Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
60 / 121
yinƙuri. Babu tsammani ta ga Nasir ya shigo office ɗin ta, ta tashi tsaye ta ce "Yaya lafiya?" "Nabila wai ke meyasa a duniya ba kya nemawa kanki zaman lafiya ne? Gaba ɗaya na kasa gane kanki a 'yan kwanakin nan, menene yake damunki ne?" Cikin rashin fahimta ta ce "Me kuma nayi?" "Comment ɗin da ki ka yi da safe nake magana a kai" yayi maganar yana ciro wayarsa ya daddana, ya buɗe facebook ɗin sa, ya tura mata wayar. Ta kalli wayar, posting ne da hukumar yan sanda tayi, na cigaba da neman Aminu Viper ruwa a jallo, saboda ayyukan ɓarna da yake cigaba da yi. Tayi comment da "Wannan abun kunya ne ga rundunar tsaron Nigeriya, ace kuna tsare da mutum a prison, a sake shi kuma a dawo ana nemansa, ba shi ne abun bincike ba, hukumar 'yan sanda, da prison, da ta shari'a su ne abun tuhuma da zargi" aikuwa mutane suka yi caa a kan comment ɗin ta, suna reply. "Yanzu yaya fisabilillahi menene laifina a cikin wannan comment ɗin nawa, ita hukumar 'yan sandan, dan ayi comment ai suka yi posting ɗin, kuma gaskiya na faɗa. Akwai ayar tambaya a kan ma'aikatar Shari'a, hukumar yan sanda da ta gidan yari a kan case ɗin nan, kar ka yi wani tunani daban, ina goyon bayan gaskiya ne kawai" "Nabila ba kowane lokaci gaskiya take tasiri a ƙasar nan ba, yanzu ki ka shigo cikin system ɗin nan, ƙasar nan ta wuce duk yadda kike tunani". "Na sani, amma rashin yin wani yunƙuri na kawo gyara, shi ne ke kawo mana koma baya yaya, ba wai ina goyon bayan Aminu Viper ba ne ba, menene gaskiyar abun da yake faruwa nake son sani" Cikin takaici ya girgiza kai ya ce "Idan kin ƙi ji, ba zaki ƙi gani ba arfa". Ya ɗauki wayarsa ya juya ya nufi hanyar fita, ya kama handle ɗin ƙofar office ɗin ya murɗa ya buɗe. Sai dai wanda suka yi ido huɗu da shi a tsaye ya sanya gabansa wani irin mummunar faɗuwa. Ya raɓa jikin Nasir ya shiga cikin office ɗin, Nabila ta waro ido tana kallonsa tana kallon Nasir. Ayshercool 08081012143 57 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Kallonta yake yi ta cikin baƙin glass ɗin idonsa, duk da ya saka facemask, babu yadda za ayi Nabila ta kasa gane shi. Nasir ya tsaya ya waiwayo, yana son sake ganin waye, duk da fuskarsa a rufe take da face mask, amma ya tsaya ƙyam a tsakiya, ya juya wa Nasira baya, yana fuskantar Nabila. A hankali ya ƙarasa takawa, yaje ya samu wuri ya zauna a kan kujera, ba tare da yayi magana ba. Nabila kuma ta kalleshi ta kalli Nasir. Nasir ya juya ya tafi, yana fita da saurin gaske ta ƙarasa, ta rufe ƙofar office ɗin ta saka mata key. Ta dawo ta kalleshi, ya cire facemask ɗin sa da glass ya ajiye a kan teburinta. "Su maciji an fito daga rami, kuma kai tsaye aka yo wurina,  dan Allah meyasa ka ke son lallai sai ka haɗu da yaya Nasir ne? Da ya gano ka da ni da kai zai haɗa duk ya kama, dan ban san me zan ce masa ba" Ta dafe ƙirjinta ta ce "Wayyo Allana, haryanzu zuciyata racing take yi, ranka ya daɗe irin haka sai ka kirani a waya, ka ce in zo kana son ganina, amma wannan dirar mikiyar da ka yi mini ohh my God me ma zan ce ne? Allah ya sa babu wanda ya sanka" ta zagaya ta buɗe fridge ɗin office ɗin ta, ta ɗauki plate ta ɗoro masa apple, ayaba da lemo ta zo ta ajiye masa. Ta tsiyayo ruwan zafi a dispenser ta haɗa masa tea mai zafi, ta buɗe jakarta ta ɗaukko ɗan ƙara min flask, ta juye masa dankali a kan plate da ƙwai, ta ce "Bisimillah, fara cin abincin sai mu yi magana naga yanzu safiya ce" yayi shiru yana danna wayarsa. "Ka ci abinci, wanne zaka fara ci?" Still bai yi magana ba, har ta fara jin haushi. "Sweetheart, magana nake fa, 'yar suga na magana" ya ɗago ya kalleta. Ta saka hannu ta karɓi wayarsa ta ajiye, ta ɗauki kofin shayin ta miƙa masa ta ce "Ba dan ni ba, dan Allah ka sha, a gabanka na haɗa, ban kuma son da zuwanka ba, balle ka ce na zuba wani abu a ciki dan Allah" tayi maganar cikin kwantar da murya. Ya saka hannu ya karɓa, sai dai kamar ƙaramin yaro, ya zubawa kofin ido. Ta ɗaukko plate ɗin dankalin, ta riƙe a hannunta, ta kalle shi ta ce "Sha mana" ya tsareta da idanunsa masu ban tsoro. Ta sauke nata idanun, saboda yadda nasa suka yi mata nauyi. Ta saka hannu ta kai kofin bakinsa, ya buɗe bakinsa a hankali, ya fara sha. Tayi ɓoyayyiyar ajiyar zuciya, ya sauke kofin, ta miƙa masa dankalin, kamar mai koyon cin abinci, haka yake ɗauka yana ci. "Yauwwa My dear" yana ci, Adam apple ɗin maƙogwaronsa, na kaiwa na komowa, sai yayi kamar zai yi magana, sai ya fasa ya haɗiye maganar tare da abincin, da ƙyar yake haɗiye abincin, a duk lokacin da ya saka abinci a gaba zai ci, haka yake ji, sai ya cakala ya bar shi, tun su liti suna lallaɓa shi ya ci abinci, har sun haƙura sun ƙyale shi, sun zuba masa ido. "Master, ciwonka ya gama warkewa, Alhamdilillah Allah ya ƙara tsarewa, ka daina zuwa in da za a cutar mana da kai dan Allah" Yayi mata shiru, yana cigaba da cin abinci. "Ko in ƙara gudun AC naga kana gumi" ya girgiza mata kai alamar a'a. Tana tayi masa hira, har ya cinye abincin tas. Ta ce "Alhamdilillah" ta miƙa masa tissue ya goge hannu. "Wai dan Allah meyasa kake ta kallona ne? Ko wani abun nayi?" Nan ma ya girgiza mata kai. "Kamar bacci ka ke ji fa, ko an sha ne?" "Me fa?" Yayi maganar yana kallon ta. Ta ce "Bakomai" "Aiki na zo yi" ya faɗa a taƙaice. Ta ce "Aikin me?" "Computer zaki bani" Ta ce "Ok, desktop ta aiki ce, bari na baka laptop ɗina" ta ɗaukki laptop ɗin ta ta bashi, ya buɗe ya fara dannawa. Ta zauna a kusa da shi, tana kallon mai zai yi, sai dai ta kasa gane me yake yi ɗin, wasu irin lambobi da alphabets kawai take gani a screen ɗin system ɗin. Sunan Yaya Nasir ne ya fito a kan wayarta, ta ɗaga ta kai kunnneta, tayi shiru. "Arfa" "Na'am" "Waye mutumin da ya zo office ɗin ki?" Ta kalli Viper sannan ta ce "Baƙona ne" "Wane irin baƙo?" Nabila ta ce "Client ɗina ne, ya zo muyi magana ne a kan wata shari'a meyafaru?" Nasir ya ce "Gaba ɗaya ban yadda da shi ba" "Daga fara ganin mutum yau ka ce baka yadda da shi ba yaya? Ka san shi ne?". "A'a kawai jikina ya bani wani abu ne, amma akan case ɗin menene?" "Is confidential, and against my professional ethics, ba zai yiwu na gaya maka ba, idan na dawo mayi magana" ta katse wayar. "Meyasa ki ke tsoron gaya masa ne? Shi ne DSP Nasir ɗin? Shi a yadda yaken nan matsoraci yake son kama ni, ai karo da karo sai rago, na raina jarumtarsa" Ta tsuke fuska ta ce "Ya haka? Yayana ne fa, banda cin fuska" Ya ɗaga kai ya kalleta ya ce "Da lokacin da nake mai zamanina ne, aka bashi aikin kama ni, sai na yi masa karayar da zai shafe shekara yana zaune yana jinya. A yanzun nan da muka haɗu, ba zamu rabu lafiya ba. Tarbiyyar Jauhar ce da girma ya sanya wasu abubuwan nake kawar musu da kai". Ta ce "A hakan? Yanzun ma fa kana zuwa ka sari mutane, ka yi faɗa da neman magana" Ya matso da fuskarsa saitin ta ta, ta ja da baya. "Lokacin da nake mai zamanina, bana bin ƙofa komai girmanta, sai dai na kama katanga kamar ɓarawo, bana biyo hanya ayi gaba da gaba da ni. Bana tsoron kowane irin nau'i na fitina ko tashin hankali, idan aka kwana biyu ban ji ni cikin rigima ba, sai na ji ni kamar mara lafiya. Aiki tuƙuru da jajircewa tayi a kaina, ba dan ƙaddara ta rusa tanadi da burikan rayuwata ba, ta ci kaso mafi yawa na tarbiyantar da rayuwata a kan tafarki madaidaici. Ki daina haɗa kanki da ita" Ta lumshe idonta ta buɗe ta ce "Shiyasa na ce tun da ita 'yar madara ce, ni kuma sai na zama 'yar suganka, amma ka ƙarasa mini labarin ta dan Allah" ya zauna sosai ya cigaba da danna system sannan ya ce "Idan na ƙarasa miki labarin ta, hakan na nufin we sealed a deal, da babu gudu babu ja da baya kenan, komai rintsi komai wahalarsa?" Ta jinjina masa kai alamar eh. "A'a ki sake tunani, mussman ranar da zata fasu kina ɓoye shahararren ɗan ta'adda kamata" "Kai ba ɗan ta'adda bane ba, ta'addancin da aka yi wa rayuwarka, shari'a ta kasa tsaya maka ya sanya ka zama haka. A labarinka da oga walid ya bani, da tun a lokacin da aka kashe yayanka, hukuma tayi abun da ta dace, da duk ba a zo wannan gaɓar ba. Muna iya jure rashin makusantanmu ne, saboda ƙarfin imani, da tuna wanda ya bamu ne ya karɓi abunsa, amma idan wani ya zama sila, na rasa mutane masu muhimmanci a rayuwarmu, wannan imani na yarda da ƙaddara ya kan yi rawa a zukatanmu, mu kasa yadda da wanda ya bamu ne ya karɓa. Kai ba ɗan ta'adda bane ba mai babban suna, cin hanci a  doka da shari'a su ne suka mayar da kai duk abun da ka zama a yau. Ba kowace zuciya ce zata jure tana kallon wanda ya cutar da ita yana rayuwa cikin kwanciyar hankali, alhalin ita an bar mata tabo mara warkewa ta jure ba. Ban ce zan kai 'yar madara ba, amma na fuskanci giɓin da ka rasa nima akwai makamancin sa a rayuwata, da yake ci mini tuwo a ƙwarya yake damuna, ina ɓuya in yi kuka wasu lokutan na ji na tsani komai, kamar na kashe kaina na huta. Jin labarinka ya sanya, na fuskanci me ka ke ji a zuciyarka. Har abada duk tsanani ba zan sake kuskuren kallonka a matsayin ɗan ta'adda ba, kuma zan tabattar wa da duniya haka, da izinin Allah. Sai an gyara fannin shari'a an murƙushe rashawa da bambancin hukunci tsakanin ɗan talaka da mai kuɗi, mai ƙarami da babban uban gida, idan ana son rage yawan 'yan ta'adda" tun da ta fara magana, yake kallonta, duk da tana yi tana zubar da hawaye, hakan ya tabattar masa da akwai wani pain a zuciyarta ita ma. Ya juya ya cigaba da danna computer, ta kifa kanta tana goge hawaye. Ta kwantar da kanta a kan teburin, tana danna wayarta. Ta ɗaga idonta ta kalli, yadda yake ta sarrafa computer, bata san me yake yi ba. Yanzun ma hotonsa take ɗauka tana murmushi, kamar ba yanzu ta gama kuka ba. "Master" yayi mata shiru. Ta sake cewa "Maciji" tai maganar tana dariya. "Viper, maciji mai hatsarin gaske, yau ka fito daga raminka, ka zo wurina, sarana ka zo yi ne?" Still bai kulata ba. Ta tashi sosai ta ce "Da ni 'yar sugar da yar madara, wacce ta fi kyau ne? Kodayake na san ma ita zaka zaɓa, kafi sonta, amma dai kyakykyawa ce? Sannan fara ce ko baƙa? Doguwa ce ko gajeriya, ina son in ganta ka nuna mini hotonta, ko ba zaka bani haɗa ni da ita ba?". Sai da ya dafe goshinsa, Nabila bata gajiya da surutu, Jauhar akwai lokutan da ba ta kula shi da hira, idan ba ya cikin mood, shi wannan surutun nata ba zai bari su daidaita ba. Ya fizge wayar hannunta, yana dubawa yana danna computer. "Wai hacking ɗin wani zaka yi ne? Ni baka yi mini bayanin me ka ke yi ba, sonake ma mu yi magana, amma ka ƙi kulani, sai aiki kake yi kai kaɗai". Ya tashi tsaye ya ce "Zan yi salla" Ta nuna masa toilet, ya shiga yayi alwala, ya fito yayi sallar azahar, sanann ya kalleta ya ce "Tashi mu tafi" Ta tashi tsaye ta ce "Ina?" "In ƙarasa miki labarina, amma bisa sharaɗin da na gindaya miki da farko, babu gudu babu ja da baya, duk tsanani da wahala" ta jinjina masa kai. Ya ɗauki facemask ɗin sa ya saka, ya sanya baƙin glass ɗin sa ya yi gaba. Dama yau hijjabi mai niƙab ta sako, dan haka ta saka niƙabin, ta bishi. Cikin ikon Allah, chamber babu kowa, duk lawyoyin sun tafi kotuna, sai massenger da mai gadi. Suka fito, ta ce "To ina zamu je? Ba zai yiwu ka ƙarasa mini a nan ba?" "I have to test you more, before i completely trust you" daga haka ya tarar musu napep, ya gaya masa in da za su je. Suna tafe tana ta addu'a, Ubangiji Allah ya kare su, ya tsare duk in da za su je, Allah kar ya sanya ya cutar da ita, ko wani ya kama su. Kasancewar rana ce sosai, layin shiru babu kowa, suka tsaya a ƙofar wani gate, ya ciro mukulli a aljihunsa ya saka ya buɗe, ya ce ta shiga. Ta shiga sannan shi ma ya shiga ya rufe ƙofa. Ta tsaya tana kallon gidan, ya jingina da gate ɗin ya tafi tunani. "Waye yake mini kokowa da ƙofa zai karya mini gate?" "Ɓarawo ne ya zo sace matar gidan" tayi dariya ta ce "Da alama ɓarawon nan, bai san gidan wa ya zo ba ko? Ka bari mijina ya zo ya same ka" tayi maganar tana fitowa daga falon, fuskarta ɗauke da murmushi da tsohon cikinta. "Wai da ke muka haɗa kuɗi muka sai rigar nan ne? Ki din ga ɗaukar mini kaya kina sawa" Ta tura baki ta ce "Kai da kaya mallakar wuya ne, da kayan da mai kayan duk mallakin 'yar madara ne" tai maganar tana sakar masa murmushi. Nabila ta ce "Ya naga ka tsaya, ina ne nan?". Yayi firgita ya dawo daga tunanin da ya tafi. Ya tunkari ƙofar falon, zuciyarsa na bugawa da sauri da sauri, ya saka mukulli ya buɗe. Falo ne sosai, komai neat sai dai yayi ƙura sosai. Ta tsaya tana ƙarewa falon kallo, taji wani abu ya kama zuciyarta. "Viper, nan ne gidanka da 'yar madara tana ina? Kuma baka tsoron azo a kama mu?" Bai ce mata komai ba yama wuce ya shiga bedroom ɗin, ya tsaya yana ƙarewa ɗakin kallo, komai ya din ga dawo masa, tamkar mai mafarki. Tana tsaye, ya fito da wani riyo a hannunsa ya zo gabanta ya ajiye, yayi kneel down a gaban riyon, ya buɗe ya shiga fesawa kayan turaren florie. Ya din ga ɗago kayan, na jarirai ne, komai na haihuwa yana ciki intact, hatta zannuwa zamzam, bagaruwa, pad pampers komai akwai a ciki. Duk wanda ya ɗago sai ya fesa masa turaren ya ajiye, muryarsa na rawa ya ce "Ɗaya daga cikin ƙamshi mafi soyuwa a wurin jauhar kenan". Gaba ɗaya zuciyar Nabila ta tsinke, gabanta ya tsananta faɗuwa, ta ɗauki kayan, ita ma ta kai hancinta. "Yanzu tana ina? Ina kuma jaririn naga kayansa na jariranta haryanzu?" Ya ɗaga kai, yana kallon in da Nabila take zaune, ya ga jauhar kwance a wurin, cikin jini, tana ɗago masa hannun tana la'ila ha illa la, ya Allah. Daga nan bai sake sanin in da kansa yake ba, sai ji yayi an watsa masa ruwa mai tsananin zafi, da ratsa fata a jikinsa. Ya yinƙura zai tashi a gigice, amma yaji shi a ɗaɗɗaure, tamkar huhun goro. Ya buɗe idanunsa da ƙyar cikin matsananciyar galabaita, amma ya kasa magana, haka zalika wuyansa ya kasa tsayawa. "Idan ya watstsake, ku cigaba da tuhumarsa, har sai ya amsa laifin da bakinsa" "Ok sir" Suka cigaba da kwara masa ruwa mai zafi, amma sai dai ya zabura ya ƙanƙame jikinsa, amma babu baki. Suka kwance shi daga mugun ɗaurin da suka yi masa, sai dai ana gama kwance shi, ya faɗo ƙasa jikinsa a sake. Ɗaya daga cikin su ya ce "Haryanzu bai gama dawowa hayyacinsa ba, ku ƙyale shi tukuna" Indabo sai kaiwa yake yi, yana komowa a falonsa,ya rasa me ma yakamata yayi, gefensa ga P.A ga kuma madaki a zaune. "Wallahi kayi mini hauka madaki, ni ban san zaka yi mini sakarcin ba. Bambancinka da Aminu kenan, abun da aka saka shi yake yi, idan ka ga ya canza, to ya hango abun da ya fi naka ne, yanzu idan ya farka ya tona mana asiri ya kenan?" P.A ya ce "Honorable, ka kwantar da hankalinka C.P yana hanyar zuwa nan, zamu ji mai zai ce mana" Madaki ya ce "Honorable, da ka san hatsarin da yake tattare da yaron nan, da baka ce haka ba, mugun shu'umi ne. Hodar nan da guba na haɗata, kisa take yi har lahira, nayi mamaki da aka ce bai mutu ba, ba laifina bane ba, nayi iya ƙoƙarina". CP ne yayi sallama, ya shigo falon, suka amsa tare da mayar da hankalinsu kansa, ya miƙa wa Indabo hannu suka gaisa. Cikin zaƙuwa indabo ya ce "Yaya ake ciki C.P?" "Eh to, maganar gaskiya fa ya farfaɗo, kuma yana daf da watstsakewa a ko wane lokaci. Abun da muka yi guda ɗaya ne, a report ɗinmu, mun shigar da cewa ya sha kayan maye ne, ya bugu ya halakka matarsa". Indabo yayi shiru sannan ya ce "Kai naji daɗi, amma kamar hanyar ba tayi ba sosai, idan ya buɗe bakinsa, zai iya faɗar gaskiya fa" C.P ya ce ba zamu bari haka ta faru ba, lokacin da muka je gidan, mun goge duk wani abu da zai nuna hujjar wani ne ya shiga ya aikata laifin ba shi ba. Sannan mun ajiye miyagun ƙwayoyi har da hodar iblis, da sunan mun kama su a gidan. Idan za a fara sharia dole a samo ƙwararrun lauyoyi, kuma a yi wa alƙalin kyakykyawan gani, ni dai daga ɓangarena komai zai tafi dai-dai da yardar Allah. Tun da dama ya riga ya shahara kowa ya san ɗan daba ne" Indabo ya yi ajiyar zuciya ya ce "Haka ne, na gode sosai da sosai C.P, zaka ga saƙo da yardar Allah, kuma zan cika alkawarin da nayi, muddin komai ya tafi cikin nasara, amma C.P ba zai yiwu ku yi masa wani abu, ku kashe shi ba kawai?" Ya ce "No, muddin wani abu ya same shi, mu kuma zamu zama abun arziki, saboda sanarwar da kakinmu ya fitar mun tabattar da yana hannunmu cikin ƙoshin lafiya" "Shikenan babu laifi, na gode sosai da sosai" ya sallami C.P ya tafi, ya ce "Aikin Naja'atu ya zo, P.A kira wo mini ita". *** "Ka yi magana ka amsa laifinka, ka sauƙaƙa mana kai ma ka sauƙaƙawa kanka, idan ba haka ba mu zamu bi hanyoyin da zasu sama mana sauƙi" Al'amin ya ɗago da kyar, saboda a cikin mayen da yake, suka yi dukan tsiya, tamkar sun samu jaki, jikinsa ya ƙara mutuwa, kowace gaɓa ta jikinsa ban da ciwo, babu abun da take yi. "Ka amsa, ka ce ka sha kayan maye ka kashe matarka" Gefen bakinsa duk jini, sun tuɓe shi, daga shi sai vest da gajeren wando, ya sake ɗaga idonsa, karo na farko yayi magana ya ce "Ina jauhar?" "Ban sani ba, ni kake tambaya ina juahar? Bayan ka kasheta?" Tsaki yayi, ya taƙarƙare ya yinƙura ya tashi tsaye, suka saka kokara suka daki ƙafafuwansa, ya hantsila ya faɗi a wurin. Duk abun nan da ake yi, da jibgar da yake ci, shi kawai mafarki yake yi, jira yake yi ya farka, dan ba ya son baccinsa ya cigaba da nisa, zai kai Jauhar asibiti da wuri. A haka aka shafe kwanaki bakwai, amma Al'amin, yaƙi sakawa ransa cewa gaske ne ba mafarki ba. Kwanaki bakwan nan, babu wanda ya zo in da yake, ba wai dan ba a samu masu zuwan ba, an hana kowa ganinsa. Liti da walid, da sauran jama'arsa babu irin sintirin da ba su yi ba, amma aka hana su ganin sa. Mutuwar jauhar, ta karaɗe kowane gidan jarida, unguwanni zuwa gidaje. Abbu yayi kuka tamkar zai yi hauka, yayi dana sanin kasancewar sa mahaifin Al'amin. Gidansu jauhar kuwa, ba su san sun yi rashi ba, sai da aka tabbatar da mutuwar jauhar, kowa kuka da zubar da hawaye. Abbu yana kuka, ya sanya gwiwoyinsa a ƙasa, yana roƙon Baba ya yafe masa, da ya san Al'amin zai kashe masa 'ya, ba zai yarda a aura masa ita ba. Baba ya girgiza kai ya ce "Alhaji Ibrahim, ni wallahi haryanzu ban ji na yadda Al'amin zai kashe mini 'ya. Akwai abun da ya faru ni ban yadda shi ya kashe mini jauhar ba" Abbu ya ce "Wace hujja kake nema ko shaida bayan wannan? Ni na haifi Al'amin, kuma kowa ya san yana ta'amalli da miyagun ƙwayoyi" Cikin kuka mama ta ce "Yaron nan ya cuce mu, bai yi mana adalci ba, haihuwar ɗa irin jauhar a gidan nan, daga kanta an gama, ba ayi ba, kuma ba za ayi ba" Hafsa ta girgiza kai ta ce "Baba nima ina bayan maganarka, ƴan kwanakin nan, ina zuwa gidanta sosai da sosai, ina haɗuwa da shi, ita take bani labarin galabar da ta ci a kansa, da bani misalai daban-daban da aurenta. Son da yake nuna mata a gabana ba ya jin kunyata ko nauyina, suna matuƙar ƙaunar junansu. Har take gaya mini na tayata da addu'a, yanzu sigari ce kawai damuwarta da shi, har sai da na ji raina ya biya, da irin kalar soyayyar da suke yi wa junansu, dan haka gaskiya ban yadda mai zamani zai kashe jauhar ba, mutumin da idan zata fita baya nan, yake sawa ana bibiyarta dan kar wani ya kawo mata farmaki, mugwayen karnuka ya ajiye a layinsu, suna gadinta lokacin da yayi tafiya, duk dan kar a taɓa ta, gaskiya ban yadda ba". Anty ma tana kuka ta ce "Babu abun da mai shaye-shaye ba zai iya aikatawa ba, dan haka ba abun mamaki bane dan an ce ya kasheta, Allah sarki jauhar wannan wane irin mummunan ƙarshe ki ka yi?" A fusace Saifu yana kuka ya ce "Kar ki sake aibata mana gawar jauhar, wallahi ba ta yi mummunan ƙarshe ba, ta bi Allah, ta yi wa iyaye biyayya, ta yi biyayyar aure, idan ana nuna ɗan aljanna a duniya to jauhar ce, koma wane irin mutum ne shi, ai ku kuka yi bita da ƙullin da ta aure shi, kuma wallahi Allah ba zai bar kowane azzalumi ba, ita ta mutu ta huta". Haka aka din ga musayar yawu, har sai da Baba ya tsawatar tukuna. Da taimakon Naja'atu Bunkure, suka haɗa kai da lawyoyin gwamnati, Indabo ya cika su da kuɗi, har da alƙalin kansa. Domin tsayawa tsayin daka wurin tattara shaidu da hujjoji. Haka zalika ta fito ta bayyanawa duniya cewa, zata tsaya tsayin daka, har sai ta ga abun da ya ture wa buzu naɗi, sai an bi wa jauhar hakkinta, na kisan gilla da viper ya yi wa jauhar, mussaman dama ya riga yayi suna a harkar sha da fataucin miyagun ƙwayoyi da kuma harkar daba. Ranar fara shari'a, haka aka zo da mai zamani a cikin sarƙa, yana ɗingisa ƙafa, saboda azabar da ya sha a hannun 'yan sanda, a kan ya amsa cewa shi ya kashe jauhar. Aka fara gabatar da shari'a, wani lawyer ya gabatar da kansa a matsayin wanda zai kare Al'amin, bai taɓa ganinsa ba, sai ranar a cikin kotun. Aka gabatar da charges ɗin da ake yi wa Al'amin. Ɓangaren tawagar lauyoyin gwamanti, da su Naja bunkure, suka din ga gabatar da shaidun bogi, suka kawo ƙwayoyin da suka samu a gidan Al'amin, tare da kawo bayanan likita, na cewa dukanta aka yi har ta kai ga rasa ranta, da abun da yake cikinta. Abun bai tsaya a nan ba, sai da aka kawo malam lawan, bayan shaƙa masa wasu muhimman kuɗaɗe, ya zo ya bayar da shaidar Al'amin ya saba dukan jauhar, idan ya je ya sha ya bugu, haka za su yi ta jiyo ihunta yana dukanta, a ranar ma sun ji kukanta, sai dai ba su yi zaton zai kasheta ba. Muryar Liti ce ta dawo da Al'amin hayyacinsa, dan duk surutan da ake yi, bai san me ake cewa ba. "Ƙarya kake yi dan ubanka, Viper ba ya dukan yar madara, ba ita ba kowace mace ma baya duka, a matsayin ku na maƙota idan yana dukanta, meyasa baku kai wa yan sanda ba, ƙarya kake maƙiyin Allah la'ananne, Viper ba zai taɓa cutar da matarsa ba, ba shi ya kasheta ba" jami'an tsaro suka yi waje da liti. Sai dai

Chapter 60 of 121