma kamar su ta yi mugun ɓaci fa, ni fa na daɗe ina kokwanton idan ba fatalwar jauhar ba ce, halayensu da na din ga nazarta na fuskanci wannan sai a hankali, gaba ɗaya sun sha banban ta fuskar halayya, amma hatta muryarsu iri ɗaya, sai dai ta jauhar ta fi sanyi da nutsuwa, wannan kuwa tsabar tsiwa da masifa ce a cikin ta ta muryar, Allah sarki Allah ya jiƙan 'yar madara". Walid ya amsa da Amin.
Major kuwa ganin Bashir ya kafe ya nace, ya sanya ya Kalle shi ya ce "Bashir, ka kama hanyarka ka bar wurin nan, wallahi ko me zaka yi, ba zan ba ka Nabila ba, kar ma ka yi tunanin ayyana kanka a matsayin mahaifinta"
"Maitama babu in da zan je, har sai ya ta ta farfaɗo, kuma sai ka bani kayata na tafi da ita"
"Ita ma ka je ka aurawa ɗan daba ya kasheta kenan"
Bashir ya ce "Ko ma wa zan aurawa, 'ya ta ce, ina da iko a kan aba ta"
Saifu ne ya din ga ba su haƙuri, a kan su yi haƙuri su daina abin da suke yi.
Viper kuwa yana zaune a cikin ɗakin, da take tana bacci, yayi alwala ya gabatar da salla, sannan ya nemi wuri ya zauna yana danna wayarsa.
Ya ɗago ya kalleta jin ta yi tari, bacci take yi, amma yanayin fuskarta ya nuna ba daɗin baccin take ji ba sam.
Sosai Nabila take kama da jauhar, babu yadda za ayi ka ce ba mutum ɗaya ba ce ba, sai ka rayu da jauhar, ka dawo ka rayu da Nabila, zaka fuskanci su na da banbanci.
Amma mafi yawa they have so many things in common.
Ya mayar da kansa kan wayarsa, ya ci gaba da daddanawa, bai fargaba kawai ya ga ta tashi tsaye, ta fizge ƙarin ruwan, jini yana zubowa daga hannunta.
Da azama ya tashi, ganin idanunta a rufe ko gani ba ta yi, ta nufi hanyar fita daga ɗakin.
Shan gabanta ya yi ya ce "Ina zaki je?" Da kyar ta buɗe rinannun idanunta ta kalle shi, ta je uban tsaki, ta raɓa shi za ta wuce, amma ya riƙe ta, ya danne hannunta da yake zubar da jini.
Ya ce "Abla, menene? Meyake damunki?" Ta tsaya ƙyam sai rangaji take yi kamar wadda ta sha ta bugu, tana lumshe idanunta ta na buɗe su.
"Abla" ya sake kiranta a hankali.
Kamar wadda ta farka daga bacci ta kalle shi, ta ce "Mafarki ne ko, ai ba gaske ba ne ko?" Kan ya kai ga ba ta amsa, ta kalli kayan jikinsa, ta kalli na ta, ta shafa fuskarta, ai sai ta saka kuka, ta fara kiran Abba da ƙarfi, tana ƙoƙarin ture Viper tayi waje.
"Shikenan, ya isa ki nutusu, bari ayi masa magana ya shigo ki ganshi, amma mu je ki zauna tukuna" kamar mahaukaciya sabon kamu, haka Nabila ta din ga misbehaving.
Viper ya yi waya, ya ce a ba su damar su shigo su ganta.
Sai ga su duk sun shigo, ga hafsa saifu da Tijjani, major da Bashir na rige-rigen shigowa, sai kuma su liti da walid da Nasir.
Bin su ta din ga yi da kallo, Hafsa ta ƙarasa gaban gadon Nabila ta ce "Waliyiyya, sannu kin tashi? Ina ɗan jaririnki yake? Shikenan yau sai ki koma gidan Master, ku ci gaba da shan soyayya" ƙuri Nabila ta yi mata da ido, dan ba ta santa ba sai a ɗazu ta taɓa ganinta.
Major ya ce "Arfa, ya jikin naki?" Tayi shiru ta sunkuyar da kai.
"Arfa Abba ne fa, ba ki gane ni ba ne?"
Bashir ya zagaya ta gefenta, yana ƙare mata kallo, cikin matsananciyar soyayya da ƙauna.
"Yarinyata, ki kalle ni, ni ne mahaifinki" yayi maganar cikin matsanancin rauni.
Nabila ta ɗaga kai, ta kalle shi sau ɗaya, ta kawar da kanta, tabbas ta ɗokanta da son ganin mahaifinta, ba irin alwashin da ba ta yi ba, na idan Allah ya sa yana raye, su ka haɗu, babu ruwanta da Al'ada sai ta rungume shi, ko a yaya yake, sai dai kash! Ba ta ji daɗin a yadda mahaifin na ta ya kasance ba, duk da ba ta san mahaifiyarta ba, amma uwa uwa ce, ba ta ji daɗin abin da ta ji game da tarihin zaman su ba.
Nasir ya ce "Nabila, ki yi magana mana"
Major ya sake cewa "Arfa, ki kalle ni mana? Meyake damunki?"
"Ni ku daina nuna ku na so na, ba kwa so na ba kwa ƙaunata, meyasa za ku yi mini haka? Ni menene laifina a tsakanin ku? Ace ina da 'yar uwa ban ganta ba, ba ta ganni ba har ta koma ga Allah, kun san me nake ji kuwa? Ban san uwata ba, 'yar uwata kuma ta mutu ban taɓa ganinta ba, duk ba kwa so na, kun fifita tsamin alaƙar ku a kai na, ta mutu fa ba zan ganta ba kenan. Abba tsananin son da ka ke yi wa 'yar uwakka ya sanya ka yanke wannan hukunci, ni yanzu ba ka yi tunanin a wane halin nake ciki ba, da na rayu kamar wata mujiya, ba wani ɗan uwa da zan ɗaga in kalla ya na so na tsakani da Allah" tayi maganar tana wani irin kuka mai matuƙar sauti.
"Shikenan da ban haɗu da Viper ba, ba zan san ina da 'yar uwa ba, Abba ka ɓoye mini, kai kuma babana, duk burin da na ci na in ganka, gwiwata ta yi sanyi, meyasa ka yi wa mahaifiyarmu haka, da ba ka yi haka ba, da babu lallai a raba ni da 'yar uwata, ban fa taɓa ganinta ba, shikenan ta tafi har abada"
Ta miƙe tsaye a kan gadon, tana neman hanyar sauka.
Viper ya ce "Meye haka ne ki ke yi? Ina kuma zaki je?"
"Ka kira mini sumayya dan Allah" tayi maganar cikin sigar magiya.
"Sumayya kuma? Me za ta yi miki?"
"Ni dai ka kirawo mini ita"
"Magariba ta yi, ba za a kirata ba sai da safe"
Likita ne ya dawo, ya ce duk a fita a ƙyaleta, a stage ɗin nan da take, za ta iya samun matsalar ƙwaƙwalwa, a ƙyaleta ta huta.
Matsananciyar nadama da jin kunya, suka mamaye Bashir yanzu shikenan Nabila ba ta farincikin ganinsa.
Shi ma major, damuwa ce ta mamaye ilahirin fuskarsa, wani irin dana sani yake yi, na raba Nabila da jauhar da ya yi, wato duk wayon bawa ƙaddara ta riga fata.
***
Gidan su jauhar, tun bayan da Zakiyya ta yaudari maman saifu, ta aurawa Alhaji mu'azzam Hafsa, dama haɗin kan na su ya lalace, kullum cikin faɗa da tashin hankali suke, sai ka ce ƙanan yara, gaba ɗaya tarbiyyar yaran sai a hankali, ba wanda yake ganin uwar wani da gashi sai tasa.
Bayan tafiyar su Major, Zakiyya ta ce "Ke kin ga wani ikon Allah, wallahi saura kaɗan na haukace, na ɗauka gamo na yi, yanzu duk tsawon wannan lokacin dama jauhar 'yan biyu ne?"
"Wallahi kuwa, abin da mamaki ba kaɗan ba, kuma wani ikon Allah, ba ya zancen uwar su, tun wancan lokacin"
Zakiyya ta ce "Eh, amma ai yana kallon hotonta wasu lokutan, wai dan Allah maman saifu, wurin wani malamin ki ka kai Bashir, da aikin nan ya ci shi, ya manta da chubaɗo gaba ɗaya daga rayuwarsa, ashe a tagayyare haka ta haife su?"
A ƙule ta ce "Ban gane wurin wani malami na kai shi ba, muka kai shi dai, ke da yarinyar nan ta rayu a gidan nan, ai da wallahi kashinmu ya bushe, yadda ya din ga rawar kan nan, ya nemi ya mayar da mu borori a kan bafulatanar daji, kawai a daina wani tone-tone"
Zakiyya ta ce "Uhumm ai shikenan, zan ga yadda dramar nan za ta ƙare, shi ya ɗauki zafi shi ma wan uwarta ya ɗauka, amma abin da ya bani mamaki na kasa ganewa shi ne, yaya aka yi mijin jauhar ya samo ta, a ina ya ganota ya kawota nan ɗin?"
"Oho sanin gaibu sai Allah"
Su ka ci gaba da hira, su na mamakin yadda al'amuran suke cike da sarƙaƙiya da ban mamaki.
***
Nabila kamar tana tura magani, haka take shan youghurt ɗin gabanta, ta na yamutsa fuska, fuskar tayi jawur, Viper ya zuba mata idanunsa ko ƙiftawa ba ya yi.
"Kin ce ke youghurt, ku ma kin ƙi sha"
Hawaye ya gangaro kan fuskarta ta ce "Ka takura mini ne, babu yadda zan yi, dan Allah ka nuna mini hoton 'yar uwata na sake ganinta, idan an tuna ba zan taɓa ganinta ba, wallahi sai na ji zuciyata ta buga da ƙarfi ban santa ba, amma wallahi ina son ta, meyasa tuntuni ban sanka ba ka haɗani da ita ba?"
Ya shafi fuskarsa cikin dakiya ya ce "Allah ne bai ƙaddara ba"
"Kenan kai nake mafarkin tana nuna mini a cikin sarƙa?
Yayi ƙuri da ido yana kallon ta.
"Wallahi Vi da gaske nake son ta, ashe haka ka ji, kai da ka santa ya ka ji da ka rasata, gara ma kai ni fa ban santa ba ma, tsakani da Allah iyayen nan nawa sun kyauta mini?" Tayi maganar tana rushe masa da matsanancin kuka.
Allurar gefen gadonta, ya ɗauka ya buɗe ya zuƙe ta, ya ce "Kwanta ki bani hannunki na yi miki, sun shigo za su yi miki ki na salla" ta kalleshi tana sheshsheƙar kuka.
"Kar ki damu, ɗan ƙwaya ne ni, kuma ɗan daba na saba riƙe sirinji da allura.
Ya buɗe cannulan ya fara yi mata allurar, a hankali jikinta ya fara sanyi, ya kwantar da ita.
"Tun daga lokacin da na fuskanci bijirewa ƙaddara na nufin halaka ta dindin ko samar da damejin da ba shi da hanyar gyaruwa, ya sanya na yi saranda, na bawa ƙaddarar damar ci gaba da jujjuya akalar rayuwarmu, domin na fuskanci ƙaddarorinmu na da alaƙa da juna. Tamkar na kashe kaina, haka na ji bayan rasa matata, ni har hauka na yi ai, na kuma yi ƙoƙarin sake sabauta rayuwata. Kar ki tafka irin kuskuren da na yi, nake ta fama da dana sanin da ba shi da wani amfani a gare ni, ina guje miki aikata haka. Ki yi haƙuri ki rungumi ƙaddara, ki karɓi mahaifinki kuma ki karɓi mariƙinki, ki sasanta tsakaninsu" cikin muryar jin bacci ta ce "Maza wasu ba su yi ba, Allah sarki babarmu 'yar fulanin riga, abin tausayi"
"Idan kuma abin da ya same ta ya na da alaƙa da jinsinta fa, su suka aikata komai, mu daina zargin jinsinmu da cutar da ɗaya, kawai mu mu zama adalai a kowane lokaci, da mahaifinki da major duk ba na yarwa. Zan iya rantse miki ban san mahaifinku da wani mugun hali ba, mutumin kirki ne, duk da ba ni hali na kirki, amma auren 'yar sa da na yi, ɗa ya ɗauke ni ba siriki ba"
Ta buɗe idanunta da kyar, cikin raɗa ta ce "Spy, wai nasiha ka ke yi mini? To ka fara yi wa kanka, zan iya rantse maka, Abbu mutumin kirki ne, bamu haɗu a zahiri ba, a waya muka yi magana amma dattijon arziki ne" ta yi maganar daidai lokacin da bacci yayi awon gaba da ita.
Dare ya fara yi, Viper ya fito daga sashin in da ɗakin Nabila yake, daga major har Baba duk suna nanz har a lokacin ba su tafi ba.
Viper ya ce "Ina ganin zaku iya tafiya gida, zuwa in Allah ya kaimu da safe, tun da an ce ƙwaƙwalwarta na buƙatar hutu, kar ta rikice gaba ɗaya. Amma dai yakamata ku sasanta kanku kafin Allah ya sanya ta sake farfaɗowa".
Major ya kalli Viper rai a ɓace ya ce "Ai kai ne kanwa uwar gamin komai, dan me zaka ɗauke ta, ka kai ta wurin wannan mutumin mara tsoron Allah, ita ma ya bari rayuwarta ta wulaƙanta kamar yadda ya wulakanta ta uwatta, kuma saboda rashin tsoron Allah ya aura maka yarinyar da ba ta ji ba, ba ta gani ba ka kasheta, kuma saboda zalunci ka dawo ka sanya ta tssya maka, take baka kariya, alhalin ka kashe yar uwatta, wane irin abu ne wannan?. Duk a dalilinka zumuncin da yake tsakanin yaran nan, ka watsa shi, ba ta jin maganar kowa sai ta ka, idan abin gaskiya ne, meyasa ni ba ka je ka same ni a gida, ka yi mini bayani ba kawai ka ɗauke ta ka kai wa wannan mutumin"
Maganganun Major sun yi wa Viper zafi sosai, yayi ƙuri da ido yana kallon major, amma bai yi magana ba.
Baba cikin mamaki ya kalli major ya ce "Ka ga wani iko na Ubangiji da yadda yake jujjuya al'amura yadda ya so, duk guje-gujen naka, da Allah ya ƙaddara, Nabila ce za ta tsaya wa mijin 'yar uwatta, ka yi ƙoƙarin tsayawa a kan iliminta da tarbiyyarta, amma Al'amin ba mutumin banza ba ne ba, haryanzu ban yadda zai iya kashe mini 'ya ba, kar ka ƙara danganta shi da kisan kan jauhar"
Saifu ya ce "Baba ka daina wannan maganar fa, ba ka da tabbas ya aikata ko be aikata ba"
Liti ya ce "Ji wani ɗan wahala kuma, to ai sai ka jira kotu ta tabattar da shi ya aikata, tun da shari'a za a fara kwanan nan. Mu mu ka yi rayuwa a gidan Viper a tsakanin sa da Jauhar. Mun san yanayin zamantakewar su, tsabar ƙauna ko sunanta ba ya iya faɗa sai 'yar madara, sai ka jira kotu tukuna, kafin ka yi wannan maganar"
Shiru saifu yayi, dan ya san halin liti farin sani, 'yan a mutun mai zamani ne.
Da kyar da siɗin goshi, aka samu suka tafi gida, shi ma sai da su ka tabbatar da Nabila tana cikin tsaron da babu wanda zai gudu da ita, dan kowa zargin kowa yake yi.
Viper a makwancinsa, yana ta jujjuya al'amarin ya san akwai sauran ƙura a gaba, major ya ɗauki zafi sosai da sosai, kuma haɗin kansu ne zai ba wa Nabila nutsuwar ci gaba da gudanar da shari'ar da take yi a cikin nutsuwa.
***
Sumayya duk wani abu da ya shafi Indabo, haka take yaɗa shi a kafafen watsa labarai ba tare da tsoro ko fargaba ba, ba shi kaɗai ba, mussaman Alhaji mu'azzam yake sanyawa ake nemo mata manyan rahotanni na bankaɗa tare da cikakkiyar hujja a kan miyagun harƙallolin da ake yi a ƙasar nan. Sai dai kash, ko an bankaɗo babu wani abu da talaka zai iya yi a kai face Allah ya isa. Dan ƴan siyasar sun din ga ƙoƙarin kare kansu kenan, lokutan zaɓe su sake lallaɓowa tare da fara ayyukan babu gaira babu dalili, da raba tallafin abin da bai kai kaso goma a cikin abin da suke wawaso na al'aumma ba. Sai dai a wannan karon al'ummar sun yi rawar gani wurin yin abin da ya dace, karo na farko a Nigeria da ake ƙoƙarin yi wa sanata kiranye. Duk da irin barazana da matasan da suke jagorantar abin suke yi, amma suka dage babu gudu babu ja da baya, dan tuni sun miƙa wasiƙa ga hukumar zaɓe ta ƙasa a kan son yi wa Indabo kiranye. Hakan ya ba wa wasu matasan daga sassa daban-daban na ƙasar nan ƙwarin gwiwa da ganin cewa ashe za su iya kawo canji ga waɗanda suke wakiltar su su ma.
Alhaji mu'azzam mutum ne na mutane, dan haka mutanensa su ka din ga kiransa a kan ya fito takara.
Dama harin kujerar inda
Bayan kammala program ɗin ta, ta ga kiran waya.
Lambar Nabila ta gani, ta ɗaga ta ce "Ke ya ne, program na kammala ko numfashi ban shaƙa ba, kin doko mini kira"
"Ta na asibitin barrack, ta na buƙatar ganinki da gaggawa" ƙuuu cikin sumayya ya yi ƙara, muryar Viper ce, a duniya Allah ya yi masa kwarjini, muryarsa da ta ji kawai gabanta ya faɗi. Kashe wayar ya yi, bayan kammala gaya mata saƙon.
A gurguje Sumayya take ƙoƙarin kammala ayyukanta, dan ya je ya ji me ya sami Nabila.
A jiya da major ya koma gida, kasa gane kansa matansa suka yi, dan babu wadda ya kula, kuma ya ce baya buƙatar kowa ta zo masa turaka.
Sai Nasir suka tutsiye, su na tambayar sa, ina su ka je jiya wuni guda ba sa nan.
Nasir ya labarta musu komai, gaba ɗaya suka yi shock. Anty ta ce "Dama mahaifin Nabila yana raye?"
"Eh, mun ganshi jiya ma, ɗan daban nan Viper da ake nema, 'yar biyun Nabila ya aura ya kashe, kuma saboda shirme take kare shi, shi ya ɗauke ta ya kaita wurin mahaifinta" al'amarin yana buƙatar nutsuwa kan a warware shi, dan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 92 Chapter of 121