ja, a gaban Alƙali zai ƙalubalance ni, ba wai a din ga yi mini barazana ba* tayi posting ɗin tana murmushi, ta ce "Sumy na zama celeb fa"
"Zaki ci ƙaniyarki ke da celeb ɗin, kina kan sirɗin duniya kina rashin mutunci, akwai buƙatar mu nutsa sosai, mu cigaba da samo hujjoji, dan mutane su yadda da abubuwan da ki ke tonawa, dan na san haryanzu akwai masu tantama a kai"
"Haka ne, wannan kuma sai idan muka sake tsayawa a gaban kotu a kan case ɗin ramma"
"Allah ya ƙarfafeki, ya baki sa'a"
"Amin godiya nake masoyiyya"
Sumayya ta ce "Amma Nabila ya za ayi da Indabo ne? Ina tsoron mutumin nan, kin ga kuma shi babba ne, tun a lokacin na so na kai report, amma yayi mini kashedi a kan haka, babu ma wanda zai yadda da ni, saboda muƙaminsa"
Nabila ta ce "Rabani da zancen wannan mutumin, ni yanzu wannan matar ce a gabana, shi kuma akwai dai-dai shi"
"Wa kenan?"
Nabila ta basar da zancen ta shiga wani.
***
"Indabo ka yi wani abu a kan lamarin nan, lallai a kama yarinyar nan a koya mata hankali, ban san da me take taƙama ba, ba a taɓa samun tsageran da yayi mini abun da take yi mini ba, idan fa asirina ya tonu, kuma naku ya tonu wallahi"
"Kar ki damu, muke da ƙasar fa, babu abun da ta isa tayi, na riga na bayar da order da ta kamata"
Ta kashe wayar, cikin fushi, tana mamakin ƙarfin halin Nabila, manyanta ma sun gaji sun ƙyaleta, ba a iya ja da ita, amma yanzu yar ƙaramar alhaki ta sakota a gaba.
Indabo ya daddana wayarsa, ya saka a kunnensa, "Barka da wannan lokaci distinguish senator"
"Barka dai, ya ake ciki ne maganar yarinyar? Na ji kun ce Dss su kamata ya ake ciki, dole fa a toshe duk wata hanya da za a tonawa bunkure asiri dole a tosheta".
"Sir yarinyar nan fa tana da wayo, kuma tana da wanda suka tsaya mata, ta tafi kotu, ta ce lallai a hana kamata kuma ba wanda ta ɓatawa suna, sai dai bunkure ta ƙalubalanceta a gaban shari'a"
Ya numfasa ya ce "Haka ta ce? Wane alƙalin ne? Wace kotun ce zan bayar da umarni a bi umarninta a ƙi bin nawa"
"Honorable ka gane wani abu, abun nan fa ya haɗa da social media, ba zai yiwu mu yi abu gabagaɗi ba, su kansu ƙungiyar lawyoyin ba zasu bari ba, kuma madam tana da magauta a cikin su kansu lawyoyin, za su iya taimaka mata, idan aka yi over reacting, to asirin da ake gudun tonuwarsa zai tonu"
Indabo ya ce "Shikenan, na fahimta".
***
Madaki ya kalli ƙafarsa, ya kurma wani irin uban ihu, tamkar mahaukaciya, Lakwari ya ce "Dan Allah ka yi haƙuri ka daina wannan ihun, hakan ba mafita bane ba".
"Ka rabu da ni nayi ihun nan, sai na kashe yaron nan, abun kunya ne ace kamar ni, ƙasƙantaccen maƙiyina, ya ga bayana ya sabauta rayuwata, sai na kashe mai zamani na ƙarar da zuriyar su*.
Lakwari ya kalli ƙafar madaki, ta kumbura kamar mai dundumi, sai wani irin koren ruwa ne yake fita daga cikin ciwon ga wari da yake yi, ga maganin da aka bashi, aka ce ya din ga sakawa, ya sanya raunin ƙara jagwalgwalewa, ko iya taka ƙafar baya yi.
"Madaki, ka yi haƙuri mu je asibiti a duba ƙafar nan, ni fa ban ga alamar ciwon nan yana warkewa ko zai warke da haka ba, ƙara jagwalewa yake yi".
"Idan na je asibiti asirina tonuwa zai yi, idan lakwayen nan suka san alkadarina ya karye na shiga uku, kai ka san ta'adin da na yi ai"
"Haka ne, amma duk da haka yakamata muje asibiti a duba ƙafar nan, tun da babu sauƙi a ciki" ya din ga lallaɓa madaki har ya samu ya amince.
Viper yana tsaye tare da su liti, ɗan mama ya shigo, Viper ya ce masa ya ake ciki?
"Komai normal, saƙonka ya isa cikin aminci da kwanciyar hankali. Na shiga area na yi bincike sosai, babu wanda ya san in da madaki yake, amma an tabbatar mini da yana jinya, kuma lakwari ne a tare da shi, sai dai ba a san in da yake ba"
Viper ya zaro russia, ya jujjuyata a hannunsa, ya kalli ɗan mama ya ce "Ka nemo duk in da suke, ina son ka samo target mai kyau, in da zan ritsa lakwari, na san ƙafarsa ɗaya ta mutu zuwa yanzu, zan hari wani wurin na daban kuma"
"Sai da kai ubangidana, abun da ka ce shi za ayi"
"Bari mu ga respond ɗin da Indabo zai yi, idan ya ga saƙona"
***
"Hello, barka da wannan lokaci"
"Yauwwa barka sir"
"Ina magana da justice maijidda ɗan rimi ne"
"Eh nice"
"Good, ina fatan kin gane mai magana?"
Tayi murmushi ta ce "Ya za ayi na ce ban gane ba sir, na gane"
"Masha Allah, akwai ƙara da wata yarinya da sauran lawyoyi suka shigar gabanki, barrister Nabila Yusuf maitama, a kan ki hana Dss kamata, da kuma hana yi mata barazana, ki bi tsarin doka ki yi abun da ya dace, na san dole za a nemi ki yi wani abu ba dai-dai ba, idan ki ka yi akasin abun da doka ta tanada, zai iya janyo wa ayi seizing license ɗinki, nima umarni aka bani daga sama"
"In sha Allah sir, zan yi abun da ya dace ba tare da son rai ba, na gode sosai da sosai"
Ya ce "Yauwwa"
A media kuwa aka cigaba da samun musayar ra'ayi, kowa da abun da yake faɗa, waɗanda bunkure foundation ta cutar, suma suka samu damar bayyana ra'ayoyin su, duk da mutanen da suke ganin hassada ta sanya ake yi wa bunkure hakan sun fi yawa.
Bayan Bunkure ta gama sakankancewa, ta gama da babin Nabila, sanarwa ta fita, kotu ta haramtawa Dss kama Nabila, ko yi mata barazana a kan abun da take aikatawa, a matsayin ta na ƴar ƙasa, tana da ƴancin faɗar albarkacin bakinta.
Indabo kuwa yana cikin majalisa, ya zauna, ya fara ƙoƙarin buɗe envelope ɗin da aka bashi, aka ce an aiko masa da ita.
Ya buɗe ta ya ƙara ciro wata ƙarama a ciki.
Hoton ciki ya kalla, Simon ne tare da Viper a cikin hoton. Simon yana daga cikin yaran da Indabo ya lalatawa rayuwa, kuma ya zama ɗaya daga cikin masu yi masa hidima, a wannan gidan da suke sheƙe aya da shi da ire-iren sa, da suka sanya neman duniya a gaba.
Wanda shi ne ya kuɓutar da Nura guduma daga gidan, ya saka shi a mota, ya haɗa shi da wani ya kai shi kano. Shi kuma ya gudu daga gidan, indabo ya bayar da cigiyar a nemo simon, ya bayar da kwangilar a kashe shi, aka tabattar masa da an kashe shi, amma hoton ya nuna masa kwanan nan aka ɗauka.
Cikin tashin hankali yake sake kallon hoton, tabbas na kwanan ne hoton, saboda Viper ya ƙara girma, fuskar nan babu annuri a tattare da ita ko kaɗan.
"Simon yana raye kenan?" Ya tambayi kansa, ya juya bayan hoton ya ga an rubuta Viper da jan abu.
Bai san ya tashi tsaye ba, sai da na kusa da shi ya ce "Honorable, ya aka yi ne? Me kake gani?"
"A'a ba komai, ulcer ta ce ta tashi" ko izini bai nema ba, yayi waje daga cikin majalisar kamar babbar rigarsa zata harɗe shi ya faɗi.
***
"Assalamu alaikum, Assalamu alaikum ba kowa a gidan ne?"
Walid ya ce "Wa'alaikum Salam, barrister yau ke ce?"
"Ina wuni Yaya walid"
Yayi murmushi ya ce "Lafiya ƙalau, yau kin tuna mini da ƙanwata jauhar"
Ta ce "Allah sarki, Allah ya sa tana aljanna"
Ya amsa da "Amin"
"Ina ogan yake?"
"Ya tafi caji"
Ta ɗan yi turus ta ce "Caji kuma, kamar wani power bank?"
Yayi dariya ya ce "Ya ce, ya fita shan iska yana wurin wancan dutsen"
Ta ce "Ok, bari na je"
"To Allah ya sa yana ƙasa, ba saman ya hau ba"
Nabila ta ce "Idan ma saman ya hau, zan bi shi"
Da tazara daga gidan zuwa dutsen, duk da daga gidan sai ka zata taku kaɗan zaka yi ka ƙarasa.
Daga nesa ta hango shi, a zaune a ƙasa-ƙasa, ta hango tashin hayaƙi a wurin.
Ta ƙarasa da ƙyar, dan duk ta gaji, kwali guda ne a gabansa, ta ƙarasa ta kai hannu ta ɗauke, caraf ya riƙe hannunta. Tsorata tayi, dan cikin sanɗa ta ƙarasa wurin, amma har ya ankare da ita ya hanata ɗauka.
Ta haɗe rai ta ce "Sakar mini hannu, nan ka gama cewa zan saka a lungu, shi ne zaka wani riƙe mini hannu?"
"Ni na kawo ki? Ban ce ki daina zuwa ba ma?"
"To ko kirana ba ka sake yi a waya ba, idan ma an kama ni, ko ma menene ya same ni, ba ruwanka ko?" Tari ta fara yi, saboda hayaƙi, sakar mata hannu ya yi, tayi sauri ta ɗauke kwalin sigarin da ashanar, ta tura a jakarta.
Satchet ɗin maganin da ya leƙo a gefen aljihunsa, shi ma ta ɗauke, tana mita "Wallahi Allah ya hore maka taurin kai, wannan shaye-shayen ne ba zaka daina ba ko?" Ya ƙura mata ido, saboda jin tana ƙamshin turaren florie irin na 'yar madara.
"Ina magana kana kallona, baka tausayin lafiyarka, yanzu duk ƙoƙarin jauhar a kanka ya tashi a banza, yawaita yi mata addu'a, istigfari da mayar da hankali a kan addu'a, shi zai rage maka damuwa, amma baka ji, kullum cikin hayaƙi, da shan miyagun ƙwayoyi"
"Faɗa fa ki ke yi mini"
"Au kar na yi maka? Ka daina mana da na yi maka mana, wannan abubuwan da kake yi ba shi yake nuna halaccinka a gareta ba, ka daina abun da ka ke yi, ka zama mutumin kirki, shi ne cikar halaccinka a gareta"
Kawar da kansa gefe yayi a hankali ya ce "Angry bird"
"Ni ce bird ɗin? Wallahi ni ba tsuntsuwa ba ce ba, da ba ka neme ni ba, ni gani ai na zo, ba a kama ni ba fa"
"Dama na san ba za a kama kin ba ai"
"Haba ya aka yi ka sani?"
"Bani wayarki" ta ciro wayarta ta miƙa masa.
Ya ciro tasa ya danna, sannan ya saka a kunnensa.
Muryar P.A ta fito rangaɗau a waya ya ce "Hello"
Viper ya yi shiru, bai ce komai ba.
Ya sake cewa "Hello", still bai yi magana ba.
"Waye ne ya ɓoye lamba yake kirana, idan ba za ayi magana ba, zan kashe, waye?"
"Mai zamani ne" waro ido P.A yayi ya ce "Wane mai zamanin?"
"Zuwa yanzu, na san saƙona ya iske shi, ya shirya, zan bayyana a lokacin da bai yi tsammanina ba, kuma ya daina wahalar da kansa a kan lallai sai an kamani, ko da an kama ni, nafi ƙarfinsa, ya kuma jirani aikena na biyu" ya katse wayar yana ajiyar zuciya.
"Kai, Oga kana burgeni, ka din ga acting kamar a film ɗin indiya hausa, wai dan Allah, a ina ka ko yi wannan halin naka?"
Ya jefa mata wayarta jikinta.
"Amma wait, wai ne ka ke yi a wayata ne baka gaya mini?"
"Yaushe zaki fara shari'ata?"
Nabila ta ce "Shari'arka akwai sarƙaƙiya boss, sonake na gama da ta ramma gobe in Allah ya kaimu zamu koma kotu." Ya jinjina mata kai.
"To zaka fara bani kuɗin aiki ai, ka ɗan ragen wani abu, na din ga zuba mai, tun da na je fa aka nuna mini file ɗin ka, nake ta up and down, ina tattara abun da zan tattara. In sha Allah zan zama sanadin daina zubar hawayenka"
"Dama kuka nake?"
"A'a murna ka ke yi"
Ya girgiza kai ya ce "Ko matata da muna tare, ta daɗe kafin ta iya kallona ta yi mini magana, balle ta yi mini baƙar magana, amma ke kin mayar da ni kamar wani sa'anki, har hantarata ki ke yi"
"Ni ɗin ce na rainaka? Ni na isa wacece ni? Amma dan Allah sweetheart meyasa ka kusa kashe ni ranar farko da na zo wurinka?"
Ya ɗago ya kalleta ya yi shiru.
"Ka amsa mini dan Allah"
"A lokacin ai kamar mahaukaci nake shiyasa"
Ta girgiza kai ta ce "A'a, wani abu na din ga gani a idonka, da na rasa menene? Dan Allah meyasa?"
"Ke ban sani ba, tashi ki bar wurin nan"
Ta noƙe masa kafaɗa tana kallon idonsa, abun da ya tsana. Yayi tsaki ya kawar da kansa gefe.
Turare ta ɗaukko a jakarta, ta toshe hancinta, ta fesa a wurin. Ba shiri ya waiwayo yana kallon hannunta.
"Gashi yanzu na saka ka waiwayo ai, gashi saya maka na yi" ya karɓi turaren, ya din ga juya shi a hannunsa yana kallo.
Ta na ƙoƙarin ɗaga wayar da ake yi mata, ta ga hawaye na ɗiga a hannunsa.
Sai jikinta yayi sanyi gaba ɗaya. "Haba mai babban suna, a yanzu fa kuka ba naka bane ba, wanda ka yi ya isa, mu cigaba da addu'a da ƙoƙarin tattara shaidun da zamu shiga kotu da su, dan Allah ka daina bana jin daɗi.
"Da jauhar na raye, da yanzu na san ta kammala law school, maybe ta haifi yaronmu na biyu ko uku, ina da tarin burika a kanta, na kyautata rayuwar ta, ta ji daɗi ta huta, saboda wahalar da ta sha a rayuwarta, amma wauta ta da rashin hankali, ya sanya ta mutu ta bar ni a duniyar. Lokacin da duniya ta yi watsi da ni, ake yi mini kallon mara amfani, ta rungume ni, ta karɓi ƙaddararta, ta kula da ni, a lokacin da nake ƙoƙarin kyatata ratuwarta na fara bata kulawa, lokacin da na fara gano haske yana tunkaro rayuwarmu, ashe yayi daidai da lokacin da zan yi girbin ya mummunar hanyar da na zaɓawa rayuwata, na rasata" yayi maganar yana ƙoƙarin mayar da hawayen sa, amma suka cigaba da zuba, kamar an kunna famfo.
"Viper, ka yi haƙuri, Allah ya ambaci masu haƙuri a wurare daban-daban a alƙur'ani, tare da yi musu bushara. Viper Allah ya fi kowa so da kishin bawansa, wataƙila mutuwar jauhar a wannan lokacin shi ne mafi alkhairin ta, a duk buɗe ido muka yi muka ganmu a duniya, dan haka ba zamu tsarawa Allah yadda muke son kasancewa ba a duniya.
Ba kowa Allah ya tsarawa jin daɗi a duniyar nan ba, ai dama ita duniyar kurkukun mumini ce, aljannar kafiri. Wani ga jin daɗin yana cikinsa a zahiri, amma a baɗini rayuwar kawai suke yi mara ma'ana.
Yanzu tsohon ubangidanka ga duniyar ya samu, yana jin daɗin amma nauyin zunubin da yake aikatawa ba zai taɓa barinsa ya rayu cikin kwanciyar hankali ba. Ba sai mutum ya samu wadata dan ya sha wuyar rayuwa, shi ne tabbacin Allah yana son sa ba, duk tsananin rayuwa da ka ke ciki, idan har ya barka da imaninka, kuma ka yi kyakywan ƙarshe, wallahi ya fiye wa ɗan Adam duk wani abun more rayuwa.
In dai ana samun aljanna a biyayyar iyaye, da biyayyar aure in sha Allah Jauhar ta samu" ya jinjina kai yana cigaba da zubar da hawaye.
Ta bashi handkerchief ɗin ta, ta ce "Share hawayen haka, kaga ni ma ka saka ni kuka, bana iya jure in ga mutum a cikin damuwa ko yana kuka, alhalin ba zan iya yaye masa damuwar sa ba.
Yanzu ni kaina, duk abubuwan da nan da nake yi, ƙarfin hali nake yi, zuciyata akwai wani ciwo da yake addabata, ina kuka iya yi na wasu lokutan, sai dai babu yadda na iya, da abun da ƙaddara ta zana mini" tayi maganar ita ma tana kuka.
Ya ɗago ya kalleta, ya motsa baki, yana son ya faɗi wani abu.
Ayshercool
08081012143
63
Ta share hawayenta, ta ɗaga kanta ta ga ita yake kallo ta ce "Ka ce mini ka yi wa Indabo aike, me ka aika masa?"
"Hotona ne"
"Hotonka kuma?"
"Eh, hotona ne da ni da wani yaronsa da yake zaton ya saka an kashe masa shi"
Ta zaro ido ta ce "Wai shi mutane nawa ya kashe kenan a rayuwarsa?"
Ya rausayar da kai ya ce "Mutane sun ɗauki duniya fiye da yadda ki ke tunani. A baya bayan matsalar da nake fuskanta a gidanmu, fatan da nake yi kullum, Allah ya bani abun yi, ko iya abinci in din ga samu ina ci, sai da na haɗu da uban gidana dodo, ya haska mini duniya da in da mutane suka saka gaba. Da na so na yi kuɗi da yanzu ni hamshaƙin attajiri ne.
A lokacin da jauhar take ciyar da ni, da fari babu abun da yayi mini zafi, gani nake kawai auren dole aka yi mini, sam ba ta gabana, sai dai abun mamakina da ita, duk abun da zan yi mata bata jin haushi, naga yadda take sana'a tuƙuru iya yin ta, dan kar mu zauna da yunwa, daga baya nayi noticing idan abinci ba zai isa ba, sai ta bani ita tayi kame-kame ba ta ci ba, a lokacin ba wai dan tana so na bane take yi mini haka, ta rungumi ƙaddara ne, kuma tana tausayina.
Daga baya sai na fara jin kunyarta, lokacin da ta roƙi na sayo mata omo, naga responsibility ɗina, amma na zuba mata ido take yi, kuma bata taɓa nuna mini ta gaji ba. Sai dai a lokacin ba ni da wata sana'a sai sayar da wiwi da ƙwayoyi, yadda take yi mini addu'a Allah ya wadata ni da halal, ya nesanta ni da haram, ya sanya na ji ba zan iya ciyar da ita da kuɗin wiwi ba.
Sai a lokacin naga ashe, bayan mutuwar Sadik kukan daɗi nayi, da na ce na rasa sana'a, dan a lokacin na din ga faɗi tashi, saboda kar na ciyar da ita da kuɗin ƙwaya.
Da in ciyar da ita da wannan kuɗin, gara na dawo na maze na ce bani da kuɗi, na san ba ɗaga mini hankali za ta yi ba.
Gashi lokacin tana ta ƙoƙarin rabani da hulɗa da Indabo, wataran idan na ga wahalar tayi mata yawa, haka nan nake zuwa na tsitsiye Indabo ya bani kuɗi.
Zuciyata ta sha raya mini, na faɗa mummunar hanya, na samu kuɗi saboda jauhar ta huta, bana nuna mata hakan a zahiri, amma zuciyata kullum a takure babu daɗi. Duk da tsamin alaƙar da ke tsakanina da mahaifina, sai da na din ga jin tamkar na je na ce ya bani aron kuɗi nayi jari, amma na kasa, mussman tuna halin matarsa.
A lokacin da tausayinta ya fara zama tsananin so a cikin raina, da tana uzzura mini ko yi mini tashin hankali, da babu abun da zai hanani kauce hanya, dan yahoo zan fara, kuma kuɗi zan samu sosai da sosai, haka nan na san in da zan yi dillancin miyagun ƙwayoyi a tsakanin manyan mutane, har da ƙasashen ƙetare na samu kuɗi, amma ban taɓa burin tara kuɗi da mummunar hanya ba.
Ina ga lokacin da tayi ɓari ne, bani da wasu kuɗi sai na wiwi, shi ne aka yi mata magani da su, amma banda haka, ban taɓa ciyar da ita da kuɗin ƙwaya ba".
"Viper, labarinku abun tausayi, kuma gwanin daɗi, Allah ya bani ikon zama kamar jauhar, ina sonta sosai"
"Sai dai ki kamanta, ba zaki iya ba, ke mafaɗaciya ce, matata kuwa kan tayi faɗa sau ɗaya ana daɗewa, shiyasa nake kiyaye abun da zai ɓata mata rai ya sa tayi fushi, har ta yi faɗa. Na gode sosai da saka ni kuka da ki ka yi"
"Saka ka kuka kuma?"
"Eh, tun da na rasa jauhar, ban zubar da hawaye ba"
"Ai kai jarumi ne, bari na tashi na tafi gida, ka yi mini addu'a, gobe in Allah ya kaimu zamu zauna a kotu"
Ya jinjina kai ya ce "Allah ya bada sa'a, bani maganina"
"Dan Allah ka daina shan magungunan nan, lafiyarka fa"
Ya ce "Duba na na menene?"
Ta ciro maganin ta duba, cikin magungunan sa ne na Asibiti, ta ajiye masa ta ce "Allah ya baka lafiya mai amfani, ya bamu nasara a kotu, in sha Allah case ɗin ka ne next, ka yi mana addu'a" ya jinjina mata kai.
Ta tashi ta ɗauki jakarta tana ɗaga masa hannu.
***
Daren yau Nabila tayi ta addu'a, suka yi waya da Barrister Habib, ya ce su haɗu a kotu.
Ya ƙara mata ƙarfin gwiwa, kafin shiga shari'a, suna tsaye a harabar kotu, tana dudduba abun da zata tsaya a gaban shari'a da shi.
Nabila ta tsaya a gaban kotu, ta ce my lord, kamar yadda na gabatar da hujjojina a wancan zaman da aka yi, akwai voice na muryar mahaifiyar ramma tana kokawa akan a nema mata hakkin 'yar ta.
Haryanzu ina da ja, a kan zargin da ake yi wa wanda nake karewa, a hirar da aka yi da mahaifiyar ramma, a gidan rediyo, wanda suka yi iƙirarin ya yi wa ramma fyaɗe, ya sha banban da wanda aka gabatarwa kotu.
Haka zalika, voice message ɗin da yake yawo, na mahaifiyar ramma, ta koka a kan wanda ya yi wa ƴar ta fyaɗe, ya dawo ya ɗauketa ta ƙarfin tsiya daga gabanta.
Lauyan gwamanti yayi suka, ya nemi da a gabatar da mahaifiyar ramma, ba wai kame-kame da abun da babu wanda ya san tushen sa ba.
Nabila nan take ita ma ta buƙaci, a gabatar da ramma, tayi mata tambayoyi.
Lawyan gwamnati ya ce Ramma na ƙarƙashin kulawar, likitoci haryanzu, dan haka ba za a gabatar da ita a gaban kotu ba.
Nabila ta sake cewa Wane irin illa aka yi mata, da har zuwa wannan lokacin za ace ba ta warke ba, a shekarun baya shekara sha uku sha huɗu ake yi wa mata aure, ba a samun matsala, suna zaune lafiya, a report ɗin da aka bayar na case ɗin ramma, abun bai zama complicated da za ace tsawon wannan lokaci tana Asibiti ba.
Lauyan gwamanti ya soki maganar Nabila, tare da neman a bashi dama ya gabatar da shaidunsa na gaba.
Wata mata ce ta fito, aka tambayi baba mai gadi, ko ya santa? Ya ce Eh, ita ma mai aiki ce a gidan.
Aka tambayi me ta sani, a game da abun da ake tuhumar mai gadi da shi, babu kunya babu tsoron Allah, ta bayar da shaidar zir, tare da tabattar da mai gadi ne yayi laifin, sai bayan da yayi aika-aikar, ta dawo daga sayen kayan miya, ta tarar da ramma, kuma daga shi sai ramma ta bari a gidan.
Baba mai gadi ya sunkuyar da kai cikin matsanancin ɓacin rai da mamaki.
Nabila ta ce ya za ayi ace gida kamar wannan babu cctv camera, akwai buƙatar idan da cctv camera a duba abun da ya faru.
Daga nan Nabila ta nemi a bata damar ta gabatar da nata shaidar ma, aka bata dama, ta buƙaci wata mata ta fito.
Nabila ta buƙaci matar ta gabatar da kanta, ta gabatar da kanta a matsayin maƙwabciyar su ramma a can garinsu.
"Me ki ka sani game da abun da ya faru da ramma?"
"Eh to, bayan an dawo da ramma gida, ta cigaba da jinya, dan sallamo su aka yi daga Asibitin birni, saboda rashin isashshen kuɗi. Babar ramma ta gaya mini wata mata ta zo ta ce zata taimaka musu, amma sai sun yarda sun janye shari'ar.
Da suka ƙi, ta ce zasu gani, bayan wasu 'yan kwanaki, wani mutum ya zo da shi da wasu, ya gaya mata shi ne ya yi wa ramma fyaɗe, kuma ta ƙarfin tsiya, ya kama hannunta ya tafi da ita"
Nabila ta ce "Ko ta gaya miki sunan wanda ya keta wa yar ta haddi?"
"A'a, ba su san sunansa ba, ramma ba ta daɗe da fara aiki a gidan ba, amma ta tabbatar da ƙanin matar gidan ne. Bayan ya sace mata 'ya, ta je birni gidajen radiyo ba a saurareta ba, haka zalika wurin jami'an tsaro, kawai lokaci ɗaya muka nemeta muka rasa".
"My lord, shaida ta tabbatar da cewa wanda ya yi wa ramma fyaɗe, ya dawo ya saceta, wanda nake karewa da ake zargi yake tsare, tayaya zai je ya sace yarinyar. Kuma har zuwa wannan lokacin, ba mu ga ramma a zaman kotu ba, shin ina ramma take?"
Lauyan gwamanti ya ce bai kamata a karɓi shaidar maƙwabciyar su ramma ba, tun da ba a kanta abun ya faru ba, dan haka ayi fatali da shaidarta.
Duk yadda Nabila ta so bayyanar da nagartar hujjojinta, amma kotu ta din ga soke su.
Nabila tana ji tana gani, aka yankewa dattijon shekara goma sha huɗu a gidan yari, wata irin bahaguwar shari'a, mara fasali balle ɗigon adalci, yanke hukunci cikin gaggawa ba tare da kammala tabattar da ingancin shaidun kowane ɓangare ba, sai dai an basu damar ɗaukaka ƙara.
Yanayin yadda ta fito a gigice kawai zai tabattar wa da mutum ba a hayyacinta take ba, sumayya da suka zo ɗaukan report ce ta nufeta da sauri, watsi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 66 Chapter of 121