Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
57 / 121
zuwa, saboda maciji ba ya raina ƙofa komai ƙanƙantarta, kuma ya tsammace ni, ta in da bai taɓa zata ba, kuma lokacin da bai taɓa zato ba. Al'amin na rufe bakinsa, madaki ya saka masa ƙarfe a damtsensa, a take kokawa ta kaure a tsakanin su, sai dai madaki ya kasa sarrafa ƙafar da Viper ya soka masa wuƙa, rabon da a zubar masa da jini har ya manta, saboda laƙanin taurin da yake amfani da shi, fitar masa da jinin da Al'amin yayi, yana nufin laƙanin ya karye, kuma a kowane lokaci, ana iya yi masa rauni da ƙarfe koma a kashe shi. Sosai suka din ga yi wa junansu illa da makami, sai dai Madaki ya fara galabaita, dan haka ya fara ƙoƙarin guduwa, dan ba ya son wasu su farga cewar ƙarfe ya fara tasiri a jikinsa. Amma Viper ya hana shi yin hakan, zuciyarsa ta din ga wata irin tafasa, ya din ga saran madaki, madaki ya saka hannu ya shaƙe Viper, take Viper ya ji abun da ya taɓa ji idan madaki ya shaƙe shi, tamkar an yi masa sarƙa da dutse, ya kasa motsi. Viper ya ji an saka masa wani abu a gefen wuyansa, a take ya silale ya ya faɗi ƙasa. Madaki ya ja da baya yana kallon yadd mutumin ya saita shi da bingida, dan bai ga ta in da ya ɓullo ba. "Zaka iya tafiya" mutumin yayi magana yana nuna masa hanya. Madaki ya ja jiki da kyar, yana ɗingisa ƙafa ya bar wurin. Wasu mutane manya manya majiya ƙarfi suka ɓullo wurin "Yaya kun tarwatsa yaran?" "Eh sir, amma fa har an sanar da 'yan sanda zancen rikicin sun taho" "Maza maza ku ɗauke shi ku tafi da shi, ayi masa treatment, ayi sedating ɗin sa, har a gama yi masa komai, kar ku mayar da shi maɓoyarsa yanzu, a bari zuwa da safe, idan yaransa sun fita nemansa sai ku mayar da shi. Su kuma su musa su tabattar sun goge duk wani trace da zai sanya a gane yazo unguwar nan" "Ok sir" Suka cicciɓi Al'amin, suka saka shi a mota, suka ɗauki wuƙarsa da wayarsa, suka tafi. Har wajen goma na dare, Nabila tana kiran wayar Viper, amma ba ya ɗagawa, hankalinta ya fara tashi, ko wani abu ne ya same shi, amma sai ta tuna, kaɗan da aikinsa ya ƙi ɗagawa mussaman ma da tayi masa laifi yau. Liti kuwa bayan ƙura ta lafa, ya koma gida, sai dai bai tarar da Viper ba, sai Walid. "Wai Viper bai dawo ba?" Yayi maganar yana kallon Walid. Walid yayi masa banza. "Malam magana nake yi maka fa" "Ban sani ba, da ni kuka fita?" Liti yayi tsaki ya ce "Bari na san yana hanya shi da ɗan mama" Walid ya ce "Ina fatan kun kashe madaki, kun wuce kun kashe Indabo" "Ban sani ba" Walid ya girgiza kai, ya cigaba da abun da yake yi. Ɗan mama ya shigo shi ma, jikinsa duk jini da alama yayi ɓarna sosai, ya ce "Oga liti ina Vipern, ina fatan yana lafiya, ni fa tun da muka afkawa su lakwari, ban sake ganinsa ba" Liti ya tashi tsaye ya ce "Kamar yaya? Ya haɗu da madakin ne?" "Ai ban sani ba, da muka rabu da ku, wani wurin yayi ai" "Bari mu jira nan da awa ɗaya mu gani" Walid ya ce "Hmm" "To yana nan lafiya, ai ba wani abun ne ya same shi ba" Walid ya ce "Na yi maka magana ne?" "To kama yi mana" Walid ya ce "Wallahi wani abun ya same shi, sai ranka ya ɓaci liti, daga kai har ɗan mama muguwar kasada cw da ganganci abun da ku ka biye masa ku ka yi. Kuma tun da ya kai i yanzu, akwai abun da yake faruwa gara kawai" yayi maganar yana miƙewa tsaye, ya ɗauki wuƙa ya soke a jikinsa, ya fice. "Ɗan mama, Walid fa gaskiya ya faɗa anya ba wani abun ne ya faru ba?" "Tashi mu koma, akwai matsala mun yi wauta da muka bar shi ya yi mana wayo, da ƙyar idan bai haɗu da madaki ba" haka suma suka tashi, suka fita. DSP Nasir da kansa ya jagoranci tafiya unguwar su madaki, bayan kiran da suka samu daga mai unguwa, sai dai da suka je ba su tarar da kowa ba. Duk ga alamu nan na faɗan dabar an yi, dan 'yan unguwar sun tabattar da hakan. Da safe Nabila har ta gama shirinta, baya ɗaga wayarta, tana zaune tana karyawa, ta shiga what's app tana duba messages, sai ga wani saƙo, an turo mata wani voice message, amma bayan an turo lambar tayi blocking ɗin ta. "Dan Allah ku taimaka mini, a ƙwato mini hakkina, an yi wa ɗiyata fyaɗe, na nemi a bini hakkinmu a kotu, amma wata Naja'atu Bunkure ta ce mana ita lawyer ce, ta ce zata taimake mu, amma wai sai mun janye ƙorafinmu, ko mu haƙura wanda yayi laifin yafi ƙarfinmu. Tayi mana tayin kuɗi bamu karɓa ba, yaron ya zo har gida, ya ci mini mutunci, ya ɗauke mini ramma ya tafi da ita ta ƙarfin tsiya, ban san ina ya kai mini 'ya ba, ya dawo ya karɓi kayanta, wai nayi haƙuri ta zama tasa. Ban san meyake nufi ba, dan girman Allah a bi mini hakkina, a nemo mini 'ya ta bani da ƙarfin ja da su, ni talaka ce, amma dan Allah a dawo mini da 'ya ta mu ji da ciwo ɗaya na keta mata haddi da yayi, ku taimaka mini dan Allah" matar ta ƙarasa maganar tana kuka. Da sauri Nabila ta tashi tsaye, ta din ga kunna voice ɗin tana saurare, wani irin gumi ya fara tsatstsafo mata, ba ta raba ɗaya biyu, wannan Muryar babar ramma ce, ita ce Muryar da aka saka a radion su Sumayya. "To amma waye ya turo mata voice ɗin?" Ta tambayi kanta. Buɗe ƙofar office ɗin da aka yi ne, ya sanya ta ɗan nutsu. Mutumin nan ne da yake zuwa wurin Barrister kabir, babban mutum ne sosai. "Na shigo ko na koma a nema mini iso?" Ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Bisimillah" Ya shigo ya zauna, ta ɗan risuna ta ce "Sannu da zuwa sir". "Yauwwa barrister Nabila, ya kike ya aiki?" "Alhamdilillah" Ya ce "Masha Allah, ai na yi wa Kabir magana, shi ya bani numbernki, kuma na kira kin ce sai na zo office" ta waro ido ta ce "Dama kai ne? Yi haƙuri dan Allah, ban sani ba na zata kawai masu haɗa lamba ne" Yayi murmushi ya ce "Kar ki damu, hakan yana da kyau ai, ai mace da aji aka santa. Sunana Wada M karofi, maybe kina ɗan jin sunana" Tayi murmushi ta ce "Oh yes, dama kai ne M karofi?" Ya jinjina mata kai ya ce "Eh barrister, ina son ki zama ɗaya daga cikin lawyoyina, masu kula mini da dukiyata da kadarorina, ina biya sosai, na yaba da nutsuwarki, na ce da ganinki zaki yi amana, na yi magana da barrister Kabir ya ƙara bani tabbacin hakan". Nabila ta gyaɗa kai ta ce "Haka ne, amma am very sorry sir, ni bana son irin wannan, a bar ni a hakana kawai" Yayi murmushi ya ce "A bar ki a hakanki anya kuwa? To shikenan idan ba za a kula da dukiyata ba, to ni a kula da ni mana" yayi maganar yana kallon ta. Murmushi ta yi tana girgiza kai ta ce "Haba sir, manya ba sa haka fa" "Subhanallah, na yi miki tsufa kenan?" "A'a ban ce ba, namiji ai baya tsufa" "To shikenan, zamu yi waya, bari na barki ki yi aikinki, idan ta kama ma sai na zo gida" "To Allah ya kawo ka lafiya ya tsare" "Amin Barrister na, ga wannan ki sha ruwan roba, ba na leda ba" yayi maganar yana ajiye mata kuɗi a kan tebur" "Ina fatan ba cin hanci ka bani ba, hakan ba zai hana in ta kama na saka alƙali ya ɗaure mini kai ba"ta yi maganar tana kallonsa. Ya yi dariya ya ce "Funny you, ni na isa, ayi aiki lafiya" ya fita yana murmushi. Yana fita ta ɗauki kuɗin ta ce "Alhamdilillah, tsuntsu daga sama gasashe, Allah ya kawo amanar baban wasu hannuna, na samu mai zuba mini mai idan mota ta iso" da sauri ta zube kuɗin, ta sake ɗaukar wayarta, ta sake jin voice message ɗin nan, tayi sauri tayi saving ɗin sa a gmail ɗin ta, dan kar ya ɓata. Kamar ta turawa Sumayya, sai kuma ta fasa. *** Ramma na kan dining tana karyawa, ta jingine waya tana kallon Abdul da shi ma karyawa yake yi. "Rahama kin taɓa gaishe ni kuwa?" "Waye ɗi na kai da zan gaisheka?" "Your life saver mana, yadda na ceci rayuwarki, da ki ka kusa mutuwa" "A'a da ka sha giya dai ka kusa kashe ni" Ya sosa kansa ya ce "Ke abu ba ya wucewa ne, sorry mana" Ta harare shi ta ce "An ƙi ayi sorryn" Ya kashingiɗa ya ce "Ɗan cire hannunki, na din ga gani sosai" Cikin rashin fahimta ta ce "Ka ga me?" Ya ɗaga girarsa yana nuna mata ƙirjinta. "Wallahi Abdul ka ɗuma asara, kai a duniya abu ɗaya Allah ya saka maka a cikin kanka ne? Haba mana" "Future governor ki ke gaya wa haka? Zan fa hanaki first lady, kodayeke wadda zan aura ce zata zama first lady, ke kuma maid ɗin ta" tayi shiru, tana tauna cornflakes. "Ki lallaɓa ni na dawo da wuri" A fusace ta ce "Kar Allah ya sa ka dawo ɗin, in sha Allah ka tafi kenan, ko jirgin ya faɗi, kai kaɗai ka mutu" Yayi dariya ya ce "Kin ga sai ki mutu kekaɗai a gidan nan ba, dan babu wanda ya san na ajiye ki a ciki. Gara ki yi sauri ki janye addu'ar ki, idan kina son ki fita" Ajiye kofin tayi, ta fashe da kuka, har da sheshsheƙa. Ya ce "Is ok, ke ce ba ayi miki abu, sai ki yi ta tsine mini, ina jin pain fa, am sorry ya isa haka, haba your excellency" maimakon ta yi shiru, sai ma ta ƙara sautin kukan, nan da nan ya rikice, ya hau bata haƙuri, amma tayi disconnecting kiran, ta cigaba da kuka. Ta ɗauki wayar, tun da ya tafi, take gwada kiran lambobi daban-daban, amma ba ta tafiya sai ta sa kawai. Ta dudduba ko ina, ko da hanyar da za ta iya guduwa, amma babu ga wata irin kewar mama da sani ƙaninta da take yi. Su liti tamkar za su yi hauka, gaba ɗaya suka rikice, da Viper bai kwana a gida ba, duk in da suke tunanin za su ganshi ba su same shi ba. Har gidansa Walid ya je, ya haura ta katanga, ya shiga amma ba su same shi ba, gashi madakin da aka ce ya zo yana unguwar, shi ma yayi ɓatan dabo, an neme shi an rasa. Gaba ɗaya hankalinsu ya tashi, mussaman liti, amma saboda tsananin ƙi faɗi, yaƙi yarda ya karɓi laifin, Walid ya din ga yi musu luguden ashariya daga shi har ɗan mama, suka yi masa shiru suka ƙi kula shi. A sukwane Nabila ta tashi daga wurin aiki, bayan cin karo da batun faɗan daba a tsakanin yaran madaki da na Viper, sai dai babu ɗaya daga cikin su da ya zo hannu, tsakanin Viper da madaki, al'ummar unguwar na cigaba da zaman ɗar-ɗar, sakamon rashin tsaro. Ofishin Nasir ta tafi, babu sanarwa sai ganinta yayi, sai da hankalinsa ya tashi ya ce "Arfa lafiya kuwa?" Ta ciro wayarta ta nuna masa posting ɗin. Ya ce "To wannan ne ya saka ki ka taho har nan?" Ta ce "Eh, na yi zaton baka sani bane" Ya girgiza kai ya ce 'No, na sani" "To yaya ake ciki?" Ya ɗan tsareta da idanunsa sannan ya ce "Ni duk kin ruɗa ni, ko kece ke binciken nan, sai haka Arfa. Na je, sun yi faɗan daba, amma babu tabbacin yazo". "Baka kama shi ba kenan?" Ya jinjina mata kai alamar eh. "To ko yaran nasa ba ka kama ba?" "Lokacin da muka je, sun yi sun watse" wata irin ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ta yi, sannan ta ce "To shikenan, ai ban zaci ka gani ba, shiyasa na zo da kaina, bari na tafi" Nasir ya ce "Yanzu mussman ki ka baro aikinki ki ka zo kawo mini rahoto, arfa mai abun mamaki, zauna na gama abun da nake yi, na rage miki hanya" Ta ce "A'a yi aikinka, ina da wurin zuwa" ta lallaɓa shi ta fice. Sai dai hankalinta ya rarrabu kashi-kashi, voice ɗin nan da aka turo mata, babbar shaida ce da zata shiga kotu da ita da ƙwarin gwiwar ta. Abdul ya kira saif a waya, ya tambaye shi yaya ake ciki ya ce masa "Wallahi Abdul babu labarin matar nan, duk wani bincike da yakamata na yi na yi, amma shiru babu labari". "Lahaula wala ƙuwwata illa billa, Saif akwai matsala me zan ce wa yarinyar nan idan ta gano mahaifiyarta tayi ɓatan dabo, bayan babu irin magiyar da ba ta yi mini ba, a kan na mayar da ita" "To wannan kuma kai ta matsewa, tuntuni da ka san abun yi a kanta da duk ba a kawo nan ba" Abdul ya ce "Dole na gano in da mahaifiyar rayya take, idan ba haka ban san kalar tsinuwar da za ta yi mini ba" Saif ya ce "Ban gane tsinuwa ba, tsine maka take yi?" "Manta kawai" ya kashe wayar, ya din ga kiran wayar ramma, saboda tun jiya da safe da tayi kukan nan, ba ta sake ɗaga wayarsa ba, hankalinsa yayi mummunan tashi, ya fara tunanin ko wani abun ne ya sameta, kar ya je ta yi wa kanta illa, dan da wuƙaƙe a kitchen, kuma tana yawan iƙirarin cewa zata kashe kanta. Kusan awanni ashirin da huɗu suka shuɗe, Nabila ba ta samu Viper a waya ba, can ɓangaren su Walid ma, hankalinsu ya kasa kwanciya, saboda yawon neman Viper. Har ta je wurin aiki, ta kasa sukuni, kawai ta yanke shawarar zuwa gidan da yake. Tana sauka daga abun hawa, wata mota ƙirar helux baƙa, ta fito daga hanyar, duk da wurin mota ba ta iya bi, tayi ta tunanin yaya aka yi mota ta bi ta wurin, ta ƙarasa gidan, tun a tsakar gida take sallama, amma shiru babu wanda ya amsa, ta nufi ɗakinsa, ta ganshi a kwance a kan katifa, gefensa ga wuƙarsa da wayarsa da ledar magunguna, yana sanye da riga baƙa armless, da dogon wando shi ma baƙi, ga damtsensa an yi masa ɗinkin rauni, da sauran wurare a jikinsa. Cikin hanzari ta ƙarasa tana faɗin "Subhanallah" "Viper meyasameka?" Sai dai kamar gawa, ta ƙare masa kallo, an yi masa askin uwar sumar da take kansa, an yi masa gyaran fuska tare da rage masa gashin da ya taru a fuskar sa. Yayi wani irin ƙayataccen kyau, hatta kayan jikinsa ba ƙaramin kyau suka yi masa ba. Wayarta ta ciro ta din ga ɗaukarsa a hoto. Ta daddaki gefen katifarsa ta ce "Viper, bacci kake yi ne? Garin yaya ka ji raunuka haka?" Sai dai shiru ko motsi baya yi. "Me ka sha har haka ne? Ko sai na ce Master zaka tashi?" Babu tsammani ta ga yana motsawa a hankali. "Madarata" Nabila ta ce "Too yau kuma?" Yayi murmushi idanunsa a lumshe ya ce "Ai a duniya babu wanda ya raina ni, daga ke sai Walid, kin daina jin tsorona gaba ɗaya zan kama ki ne" murmushi yake yi sosai, wanda hakan ya bayyanar da tsantsar shauƙi da soyayyar da yake yi mata. Surutansa ya cigaba da yi ya ce "Yakamata na gaya miki wani abu, da yakamata ace kin sani, amma sai kin haihu tukuna, saura kuma ki isheni da tambaya na san halinki" ya buɗe idonsa a hankali, ya kalli Nabila da ta zuba masa ido, ya miƙa hannunsa ya riƙo nata ya ce "Zan gaya miki me na je yi Lagos ne" sai kuma ya saki hannunta yana girgiza kai. "Laaa, ke ya aka yi ki ka dawo da shi, Walid ƙaraso ka ga" liti yayi maganar yana shigowa ɗakin. Gaba ɗaya su ukun suka shigo, suka kewaye ta. "Da gidan uban wa ki ka kai shi?" Ta kalli Liti ta ce "Kamar yaya?" "Gidan uban wa ki ka kai shi?" A ƙule ta ce "Gidan ubana, tayaya zan iya ɗaga wannan shirgegen ƙaton" "Ƙarya ki ke yi haɗa baki aka yi da ke aka ɗauke shi, wannan kayan na jikinsa ma ba nasa bane ba macuciya" Walid ya ce "Ya isa dan Allah, Barrister nemansa muke ko sama ko ƙasa bamu ganshi ba, a ina ki ka gano shi?" Ta ce "Wallahi yanzu na zo, bana samunsa a waya, yanzu na zo kawai na tarar da shi a kwance, wallahi ban san ma neman sa ku ke yi ba, duba wayarsa zaka missed calls ɗina da yawa. Amma dai naga wata baƙar helux ta fita daga hanyar nan, ban san ta ina suka biyo ba, na riƙe lambar motar a kaina" Walid ya ce "Karki damu, na yadda da ke" "Wallahi mai laya, ka cigaba da sakankancewa da yarinyar nan, sai tayi dalilin an kashe ku tukuna" Liti ya ƙarasa gaban Viper ya durƙusa a kansa, cikin zafin nama, viper ya danƙi wuƙarsa ya saita ta a cikin liti yana wani irin huci. Liti ya buɗe baki ya ce "Ni zaka sa wa russia Viper?" A hankali ya ƙara buɗe idonsa, ya hankaɗe liti gefe ya ce "Na zata madaki ne" sai kuma ya kalli jikinsa, ya kalli kayansa, ya kalli damtsensa ya ga ɗinki, ya kalli Nabila ya kalli ɗakin ya ce "Ke a ina muka rabu da ke?" Ta ce "A titi, bayan ka dire daga adaidaita sahu". "Me ki ka yi mini?" Nabila ta ce "Au kaima ni ka ke zargin na sace ka kenan?" Walid ne ya yi masa bayanin abun da ya faru, ya lalubi wayarsa da sauri yana duddubawa. "Don't endanger your life again, madaki is still not your mate, da sauran lokaci" ya ajiye wayar ya sunkuyar da kansa, da yayi masa nauyi yana tuno abun da ya faru a ranar. Nabila ta kalli Walid ta ce "Yay walid, yayana yana zuwa wurin sayar da shayinku, kuma akwai jami'ansa a farin kaya suna zuwa, kayi taka tsantsan, yanzu aikinsa a kanka yake. Kuma ka kula da wanda suke zuwa wurin sosai, kar wani information yayi leaking a wurin" Liti ya ce "Munafuka, wadda take kwarewa ɗan uwanta baya ne, ku ke tunanin kuma ba zata bar ku ba wataran. Shegen yayan naki azzalumi, ƙugu kamar gatari" Nabila ta ce "Allah ya isan sa, kuma ni ba munafuka ba ce, kuma wallahi idan baka kiyayeni ba, zan kuma sakawa a kama mini kai, sai igiya tayi saura" tayi maganar tana hararsa ta ɗauki jakarta. Ta durƙusa a gefen Viper ta kai bakinta, kunnensa ta ce "Viper, zan tafi zan je wani wuri, zamu yi waya, ka samu ka ci abinci, kar ka takurawa kanka da tunani da yawa, kar ka sha ƙwayoyin da za su yi maka illa. Saboda muna son ganinka cikin ƙoshin lafiya da ni da 'yar madara, na ji ka ce zaka gaya mata wani abu, to nima sai ka gaya mini, tun da nice amarya. Kayan nan sun yi maka kyau sosai da sosai, ka ci abinci kayi salla ka huta, ka bar wayarka a buɗe zamu yi magana dan Allah, ka yi mini addu'a zan cigaba da shari'a da su bunkure, take care dear" ya ɗaga kai ya kalleta, taƙi kallonsa tayi waje. Liti ya ce "Makira, duk makircinki sai ya koma kanki". Ta galla masa harara ta tafi. *** Abdul yana ta kiran ramma, har ya fitar da ran zata ɗaga, yaji ta ɗaga muryarta ƙasa-ƙasa. "Bacci ki ke yi ne?" Ta ce "Eh" "Eyya sorry na tashe ki, nake ta kiranki a waya amma ba kya ɗagawa, lafiya dai ko?" "Haushinka nake ji ne, zan iya ɗuɗɗura maka ashar, shiyasa bana ɗagawa" Yayi dariya ya ce "Yanzu kin huce?" "Eh" "To masha Allah, kin tashi lafiya?" "Eh" "Duk muryarki wani iri, anya lafiya kuwa?" Ramma ta ce "Ba wani lafiya, ni na gaji da zaman gidan, nikaɗai kamar mayya sai tv da haushin karnuka, ni ba prisoner ba". Abdul ya ce "To yanzu ya ki ke so ayi?" "Ni koma yane ayi" Ya ce "To shikenan, zan dawo gobe in Allah ya kaimu" "Ba sati ka ce zaka yi ba?" Ya ce "A'a hankalina yaƙi kwanciya ne, zan dawo gobe in Allah ya kaimu " Ramma ta ce "To Allah ya tsare" "Kin fasa in faɗi a jirgin, kar in dawo?" "A'a jirgin ya faɗi kai kaɗai ka mutu" "Muguwa ba Amin ba" "Ban kai ka mugunta ba ai" Yayi dariya ya ce "Sai anjima". *** Washegari ya kama ranar da Nabila zasu cigaba da shari'ar mai gadi, ta shiga office ɗin ta, ta tarar da wani file a ajiye a kan teburinta, har ta fara masifar na meye wannan aka ajiye mata a kan tebur. Ta nemi wuri ta zauna, ta ɗauki wayarta, ta shiga social media ta rubuta, kuraye masu fatar akuya, an kusa walƙiyya mu ga kowa" ta yi tagging ɗin Naja bunkure.Washegari ya kama ranar da Nabila zasu cigaba da shari'ar mai gadi, ta shiga office ɗin ta, ta tarar da wani file a ajiye a kan teburinta, har ta fara masifar na meye wannan aka ajiye mata a kan tebur. Ta nemi wuri ta zauna, ta ɗauki wayarta, ta shiga social media ta rubuta, kuraye masu fatar akuya, an kusa walƙiyya mu ga kowa" ta yi tagging ɗin Naja bunkure. M karofi ya kirata, ya din ga yi mata surutu, da neman ta bashi damar zuwa gidansu, ta ce masa yanzu aiki take yi, bayan sun yi sallama, ta ja file ɗin tana dubawa. Sunan Naja'atu Bunkure ne a sama, sannan aka fara bayanin tarihin rayuwarta tiryan-tiryan, har zuwa fara aikinta, yadda ta taso cikin rayuwar ƙunci da wahala, yadda ta zama lawyer, bayan fyaɗe da aka yi mata da ƙanan shekaru, gaɓar da Nabila ke son ganin meyafaru, a nan aka tsaya. Ta daki tebur, ta din ga jujjuya file ɗin tana tunanin waye wannan ya kawo mata file ɗin nan, da kyar idan ba shi da alaƙa da wanda ya tura mata voice message ɗin nan. *** DSP Nasir yana zaune yana rarraba ido a ƙaton falon, da ko ina sanyin A.C ne ke ratsa shi. Babu tsammani mutumin ya fito, ya samu wuri ya zauna, cikin girmamawa Nasir ya ce "Barka da wannan lokaci sir" "Yauwwa barka, DSP Nasir Yusuf maitama, ɗan uwan barrister Nabila Yusuf maitama" ya ɗago ya kalle shi. "Na san zaka yi mamakin kiran da nayi maka ko?" Nasir "Ƙwarai sir, na san ni dai babu wani abu da ya taɓa haɗa ni da kai, amma ka saka a nemo ni, kuma ga sunana ka kama, da na ƙanwata" Indabo ya gyara zamansa ya kalli Nasir ya ce "Nabila!" Cikin rashin fahimta ya ce "Me tayi?" Ayshercool 08081012143 55 🔞₦500 ne via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143 Wanda za su jira document 1K ne. 90009343 'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa Arewabooks ayshercool7724 Cikin rashin fahimta, Nasir ya ce "Amma Yallaɓai me tayi ne?" Indabo yayi murmushi ya ce "Bari mu ɗan ajiye batun ta a gefe. Aminu Viper, wanda aka fi sani da mai zamani a baya, kai ne incharge of bincike da ƙoƙarin kama shi haka ne?" Ya jinjina kai ya ce "Eh sir" "Na san kana fuskantar matsin lamba, daga wurin na sama da kai, a kan lallai ka kama Viper. Duk da abun mamaki ne, a baya yana tsare a prison lokaci guda yayi ɓatan dabo sama da shekara guda ana nemansa". Nasir ya ce "Haka ne sir" Indabo ya sassauta muryarsa ya ce "Akwai jiƙaƙƙiya tsakanina da Viper, wanda barazana ne ga siyasata da mutuncina. Saboda haka na yanke shawarar yin gaba da gaba da kai mu tattauna wataƙila kafi bawa aikin muhimmanci, tun da na samanka kawai nake gani, kai bamu taɓa haɗuwa ba, kuma Alhamdilillah sai na yi sara a kan gaɓa" ya ajiye masa wata jaka ya ce "Ga wannan ka sha mai, sannan akwai fuloti mai rai da lafiya a unguwar tudun yola da takardunsa a ciki, wannan zai zama wani ɗan hasafi, ko in ce ihsani domin ƙara maka ƙwarin gwiwa, idan aiki ya kammala, ina da kyakykyawan Albishir gareka, muddin Viper ya zo hannu, ko ma ya bar duniyar baki ɗaya ina da ƙarin Albishir gareka. Ɗana na shirin zama deputy governor a garin nan, zaɓe mai zuwa. Kuma ka san kujerar da nake kai, ka san ma'anarta. Zan iya yi maka alƙawarin zama CP na jihar nan, kai koma na yi maka babban muƙami a ƙasa. Akwai kyautar mota irin ta sanatoci, da gwamanti kan yi gwanjon su, gida ko fili sai wanda ka zaɓa. Kar ka yi dogon tunani, ba wai cin amanar ƙasa zaka yi ba, taimakon kai da kai

Chapter 57 of 121