Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya fara tambaya? Amma sai aka nuna masa yana can wani dakin jikinsa shima da sau?i, Dole hankalin sa ya Wan kwanta tunda ya ga alamun ba a rasa rai ba, dayake yana jin jiki tunda a cikinsa ne ya samu raunin, dole aka sake mishi wani alluran barci bayan an ba shi magunguna ya sha, sannan aka sake saka mishi drip, Itama Madinan haka aka yi mata tunda a halin da take ciki kamar bata gama dawowa cikin hayyacinta ba, hatsarin ya ruWa ta da yawa, Shi kuma Abokin Mashkur ma an sallame sa tun yamma, Yayinda aka bar ?an uwan su Mashkur dana Madina a cikin jejeto, A halin yanzu Umma ce da Inna lami, su ne kaWai a wurin Madinan suka kwana, Yaya Haula Baban Sasa ya hana ta kwana, suma duk sun zo tunda suka ji hatsarin da sassafe, A washe gari ma suka sake zuwa su kansu hankulansu ya tashi, musamman da suka san halin da Angon yake ciki abun sai du'a'i, kowa da salati yake fitowa sabida a halin da suke zuwa su tarar dashi, Zuwa wannan lokacin su kansu su Ansar sun san halin da Mashkur yake ciki, Madina kuka sosai ta dinga yi tana kiran sunan shi, tuni jikinta ya rikice wani zazzafan zazzaSi ya rufe ta, Ansar kuwa kasa zama yayi dole sai da aka kaishi inda yake, lokacin da ya ga halin da Mashkur yake ciki sai ga hawaye suna gudun tsere a kan fuskarsa, jikinsa na wani irin rawa yana ?o?arin tashi daga kan kujerar da aka kawo shi; amma bazai iya ba, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Allah Sarki! Babu rabon Madina tayi rayuwa da Mashkur, domin Allah ba ya barin wani don wani, shi ne mai raya wa kuma shi ne mai kashe wa, Kwana biyar da abun ya faru har lokacin Mashkur bai san inda kansa yake ba, ko buWe ido bai taSa yi ba har sai da rai yayi halinsa, sai dai aka wayi gari aka gansa ya rasu, Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un..! Lallai rai ba?on duniya ne... Ba a yi wani don wani ba kuma babu wanda zai tabbata a cikin duniyar nan, kowa sai ya WanWani mutuwa, lokaci Waya Allah ke lamarin sa, basu taSa kawo wa a ransu koda wasa wannan mummunar ?addaran zata faru ba, sai ga shi abu kamar ?ibtawar ido an yi an gama, Mashkur ya tafi... Ya tafi tafiya na har abada, ya tafi tafiyar da yayi sanadin shiga ?uncin wasu mutane, tafiyar da ya girgiza ilahirin ?an uwansa, tafiyar da ya kawo wani sabon babin mummunar ?unci a cikin *RAYUWAR MADINA.* Duniya tayi mata ?uncin da inama ace ita ce ta mutu ba shi ba, inama ace wannan ranan bata zo ba, imana ace bata san shi ba tun farko, Wayyo Allah! Mutuwar da ya Wimauta ta ta kasa gane inda take tsawon mako guda, Kai ba ita kaWai ba hatta Ansar da yake jin shi kaWai aka yi wa mutuwar, duniyar tayi masa zafi mai muni, yayi kukan rashin Wan uwansa, kuka bana wasa ba, wanda yasa dukkansu jikinsu ya ?ara rikice wa suna asibitin har lokacin ba a sallame su ba, Mummy tun ranan da ta sume jikinta ya rikice sai da ta kwana a asibiti sannan aka mayar da ita gida, A cikin su; Daddy ne kawai mai ?arfin hali, shi ne kaWai wanda ya iya jure wa bai faWi ?asa ba, amma yayi kuka sosai, ya ji mutuwar Wansa da yayi tsananin girgiza sa sai dai ramewa da ya soma yi a tsaitsaye sabida ciwon da yake fama dashi To komai na Allah ne dole ne muyi hakuri duk abun da ya samu Bawa, kowa zai je inda ya je, Allan da yayi sa shi ya fi kowa sonsa kuma ya amshi abun sa, dole su saka dangana kamar yanda Allah ya saka wa kowanne Bawa mantuwa, Yau ga shi har sati biyu da rasuwar Mashkur, abun kamar almara, Madina kuwa sai dai aka mayar da ita gidan Umma tun sanda aka sallame ta, duk da har lokacin jikin bai yi dad'i ba kullum ranan duniya sai tayi kuka, kullum hawaye na zuba a kwarmin idanunta, tayi mugun sauya wa wannan lokacin ta zama Abar tausayi, lallai ita aka yi wa mutuwa, kullum bakin ta ba ya rabo da kiran sunan Mashkur, bata da magana sai kuka da kiran sunansa abinci ma bata iya ci sai da rarrashi, Haka Umma ta dinga kula da ita tana bata baki da nuna mata, "?addara????                         ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? nsu ne haka basu da yanda zasu yi, Allah ya fi su son shi fiye dasu, addu'a Mashkur yake bukata a wurin ta ba wannan koke-koken ba, hanyar da zata iya saka mishi kenan." Amma Madina sam bata gane lissafin nan, bata sanin me Umma take furta wa, a Wimauce take, zuciyarta a cinkushe take da wani irin ?unci da ba?in ciki, sai yanzu take ?ara tabbatar wa da tabbas ta zo duniya a rashin Sa'a, komai yana faruwa a rayuwarta daki-daki, yanzu ma komai bai sauya ba, ashe na Wan lokaci ne Wan farin cikin da take dashi? Ashe bazai Waure ba? mutumin da ya zo ya kawo mata sauyi a cikin rayuwa ya tafi, Mashkur ya tafi, ta kasa gasgata hakan, tana jin kamar har ta koma ga Allah baza ta taSa samun kwanciyar hankali ba, baza ta taSa samun farin ciki ba, a wannan lokacin bata ga amfanin rayuwarta ba, babu amfani, Wannan yasa ta ?ara ?untata kanta fiye da halin da ta shiga a baya, Babu irin lallaSawan da Umma bata mata ba don dai ta ga ta dawo da walwala da farin cikin ta kamar baya, amma abun ya faskara, babu ranan duniyar da zata zo ta wuce Madina bata zubar da hawaye ba, ta dena cin abinci, ta dena magana, tana zaune a koyaushe da hijabi a jiki tana faman tunani da koke-koke, ko wanka ta dena yi, har wani irin rama da ba?i tayi bakinta duk ya bushe yayi jazur; ko ruwa sai Umma tayi da gaske take bata, a ganinta babu amfanin rayuwarta a yanzu tunda farin cikin ta ya tafi, mutuwar da ya gigita mata lissafi karshe ko cikakken lafiya ta gagare ta, abun sai ya zama kuma har kwanciya tayi jikin yayi zafi, An kaita asibiti tayi kwana biyu ana mata ?arin ruwa sabida cutar yunwa da ke son illata ta, ga kuma asalin ciwonta na ciwon damuwa da ya fara dawowa, wanda Likitan sun ja musu kunne, "a kula da ita matu?a, domin tabbas zai iya shafan ?wa?walwanta kamar yanda ya so yayi a baya, idan ta ci gaba da kasancewa a cikin wannan halin zata iya rasa tunanin ta, kuma zuciyarta zata iya buga wa lokaci guda." Umma kuka ta dinga yi domin abun ya fi ?arfinta, bata san ya zata yi ta dawo da farin cikin da ?arta ta rasa ba, babu abun da bata mata don ta saka ta walwala ba amma Madina bata san tana yi ba, ko magana ta dena yi, sai a yi kwanaki basu ji muryanta ba, koda tayi magana sau Waya to muryan ma baza a ji ba balle a gane mai tace, sai dai ta nuna abu da hannu, abu kamar wasa ciwon ya zama babba, Iyayen Mashkur da suka zo suka ga halin da take ciki, su suka Wauke ta aka wuce da ita Asibitin ABU shika Zaria, Tayi jinya har na sati Waya ana kula da ita, kamar in an soma ganin sauyi sai jikin kuma ya ?ara rikicewa, da farko sun yi tunanin ta dena magana ne don kanta, ashe ba haka bane, ciwon ne yasa bata iya magana, akwai abun da ya tokare mata ma?ogwaro, kuma irin ciwon nan na damuwa da ?unci yana haifar da hakan, Yau kusan kwananta goma a asibitin abun dai babu daWin ji, ?an ?auye duk sun zo sun gaishe ta, Yaya Yunus kusan kullum sai ya zo asibitin duba ta, babu abun da ba ya siyo wa don ita, amma bata san ma yana yi ba Iyayen Mashkur suma kusan koyaushe suna zuwa asibitin, Hajiya Ummee ma tare suke zuwa tunda tun mutuwar Mashkur bata koma gidan ta ba, gidan yayi mata ?unci yana tuna mata da Mashkur, shiyasa tunda ta koma ta kasa barci, sai ta koma Kaduna, Duk wannan abin shima Ansar yana gida har wannan lokacin bai koma Riyadh ba, shima rashin Wan uwansa yasa jikinsa duk yayi sanyi ya kasa taSuka komai, shiyasa ya kasa jirga wa daga wurin ?an uwansa, Wannan zuwan da zasu yi sai suka zo dashi duba Madina, tunda bai taSa zuwa ba ko an ce ya zo su je zai ce musu, "bazai iya ba." Wannan karon Daddy yace, "su tafi tare." Don haka shi ne ma ya tu?o su har zuwa Zaria, kai tsaye asibitin suka wuce, A lokacin da suka je Umma ce kaWai a tare da ita, ita kuma Madinan ta samu barci a time Win Ansar kuwa tunda ya kalle ta sai ta zame mishi tv tsaban mamakin yadda ta sauya, irin raman da ya ga tayi; tayi mugun sauya mishi kamar ba ita ba, shiyasa ya kasa Wauke ido a kanta yana jin wani irin mugun tausayin ta a ?asan ransa, a lokacin sai ya tuno Wan uwansa wanda yasa nan take idanunsa suka cika da hawaye, sai kawai ya fice a Wakin batare da ya bari sun kula dashi ba, tafiya kawai yake yi har sai da ya fice a cikin asibitin duk girmansa, ya doshi bakin gate batare da ya san ma yana tafiyan ba, kawai yanda tunanin Wan uwansa da kuma ?uncin da ya ziyarce shi ne yasa shi ficewan, Sai da wayansa tayi ?ara sannan ya ankare da inda yake nufa, take ya tsaya yana laluba wayan ya ciro, Numban Shamsuna ya gani sabida bai yi saving ba but ya san nata ne ko don kiran da take masa, bai amsa ba sai da ta kira ana biyu, sannan da?yar ya amsa but ya gaza mata magana sai ma juya wa da yayi ya koma cikin asibitin, Ita kaWai take surutun ta yana amsa mata da?yar sabida halin da yake ciki, da yaga zata cika sa da surutu sai ya kashe wayan ma tunda bai ga amfanin kiran da tayi masa ba, kiran ne ya sake shigo wa but ya ?i daga wa har ya katse, sai ma tsaki da ya ja yana mayar da wayan cikin aljihu, Jima wa kaWan ya ji ?aran shigowar text, kamar bazai duba ba sai kuma ya buWe ya duba, Text ta tura mishi kamar haka, "I'm sorry my love, na kasa barin ka ka huta duk da na san halin da zuciyarka take ciki, amma meyasa Ni baza ka yi min adalci ba? Duk wannan fa abun da nake yi sonka ne ya jawo haka, don Allah ko sau Waya ne ka kasance dani domin sanya ka farin ciki, duk da na san bazan wanke abun da kake ji a zuciyarka ba amma zan iya mantar da kai kaso mafi yawa daga damuwarka, idan har kana cikin ?unci ba na samun natsuwar zuciya, please my love, today one day come to my place I have something surprising to give you, you will be happy and forget everything that bothers you, idan har ka amince zan tura maka address na club Win da zamu haWu, i love U! Sai na ji ka." Message Win ya goge ya mayar da wayan tare da ci gaba da tafiya, Kai tsaye Wakin da aka kwantar da Madina ya nufa, wanda da?yar ma ya gano Wakin ya koma, Lokacin da ya shiga ta farka, har an zaunar da ita a saman gadon an saka mata pillows a bayanta, Umma na bata ruwan tea a baki da cokali, a hankali take Wibowa take bata tunda da?yar take sha, idanunta kusan a rufe suke sabida magagin barcin da take yi, alluran da aka yi mata bai gama sakin ta ba, Lokacin da Ansar ya shigo Wakin sai ta bi shi da ido tana son ware idanun a kansa, da?yar take bude su waWanda sun yi narai-narai da su sun gama jigata sabida halin rashin lafiya, a lokacin da suka haWa ido sai da zuciyarta ta buga ta wani zabura kamar zata faWo kan gadon, Tean da ke hannun Umma ta kaSar dashi ?asa batare da ita ta ankare ba, Gaba Waya suka saka salati sabida a tunanin su tean ya zube mata kar ta ?one, Amma ita sam Madina bata san me suke yi ba wani irin bugawa zuciyarta take yi; domin a lokacin da ta ?ara bude idanunta ta kalli fuskar Ansar sosai, sai take ganin kamar Mashkur ne a gabanta a tsaye yana bin ta da ido, shiyasa ta dalalo idanu waje ta nuna sa da yatsa bakin ta na rawa ta furta, "Ya.. ya .. MmashKurr!" A Wai-Wai maganar nata ta fita cikin dashashshiyar murya. _Don Allah waWanda suka fara sharhi a kan mutuwar Mashkur, su yi ha?uri babu yadda zan yi ne domin labarin ne ya zo a haka, tun farko haka na tsara, labarin nan ba nayi bane don jin dadi, a'a wani ?alubale ne na *RAYUWAR MADINA* da ke faruwa da ita, ?addaranta ce ta zo a haka babu yadda zan yi in sauya, don Allah kuyi hakuri, kuma ku sani kowanne Bawa ai zai mutu ba dole sai ya gama rayuwarsa ba, kwatsam a lokacin da Allah ya bar maka wani don ka ji daWi a rayuwa zai iya daukansa tunda ba ya barin wani don wani, already Mashkur ya gama taka rawansa a labarin, shiyasa na kawar dashi... Ina godiya fan's da soyayyar ku ga littafin nan nawa, love U so much._ Kuma masu cewa zasu dena karantawa don Allah a yi hakuri a karisa karanta wa kun ji ko ?an aljanna.=??=?? [3/5, 9:57 AM] Oum?ahira: =؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎? ? ? *RAYUWAR MADINA* =ا? =؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎? _Writing Story:_ *NAFISAT ISMA'IL* ? ? ? ? ?? _(UMMUDAHIRA)_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT>???* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*

Chapter 41 of 55