faɗi in da yake ba"
Indabo ya ce "Ƙyale 'yan sandan nan, sonake na riga su samunsa, idan na riga su kawai kashe shi za ayi salin alin, duk madaki ne yayi mini shirme wallahi, amma yanzun ma komai zai daidaita"
"Kar ka damu honorable, ai kai maganin kowane shege ne a ƙasar nan, ba ma ɗan daba ba, zamu yi maganinsa, amma da alama kamar kana da maguatan ɓoye, da suke tallafa masa"
"Na sani, amma yanzu duk ba wannan ba, a cigaba da abun da yakamata"
P.A ya ce "To shikenan, na barka lafiya "
Bayan fitarsa Indabo ya shiga cikin gidansa, ya tarar da Abdul a falo, tare da mahaifiyarsa.
Ya kalli indabo ya ce "Welcome"
"Thank you" ya zauna ya kalli Abdul ya ce "Dama nemanka nake yi".
Abdul ya ce "To gani"
"Ya maganarmu ta rannan?"
"Daddy maganganun namu ai da yawa, wacce daga ciki?".
"A'a, ka san wanda suka fi muhimmanci ai, mun daddale da jam'iyya, kai za a tsayar mataimakin gwamna, tun yanzu yakamata ka fara harkar campaign, da buga pastoci. Amma ka san dole ka daina duk wani shashanci da kake aikatawa. Sannan maganar da nake yi, maganar aure, shekara talatin da biyar, uban me ka ke jira? Muddin lokaci ya cigaba da gabatowa, abokan adawa suka san baka da aure, sai ku samu matsala a harkar takarar nan, amma da na yi maganar auren sai ka din ga gocewa"
Ya ɗan tsuke fuska ya ce "Wai constitution ne ya ce dole sai mutum yayi aure zai yi shugabanci meye amfanin auren mutum a cikin siyasa to?"
Indabo ya ce "Ban sani ba, idan ba zaka yi ba, ni ina da wadda zan haɗaka aure da ita, ga 'ya'yan abokai da yan uwa nan sai dai ka ji an yi".
Hajiya Bilki da tun ɗazu ba ta yi magana ba sai yanzu ta ce "Haba distinguish, ka bi shi a hankali mana, zai yi, ba sai an yi masa dole ba".
"Ba zan bishi a hankalin ba, na gaji da wannan shirmen nasa, rayuwarku nake ƙoƙarin ingantawa, wataƙila idan ya zama mataimakin gwamna, shi ya fi ni samun dama, ya kuɓutar da ɗan uwansa".
Hajiya Bilki ta ce "Distinguish, kai da ka fishi daɗewa a harkar, ba ka samu yin hakan ba sai shi, ni na karaya da lamarin jafar"
"No, kar ki yi mamaki ya fi ni samun authority, da damar fitar da shi, da dai a nan Nigeria ne, da tuni an daɗe da wuce wurin"
Ta ce "Haka ne, Abdul dole ka yi haƙuri ayi maganar auren nan, tun yanzu za a fara share fagen samun damar yin nasarar ka, dan idan ku ka gama tenure ku, kai zaka yi gwaman nan gaba"
Cikin sangarta ya ce "Mummy ba ƙi na yi ba, auren ne ba na so"
"Aikuwa haka zaka yi haƙuri" suka cigaba da tattaunawa a kan yadda tsare-tsaren za su kasance.
***
DSP Nasir na tsaka da aiki, aka sanar da shi yayi baƙuwa, ya ce ace ta shiga, tana shiga ya ga Nabila.
Yayi murmushi ya ce "Ke ce baƙuwar dama?".
"Eh mana, ko na koma ba ka san ganina?"
"A'a ni na isa na na ce haka. Zauna bari na kawo miki lemo, daga wurin aiki ko daga ina?"
Nabila ta kashingiɗa ta ce "Na je wani trial ne"
Ya ɗaukko mata ruwa a fridge ya ce "Sannu"
Ta ce "Yauwwa" ta karɓi ruwan ta sha, ya ce "Amma kin bawa kanki wahala da yawa, wace court ɗin ki ka je, har ki ka iya biyowa nan?"
Ta ajiye robar ruwan ta ce "Wani wuri na je, na ga wani client, DSP"
"Na'am barrister Nabila maitama "
Tayi murmushi ta ce "Wai ina mutumin nan?"
Ya ce "Wanne?"
"Wanda ku ka kama, haryanzu bai faɗi in da Vipern yake ba?"
"Ina fa zai faɗa, yana ta wahalar da mu".
"Dan Allah ka nuna mini shi"
"Ki yi masa me?"
"Babu komai, ganinsa kawai zan yi"
Nasir ya ce "To bari na gama aikina, sai mu je ki ganshi"
Nabila ta zauna ta jira Nasir ya gama abun da yake yi, ta ɗauki jarkar ruwanta suka fito, yana ta nuna wa abokan aikinsa ita, yana gaya musu ita yana gaya musu ƙanwarsa ce, lawyer ce. Suka gaggaisa da abokan aikinsa, sannan suka ƙarasa in da liti yake.
Laɓensa duk ya bushe, saboda yunwa da ƙishirwa, yana ganin Nabila ya ganeta ya ƙura mata ido, ta kawar da kanta ta ce "DSP tun da ya ce bai san in da yake ba, haka zaku cigaba da ajiye shi?"
"Eh har sai ya yi magana tukuna"
Ta girgiza kai ta ce "Amma a doka, ai kotu za a kaishi ko a sake shi, ina ga fa tun da ya ce bai sani ba, bai sani ɗin ba"
Nasir ya ce "Ya sani ba zai yi magana ba ne" ta miƙa wa liti ruwan hannunta, ta ce "Ga ruwa" banza yayi mata, Nasir ya juya ya fita yana amsa waya daga wurin ogansa.
Tayi ƙasa da murya ta ce "Na san na yi muku laifi, amma dan Allah ka yi haƙuri, zan san yadda zan yi ka bar wurin nan".
Ta ciro wani ruwan a jakarta ta bashi, ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, na fahimci kuskuren da na yi, ban kyauta ba amma zan gyara komai"
Nasir ya dawo ya ce "Mu tafi?"
"Eh, amma gaskiya, yakamata a san abun yi, kar a taka doka da yawa"
Ya ce "To masu doka, mu je gida"
"Da gaske fa nake, ko mu shigar da hukumarku ƙara".
Ya mayar da abun wasa, suka tafi gida.
***
Ƙarfe huɗu na yamma, Nabila ta shirya ta fita, ta tafi gidan matar da aka ce an yi laifin fyaɗen nan a gidanta.
Ganin Nabila cikin shiga mai kyau, ya sanya masu gadin ba su tsaya tuhumar wacece ba, suka bata damar shiga gidan.
Sai da haushi ya fara kamata, saboda jiran da aka bar ta tana yi, daga baya matar gidan ta fito, suka gaisa da Nabila.
Nabila ta ce "Na san baki sanni ba, sunana barrister Nabila Yusuf maitama, lawyer ce ni mai zaman kaina. Akwai mai gadin gidan nan malam isyaku, da ake accusing da laifin fyaɗe, ni ce lawyer sa. Na zo ne dan Allah in ji details ɗin abun da ya faru".
Matar ta tsuke fuska ta ce "Ke, ni ki ka zo ki yi wa wannan tambayar? Wurin 'yan sandan na je na fara karɓar report, an ce na dawo station ɗin da aka fara case ɗin, amma na ga dacewar fara zuwa gidan nan, tun da an ce yarinyar 'yar aikinki ce, kuma ainihin wanda ya yi laifin kina da alaƙa da shi, ku ka yi framing ɗin sa aka ce shi ne. Yanzu duk ba wannan ba a matsayinki na uwa kuma 'ya mace nake so mu fara magana. Ina yarinyar take? Ina ne gidan iyayenta? Ban damu da sanin koma waye yayi laifin ba, fatana kawai a wanke mai gadi, tun da kun san wanda yayi laifin "
Matar ta miƙe ta ce "Ki koma wurin jami'an tsaro, su zaki yi wa wannan tambayar, kuma ba ki da wata hujja, da take tabattar da ba shi yayi ba, idan kin gama kina iya tafiya"
Nabila ta miƙe tsaye ta yi murmushi ta ce "Na gode sosai antyna da bani lokacinki" ta juya ta fice.
Station ta sake nufa, wanda a nan aka fara case ɗin, aka nemo statement ɗin da aka rubuta, da sunan Asibitin da aka kai ramma, na cikin gari, tana tsaka da dubawa, wanda yake evening duty, shugaba a wurin, ya fito afujajan, ya ƙwace file ɗin wai ba a ba su damar su bata file ɗin tayi bincike ba.
Cikin mamaki da takaici Nabila ta ce "Waye zai bayar da damar, bayan wadda ƙasa ta bayar, lawyer ce fa ni, dan me za a hana ni damar dubawa, doka ta bani damar neman hujjojin da zan gabatarwa kotu, na wanda zan kare, yaya za ayi a hana ni"
Fafur suka hanata, suka ce ta tafi, ta kira Nasir a waya, amma wayarsa ta ƙi shiga, ranta yayi mummunan ɓaci.
A gajiye ta koma gida, ana ta kiraye-kirayen sallar magariba, ta yi wanka tayi salla, ta ɗaukko wayarta ta kira sumayya.
"Ke ya ki ke aikin?"
"Sumy raina a ɓace yake, kin san menene?" Sumayya ta yi sauri ta katse wayarta, ta saka a Flight mode, ta ɗauki wayar ummanta, ta kira Nabila ta ce "Sorry wayar ce caji ya ƙare"
Nan ta labartawa Sumayya abun da yake faruwa.
Sumayya ta ce "In dai ƙasar nan ce, ai kaɗan ki ka gani d.....
Cikin sauri Nabila ta katseta ta ce "Sumayya few months back, ina wannan case ɗin da yaya murtala ya saka, har aka kusa korarsa? The case are similar".
Sumayya ta ce "How?"
"In so many ways, dan Allah ki sake binciko mini labarin, ko ma ki haɗani da yaya murtalan, ke zan ma zo na same shi, the same yadda matar ta ce an yi wa yarinyar fyaɗe, ɗan yayan matar gidan, shi ma dattijon nan haka ya ce mini, ɗan yar matar gidan ne yayi abun ba shi ba ne ba, shi asibiti kawai suka kaita, da shi da ɗaya mai aikin da wani mai yi musu hidima a gidan, definitely duk case ɗin ne but i want to confirm"
Sumayya ta numfasa ta ce "Ban ƙi ta taki ba, amma ki bi a hankali, kin ga a kan case ɗin, sai da Murtala ya kusa rasa aikinsa, ke daga ji kin san case ɗin babba ne"
"Sumayya tsoron da muke ji, da ja da baya shi ke saka wasu ma suke Fuskantar irin matsalolin, idan na gama bincike na, i will raise the case, hatta 'yan sandan nan da abun da suka yi mini, duk sai na yaɗa, just support me sumy, Allah zai taimekemu, ke 'yar jarida ce, zaki iya kema".
Sumayya ta ce "Haka ne, amma kar ki kira ni a wayata, zan ki ra ki da wani layin, sai mu haɗu da yaya murtalan" ta yi wa sumayya godiya, tana sake bawa kanta ƙwarin gwiwar lallai za ta tsaya wa wannan dattijon kuma za ta yi nasara.
***
Abdul ne yake kallon ramma, yadda duk take a takure, tana kallon tv, amma hankalinta ba a kan tv yake ba.
"Rahama"
"Na'am" ta amsa tana kallonsa.
"Meyake damunki ne?" Tayi shiru ta sunkuyar da kai.
Ya kwanta a kan cinyarta, ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana danna remote.
Ya tashi ya ce canzo hijjabinki ki zo, ta yinƙura jikinta na rawa, ta sako hijjabi, ta fito.
Ta tarar da shi a tsaye da mukulli a hannunsa yana waya.
Ta ƙaraso jikinta yana tsuma, tunaninta ko gida zai mayar da ita, ya riƙe hannunta, ya buɗe ƙofar falon suka fito.
Da kansa ya sakata a mota, ya rufe sannan ya zagaya ya kunna motar ya fita da ita.
Sai kallon gari take yi, duk da dare ne ko ina da hasken fitila, tun da ya kawota a sume, ba ta sake fita ba, kuma ba ta san a ina take ba.
"Gida zaka mayar da ni?"
Ba tare da ya kalleta ba ya ce "Ai na ce ki daina wannan tunanin ma"
Cinema ya kaita, wai kallon film, bayan tv suka baro a gida, ta din ga waige-waigen yadda za ta yi ta gudu, amma a in da suke zaune, yana rungume da ita, ga wurin duk ƙabilu ne, abun da ta fuskanta, ba iya cinema ne wurin ba, dan daga can wani wuri, kaɗe-kaɗe na tashi.
"Naga ki na ta waige-waige, ba mahaukaci bane ni, da zan kawo ki inda zaki iya guduwa, ko ki yi wa wani magana ba, kowa sabgar gabansa kawai yake yi a wurin nan, gara ma ki nutsu"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Ko bangon duniya zaka kai ni, idan Allah ya yi niyyar fitar da ni ba ka da dabara".
Yayi murmushi kawai, sai da ya gama abun da yake yi, ya ɗauke ta, suka tafi ya kulleta a mota, ya sayo mata abinci, ya mayar da ita in da suke.
***
Nabila kuwa tana ta bin kwatancen da dattijon nan yayi mata, na gidan zulai ɗaya mai aikin da suke aiki tare da ramma, amma ta kasa gane kwatancen, ganin ta gaji, kuma ta hanyar ake bi, a je in da Viper yake, ya sanya ta tare abun hawa, ta sake tafiya.
A wannan karon da ta sauka, google map ɗin ta buɗe, tana duba abubuwan da suke wurin, ba tare da gazawa ba, ta cigaba da yawon bulayin neman gidan, cikin sa'a bayan shafe mintuna talatin tana bulayi, ta hango gidan.
Wata irin ajiyar zuciya ta yi, sannan ta nufi gidan.
Ƙofar gidan a rufe, ta saka hannu ta tura ƙofar, tayi sallama.
Ƙofar ta buɗe, sai dai ba ta ji motsi ko alamar mutum a gidan ba.
Duk da gabanta faɗuwa yake yi, amma haka ta ke ta addu'a ta shiga. Tsakar gidan ko ina shirgi, can bokiti, ga tukunya can kaya sauran sigari tsakar gidan kaca-kaca.
Ta ƙarasa ta leƙa ɗakin, ta hango Viper durƙushe a kan gwiwarsa, yana ƙoƙarin yi wa kansa allura, sai dai hannunsa sai rawa yake yi, gashi ya huda jijiyar, jini ya fara zuba.
Da sauri ta ƙarasa, ta durƙusa, ta gyara masa sirinjin, ta cigaba da zuba masa ruwan allurar.
Rintse idanunsa yayi, jin yadda allurar take ratsa jikinsa.
Babu tsammani, ta zare sirinjin ta ce "Wannan abun da ka ke yi, zai iya shafar ƙwaƙwalwarka fa" ba ta gama maganar ba, ta ji ya faɗo a jikinta, ta faɗi a wurin saboda nauyinsa, ƙoƙarin ture shi take yi, dan ji ta yi tamkar wani ƙaton dutse ne ya faɗo mata.
Ya ɗago idanunsa ya kalleta, ya saka hannu ya shaƙe wuyanta.
Numfashinta ya fara fita sama-sama, ta rirriƙe hannunsa idanunta suka yo waje.
Walid ne ya faɗo ɗakin da gudu, ya fara ƙoƙarin janye Viper daga kanta.
A tunaninsa jikin Viper yayi sakin da zai ture shi kawai, amma ya ji da ƙwarinsa.
A wahale ta ce "Zaka kashe ni fa" a hankali ya saki wuyanta, Walid ya ɗago shi da ƙyar, ya kalli walid, ya kalleta ya sake mayar da idonsa kan Walid da ƙarfin gaske ya ce "Walid"
"Na'am Al'amin"
"Walid matata, matata walid! Ɗa na Walid mata ta" yayi maganar yana wani irin ƙaraji, tare da jan rigar walid da ƙarfin da sai da ta yage.
"Easy maza, easy yi haƙuri"
"Walid zan haukace, walid kaina zai tarwatse, me zan yi ne wai, ka fitar mini da yarinyar nan, ba na son ganinta matata walid" yayi maganar yana girgiza kansa.
Nabila ta tashi da kyar, tana ta haki, ta ce "Zaunar da shi zan yi masa magana dan Allah"
Walid ya ce "Ɗauki jakarki ki tafi, yi sauri"
Kawai Viper ya shammaci Walid, ya buga kansa da ƙarfi a jikin bango, take jini ya fara biyo hancinsa, ya faɗi ya suma a wurin.
Nabila ta ƙwala ihu, saboda sautin da kansa ya bayar, da ya buga kan, Walid ma a rikice ya ɗago shi, amma ko motsi baya yi.
Ayshercool.
08081012143
49
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
Wanda za su jira document 1K ne.
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
Cikin matsanancin tashin hankali Nabila ta nufe su, Walid ya rikice, ya rasa me ma yakamata ya yi ya taimakawa Viper.
Cikin azama Nabila, ta ɗaga kan Viper yana kallon sama, ta ciro hular kanta, ta toshe hancinsa da yake zubar da jini, ya zamana ta gefen bakinsa yake numfashi.
Cikin kuka ta kalli walid ta ce "A kai shi asibiti mana, ya bugu da yawa, tun da abun ya kai ga zubar da jini ta hancinsa"
Walid ya ce "Ba za a kai shin ba, uban waye ya ce ki kuma zuwa ai duk ke ki ka ja?"
Cikin rashin fahimta ta ce "Ni kuma? Ni me na yi? Zuwa na yi na bashi haƙuri a kan abun da na yi bisa kuskure, wallahi ban yi masa komai ba, tarar da shi na yi yana yi wa kansa allura jikinsa yana rawa, na karɓa amma wallahi ban yi masa komai ba. Ko duk haushin abun da na yi wa ɗan uwanku ne? Na je station ɗin ai, kuma na yi magana da shi, dan Allah ku yi haƙuri rashin sani ne ya sanya na aikata abun da na yi masa, abun da ake faɗa a gari a kansa daban, ni kuma ban san gaibu ba, amma dan Allah ku yi haƙuri" tayi maganar hawaye wani na bin wani a fuskarta.
Walid ya ce "ya isa haka, tashi ki tafi"
"A haka za a bar shi, ba zaka kai shi asibiti ba?"
"Ta yaya zamu kaishi asibiti ana nemansa a kama shi?"
Fizge-fizge Viper ya fara yi, yana ƙoƙarin tashi, Walid ya daddane shi, cikin ɗaga murya ya ce "Walid"
Ya ce "Na'am Al'amin"
"Liti" walid ya ce "Ya shiga banɗaki".
Viper ya sake cewa "Mai laya"
"Na kiyayi mai zamani, Allah ya ƙara maka lafiya"
"Gobe zamu je asibiti da ƙanwarka 'yar madara, sun ce inducing za su yi mata 'yar madara za ta haihu, ragonta yana ƙauye wurin Hajiya"
Walid ya ce "Masha Allah, Allah raba su lafiya"
"Walid"
"Na'am mai zamani"
"Cikin nan yana ba ta wahala, nima na ƙagu ta haihu, na ga yarona, sunan ƙanina nura zan mayar, idan ta kuma haihuwa na saka sunan Sadik".
Walid ya ce "To Allah ya kawo mana su lafiya da albarka"
Wani irin ihu ya hau yi, yana ƙoƙarin ture Walid, cikin ƙaraji ya ce "Walid matata ɗa na, ba zan iya komai ba, ka riƙe madaki, kar ya illata mini mata, ka riƙe shi walid wai me ka ke yi ne?"
Sosai suke kokowa da Walid, ga hancinsa na cigaba da zubar da jini, ga damuwa da fita hayyaci a dalilin allurar nan.
Walid ya ce "Sai na ci uban ɗan mama idan ya dawo, bai ji me na gaya masa a kan kawo maka kayan maye ba, sai ya saka mun yi babu ka rasa ƙwaƙwalwarka tukuna".
Nabila kuwa iya ƙarfinta take kuka, tsananin tausayinsa ya mamaye zuciyarta, da ƙyar walid ya danne shi, a hankali jikinsa ya saki, ya daina motsi, amma yana motsa idanunsa, a buge yake ya fita hayyacinsa amma ba bacci yake yi ba, abubuwan da suka wuce ne suke dawo masa cikin mayen.
Nabila ta ce "Dan girman Allah ka gaya mini ƙarashen labarin nan, ina jauhar ina abun da yake cikinta?".
Walid ya ce "Kin ga ni ba wannan ne a gabana ba, lafiyar ɗan uwana da taya shi ɗaukar fansa ita na saka a gaba, dan haka ki tashi ki tafi kawai"
Nabila ba ta sake magana ba, ta tashi jiki a sanyaye, ta ɗauki jakarta, har ta kai bakin ƙofa, ta waiwayo ta sake kallonsa, hakan yayi dai-dai da buɗe idanunsa, sun yi jawur gwanin ban tsoro, ya tsura mata ido, a hankali ta juya ta fice.
Cikin maye ya ce "Mai laya"
"Allah ya taimaki mai zamani"
"Ba na son ganin yarinyar nan, zan iya fara kisan kai a kanta".
Walid ya girgiza kai ya ce "Ba ka taɓa yi ba, kuma ba zaka fara a kanta ba" surutan da Viper ya cigaba da yi ne, ya tabattar wa da Walid ba ya cikin hayyacinsa.
***
Ramma ta na zaune, ta na cin farcenta, tana zancen zuci, ta ji Abdul ya kama hannunta.
Sai da ta firgita, kasancewar tayi zurfi a zancen zuci.
Hannunsa riƙe da nail cutter, ya fara cire mata faratan ya ce "Ƙazama kawai, da baki ki ke cin farce" janye hannunta ta yi ta ce "Ni kar ka shafa mini cuta" tayi maganar tana haɗe rai.
"To cuta ta nawa kuma, in dai ina da ita da tuni kin ɗauka ta can wurin. Duk rashin ji na, ina using protection, a kanki ne kawai nake gaba gaɗi, shi ma dan na san am safe na killace ki" tsaki ta yi ta kawar da kanta gefe.
Ya kama hannunta, ya cigaba da yanke mata farcen ta ce "A banza, wallhi ko haɗiyeni zaka yi, ka fito da ni, ba zan yafe maka zaluncin da ka yi mini ba"
Bai kalleta ba ya ce "Dama ban ce ki yafe mini ba ai" ya na cikin yanke mata, ta ga yana ɗan yamutsa fuska, ya gama ya tashi ya koma ɗaki, ta kalli falon komai tsaf solomon yake gyarawa, a ranta ta ce "Dama aure ne da ni, ace nan gidana ne ba wannan ƙazantar ba. Tunanin hakan kawai ya saka idanunta cika da hawaye.
Ta ɗaukko magazines ɗin da ke falon, tana ta kalla, har ta manta da shi a gidan, ta shiga bedroom ɗin, ta tarar shi a kan gado yana murƙususu.
Ta kalleshi ta ce "Menene?"
A wahale ya ce "Kira mini solomon" ta juya ta fita, ta kiro shi.
Ya ɗaga kai ya ce masa ya kawo masa biro da takarda.
Ya kawo masa, yayi rubutu a jiki, ya ce yaje ya sayo masa.
Solomon ya fita cikin sauri, ta kalleshi ta ce "Wai menene?"
Ya ce "Epigastric pain ne"
"Me kenan" ya nuna mata cikin sa.
Ramma ta ce "Sannu Allah ya sa mutuwa zaka yi na huta"
Yayi mata shiru, ya cigaba da juyi, ya dunƙule hannunsa yana dukan gadon a hankali, yana yi yana miƙa alamar yana jin jiki sosai.
Ta tsaya tana kallonsa, gumin da yake yi, ya sake tabattar mata ya fara galabaita.
Yayi mata nuni da hannunsa ta je, ta ce "In zo in yi maka me?"
Girgiza kai ya hau yi, yana kiran "Mummy, rahama cikina am in pain"
"To sannu"
Ta samo jarka da ruwa, ta tofa masa bisimillah ƙafa 19, da suratul fatiha ƙafa 7, ta hau kan gadon ta ce "To tashi ka sha ruwa" ya tashi da ƙyar ya karɓa, ya shanye, yayi jifa da jarkar, ya kwanta a kan cinyarta ya ce "Rahama cikina"
"Allah ne yayi maganinka, a cikin sakans idan ya ga dama, zai rabaka da rayuwarka, ka ga idan mutuwa zaka yi, ga saɓo kana yi, ga zaluncin da ka yi mini, Allah ya sa ka mutu".
Abdul ya ce "Da na mutu shahidi, ciwon ciki ne ya kashe ni, kuma ƙarshe ace ke ki ka kashe ni".
"Ko shahidi ka mutu kan ka shiga aljanna, sai ka shiga .... Sai kuma ta yi shiru. "Allah dai sai ya ƙwatar mini hakkina a wurinka na zalunta ta da ka yi"
Solomon yayi knocking, Abdul ya ce ya shigo, ya shigo da leda a hannunsa, Abdul ya karɓa, ya sakawa kansa butterfly needle, ya saka ramma ta haɗa allurar da aka kawo, ya ce tai masa.
"Ni ba zan iya ba, tsoro nake ji"
"Tsoron me malama, ciwo zai kashe ni"
"To ni taɓa yi na yi?"
Cikin tsawa ya ce sai ta yi, hannunta na rawa, ta zuba allurar a cikin butterfly needle ɗin.
A haka ya nuna mata yadda za ta saƙala masa ruwa, yana yi suna faɗa, ta saka masa ya sa hannu ɗaya ya janyota, ya sake kwanciya a kan cinyarta.
Yadda yake wash wash da kiran sunanta, sai ya ƙular da ita kamar ba namiji ba.
"Ni ka daina kiran sunana tun da ba ni na ɗora maka ba"
"Wash rahama cikina" tsaki ta yi ta ce "Wai shekarunka nawa?"
"36yrs" yayi maganar yana kallonta.
"Amma an yi asarar ƙuruciya, idan ba ka yi wasa ba kana cikin wanda annabi ya ce kun yi asara, ka tafiyar da ƙuruciyarka a shirme da shashanci, a mintuna ashirin ɗin nan da Allah ya ga dama, da yanzu babu kai, me zaka ce wa Allah, ka sha giya ka kwana kana zina da 'yar da ka raba da uwatta, ka canza tunani da halaye, ko Allah ya yi maka rahama".
Ya lumshe idanunsa ya yi shiru, bai ce mata komai ba.
***
Nabila kanta tamkar zai tarwatse ita ma haka take ji, so take ta kamo bakin zaren tallafawa Viper. Babban abun da yake buƙata yanzu rehabilitation ne, a fara nesanta shi da shaye-shaye, sannan a kwantar masa da hankali da ƙoƙarin tirsasa masa karɓar ƙaddararsa ta hanyar da ya dace. Sannan a fuskanci kamo zaren tsaya masa, ya ɗauki fansar abun da aka yi masa ta hanyar doka, ba ta hanyar da yake tunanin ɗauka ba, sai dai alamu sun nuna mata ba zai sarrafu cikin sauƙi ba, balle a samu fahimtar juna da shi, sai dai ta ƙudurce a ranta, duk tsanani da wahalar lamarin, za ta tsaya a kan sa, ko da kuwa sanya rayuwarta cikin hatsari ne, za ta yi domin taimakon Viper.
Sai dai hakan ba zata yiwu ba, sai ta ji ƙarshen labarinsa, amma ta yaya?. Da ta tuna yadda yake kururwa yana kiran matarsa, ɗansa sai ta ji ta karaya, tausayinsa ya ƙara kamata.
Ringing ɗin wayarta ne ya katseta daga tunanin da take yi, ta ga lambar sumayya, ta ɗauki wayar ta kara a kunnenta.
Sumayya ta ce "Na yi wa Uncle murtala kwatancen gidanku, zai zo ya same
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 51 Chapter of 121