"Na sani, na kuma fahimce ka, amma hakan babu abin da zai canza. Addu'a da ci gaba da jajircewa ce kawai za ta kawo mafita, ka yi haƙuri dan Allah Vi ka saka wani abu a cikinka" ya ƙura mata ido na wani ɗan lokaci, kawai ya tashi tsaye ya ce "Idan kin gama ki same ni a mota" sosai tausayin sa ya mamaye mata zuciya.
Jiki a sanyaye ba tare da ta samu ta yi breakfast ɗin ba, ta bi bayansa.
Da suka kai ta wurin aikin ma, har ta shiga ta ji kamar ana bin ta, ta waiwaya ta ga shi ne ya biyota. Ba ta ce masa komai ba, ta shiga office ɗin ta ya bi bayanta.
Kujerar cikin office ɗin ya samu ya zauna, bai kulata ba, ita ma ba ta ce masa komai ba, ta ci gaba da aikinta, gani yake yi yana kawar da kai, wani abun zai sameta ita ma.
Har ta gama aikinta na ranar yana zaune, sannan Liti ma ya saka an mayar da shi cikin barrack.
Duk yadda ya bi wayar Indabo abu ya gagara, sai taƙi shiga, gashi gani yake yi kamar babu wani ƙoƙari da ake yi a kan neman Walid ɗin.
Kwatsam Nabila na shirye-shiryen tafiya, ya sake jarraba wayar Indabo, cikin sa'a ta shiga kuma ya ɗaga, Viper ya miƙe cikin zafin rai ya ce "A karo na ƙarshe, ina Walid yake?"
"Babu wata barazana da zaka yi mini Viper, sharuɗɗa zan saka maka, wanda dole sai ka bi su. Na farko ka saka wannan yarinyar ta janye ƙorafin da ta shigar a kan Bunkure a ma'aikatar Shari'a, sannan ka tattaro duk wani bincike da ka yi a kaina, na yinƙurin tona mini asiri, da wannan wayar da ka ke amfani da ita ka bani, sai a saki Walid, idan ba haka ba wannan banzar yarinyar ita ce next target ɗina a kanka, sai na saka an wulaƙanta ta, wulaƙanci mafi muni na tagayyara rayuwarta, fiye da yadda ka ke tunani" Viper ya ɗaga kai ya kalli Nabila da take kallonsa, amma ba ta san me ake cewa ba.
Viper ya ce "Saboda abin da nake shiryawa a kanka ne ya sanya ka kashe P.A?"
Indabo ya ce "Eh, ban damu da a in da ka samu labarin hakan ba, iyaka na san ba ka da wata cikakkiyar shaida a kan ni ne kashe shi, duk wanda ya ci amanata, sai na kawar da shi. P.A ya ci amanata ya haɗa kai da kai, domin yana ganin ya zame ya bar ni shi ne zai sanya ka ƙyale shi".
Viper ya sauke numfashi mai zafi, cike da dana sanin, sanin Indabo a rayuwarsa ya ce "Idan kuma ina da shaidar kisan kan da ka yi wa P.A da hannunka fa?"
"Gwargwadon yadda ka ci gaba da zurafafawa, gwargwadon yadda zan ci gaba da hura wutar da ka ke ciki, ba dai kana yi wa kanka iƙirarin ƙarfen cikin wuta ba, idan ba zaka ɗakku da hannu ba, zan ci gaba da iza wutar da ka ke ciki, sai ta kai matakin da zata narka ka"
Viper ya datse laɓɓansa na ƙasa, ya fesar da wani zazzafan numfashi, ya ce "A ina zan kawo maka abin da ka buƙata?"
"Zan turo maka adireshin wurin, kuma ba kana bayarwa za a sake shi ba, sai na ba wa ƙwararru sun tabattar da ingancin abin da ka bayar, kuma a yau ba gobe ba, yarinyar nan ta janye maganar Bunkure"
"Na ji, zan yi abin da ka ce, amma yarjejeniya ɗaya idan ka saɓa, wutar da kake ƙoƙarin narkani da ita, kai zata ƙona" Indabo ya katse kiran.
Viper ya kalli Nabila, ta ce "Vi wai lafiya?"
"Zamu je ma'aikatar shari'a, ki janye ƙorafin da ki ka shigar a kan Naja'atu Bunkure"
A razane Nabila ta ce "Saboda me?"
"Saboda haka na ce" yayi maganar a fusace.
Nabila ta ce "Akwai dalili dole, ka gaya mini, idan ba haka ba zan iya janyewa ba gaskiya, gaba ɗaya wahalata a kan lamarin matar nan na ɓata lokacina, kawai kuma sai na janye?"
"Sai kin janyeta, babu wani bayani da zan yi miki, dolenki ki janye" yayi maganar yana kallon Nabila, yana hasko cikin bala'i da tashin hankalin da zai shiga, idan aka taɓa ta.
****
Goye yake da Jaka a bayansa, a dajin Allah shikaɗai, sai waige-waige yake yi.
A kan babura da manyan bindigu, wasu mutane suka ɓullo, suka zagaye shi.
"Ka ajiye jakar, ka ɗaga hannayenka sama" wani yayi masa umarni.
Ya ajiye jakar, ya ɗaga hannayensa, ɗaya ya karɓi jakar, ya zazzage, ya dudduba ya ce "Kayan ne"
Wani daga cikinsu ya ce "Za a aika shi ne?"
"A'a kai ba a ce ba, jami'i ne, asirinmu zai iya tonuwa, mu ware kawai".
Suka ja baburansu, suka yi gaba, suna tafiya aka turo masa saƙo.
"Ke je dutsen da yake in da kuke, ka ɗauki gawarsa" kamar mahaukaci, haka Viper ya sake gigicewa, daga in da aka saka shi kai kayan, bai isa in da Walid yake ba, sai bayan awanni uku.
Yana zuwa ya lura da ba a lokacin aka yar da shi a wurin ba, kamar ya kwana a wurin, an ɗaure masa hannu da ƙafafuwa, an tura masa tsumma a baki, an ɗaure wuyansa da wayar cable, ga jikinsa ko ina a farfashe saboda duka.
Fuskarsa ta kumbura suntum, duk jini, ƙanan ƙwari sai bin sa suke yi.
Kamar yaro ƙarami, Viper ya fashe da kuka yana kwance Walid, ya kwance wayar da take wuyansa, ya ɗaga shi yana kuka, yana kiran sunansa.
Ya ƙanƙame shi a jikinsa, kawai ya ji zuciyarsa na bugawa, a hankali.
Zumbur ya miƙe, yana ambaton Allah, ya goya shi a bayansa, gani yayi idan ya tsaya buge-bugen waya, zuciyarsa zata daina bugawa, haka ya kwashi tafiya, har rukunin kamfanunnukan nan, ya ce su taimaka masa su kai Walid Asibiti.
Kai tsaye barrack ya tafi da shi, ya kai shi asibitin cikin bariki, babu wani jinkiri aka rufu a kansa, yana da rai bai mutu ba, sai dai babu tabbacin ya tashi.
Duk da Nabila tana cike da ɓacin rai da damuwar sakata janye ƙorafi da yayi, ba tare da ya yi mata bayanin komai ba, amma tana ganin saƙonsa na yana Asibitin cikin barrack tare da Walid, ta tashi tana tsuma, ta saka hijjabi ta fita.
Yanayin da ta ganshi ne ya karya mata gwiwa. Ta ce "Vi ya ake ciki?"
"Yana ciki sai dai babu ya rayu" yayi maganar yana zubar da hawaye.
"Kayi haƙuri vi, ka kwantar da hankalinka, in sha Allah Walid zai tashi da ikon Allah"
Sai ita ta kira su Alhaji mu'azzam, da Liti ta sanar musu an ga Walid.
Babu jimawa wurin ya ɗinke da jama'a.
Hatta Abbu yana wurin, Shahida ma kasa zama tayi, sai da ta biyo Abbun.
Abbu sai shi ya kama hannun liti, yana ta rarrashin sa, gaba ɗaya ya firgice, an tuɓe Walid daga shi sai gajeren wando, duk jikinsa shaidar duka, aka yi dressing ɗin raunukan jikinsa, aka ɗebi jininsa ana ta gwaje-gwaje.
Duk wani abu da za a buƙata wurin bincike, sai da suka ɗauka, kafin a taɓa shi.
Ɗaya daga cikin likitocin ya fito, ya ce "Ku kwantar da hankulanku, Alhamdilillah. He's responding to treatment. Vitals ɗin sun dawo normal, in sha Allah muna saka ran ya farka a kowane lokaci. Idan ya farka zamu tura shi sauran gwaje-gwaje.
Sai a lokacin suka ɗan samu nutsuwa.
Cikin dare aka kira Viper wurin ogansa, Ya sha faɗa a kan abin da ya yi ba tare da ya sanar musu ba. Shi dai yayi shiru, dan a halin da yake ciki, babu umarnin wanda zai iya tsayawa saurara, ya sha faɗa duk da yayi bayanin abin da ya faru a yanzu.
Ya numfasa ya ce "Jami'anmu sun tafi, za su dawo da wayar, duk wanda aka kama da wayar ɓatar da shi zamu yi, cin amanar ƙasa da ƙoƙarin tonon asiri ne, duk wanda aka kama da wayar ba jami'inmu ba" Viper dai yayi shiru, domin an ce ya saurari punishment ɗin da za ayi masa.
****
Sai da Walid ya kwana a Asibiti, ya wayi gari, sannan ya motsa ya farka.
Liti ne ya ga ya motsa hannunsa, ya tashi da sauri, ya nufe shi yana zazzare ido yana kiran sunansa.
Walid ya buɗe ido ya kalli Liti, ya yinƙura zai tashi Liti ya ce "Kai kar ka tashi, a asibiti kake"
Ya ɗaga kai yana kallon ɗakin, Viper ya ƙaraso, yana cewa "Mai laya, kalleni ka gane ni?"
Murmushi ya yi ya ce "Na kiyayi mai zamani"
Viper ya rasa me ma zai yi dan farinciki, ya zuba masa ido, yana haɗiye ƙwalla.
"Na kasa tashi ku ɗaga ni"
Viper ya sako hannu ya ɗago Walid, sai da ya yi ƙara saboda ji yayi kamar su na kakkarya shi.
Liti ya ce "Wai dan Allah meyafaru, suwaye suka ɗauke ka?"
"Jama'ar Indabo ne, wai sai na gaya musu abin da Viper yake shiryawa a kansa. Na ce ban sani ba, na daku tun da suka ɗauke ni, a ɗaure nake, sai ranar da suka shaƙe mini wuya da cable na zata mutuwa ma nayi wallahi"
Viper ya ce "Muhsin, ka yi haƙuri, duk ni ne sila ka yafe mini dan Allah"
Walid ya ce "A'a rashin jinmu ne dai sila"
Likitoci sun yi mamakin ganin Walid a zaune yana ta magana.
Sai dai aka yi masa wanka, aka saka masa kaya, ya ci abinci, aka je aka yi masa hoto, aka tarar da karaya a hannunsa na dama.
Da yamma Viper yaje har gida, yake gaya wa Abbu yanayin jikin Walid, suka yi ta murna, Shahida tana son ta ce masa tana son sake zuwa duba Walid, amma ta kasa.
Babban abin da ya tsaye mata, bai wuce jin yadda yake bawa Abbu labari cewa Walid ba shi da uwa ba shi da uba, ba wa ba ƙani, shikaɗai yake gararambarsa, dangin iyayensa ba masu zuciya bane ba, duk ba su da ƙarfi, amma babu wanda ya damu da shi a cikin su.
Lokacin da Viper ya yi wa Shahida tayin auren Walid, ita dai ba ta ji tana son shi ko akasin haka ba, amma abin da Viper yake gaya wa Abbu, na cewar maraya ne gaba da baya, sai ta ji wani irin matsanancin tausayinsa, ya cika mata zuciya. Ta ji zata iya kowace irin sadaukarwa, domin rayuwa da shi.
Sai dai ta sha mamaki jin cewa wai har ya farfaɗo ya tashi yayi magana, dan lokacin da ta je, baya cikin hayyacinsa.
A cikin daren ranar, aka yi wa Walid ɗori a hannu, wajen ƙarfe biyu aka fito da shi, liti ya ce Walid sai ya matsa masa saman gadonsa sun yi squating, tun da shi ne zai kwana da shi, kar yaje yana bacci a zo a sake sace shi bai sani ba.
Abin ka da an kwana biyu babu bacci, yana hawa gadon, sai bacci, Walid kuwa zugi ya hana shi bacci, tun bayan da alluran da aka yi masa suka sake shi.
Da Viper ya zo ya tarar da su, fizgo liti ya so yi daga kan gadon, amma Walid ya hana shi.
Duk wata sangarta da rashin mutunci, idan suna tare liti ya iya ta, amma idan aka fita fagen rashin mutunci na 'yan daba, babu wasa.
Viper ya ce "Shahida na gaisheka, ta ce ayi maka sannu"
Kawai yayi murmushi yana kawar da kansa gefe.
"Au ba zaka ce kana amsawa ba? Aishikenan. Ni dai ina ta sake yi wa Allah godiya, da Allah sa ka farfaɗo, da ka mutu ba zan yafe wa kaina ba, kuma da tarayyar mu, ba ta da wani amfani, Allah ya ƙara tsare mini ku, ya baka lafiya".
Walid ya ce "Tarayyar mu tayi mini rana ni, Viper nifa abin da ka yi mini, ban ga wani abu da zai sameka na ja da baya na barka, babu shi. Ka yi mini da aljihunka da jikinka, da lafiyarka babu wanda baka wahalata mini....
"Ka daina wannan maganganun, bau ne past ya riga ya wuce, kuma ni mahaifiyarka tawa ce, a haka na ɗauki abin"
Yayi murmushi ya ce "Mai zamani, wanda zai tsaya maka, a lokacin da baka da komai, ka ke neman taimako, ba tare da tsangwama ko tunanin samun wani abu daga gareka ba, baka da babban masoyin da ya wuce shi, shiyasa da kai da mai gida dodo, ba zan gushe ba ina yi muku fatan alkhairi, da roƙa mana gafarar Allah"
Viper ya ce "Nima hakan take ai, a duniya yanzu bani da tamkarku, da kai da wannan garujen" yayi maganar yana nuna liti.
Walid ya kalli liti yana dariya.
"Ya fi ni shiga tashin hankalin rashin ganinka, baya bacci, baya iya cin abinci wai ina zai saka kansa, babu kai ɗan mama" dariya suka yi tare, liti kuwa bai san suna yi ba.
****
Ƙaton ɗaki ne babba sosai, ɗauke da computers, da wasu na'urori, Viper yana zaune a kan computer da shi da wasu a cikin wurin.
Wani video ya kunna, aka saita a jikin majigi, Videon babu murya, amma Imdabo ne a ciki, yayi wasu maganganu, P.A yana ja da baya, kawak ya harbe shi sau uku da bindiga.
Viper, mutumin nan yaƙarsa sai da techniques, ba za su taɓa bari a hukunta shi a cikin ƙasar nan ba, ya aka yi ka samu Videon?.
"Eh kamar yadda na gaya maka da farko ne, P.A ɗin sa ne ya samo mini wasu informations ɗin a kansa, saboda a zaman kotu ya ɗauka za a ambaci sunansa, yayi hakan da a wanke shi.
Lokacin da Indabo ya buƙaci ganinsa, na bashi cameran, na ce ya saka a gaban rigarsa, zan din ga ganin komai, ni kaina ban yi zaton zai kashe shi ba".
Mutumin ya dafa kafaɗar Viper ya ce "Ka kwantar da hankalinka, na san yadda ka ke ji a zuciyarka a kan mutumin nan, kuma na san legally ba zasu hukunta shi ba, tun da yanzu ayi shiru da maganar tuhumar da ake yi masa. But you have my support hundred person, either legally or illegally sai mun ɗauki mataki a kansa. Saboda ba shi da amfani a cikin al'umma ko kaɗan, da kunya ace irin wannan ne suke mulkar al'umma, amma ba wani abu in sha Allah"
Cikin damuwa Viper ya ce "Sir na baku recording na wayar da muka yi da shi, yarinyar da zan aura, tana cikin hatsari sosai da sosai, ban san me zai iya yi mata ba, ba zan iya jurewa ba idan ya taɓa ta, ga aikinta da ta sha wahala a kai ya salwanta"
"Bai salwanta ba Viper, kuma ina baka tabbacin babu abin da zai sameta, babu kuma abin da zai samu wani naka, kar ka damu" Viper ya jinjina kai yana jin ƙwarin gwiwa.
Asibiti ya koma wurin Walid, ya tarar da Shahida, ta yayyanka masa ayaba a kan plate, ta ajiye masa yana ɗauka da hannun hagu yana ci, yana ganin Viper ya zabura, kamar wanda yake aikata rashin gaskiya, sai da Viper ya so yayi dariya, amma ya maze.
A haka Nabila ta zo ta tarar da su, tayi masa sannu, Walid yayi ta yi mata godiyar suna ɗawainiya da shi.
Nabila ta ce "Vi ai su suka sha ɗawainiya, dan Allah tun da ka farfaɗo ka saka shi ya ci abinci Please, haryanzu baya mayar da hankali, duk ya rame. Ya fi yi mini kyau lokacin da kumarinsa"
Walid ya ce "Vi an ce ka din ga cin abinci ka rame"
"Zan zageka da kai da Vi ɗin"
"Allah ya baka haƙuri, an hanamu faɗar master, Vi ɗin ma an hanamu, to ai shikenan"
Nabila ta rausayar da kai ta je bayan Viper ta yi ƙasa da murya ta ce "Zamu je ganin likita kar mu makara fa" ɗagowa yayi ya kalleta, kamar ba zai tashi ba, sai kuma ya tashi ya nufi hanyar fita.
Fitarsu ke da wuya ya tsaya cak, ya waiwayo ya kalleta ya ce "Kar ki sake ƙoƙarin yi mini yawo da hankali, ko kuma nuna kin damu da ni, bana son yaudara" yayi maganar yana nunata da yatsansa.
"I don't fake it, kai baka san halin da ka saka ni ba, lokacin da na nuna maka so saboda Allah. Na ji da farko i fake it, daga baya kuma da gaske na ƙaunace ka Vi, yakamata ƙwaƙwalwarka ta tunatar da kai, abubuwan da ka yi mini, kuma ka gaya mini. A gabanka abokinka har ce mini yayi bani da class, ina yawo a cikin maza, duk dan ina sonka, ina fatan daga kaina, zaka din ga kiyaye abin da zaka gaya wa mace, mata bama mantuwa.
Duk motsin da nayi ban taɓa burgeka ba, kullum cikin kyarata ka ke yi, amma haryanzu ina yi maka kallon abu mai muhimmanci a gareni, mussaman kulawar da Jauhar ta samu a wurinka, ka yi mini afuwa Vi, bana fatan ƙuntata zuciyarka".
Cikin tsananin dakiya da jarumta, ya jinjina kai, ya ce "Na fahimta"
Duk yadda ya so cire Nabila daga zuciyarsa abu ya gagara, sai a lokutan nan, da ta fara yi masa wulaƙanci ya ga ashe ya shaƙu da ita, shaƙuwa ba ta wasa ba.
Cikin ikon Allah Walid ya samu kulawa sosai da sosai, gashi ba shi da ƙan jiki, nan da nan jikinsa ya fara warkewa, sai dai ya kan manta da ba shi da lafiya, idan yana riƙe da wayarsa, Shahida tana turo masa saƙonnin, babban abin da ya ƙara yi wa Shahida daɗi, ita kanta kunyarta Walid yake ji, balle yayi kule-kulen mata, saɓanin mijin da ta rabu da shi, saboda yana da kuɗi, yan mata kowa ma kulawa yake yi, kishi kamar ya kasheta, gashi ba abin da yake iya amfana mata.
***
Sallamar da ake ta dokawa a tsakar gida ne, ya sanya dattijon mutumin, sauke farin tabarau ɗin fuskarsa ya ce "Waye ne?"
Ya bankaɗo cikin ɗakin ya ce "Nine, ko har an manta da ni ne, nake ta sallama aka yi shiru?"
Dattijon ya ce "Ina fa, waye ya isa ya manta da sarkin gida? Maraba lale da Abdallah"
Liti ya ƙarasa ya na faɗin "Likkafa ta ci gaba, gida ya sha gyara"
"Yau kai ne a gidan ka tuna da mu kenan?"
"Ai kullum kuna raina, na san ina zuwa dattijuwarka za ta tayar mini da hankali, ta saka ka kore ni"
"Hmm sannu, na samu labarin ɗaya uban naka yayi free, kotu ta wanke shi ko?"
"Aiba shikaɗai ta wanke ba, har mu, ai bamu da wata nutsuwa idan yana cikin damuwa. Ban ga tsohuwar nan ba, ko ta rasu"
"A'a ni uwata ba ta mutu ba, tana nan ƙalau, sun fita da gyatumarka"
Liti ya ce "Lallai ta sha miya, amm Alhaji, dama na zo baƙi ne, wata bazawara ce take so na, shi ne ta turo iyayenta, suka zo nema mata aurena wurinka, tana fatan zaka bata ni"
"Ikon Allah, ita bazawarar"
"Eh, amma dan Allah kar ka yarfa ni, ko ka tona mini asiri ka ce wai ba na ji, abu ne da aka yi shi ya wuce, yanzu na shiryu na daina, dan Allah kar ka ce musu wai bana ji, kaga sirikaina ne"
Alhaji ya yi dariya, ko bayan shekara dubu, Abdallah ba zai canza hali ba,duk da Ya lalace yana son abin sa, amma gwaggo mahaifiyarsa ke nema tayi masa baki, saboda soyayyar da yake yi masa, kuma hakan yana da alaƙa da tsanar da ta yi wa babar litin ya ce "To Baba, ba zan yarfaka ba"
Liti ya fita waje, yayi musu iso, Abbu ne tare da Baba, mahaifin jauhar, da kuma Viper.
Alhaji ganin Liti da manyan mutane, ya tashi ya karɓe su cikin girmamawa. Bai fi sau biyu ya taɓa ganin Viper, yanzu da kyar ya gane shi, saboda lokacin da ya san shi yana da ƙuruciya sosai.
Nan Abbu ya gabatar masa da kansu, tare da gaya musu abin da ya kawo su, a kan yayi haƙuri, ya yafewa Liti, tun da yanzu duk sun watsar da shirirtar da suka yi a baya, dama har da ƙuruciya.
Nan Alhaji yake sanar da su, yadda ya kai liti ƙasar waje karatu, amma ya dawo an koro shi, sai ma shaye-shaye da ya koyo, ga rashin kunya da yake yi wa kakarsa, wanda hakan ya ƙara tunzura shi a kan litin.
Viper ya ce "In sha Allah Alhaji, Abdallah ya shiryu ba zai sake ba, dan Allah ayi mana afuwa, ayi haƙuri"
Alhaji ya ce "Dama baku muke ƙi ba, halayenku ne ba ma so marasa kyau, Ubangiji Allah ya ƙara rufa mana asiri"
Nan kuma hira ta ɓarke a tsakanin su Abbu, tare da tattauna manyan matsalolin da ya jefa yaran nasu ga halaka.
Bayan sun gama da gidan su liti, suna tafe, tausayin Walid ya mamaye zuciyar Viper, su duk sun daidaita da iyayensu, shikuwa ba shi da kowa, sai Allah sai barbaɗaɗɗun danginsa marsa amfani. Yayi Addu'ar Allah ya sa Shahida ta rayu da abokin nasa cikin aminci da mutuntawa, mussaman da ya ga ya fara sakewa da Shahidan.
Maganar Baba ce ta dawo da shi hayyacinsa da ya ce "In sha Allah, gobe zan je gidan Major, mu yi wadda za mu yi, ya bani 'ya ta, na ƙarasa riƙonta na aurar da ita, na fuskanci bai san zuru ba".
Ayshercool
08081012143
101
Abbu ya ce "A'a Alhaji Bashir, abi komai a hankali, zamu je mu same shi sai a tattauna".
"Alhaji Ibrahim, na san na yi wa maitama laifi, amma yadda yayi reacting ban ji daɗin hakan ba. Gaba ɗaya ya tsaya mu fuskanci juna yaƙi, ya mayar da ni kamar maƙiyinsa nima fa a ƙa'ida yayi mini ba dai-dai ba".
Sai a lokacin Viper ya ce "Baba dan Allah ka yi haƙuri ku sasanta, wannan rashin jituwar taku, yana taɓa Nabila sosai da sosai.
Kuma haryanzu tana cikin barrack a zaune, ta rasa yadda ma zata yi dan Allah ku yi haƙuri ku sasanta".
Baba ya ce "Ba ƙi na yi ba Aminullahi, na bashi duk wata dama, a matsayin sa na wanda yake uba a gareta, kuma ya raineta, idan ya gaji ni ya bani abata, nima na rayu da ita ko yaya"
Viper ya ce "Haka ne, kana da gaskiya. Amma ka yi haƙuri dai, a bi komai a sannu, aje a same shi, ayi masa bayani, na san zai fahimta in sha Allah" haka Viper ya ci gaba da rarrashin sa.
Alhaji kuwa hira suka ɗora da Liti, kamar ba barin gida yayi, kusan shekara guda bai ganshi ba. Ya din ga bashi labarin gwagwarmayar da suka sha, da halacci da kirkin matar Viper, tare da ba shi labarin yadda Nabila ta shigo rayuwarsu, ashe 'yar uwar marigayiyya ce.
Sallama aka yi a tsakar gida, Alhaji ya amsa, Liti kuwa ya tsuke fuska.
Sai da mahaifiyarsa tayi turus da ta ganshi, ta ce "Abdallah yau kuma kai ne a gidan"
"Saboda ba sunan babanki bane ba, kuma ba sunan mijinki bane ba, shiyasa ki ke faɗar sunan yadda ki ka ga dama kamar ke ki ka raɗa masa, to sunan mijinki usmanu ki ka faɗa" tsohuwar da suke tare ta yi maganar a hasale.
Ta mayar da idonta kan liti ta ce "Sannu ɗan nema, kai kuma sai yau Allah ya dawo da kai, shanshani mai ƙafar gantali"
"An saka mini sunan kirki, saboda wani sunan mijinki, kin ɓata mini suna wani liti. Kuma nan fa ke ki ka saka aka koreni, ba dole na tafi ba, ni wallahi na zata ma kin mutu"
"Salamatu ce zata mutu ba ni ba, babarka ba"
"Kowa ma dai sai ya mutun nan, duk ƙulafucin mutum da duniyar kuwa"
Alhaji ya yi gyaran murya ya ce "Baba gwaggo ce fa, mahaifiyata ce" liti yayi shiru yana hararta.
Mahifiyrsa kuwa kallonsa take yi, ta zata tafiyar da yayi, zai sake lalacewa ne, dan abin yana damunta, amma sai ta ga kamar ya ɗan nutsu, babu askin banza, gashi normal shiga yayi, kuma babu alamar buguwa a tattare da shi.
Har yamma yan tare da mahaifinsa, saboda ya fi shaƙuwa da shi, yan uwansa duk mata ne suna gidan aure, shi ne kawai namiji.
Da yamma aka gama abincin dare, aka zuba masa, ya saka fulasan a leda ya ce tafiya zai yi.
Alhaji ya ce "Ina kuma zaka je?"
"Can in da nake mana Aljaji"
"Au sake barin gidan zaka yi?"
Liti ya ce "A'a, dama zuwa nayi ai na gani, idan zaku haƙura ku yafe mini to, idan kuma naga za a sake tozarta ni, idan na cika wandona da iska nayi gaba, in tafi ikko. Amma Alhamdilillah na ji daɗi da naga ba a hantare ni an koreni ba, wurin yan uwana zan koma, Walid ba shi da lafiya yana Asibiti, ni nake kwana da shi, amma zan dawo ai. Na gode sosai da ku ka yafe mini"
"Dama ba tsanarka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Chapter 112
Chapter 113
Chapter 114
Chapter 115
Chapter 116
Chapter 117
Chapter 118
Chapter 119
Chapter 120
Chapter 121
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 107 Chapter of 121