saura fa, haba Vi"
"Ba zan jima ba, ki yi haƙuri yanzun nan zan dawo fa"
Ta ɗaga shi ta ce "To a dawo lafiya, banda rigima" ya sumbaci goshinta yana murmushi ya sauka.
Sai dai ba ta san ina za shi ba, ba ta san lokacin da ya dawo ba, dan sai asuba da ta ji yana tashinta tayi salla.
Gidansa da ya zauna da Jauhar, ya tafi, gidan ya yi ƙura sosai, saboda ya kwana biyu bai zo ba.
Ya haska gidan da fitilar wayarsa, kamar walƙiya ƙwaƙwalwarsa ta tariyo masa wani moment da suka yi.
Ta shigo ta tarar da shi a falo, ta ɗago masa wata jarka ta ce "Master, waye ya sha wannan abin?"
"Ni ne, ba lemo ba ne ba?"
cikin halinta na shagwaɓa ta ce "Master magani ne fa"
"Haba dai, na basir ko shawara? Ni fa in ce, ai na zata lemo ne da, amma bakomai ai tun da maganin basir ne"
Kamar ta yi kuka ta ce "Ni meye haɗina da wani basir dan Allah, kai komai na ajiye sai ka cinye, da wanda na baka da wanda ban baka ba, har nawa da naka duk sai ka haɗa ka cinye" tayi maganar tana hararsa.
Yayi mata shiru, ta gama fushinta, sai da ta manta, sannan ya ce "Ai ki na da kuɗi, a kuma haɗo miki wani mana, ke ki na neman kuɗinki da kyar, su na yi miki wayo, su na karɓar miki kuɗi, suna haɗo abin da baki sani ba su na baki"
Ta kalleshi ta ce "Su wa?"
"Masu ce miki ki sai maganin mana, ai ina jinku, ni da na zata lemo ne ki ka yi ba ki san mini ba, shi ne zan sha rabona sai daga baya na fuskanci menene a ciki, amma bakomai ai ni na sha miki maganin, zai yi miki amfani" banza ta yi masa, ta ƙi kula shi.
Dariya ya yi ya ce "Hajiya magana nake fa"
"Sai dai ka yi kai kaɗai, ba zan kula ka ba"
Murmushi ne ya suɓuce wa Viper, ya din ga jin tamkar ya buɗe idanunsa ya ganta.
Ya jima a gidan, sannan ya fita ya nufi hanyar gida.
Wurin ƙarfe takwas da rabi, Nabila ta fito tana kiransa, dan ta farka baya kan gadon.
Waya ta tarar da shi yana yi.
"Walid jiya kasa bacci na yi, na je gidanmu ne, na daɗe a can sai kusan ɗaya saura na koma gida. Ina ga zan sayar da gidan nan ne, ko kuma a gyara shi a zuba 'yan haya a ciki".
Ƙoƙarin barin wurin ta yi, ya ɗago suka haɗa ido, ya katse wayar ya ce "Ranki ya daɗe, ya aka yi ne? Ko in zo?"
Ta girgiza masa kai ta ce "Dama waya nayi da Abba ne, na fara yi masa maganar su Walida ne, amma na ga kana waya, bari na shiga ciki" ta ƙarasa maganar a gurguje, kamar mai tsoron wani abu, ko mara gaskiya.
Mintuna goma, ya ji ya kasa jurewa, ya tashi ya shiga bedroom, ya tarar da Nabila ta zubo da kaya tana ninkewa.
"Abla" ta ɗago ta kalleshi, ta mayar da kanta ta sunkuyar.
Takawa yayi gabanta, ya karɓe rigar hannunta, ya ce "Kalle ni, menene?" Ta sunkuyar da kai ta ƙi kallonsa.
"Abla am talking to you" kawai hawaye ya fara gangarowa daga cikin idanunta.
"Ya Salam Abla why, kishi ki ke?" Tafukan hannayenta ta saka a kan fuskarta tana kuka mai tsuma zuciya.
Cikin rikicewa ya ce "Ki fahimce ni abla, ki tsaya na yi miki bayani" yayi maganar yana riƙe hannunta.
Girgiza masa kai ta yi, ta ƙwace hannunta ta fice daga ɗakin.
Ya dafe kansa cikin tsananin damuwa ya sake bin bayanta.
**
Indabo kamar yana kan ƙaya haka yake jin zamansa a Nigeria, gani yake komai ma zai iya faruwa.
Da sassafe ya yi sallama da matarsa, bai tsaya ya saurari Abdul ba, ya tafi airport.
Sai dai yana cikin jirgi, wani mutum da facemask ya bashi wata takarda ya tafi, bai san waye ba, kuma mutumin bai yi masa magana ba, bai tsaya ba domin amsa tambayar da Indabo zai yi masa ba.
Ayshercool
08081012143
Bin bayan Nabila yayi yana kiran sunanta, amma ba ta tsaya ba, ya cim mata a ɗaya bedroom ɗin, tana ƙoƙarin rufe ƙofa.
Ya buɗe ƙofar ya tsaya yana kallonta, fuskarta ta koma ja, haka idanunta ma sun yi jawur.
Jiki a sanyaye ya ce "Abla, dan Allah ki tsaya ki saurareni, na yi miki bayani ba yadda ki ke zato ba ne"
Girgiza masa kai ta yi ta ce "No need, ba sai ka yi ba, na riga na fahimta"
"Ba ki fahimta ba abla, kin yi mini gurguwar fahimta, dan Allah ki tsaya ki ji"
Cikin kuka ta ce "Ni ba sai na ji ba, na riga na fahimta, ba zan taɓa samun gurbi a zuciyarka ba, ni ka aureni ne kawai ka din ga kallon hoton jauhar, ba zaka taɓa so ma ba, this is the chance you ask me to give you, shikenan na fahimta"
Diriricewa yayi ya ce "Ba haka bane, baki fahimce ni"
"Ba sai na fahimta ba, your actions show's, da tuntuni ka bar ni na tafi a kan yadda na bar wa zuciyata, na aurenka shi ne sabuwar jarrabawar da zan fuskanta, ka yi mini maganganun da suka sanya na ji na aminta ina da kima a idonka, amma bakomai"
Riƙota yayi yana goge mata hawayen fuskarta ya ce "Ko ba zaki saurare ni ba, ki daina kukan nan dan Allah ba na so" fizgewa ta yi daga jikinsa, ta shige toilet, yana jin yadda ta fashe da kuka mai tsuma zuciya.
Har cikin ransa yake jiyo kukan nata, ya nemi wuri ya zauna jiki a sanyaye, tun yana sanya ran zata fito, har ya haƙura ya tashi ya fita.
****"
"Na san wasiƙata zata iskeka a dai-dai lokacin da yakamata, kafin na jaka da nisa, bari na ɗan ja ka baya, zamanin da kana yaron 'yan siyasa, kun zo garinmu wani sha'ani, aka kai mu wurinku, wai zaku bamu tallafi, aka haɗamu 'yan matasan yara marasa galihu, aka kai wa uban gidanka, ya zaɓi wanda zai lalata, saɓanin cewar da aka yi za a bamu tallafin karatu da sana'a.
Ina cikin waɗanda bai zaɓa ba, dan haka ban san me za ayi musu ba, na shiga damuwa burina ba zai cika ba na karatu, ba a zaɓe ni ba, ba zan samu tallafi ba. Ka yi amfani da wannan damar ka keta mini haddi, da sunan zaka saka ubangidanka ya bani tallafi.
Matan da ka lalata da yawa, na san babu lallai ka tuna, sai dai shi irin wannan mikin, ba ya taɓa goguwa a zuciyar wanda aka illata.
Naja'atu Bunkuren nan dai, da ka lalata da ƙuruciya a garin bunkure lokacin kana yaron ɗan majalissa, ni ɗin ce dai, ƙaddara ta sake haɗa mu, ba tare da ka gane ni ba. Sai dai ba tare da ka sani ba, ka cika alƙawarin da ka yi, na tallafar karatuna, kuma muka ɗora daga in da ka dasa aya.
Ganin ina morarka, ya sanya na haɗiye mummunan ƙudurin fansar da nake da shi a kanka.
Sai dai duk da haka, na yi shirin ko ta kwana ta kowace irin fuska, saboda sanin tsagwaron mugunta da zaluncinka.
Lokaci ya yi da ka ke tunanin, ka ci moriyar ganga ka ya da kwauronta, ina! Idan har ka zauna a gida Nigeria, tonon sililin da zan yi maka ba zaka taɓa sha ba, haka zalika in da zaka ma ba zan bar ka ba, duk in da zaka shiga a faɗin duniya sai na kawo ƙarshenka, dan haka ya rage naka, ko ka dawo Nigeria, ko kuma ka tafi duk in da ka ke so, sai na kawo shafe tarihinka ta hanya mafi muni, zai zama daidai da ɗaukar fansar abin da ka yi mini a baya, aikin da na yi maka tsawon lokaci ma kuma ya zama halacci ga ɗawainiyar da ka yi da ni, na barka lafiya" tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa haka take bugawa, sam bai san ta ina yakamata ya fara ba, ya koma Nigeria ko kuma ya ƙarasa Saudiyya?.
Nan ya shiga lissafi, me take tunanin ta ƙulla masa, da har take iƙirarin kawo ƙarshen sa a duk in da ya shiga a faɗin duniya?
Har labarin lalatar da ya taɓa yi da yarinya a garinsu ya taɓa bata, amma ba ta taɓa nuna masa cewar ita ce ba, ashe duk tsawon lokacin nan wani abu ne a ranta game da shi.
Ya rasa abin da yake yi masa daɗi, gaba zai yi ko kuwa baya, duk iya tunaninsa ya rasa wane irin tuggun take shirya masa.
*****
Abbu kuwa ya gabatar wa da maman ramma, abin da Viper ya zo masa da shi, gam da ya aureta, ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Alhaji Ibrahim, ni a wannan shekarun nawa, me nake nema da zan sake yin aure?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba fa ki yi hamsin ba, kuma auren nan duk in da aka je aka dawo, shi ne rufin asirinki, kuma sai hankalinki ya fi kwanciya, amma ki yi tunani a kai"
Bayan tafiyarsa ta din ga tunani, ƙarshe dai maganar tayi ta cin ta, take gaya wa ramma.
"Amma na ji daɗi mama, babu abin da zamu cewa yaya Aminu sai Allah ya saka da alkhairi, da har ya ce ki auri mahaifinsa"
"Ramma ni gani nake yi abin bai yi tsari ba, goɗai-goɗai da ni na hau yin aure?"
"Mama ai mu ma sai mun fi jin daɗi ace ki na da aure, aure security ne, dan Allah ki amince kar ki ce a'a"
Ta ce "Ai abin ne sai a hankali, amma zan yi addu'a dai"
"To sai mu tayaki addu'ar, kin ga nan gidan ma, bamu sani ba ko Daddy zai yi amfani da abin sa, kin ga ya yi mana ƙoƙari, kalli shi yake ciyar da mu, yake yi mana komai, kin ga kuma yau da gobe sai Allah. Amma idan aure ki ka yi ai mijin ba zai gaji ba, tun da hakkinsa ne" shiru ta yi tana kallon ramma, tabbas maganganunta haka suke, ita ba ma tayi wannan tunanin ba, dan haka ta ce "Kuma fa da gaskiyar ki rahama, amma ni duk na fi son na ga kin tare tukuna a naki ɗakin"
"Eh, ya ce babansa ya bar ƙasar, ya kuma gama gyara in da zamu zauna, ya canza shawara yanzu, wai zan tare amma fa har kayan ɗakin duk ya saka"
Mama ta ce "Ai ni wannan mijin naki, rigimarsa ta yi yawa, na ma daina ce masa ya bari, Allah ya taimaka" ramma a zuciyarta ta amsa da Amin.
Nabila kuwa fafur ta daina sauraren Viper, duk rarrashin da ya so yi mata, fafur taƙi tsayawa ta saurare shi.
Zata dafa abinci ta bashi, da duk wani abu da yakamata ta yi masa, amma ba ta zama in da yake, babu hira babu duk wani abu na soyayya da take yi masa.
Duk yadda yake murnar hutun da ya samu, zai zo su samu isasshen lokacin da zai bata kulawa da soyaya, amma komai ya ɓaci.
Zaman gidan ma ya daina yi masa daɗi ko kaɗan, duk ɗaukinsa da son kasancewa da ita, yanzu fargabar tunkararta ma yake yi, dan sam babu fuskar hakan, sai yayi ta maza yake iya tunkararta, shi ma sai dai yayi kiɗansa da rawarsa shikaɗai.
Sosai yake jin tausayinta, sai dai taƙi ba shi damar ya fahimtar da ita abin da yake son ta sani.
'yan gidan Nabila su suka zo mata wuni, har da Walida da baba magajiya, dama bata saka ran ganin Sauda ba, har da Anty.
Ta ji daɗin zuwan na su, kuma babu wanda ya fuskanci tana da damuwa, suka wuni suka yi wasa da dariya, sai da ta ji kamar kar su tafi.
Abu kamar wasa, Viper ya daina cin abincin Nabila, idan ma ta ajiye ba zai ci ba, ya koma kwana a ɗaya ɗakin, hakan ya saka a jere kwana biyu baya kwana a gida ba ma ta sani ba, sai kwana na uku, da bata ganshi a gidan ba, wunin ranar.
Bayan magariba sai ga Walid, ta yi masa maraba ta karɓe shi hannu bibbiyu, bayan sun gaisa ya ce "Barrister, meyafaru ne tsakaninki da mai zamani, muna murna an yi aure komai kuma zai wuce, shi ma zai samu nutsuwa yanzu ya ji daɗin rayuwa kuma sai a fara rigima?"
"Wani abin ya ce na yi masa?"
"Bai faɗa ba, amma alamu sun nuna, kamar a gidan da muka zauna yake kwana, me yayi zafi haka?"
Cikin mamaki ta kalle shi ta ce "Kwana kuma? A can yake kwana?"
"Wallahi Nabila da gaske nake yi miki"
Kawai ta fashe da kuka ta ce "To ni ya zan yi ne? Duk iya ƙoƙarina baya gani, Jauhar ce kawai a ransa, ni ba ni da wani gurbi a zuciyarsa. Zuciya ce fa a ƙirjina, ina son 'yar uwata, amma abin da yake yi mini yayi yawa. Muna tare da daddare har ya kwanta ya ce mini fita zai yi, sai ji na yi kuna waya, wai gidan da suka zauna ya tafi, a wannan daren ni bani da amfani kenan? Ba zan hana shi tuna Jauhar ba, amma ni fa? Kodayeke dama ni na ce ina son shi, dole na jure duk abin da zan gani"
Walid ya ce "Subhanallah, kuskuren fahimta ne Nabila, tun yamma muka yi magana da shi, ya ce mini ya ji wani wa'azi, an ce gado nauyi ne a kan mamaci, har sai an raba ake sauke masa wannan nauyin.
Shi ne ya ce mini tun da kema gaki, kina cikin magadanta, zai je ya duba gidan, yayi magana da su Baba, ina ga tun zuwan da ku ka yi, bai sake zuwa ba.
Da safen ma, da muka yi magana ce mini yayi abin ne yake ta damunsa, ya kasa bacci, ya ji bai kyauta ba ace tsawon wannan shekarun ba a sauke wa Jauhar nauyi ba, kuma baba bai yi masa magana ba, kawai ya fita a daren, ya je ya sake dudduba gidan, ba wai dan baki da amfani ba ne ba Nabila.
Wallahi kulawar da ki ka samu, Jauhar ba ta sameta daga gare shi ba shi fa yanzu duk wannan abin da yake yi, ihu ne bayan hari kawai, amma wallahi yana sonki Nabila.
Kin san sunanki da nasa ya hargitsa ya fitar da sunan da yake kiranki da shi Abla? Ki din ga yi masa uzuri, a hankali zai daina, zamansa da Jauhar ba abu ne da zai manta lokaci guda ba, yarinyar ta sha wahala ne sosai, kuma ba ta wani more shi ba, an kashe ta a dalilinsa. Da bakinsa yake faɗar ki na da haƙuri matuƙa da kawaici, amma ina ƙara baki haƙuri, dan Allah ku sasanta"
Tayi ajiyar zuciya, ta jinjina kai ta ce "Wallahi ina yi masa uzuri, shi ma ai ya sani amma In sha Allah zan ƙara, na gode sosai da sosai "
"Yauwwa Nabila, ai wallahi tun da ya ce mini wai kin goyi bayan soyayyar liti da ƙanwarki na sara miki, ba ki da riƙo, kuma ki na da haƙuri sosai da sosai, Allah ya baku zaman lafiya ya ƙara muku fahimta juna"
Ta amsa da Amin, tayi ta masa godiya, ya tafi.
Kamar ta kira Viper a waya, sai ta ƙyale shi, sai da gari ya waye, tayi girki ta shirya ta fita.
*****
Cikin matsanancin tsoro da fargaba, indabo ya sauka a airport, yana ta tunanin abin da ka iya faruwa, na sharrin da Bunkure ka iya ƙulla masa.
Sai dai ya ga ya wuce airport lafiya, babu abin da ya faru, har ya isa masaukinsa, bai haɗu da wata matsala ba.
Ya kira abokansa ya sanar musu takardar da Bunkure ta aiko masa da ita, suka bashi ƙarfin gwiwar ka da ya damu, barazana ce kawai ba wani abu ba, yayi zamansa zuwa lokacin da komai zai daidaita.
Kankarofi kuwa yana ta campaign ɗin sa, na takarar sanata, kujerar da Indabo yake kai.
Kuma yana ta ci gaba da samun karɓuwa ta kowace kusurwa.
Jidda ƙanwar indabo kuma tana ta nacin sai ta koma ɗakinta.
***
Kamar daga sama haka Viper ya ji sallamar Nabila, sai dai bai iya amsa mata ba, cikin ɗakin ta shiga, aikuwa ta same shi a zaune a kan katifa.
A ranta take mamakin halinsa, daga samun saɓani yayi yaji, ƙasan zuciyarta, take addu'a Allah ya sa bai sha wani abu ba.
Ba ta ce masa komai ba, ta ajiye flask ɗin, ta ƙarasa kusa da shi ta zauna, bai kulata ba, ta saka hannunta ɗaya a bayansa, ɗaya kuma ta juyo fuskarsa ya kalleta, ta marairaice ta ce "Na zo biko ne, am sorry Vi, son da nake yi maka ne ya janyo komai, kuma tunanin da nake yi, ba ni da matsayi a wurinka ne ya sanya nake shiga damuwa, but am sorry" bai yi magana ba ya ci gaba da tsareta da idanunsa.
Ta shafa fuskarsa ta ce "Talk please" kamar gunki yaƙi magana.
"Please talk Vi"
"I love you" yayi maganar yana tsareta da ido.
Idonta ne ya ciko da hawaye ta ce "And you mean it?" ya jinjina mata kai alamar eh.
Rungume shi ta yi, hawayen farinciki na zubowa daga idanunta, gadon bayansa take shafawa zuwa kansa ta ce "Dama zaka iya bani gurbi a zuciyarka?"
"Na daɗe da baki Abla, baki yadda da kanki bane ba, shiyasa ki ke ganin kamar ba da gaske nake ba. Tashin hankalin da na shiga, da na ji an ce gado nauyi ne, ya sanya na kasa jurewa na tafi a daren, communication gap aka samu a tsakanin mu, dole mu zama masu saurarar juna da yi wa juna uzuri domin zaman auremu ya ɗore kuma ya yi daɗi.
Na yadda ke ba Jauhar ba ce ba, kuma ina ƙoƙarin na rayu da ke a Nabilanki, amma sai kin yadda da kanki, kin kuma rage zargi.
Abla ina yawan gaya miki Al'amin ba butulu bane ba, bana manta halacci komai ƙanƙantarsa kuwa. Balle ke naki da ceto raina, hankalina kacokan ki ka yi, rayuwarki ki ka saka a hatsari mai ban tsoro ki ka ceto ni, tayaya zan zama butulu, a ɗakin nan na kusa ajalinki, amma bai hanaki ci gaba da bibiyata ba, wane irin butulu ne ni da zan kasa buɗa miki zuciyata ki shiga? Ki manta da matsayin Jauhar a zuciyata, ki kalli kanki ke ɗaya kawai, wasu lokutan wasa nake yi miki a wasu abubuwan, amma tun da ba kya so, in sha Allah na daina, amma ina ƙaunar 'yar sugar, wannan kalaman ko 'yar madara ban taɓa gaya wa ba, sau ɗaya na taɓa furta wa jauhar ina sonta a rayuwata, daren da za a kasheta, amma ke ba na son na maimaita wannan kuskuren ina sonki Nabilatul arfa, Ablana kuma 'yar sugana"
Ita kanta ba ta san takamaimai kukan me take yi ba, ya ci gaba da rarrashinta, da duk kalaman da shi kansa bai san ya iya su ba, tare da ƙoƙarin wuce makaɗi da rawa.
A hankali ta ce "Vi ba fa a gida muke ba"
"Eh, ai ke ki ka ɓata mana honeymoon a gida, sai mu yi a nan"
"Honeymoon a kango?" Tayi maganar tana murmushi, bai san lokacin da ya tuntsure da dariya ba, ya tashi zaune yana kallonta ya ce "Gidan gwaurontakar namu ne kango?"
Tana daga kwance ta yi murmushi ta ce "Kogon da macijina ya din ga ɓuya ba"
Ya gyaɗa kai ya ce "Ke ce jarumar da ki ka samawa wannan maciji 'yanci, ya ci gaba da rayuwa da cikakken 'yanci.
Abla a lokacin da ake nemana ruwa a jallo, ba ki duba kamani tare da ke barazana ne a gareki ba, ba kya lissafa wannan, 'yanci kawa ki ke nema mini, na bar kogon da yake tamkar kurku a gare ni, wai duk tayaya zan manta wannan ne?" Ya ƙarasa maganar yana kwanciya a jikinta.
Ta rungume shi sosai, tana sauke numfashi.
A nan suka karya, hankalinsu kwance kamar su na gida, su ke gudanar da soyayyar su.
Har Dutsen da ta kan je ta same shi, su ka je, ta din ga tuna masa wasu abubuwa da suka din ga faruwa, suna nishaɗi.
Har yamma suna can, sannan suka tafi gida.
Viper ya tambaye ta, a raba kayan jauhar a bata, ko a sayar a raba kuɗi kawai a bata.
"Ba zan iya amfani da kayanta ba"
Dumm ya ji a ƙirjinsa, amma ya daure ya ce "Meyasa?"
"Zan daɗe ina kallon kayan ina tunata"
Ya ce "Ko dai kishin ne?"
"Ko kaɗan, rayuwarta da yadda ta rasu, ba zai taɓa barin ƙwaƙwalwata da zuciyata ba, ba zan iya amfani da kayan jauhar ba, rashin haɗuwa da jauhar a rayuwata wani miki ne za ba zai taɓa warkewa daga zuciyata ba. Idan ma an raba, ayi amfani da abin da na samu a sai wani abu da ladan amfani da shi zai isketa da mahaifiyarmu a makwancinsu"
"Shikenan, zan yi magana da Abba abin da ya ce shikenan"
Gidan Major kuwa, Mama ta takurawa Nasir a kan ya auri 'yar ƙawarta da take so ya aura tuntuni.
Aka fara shirye-shiryen biki, aka yi masa transfer a wurin aiki, zuwa kudancin Najeriya, kuma aka rage masa matsayi sosai da sosai a in da aka kai shi.
Walida kuma sosai suke soyayya da liti, dan kuwa akwai shi da shiga rai.
Sosai Viper yake ƙara ganin kimar Nabila, saboda rashin riƙonta, maganar bikin Sumayya ita ma ta taso, Nabila su na ta shirye-shirye.
Viper sai da ya samu Liti, shi ma ya ja masa kunne, a kan abubuwan da yake yi wa Nabila.
Nabila ta sake komawa duba mama, an sallamota daga asibiti tana gida, sai dai wata irin wahalalliyar jinya take yi, gaba ɗaya yaran babu mai tausayinta.
Har gidan su Shahida ta je, ta zazzagaya ta sada zumunci.
Bayan ta dawo, ta tarar da Viper yana ta mita.
Ta ce "Meyafaru ne?"
"Kuɗin da muke rabawa na ribarmu, na wurin shayin nan, wai ba za su bani ba, wurin refilling ɗin gas, Walid zai din ga zama idan ya dawo daga kasuwa, zai din ga zama".
Ta ce "To menene a ciki, idea ce mai kyau"
"To ai ni kuɗi nake so, harkar bikin nan na kashe kuɗi sosai, na sakankance na saka rai, suka ɓullo da wannan maganar"
Ta ce "Vi ai idea ce mai kyau, zaman haka ka dogara da aikin gwamanti kawai, ba zai yiwu ba, gashi shiru an ce za ayi maka ƙarin girma amma haryanzu shiru"
"Wannan ƙarin girman duk matsala ne"
"A'a ina fatan mu samu ci gaba, a kan komai"
Cikin ikon Allah aka saka ranar tarewar ramma, kuma maman ta amince da batun auren baban Viper.
Nabila ta mayar da hankali wurin gyara ramma ma, ta biya kuɗin yi mata gyaran jiki, sannan ta saka maman yusuf likitan mata haɗata.
Viper ya yi ta mita, saboda Nabila ta koma aiki, haka abubuwa suka yi wa Nabila yawa, zama matar gida babu sauƙi ga komawa aiki.
A haka lokacin hutun Viper ya cika, zai koma bakin aiki.
Daga shi har ita kamar su cinye juna, dan tun bayan da suka shirya, yake ta ƙoƙarin kare duk wani abu da zai sanya ta ji babu daɗi, ita ma daga nata ɓangaren tana ta ƙoƙarin kiyaye abubuwan da zai janyo su samu saɓani.
Tun dare ta haɗa masa jakarsa, ta yi masa snacks, ta yi masa cincin da dambun nama, yadda zai daɗe yana amfani da shi.
Sun sha soyayya ranar, kamar kar su rabu.
Da safe wurin ƙarfe goma, ya tafi duk sai ta ji babu daɗi, gidan yayi mata wani iri.
Kwanan Viper biyu da tafiya, Walid ya rako liti har gida, ya zo ba wa Nabila haƙuri.
Nabila ta ce "Da zan riƙe abin da ka yi mini a raina, hatta alaƙarka da Vi sai na rabata, duk da tasirin shekarun da ku ka yi tare. Kawai da ka din ga iya bakinka, wani idan ka cutar da shi da harshenka, har abada duk aikin alkhairin da zaka yi masa, ba zai shafe tasirin abin da ka gaya masa ba, Allah ya shiryeka" duk da ya ji haushin kausasan maganganun da tayi amfani da su a kansa, amma ya danne.
Bayan sun fito yake cewa Walid "Yanzu da gaske sai ta raba alaƙata da Viper, duk tsawon lokacin da muka ɗauka tare?"
Walid ya ce "Macece fa, wallahi sai ta raba"
"Kai ƙarya ne ba zai yiwu ba, ba wata mace"
"Galibinmu uban meye ya koro mu daga gidan iyayenmu, idan ba tasirin kaidin mace ba, ka daina cika baki malam"
Sai kuma ya ce "Kai haka ne fa, to Allah ya kyauta"
Nabila ta samu labarin mutuwar Madaki, ya mutu an rasa wanda zai zo ya karɓi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 117 Chapter of 121