zata din ga dumbuzo abin da ta samu ta din ga kai mata, domin kuwa har ta fara tsara irin rayuwar da za ta yi, a matsayinta na surukar ƙaramin minista a Nigeria.
Babu irin huɗuba da dabarun ha'inci, da ba ta koyar da hafsa ba, haka ba ta fasa shige-shige ba, cike da fatan a karon farko hafsa ta haifo ɗa namiji, domin idan kankarofi ya mutu su samu dukiya, domin kuwa yaransa mata ne. Amma tun da hafsa ta bar gidan, wata kusan shida, ko Kanon ma ba ta tako ba, sisi ba ta turawa Zakiyya ba.
Ta din ga kiranta a waya, a kan ta aiko da kuɗi, a sake bi mata malamai ayi maganin uwargidansa, kuma a kama mata shi, amma ta ce ita baya bata ko sisi.
Hafsa ta sanya wa ranta, a wannan karon ba zata yi asarar kuɗinta ba, babu wani mushiriki da zai sake cin sisinta, saboda ta mallake Alhaji mu'azzam.
Ta yi amfani da shawarar Jauhar, da ta bata tun tana raye, ta kama addu'a, da miƙawa Ubangiji lamarinta, tare da yi masa biyayya dai-dai iyawarta, sai kuma uwa uba gyara da take yi, yadda yakamata ba tare da ta yi abin da zai cutar da lafiyarta ko imaninta ba.
Sai dai mai rai ba a rasa shi da motsi, duk da irin kula da tattalin da Alhaji mu'zzam yake yi mata, ba shi da isashshen lokacinta, kuma har zuwa yanzu ya kan bi abin da matarsa uwargidansa take so, bai fiye son ɓata mata ba, gashi kusan kowane lokaci cikin aiki yake ba shi da lokaci.
A wannan karon ba ta yi yinƙurin yin fito na fito da uwargidansa ba, dan taga alamar baya son hakan, kuma ita rayuwa yar siyasa ce, a gabansa babu abin da ya yi mata zafi, da ko sako zancen matar, a bayan idonsa kuwa ba ta jurewa idan ta kira ko ta yi yinƙurin ci mata mutunci.
Kuma dai-dai gwargwado kankarofi yana sakar mata kuɗi tayi yadda take so, ko kyauta zata yi a gidansu, Baba take aikawa kuɗi, ta san koba komai kowa zai amfana a kan ace Anty kawai take bawa, dan ta san ƙarshen kuɗin a yawon bin bokaye zai ƙare.
Daf da azahar su Abbu suka iso gidan su Nabila, kafin nan tuni ta kammala abincin karɓar su.
Abbu ne da Baba da kuma Major suka zo tare.
Nabila ta yi farin cikin zuwansu sosai da sosai, sai dai Major yayi ta faɗa a kan yadda ba su faɗi abin da ya faru ba.
Major kawai kallon Nabila yake yi, yadda ta fututtuke da ba ta son auren, amma tayi ƙalau da ita.
Sun daɗe a gidan, sai da Major ya zaga a cikin barrack ɗin, suk sai juniors ɗin sa a aiki, duk sun yi retire.
Daga nan suka je gidan Alhaji mu'azzam, suka wurin hafsa, ita ma kamar ta taka dan murna, iyaye akwai daɗi.
Sai dai ba su daɗe a gidan hafsa ba, saboda yamma suka kama hanyar kano.
Nabila na kitchen tana ta ƙoƙarin yin wanke-wanke, Viper ya shiga kitchen ɗin ya tarar da ita.
"Sannu"
Ta kalleshi ta ce "Yauwwa"
"Ki na iya aikin a haka?"
Ta ce "Eh mana, me ka gani?" Yayi murmushi ya ce "Bakomai, dama dai shekaranjiya suka zo, yau na so nima na yi zaman jinya, anyway sannu Abla, na so na yi appreciating iskar fankar jiya unfortunately....
Katse shi ta yi da "Ni dai na ga ta kaina da wannan fankar"
Ya jingina da jikin bango, ya ce "Na yi ƙoƙari fa Abla, shekara ta nawa ina zaune haka, kodaye ba na gane komai sai 'yan kwanakin nan"
"Dan Allah vi ka ƙyale ni da zancen fankar nan"
Dariya ya yi ya ƙarasa kusa da ita, ya saka hannunsa a sink ɗin, yana tayata wanke kwanukan.
****
Abdul shi yake kai Ramma makaranta, haka idan an tashi, idan kuma yana da ayuuka da yawa da kanta take tafiya.
Mama sam ba ta son kaita makarantar nan da yake yi, tafi so ta tare, saboda gudun abin da aka iya faruwa, dan haka ta ya tan kunnen ramma, a kan lallai gara ta tare, can su ƙarata kar su ɗaukko mata magana a titi.
Allah ya taimaki Abdul, hankalin Indabo ba ya jikinsa, hatta ita mahaifiyarsa ba ta cikin hayyacinta, amma shi sam hakan bai dame shi ba, yadda zai gina rayuwarsa da ta rahama yake yi.
Surutun abin da ya faru da Bunkure kuwa, ya ci gaba da zaga wa lungu da saƙo, gaba ɗaya mutane suka din ga Allah wadai da yadda ta daɗe tana cutar jama'a.
Viper kuwa bai bari Nabila ta yi girki ba, ordern abinci ya kuma yi musu, yana ta lallaɓata.
Bayan sallar isha'i, ya kira Walid, yayi sa'a kuwa ya ɗaga.
"Mai laya"
"Mai zamani, ya gida ya ƙanwata?"
Viper ya ce "Lafiya ƙalau, tun ɗazu nake kiranka, su Abbu sun zo fa yau, har da sirikaina"
Walid ya ce "Kash, amma wallahi da na san za su zo, biyo su zan yi"
"Ai gara da baka sani ɗin ba, ka zauna ka kula mini da ƙanwata, tun la'asar na kiraka ai baka ɗaga ba"
"Sai magariba na ga missed call ɗin naka, muna asibiti ne, Shahida ba ta jin daɗi tun asuba muke can, sai magariba muka dawo"
Viper ya ce "What? Muhsin haka muka yi da kai? Daga aura maka yarnya ka haɗata da aiki, wane irin abu ne haka?"
Walid ya ce "Innalillahi me zamani meye haka wai? Fura ta sha ta ɓata mata ciki, take ta amai da gudawa muka tafi asibiti fa"
"Ba wani nan, laulayi ne, matsalar aurawa tuzuru yarinya kenan, gamo da kasawa sai wannan al'amari, to ni dai idan namji ne ayi mini takwara"
Kashe wayar Walid ya yi, jin abin da Viper yake yi masa.
Nabila kuwa sai kallon Viper take yi, dama haka yake da tsokana har haka, kuma yana yi yana wani mazewa, kamar ba daga bakinsa suke fitowa ba.
Shahida kuwa dariya take yi wa Walid, yadda ya dage yana yi wa Viper rantse-rantse.
"Wallahi my kana bani dariya, ya san kunya ka ke ji, shiyasa yake yi maka wasu abubuwan, ka fiye kunya, ni har dariya ka ke bani"
Yayi murmushi ya ce "Ai na fuskanci tsokanar ta wa yake yi kawai"
"My ka san sai yanzu na san Yaya Al'amin yana wasa da dariya, wallahi da ko kallona ba ya yi, ban taɓa zaton yana wasa da dariya ba"
Walid ya yi murmushi, yana shafa gefen fuskarta, ya ce "Ki daina tuna bayan nan, amma Viper mussaman lokacin marigayiyya, bayan ta fara saita mu, yana wasa da dariya, kin san rayuwar ta mu ce, duk sai a hankali sai godiyar Allah. To ya ki ke jin jikin naki yanzu?"
"Da sauƙi, amma ba zaka yi mini wayo ba, ni duk ka daina jin kunyar tawa yanzu"
"Ai mai zamani gaskiya ya faɗa, da ya ce matsalar a ba wa tuzuru aure kenan, bai iya cin ƙwan makauniya ba"
Tare suka yi dariya, cike da nishaɗi da jin daɗi.
Nabila kuwa ta ɗauka, yau za ta sake, ta samu isasshen bacci, dan tun da ta fara jinyar Viper, ba ta samun bacci, ta zata ya samu abin da yake so, zai bari yau ta yi bacci.
Amma sai ta riski abin da ba tayi tsammani ba, dan kusan gara jiya da yau, dan jiyan ƙyaleta kawai ya yi, yadda yake nanata zancen fankar nan, sai da ya tabattar mata da gaske tsawon lokacin da ya ɗauka, yana zaune haka ya dame shi, dan ta gazgata yadda yake ba wa fanka muhimmanci.
Ɓangaren Abdallah Liti, barkwancinsa ya sanya yake da mutane sosai a kasuwa, amma hakan bai hana shi yin faɗa da muzurai wasu lokutan a kasuwar, dan ma idon Abbu yana hana shi yin wani abun.
Sai dai Abbu yana jin daɗin aiki da su sosai da sosai, ba su da ƙyuya ko kaɗan, kuma ya sha jarraba amanar su, ba tare da sun sani ba, amma ko kusa ko da wasa babu wanda ya taɓa yinƙurin cin amana.
Sai da ya ƙara dana sanin ɗaukar su Abba ya ɗora su a kan harkokin sa, suka din ga ɗurka masa sata, suna cutarsa. Da su Al'amin ya riƙe, da yanzu dukkanin su, sun tsaya da ƙafrsu.
Sai dai ya yanke shawarar zai tallafa musu sosai da sosai, su tsaya da ƙafafuwan su, dan ya san bai isa ya biya su, wahalar da suka yi da ɗan sa ba.
Samunsu a kasuwar, ya sanya wasu lokutan ko zuwa baya yi, sai ya zauna a gida ya ɗan huta, ko yaje wasu sha'anunnunkan, za su kular masa da komai babu cuta ko cutarwa.
Idan yana cikinsu, sai ka ɗauka shi ne ya haife su, har shawara ya kan yi da su a kan harkar kasuwanci, bai yi da abokan sana'arsa ba, saboda su ba za su cuce shi ba ko su yi masa hassada ba.
Abbun ne yake tsokanar liti ya ce "Abdallah, kai haryanzu babu wadda ku ka daidaita ne? Su sun yi aure sun bar mini kai a haka fisabilillahi, yakamata ka motsa kai ma na aurar da kai"
Liti ya ce "Ai abbu wadda nake so ɗin kamar tafi ƙarfina, gani nake kamar ba za a bani ba" yayi maganar cikin damuwa.
Walid sai hararsa yake yi, yadda yake sakin jiki yayi hira da Abbu shi ba ya iyawa.
Abbu ya ce "Haba dai, ni da ina da wata 'yar ai da na baka, amma meyasa ka ce ta fi ƙarfinka?"
Jiki a sanyaye ya ce "To ai ana ganin ni ba mutumin kirki bane ba, ba kowa zai iya jihadin da ka yi ba Abbu"
"In ji waye ya ce maka ba mutumin kirki ba? Wannan wani abu ne da aka yi shi ya wuce, kuma yanzu Alhamdilillah, babu abin da za mu cewa Allah sai godiya. Kuma gaka da sana'a ka shiryu yanzu ba kamar da ba, in sha Allah za a baka, yar gidan waye idan ma baban naka ba zai tambayar maka ba, ni sai na wuce maka gaba"
Liti ya ɗan yi shiru ya ce "Ƙanwar matar mai zamani ce, wata Walida a gidan su take, 'yar major ce"
Abbu ya ce "Au to ashe ma 'yar gida ce, shi ne ka ke ta damuwa"
"Ina jin tsoro ne, gani nake kamar ba zai bani ba, kuma Walid ma cewa ya yi na nemi wata, ba lallai a bani wannan"
"Ita yarinyar kun daidaita? Kana zuwa wurinta ne?"
Ya jinjina masa kai alamar eh.
"An gama, ka fara tarin abin da ya sauwwaƙa ba zai gagara ba in sha Allah" washe baki liti yayi cikin matsanancin farinciki, Walid kuwa kamar ya mare shi, saboda ba ya jin kunya ko kaɗan yake wannan maganganun da Abbu.
Shahida ta je har gida gaida Abbu, ta yi masa farfesun kaza, taje gaishe shi, sai da ta tuna masa da jauhar, lokacin azumi ta saka Al'amin a gaba suka zo musu sannu da shan ruwa.
Rahila kuwa, ko kallon kirki ba ta yi wa Shahida ba, duk yadda shahidan ta din ga raɓarta, amma ta din ga hantararta, tana ƙarewa auren zagi.
****
Viper har tausayin Nabila yake ji, domin yanzu zaman ɗari-ɗari takeda shi, saboda yadda ya addabeta, har ta fara yi masa zancen, tun da ya ji sauƙi, zata koma Kano, hutunta ya kusa ƙarewa, ya ce ba za ta koma ba, shi ma an kusa sallamar shi, zai je hutu, sai su tafi tare.
Har murna take yi idan ya ɗan fita baya nan, ta samu ta ɗan sake.
Da ya dawo kuwa ta shiga fargaba da tashin hankali.
Da safe wurin ƙarfe tara da mintuna, Viper ya zuba wa Nabila ido da ta kasa tashi, take ta lumshe ido, alamar bacci bai isheta ba.
"Abla yau ba zamu karya bane ba? Yunwa nake ji fa"
Ta buɗe idonta da kyar, ta ce "Tun wurin 8 fa na tashi, na yi niyyar ɗora breakfast ɗin, kai ka hana ni, kuma ga wani irin bacci da nake ji" tayi maganar tana ci gaba da lumshe idanunta.
Ya saka hannunsa, ya shafi fuskarta, ya yi ƙasa da muryarsa ya ce "Na sani ki na haƙuri, amma ki ƙara kin ji 'yar sugar na, duk da wasu lokutan ki na yi mini bore, but am appreciating jazakillahu bil janna" ɗan ƙara sunkuyar da kai tayi, cike da jin nauyin sa, dan haryanzu tana jin nauyinsa sosai da sosai. Sannan ta jinjinawa ƙoƙarin sa, irin yadda ta din ga shishishige masa dan ta dawo da shi hanya, da keɓewar da suka din ga yi, amma ko da wasa bai taɓa yinƙurin yi mata abin da bai dace ba, wanda hakan ne ya sanya ta ƙara sakin jiki da shi sosai.
Maganar sa ce ta dawo da ita hayyacinta ya ce "Kin san wani abu kuwa?"
"A'a sai ka faɗa"
"Liti ne ya zo mini da wata magana, wai wata sisternki yake so, na manta sunanta, wadda muka tarar da baba uwani a wurinki a asibiti"
Ta buɗe idonta ta ce "Wai Walida?"
"Yes ita, wai sonta yake yi, amma ki na ganin Abba zai ba shi aurenta kuwa? Tun da kin ga ga tarihin rayuwar mu"
Nabila ta ce "Me zai hana, Walida tana da sauƙin kai, kuma ba ta da dogon buri ita da Anty mamanta"
Viper ya ce "Ina fatan ba zaki yi ramuwar gayya abin da yayi miki ba, ki saka a hana shi ita ba"
Nabila ta ce "Haba dai, ai wannan ya wuce, ai in dai tana son shi shikenan, mu dama fatanmu kullum idan aka samu wanda ya tuba ya daina ɓarna, al'umma su karɓe shi, a mutunta shi, in sha Allah ba zai gagara ba"
Viper ya ce "Mun gode sosai da sosai my sugar girl"
Dariya ta yi tana tashi zaune ta ce "Wai kun gode, kamar an yi wani abu"
"Bari idan muka karya, zuwa eleven, sai mu je na kai ki gidan hafsa"
Cikin murna ta ce "Amma na ji daɗi sosai da sosai, na gode Vi"
"Never mind, mu je ayi wanka, sai mu yi breakfast ɗin"
Ta ji daɗin zuwanta gidan hafsa, ko ba komai, ta rage zaman kaɗaici.
Ta din ga tsokanar hafsa wai anya ba ciki ne da ita ba, saboda yadda ta yi ƙiba.
Hafsa ta ce "Wallahi ba wani ciki Nabila, jiya na gama period kwanciyar hankali ce kawai da cin abinci, ni abin ya fara damuna ma,wata shida ko ɓatan wata ban yi ba"
"Kai hafsa, me aka yi da maza kwata kwata yaushe aka yi auren? Dan Allah kar ki ɗaga hankalinki"
Hafsa ta rausayar da kai ta ce "To, amma ina son yara Nabila, dan Allah ki yi mini addu'a, ka da Allah ya jarrabe ni da rashin haihuwa, ina son yara sosai da sosai"
Nabila ta ce "Dan Allah kar ki damu kanki, komai rabo ne kuma lokaci ne, daga yin auren ai yayi wuri ki fra wannan maganar" tayi ta kwantar mata da hankali, daga nan kuma suka ɓuge da hira, wanda galibi hirar ta karkata ga yanayin zamantakewar aure bawa junansu shawarwari, da zancen kayan likitar mata maman dr . Wadda cikin ikon Allah, magungunanta suka ɗaga darajarsu a idon mazajensu fiye da yadda suke tunani, ita mace ai yar gyara ce da kwalliya, babu borar mace sai wadda ta so.
(0706 971 1327 da kayan likitar mata, bbau ruwanki da matsalar sanyi, ko fargabar amfani da kayan da baki san da yaya aka haɗa su ba, domin tsoron cutar da lafiyarku. Domin ɗaga likkafar taku kimar, ku kasance masu yawan ibada da addu'a, biyayya tare da gyara da ingantattun magunguna na gyara)
Sai da suka kira Sumayya su ka yi video call da ita, domin daga abin da Nabila take missing, har da Sumayya.
Cikin ikon Allah, hutun wata guda Viper ya samu, domin ya ƙarasa jinyarsa, dan haka suka nufo Kano.
Nabila cike da murna ta dawo, sai dai gidan su ya sha uwar ƙura, suna zuwa mayafinta kawai ta ajiye ta hau gyara.
Viper ya taimaka mata da abin da zai iya, ya tsallake ya fice, ya tafi wurin 'yan amanarsa.
Tas Nabila ta ƙalƙale gidan, ta kira sumayya a waya, ta gaya mata ta dawo, ta ce mata za ta zo.
Ta kuma kira Walida a waya, bayan sun gaisa take yi mata maganar liti.
Da fari nuƙu-nuƙu ta fara yi, daga baya kuma ta saki jiki ta yi mata bayanin komai.
A fitar da Viper ya yi, har gidan su ramma ya je, yaji daɗi da mama ta gaya masa ta koma makaranta, amma ta damu da rashin tarewarta, ta gaji da yadda sai dai ya zo ya ɗauketa su na yawo a gari.
Viper ya ce kar ta damu zai yi magana da Abdul ɗin.
Bayan ya koma gida yake gaya wa Nabila, da weekends Walid da liti za su zo, dan tun da aka yi bikinsu, Walid ne kawai ya zo.
Ta ce masa to.
Can gidansu Hafsa kuwa, 'ya'yan mama da Anty Zakiyya ta yi wa asiri, da kyar ta samu suka auru, kullum cikin ciwo suke, dan ɗaya daga cikinsu kamar zata zare, idan ta fara aljanu kamar zata haukace, hakan ya tsananta wutar ƙiyayyar da ke tsakanin su, kuma aka yi rashin sa'a, dukkaninsu babu wadda take jin daɗin zaman aurenta, ɗaya kishiyoyi sun sakota a gaba, sai da aka yi saki biyu a shakera biyu.
Ɗaya kuma dangin miji da maƙwabta, sun hanata sukuni, ga miji ba ya son haihuwa.
Abin duniya ya isheta, ta rasa abin da yake yi mata daɗi, ga Tijjani ya auri wata fitinanniyar yarinya da ba ta da kunya, ba ta ganin mutuncinta ko kaɗan, shi kuma ya zama tamkar soko, sai abin da take so shi yake yi, ba ya ji ba ya gani a kan matar nan, bai ƙi ya ɓata da kowa ba a kanta, ciki har da maman. Dan idan ta yi masa ƙorafi a kan matar, sai ya daina zuwa gaisheta.
Saifu ne dama mai ɗan dama dama, shi ma kuma ba ya ji, ya haɗa kai da yaran masu kuɗi, yana ta rashin ji, duk da ya rage, ga kuɗi yana samu, amma ya fi mayar da hankali a kan shaye-shaye da kashewa 'yan mata kuɗi, sam ba ya yi wa rayuwarsa wani tanadi.
Waɗannan tarin matsalolin ne, suka haɗu suka addabi zuciyar mama, ta kasa sukuni da jin daɗin rayuwar, duk in da ta motsa ɓacin rai da damuwa sun baibiyeta cikin yaranta kowa da halinsa.
Kawai aka wayi gari tana wanka, ta yanke jiki ta faɗi a cikin banɗaki, aka ɗauketa aka kaita Asibiti, a nan aka tabattar da ta samu shanyewar ɓarin jiki.
Ba ta iya yi wa kanta komai sai dai ayi mata, hatta najasa a kwance take yi, kasancewar jinya ba abu ne na ɗan lokaci ba, ya sanya yaran nata suka fara ƙosawa suke bata wahala.
Hakan bai zame wa Zakiyya izina ba, dan a iya cewa ita murna ma tayi, yanzu miji ya zama nata itakaɗai.
****
Liti sai ƙarewa gidan Viper kallo yake yi, an zuba wa Nabila kaya na alfarma, gidan yayi kyau sosai da sosai.
Nabila ta gabatar musu da kayan ciye-ciye, take cewa Walid "Shi ne yau baka kawo mini Shahida ba"
"Ai ita na kawo ta ma, ke fa baki taɓa zuwa gidanmu ba"
Tayi murmushi ta ce "In sha Allah zan zo, ai ina son zuwa ziyara sosai da sosai, dan ba sai na jira Vi ba, shi sabgoginsa da yawa".
Suka hau abinci da ci, Walid yana ta santin abinci, amma liti da ya karkace sai cewa ya yi "Abincin nan ya kusa kamo na 'yar madara daɗi, ita fa miyar 'yar madara sai ka kwana uku kana jin magginta a bakinka"
Walid ya ce "Sannu faisal, ka tsayar da kunnuwa kamar zomo, ka na ta gizo, ka yi wa mutane shiru"
Ta basar ta ce "Vi wai yaushe ɗan mama zai dawo ne?"
Viper ya kalleta ya ce "Sai ya shekara biyu ai, in sha Allah zan je na gano shi"
"Har shekara biyu, bai yi yawa ba?"
"Ni da na yi biyar mutuwa na yi?"
Tayi murmushi ta ce "To ai kai kai ne, shi kuwa abin tausayi"
Yayi murmushi ya ce "Shi ma zai jure ai"
Walid ya ce "Ina fatan Viper ne ya daka sakwarar nan, dan ta yi daɗi ta daku"
Ta ce "Mara lafiya ne zai daka? Haryanzu hannunsa yana yi masa ciwo fa"
Liti ya sake kallon falon ya ce "Ohh Allah sarki yar madara, gidanku na tuna Viper, da ta tare babu ko plasta, aka saka mata kayanta a ciki haka, gashi ta mutu, wata ce take morar arzikinka"
Viper dai bai yi magana ba, Nabila ta tashi ta ce "Bari na shiga daga ciki, ku gaida gida zan ɗan kwanta"
Viper ya kama hannunta, ya yi kissing bayan hannunta, ya ce "Allah ya ƙara zaƙin hannu, abinci ya yi daɗi sosai"
Cikin jin kunya ta ce "Allah ya ƙara buɗi, cefane yayi kyau sosai" ta tafi tana murmushi.
Liti ya ce "Haryanzu ina jin ba daɗi, idan na tuna ba jauhar ce ke more soyayyar nan ba"
"Abdallah" Viper ya kira sunansa yana kallonsa.
Ya kalle shi.
"Ka daina yi wa Nabila abin da ka ke yi mata, son Nabila son Jauhar ne. Wani darasi da na ƙara koya a rayuwata da Jauhar, shi ne dama sau ɗaya take zuwa a rayuwa, ko ka yi amfani da ita ko ta wuce. Na samu dama na saka halaccin da Jauhar ta yi mini da soyayya da kulawa, amma ban yi ƙoƙarin hakan ba, sai a ƙarshen rayuwarmu, kuma mutuwa ta zo ta rabamu. A yanzu wata damar na samu na saka halacci da alkhairi, dan haka a daina kushe mini Abla please"
"Tuba nake maigida an daina in sha Allah"
Ya tashi ya yi musu rakiya, sai da ta jiyo falon shiru, sannan ta fito ta hau gyarawa.
Yayi mamakin bayan dawowarsa, da take masa dan Allah su je su duba mama a asibiti, tun su na Abuja, aka ce mata tana asibiti babu lafiya.
Shi mamakin da take bashi, kamar gaba ɗaya rayuwarta ba ta da riƙo, komai girman laifin da aka yi mata kuwa, da ta gama buyaginta, sai ta saukko.
A daren suka je suka dubata, Nabila har da ba su kuɗi, sai da ta yi kuka, ganin yadda bakin maman ya karkace, sai zubar da yawu yake yi, ga wani irin warin kashi da take yi, duk da da pampers a jikinta, da alama tun safe ba a cire mata ita an canza wata ba.
Da daddare suna kwance, tana jikin Viper, ta ce "Vi"
"Mmm"
"Dan Allah in tambayeka mana, amma kar ka ji haushi Please"
Ya ce "Idan kin san zan ji haushin kar ki yi"
"Am curious"
"Go ahead"
"Na ga ka na da kishi sosai, amma na ga kamar akwai shaƙuwa sosai, tsakanin Jauhar da su yaya Walid"
Murmushi ya yi mai sauti, tare da shafa bayanta ya ce "Haka ne, dan ma Allah ya jiƙan rai Nura baya raye, ta fi shaƙuwa da shi sosai da sosai. A lokacin da ta shigo rayuwata, daga ni har su babu wani mai guiding ɗin rayuwarmu, ba mai saka mu, babu mai hana mu, abin da muke so shi muke yi.
Bayan ta shigo rayuwata, ta fara ƙoƙarin nuna mana mu ma mutane ne.
Tana da kirki da sauƙin hali sosai, a duk lokacin da na shiga matsala, babu wanda yake tsayawa a kaina, sai ita, su kuma su na dafa mata, babu wanda zai saurareta idan ba su ba.
Ko sakakken abinci ta yi, sai ta ajiye musu.
Gashi tana matuƙar girmamasu, saboda ta san dai babu wanda ya damu da mu, sai su ɗin dai.
Saboda ita muka daina askin banza, kamar babarmu, haka za ta zauna ta yi ta mita, bayan na haɗu da Nura kuwa, tun da ta fuskanci matsalarsa shi ma ta rashin kulawar iyaye ne, da ƙarancin shekaru, take tausaya masa.
Ya girmeta, amma shi ne ɗan aikenta, har kasuwa yawon sayo mata kayan shirin dutse shi yake yi mata, ina jin kishin ba bana ji ba, amma na yadda da ita, kuma idan na wulaƙanta su, saboda su daina zuwa in da take, idan na shiga matsala wa zai taimaka mata?.
Ta kai ta kawo, Nura sai ya samo abin sa, bai kalli in da nake ba, sai dai ya zo wurinta.
Idan matsala ce da shi ma, ita zai gaya wa saboda ni masifaffe ne, ta rayu da mu da tausayi ne, da kulawa babu ƙyama da jin cewa bamu da amfani, shiyasa Liti kullum cikin yabonta yake. Ta shiga cikin tashin hankali, ta kaɗu sosai da mutuwar Nura"
Ta sauke numfashi ta ce "Na fahimta, Allah ya yi musu rahama gaba ɗaya"
Ya ce "Amin my sugar girl"
"Bari zan ɗan je na dawo"
Ta kalleshi ta ce "Yanzu kuma? Ƙarfe tara
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 116 Chapter of 121