Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya kawo mana ?arshen wahalar rayuwa._ *DATA SHARE* Call, message or whatsap? 07065334256 *MTN* 500MB 150 1gb 270 2gb. 500 3gb. 800 4gb. 1100 5gb 1400 6gb. 1700 Verlid for 30 days. ______________ *EPISODE 44* _____Madina da saurin razana tuni ta firgice tunda ta fahimci hannun wanda take, ihun da ta tsandara ya fito da Umma a guje, ko hijabi babu a jikinta sai ga ta a bakin zauren hankalin ta a mugun tashe, HaWa idon da suka yi da Yaya Yunus ne sai ta ja birki tana bin sa da kallo cike da mugun mamaki gami da wani irin tsantsan tsana da Sacin rai, Shi kansa tuni ya saki Madinan ta ruga aguje wurin Umma, Da sauri Umma ta ri?o ta tana duba jikinta cikin sauri, muryanta da ke nuna tashin hankalin ta take furta, "me yayi miki? ????                         ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? Yayi miki wani abu ne Madina faWa min?" Yanda Madinan ta ruWe sam ba ta jin Umman sai kuka take yi tana ?an?ame ta; jikinta na wani irin kerma kamar zata zube, da sauri ta tura ta cikin gidan tana kallon Yaya Yunus da ke tsaye kansa a ?asa, don kamar mara gaskiya haka ya koma a wurin, A fusace tace, "me ya kawo ka wurin mu; mai ka zo yi a gidan nan?" ?ago kansa yayi duk da yana nuna alamun kunya, cike da sanyin murya yace, "Umm.. Umma na zo duba..." Bata bari ya ?arisa maganar ba ta daka mishi tsawan da sai da ya firgita shi, don a lokacin a mugun Sacin rai take wanda ta kasa Soye fushinta, cikin amon muryanta kamar zata kai mishi duka tace, "kai ka kula ka san inda zaka yi iskancin ka, wlh summa tallahi idan har ka sake zuwa Kofar gidan nan har ka taSa min ?ata, sai nayi Shari'a da kai, sai na ci maka mutuncin da har ka mutu baza ka manta dani ba." Ko saurara masa bata yi ba ta juya fuu ta shige cikin gidan Wanda shi Yaya Yunus ya kasa ko jirgawa a wurin koda jin bayanan ta, kuma hakan bai sa ya karaya ba don da shirinsa ya zo kowanne irin wula?anci ne zai iya fuskanta in har zai samu Madina, yanzu ita ce farin cikin sa da tunaninsa, bazai iya tafiya batare da ya amayar da abun da ke ransa ba, don haka ya taka ya nufi cikin gidan babu tsoro bare tunanin abun da zai je ya dawo Kwatsam Umma sai ganinsa tayi ya shigo musu gida, wanda a lokacin ta tasa Madina tana rarrashinta; wacce sai rusa uban kuka take yi, Saurin zabura tayi ta mi?e tana dubansa kamar zata sha?e shi don takaici, tace, "uban me ya sake shigo da kai? Baka ji kashedin da nayi maka bane?" Madina wacce bata ankare da zuwan nasa ba, since ta haWa kai da gwiwa, muryan Umman ne yasa ta Wago kanta, itama a mugun tsorace ta zabura ta shige Wakin Umma ta rufo ?ofan Umma kuma sai ta Wauki Khalifa da ke kwance a saman tabarma yana barci, ta rungume shi tana shirin shige wa Waki, Yaya Yunus yayi saurin cewa, "Umma, Ni fa a kan Yarona na zo, duk da na san nayi muku laifi amma na zo na baku hakuri ne." Wani juyowa da Umma tayi tana kallonsa kamar zata kifa masa mari, takaici ma yasa ta kasa yin magana sai shigar da yaron tayi Wakin Baba tunda Madina ta rufe ?ofan, ajiye shi tayi ta fito da sauri "Umma don Allah ki saurare Ni na san ban kyauta muku ba, hakan ne yasa na zo in baku hakuri shiyasa na tako ?afana har gidan nan don in amshi kuskure na." "Lallai ma Yunusa baka da ta ido, kai har kana da bakin da zaka zo kana bamu ha?uri ashe akwai wannan ranan? To mun ji ka bamu hakuri amma baka da hurumin da zaka shigo mana gida kai tsaye haka tunda babu gadon ubanka ko uwarka a nan; ko akwai?" TafaWa a fusace cikin tsawa, Duk da ya ji zagin da tayi masa amma ya kasa ko magana bare ya amsa ta, Tace, "ai na san baka manta abun da ka ce a game da Yaron nan ba, don haka ka Sace mana a gida tun kafin in tara maka jama'a, kuma daga yau sai yau kar ka sake gigin shigo mana gida idan ba haka ba wlh ina da mai min maganin ka." Sai ta juya itama ta shige Wakin Baban itama ta bugo ?ofan, Hakan yasa ba shi da zaSi ban da ficewa a gidan Umma kuma sai da ta tabbatar da ya tafi sannan ta fito ta je ta buga wa Madina kofa, "Madina fito ki buWe ?ofan nan. Madina..." Kiran sunanta ta hau yi tana buga ?ofan, sannan ta zo ta buWe mata har lokacin kuka take yi duk ta firgice ta haWa majinu, Umma tace, "ki dena kukan nan don yanzu bai da wani amfani, domin wannan karon sai inda ?arfina ya ?are in dai ya dawo don ke ko Wanshi ne, bamu da wata ala?a dashi bazan taSa bari ya sake shigowa gidan nan ba bare har yayi miki wani abu, ke ma ina so ki cire wannan tsoron a ranki Madina babu abun da zai faru da ke sai alkhairi, muddin ya sake dawowa to da Mashkur zan haWa shi na san zai taimaka mana, don haka ki dena kuka kinji ko? Allah zai mana maganin shi, zauna ki ci abincin ina zuwa." Cikin kukan ta furta, "ba na jin yunwa Umma." Kallonta tayi tace, "ba na son gardama tunda nace kar ki sanya wata damuwa a ranki ki dena kukan nan, in dai muna tare ba abun da zai miki, zauna nace ki ci abincin." Ba don ta so ba haka ta zauna a saman tabarman, sai dai ta kasa cin ko loma Waya ne koda Umma ta tafi ta barta, Har ta fito daga bayi bata saka hannu ta soma kai abincin baki ba, Umma tace, "Madina, ba magana nake miki ba? Ki ci abincin nan nace kar ki bari in sake miki magana kin ji ko?" Ganin ran Umman a Sace yake shiyasa ta soma ci ba don yana mata dad'i ba, sai dai bata da yadda zata yi ne, amma a yanda Yaya Yunus ya tsorata ta ?iris ya rage zuciyarta bata yi bindiga ba, gani take yi kamar zai dawo domin ba ?aramin tsoron shi take ji ba, sam ba ta son ganin fuskarsa sabida tsantsan tsanar da take mishi, Sai da su Hassana suka dawo makaranta ne sannan har ta soma sakin jikinta ta Soye hawayen da ke fuskarta, Sai dai a ranan a Wari-Wari ta kwana da tunanin wani abu mummuna zai iya faruwa da ita, a duniya mutanen nan biyu tayi musu mugun tsanar da ko a mafarki ba ta fatan su haWu, gani take yi idan har suka haWu dole ne mummunar ?addara sai ya faru da ita, sun azabtar da ita da ba ta fatan ?ara ganin su har abada, ba ta sonsu ta tsane su, Shiyasa tun ranan sai walwalanta ya gushe gaba Waya, wani irin ?unci da damuwa ne yayi mata yawa sam ba ta son ko magana ta ri?a yi, Duk da Umma tayi mata faWan hakan amma ta kasa manta abun da ya faru, ga shi tun ranan ma ta ?i bin Umma gidan Hajiya sabida ba ta son abun da zai takura mata, ta fi son ta kaWaita daga ita sai Yaronta, ce ma Umma tayi, "zata zauna a gida ba ta son zuwa gidan Hajiya." Umman bata matsa mata ba shiyasa ta bar mata Khalifa sai tace mata, "ta rufo ?ofan in har ba muryanta ta ji ba kar ta buWe." Koda Umman ta je can gidan Hajiya, Hajiya Ummee ta tambaye ta ina Madinan?, Tace mata, "tana gida ta ?i biyo ta." Amma kwata-kwata bata sanar mata da abun da ya faru a jiya ba, Shi kuwa Mashkur ba ya nan ma tunda da sassafe ya wuce wurin aikin sa Madina kuwa a gida ta wuni tare da Khalifa ta rungume sa tana ta kuka, sai da tayi mai isanta sannan barci ya Wauke ta Yaron na kwance a gefenta, Can kukan Yaron ya tayar da ita ta tashi zaune tana kallonsa, Waukansa tayi ta soma shayar dashi tana kallon fuskarsa soyayyar yaron na ?ara shiganta, a zahiri Yaron kama yake yi da ita sak, sai dai kasancewar duk jininsu Waya da Yaya Yunus kuma kamanninsu Waya, wanda ya kalle sa ya san dole Wansa ne don shima ba abun da ya baro sa, sai dai shi Khalifan hatta sajen da ya ?awata fuskar Madina irin nasa ne, sai manyan idonta da ya biyo, A yadda take ?aunar Yaronta tana jin ko mene ne zata iya yi domin sa, idan har Yaya Yunus ya zo amsar shi ne to wlh baza ta taSa ba shi ba, sai dai idan har ta mutu, tuna wannan shiyasa ta sake fashewa da kuka, cikin kukan take cewa, "don Allah Umma kar ku bari ya sake cutar dani, bazan iya ba shi Yarona ba, sai dai idan na mutu." Sai ta ci gaba da kukan tana sake rungumo shi a jikinta bayan ta gama ba shi nonon, ta kasa yin shiru sabida gani take yi kamar Yunus ya zo amsar yaronsa ne kuma a koyaushe zai iya dawowa, hankalin ta ya kasa kwanciya har sanda ta tabbatar da umma ta kusa dawowa sannan ta share hawayenta gudun ta gane halin da take ciki, amma kuma dole ne a gane tunda ana kallon fuskarta an san ta sha kuka, Shiyasa koda Umman ta dawo ta kasa haWa ido da ita Soye fuskarta tayi kar ta ga halin da take ciki, Umman kuwa dayake hankalin ta ba ya kanta bata kula sosai ba, sai dai maganar Hajiya da take mata tana faWa mata, "tayi faWan rashin zuwan ta, don haka gobe zamu tafi tare don ban ga amfanin zamanki ke kaWai ba, ko don wannan Wan iskan da ya soma zuwan mana gida dole ne mu tafi tare, don ban san mai zai zo yayi muku ba in babu kowa kar ya cutar da ke ko ya gudu da yaron ma." Jin hakan ne yasa ta fashe mata da kuka, "Umma don Allah kar ki bari ya ?wace min Yarona, tunda yace ba ya sonshi yabar min shi bazan yarda ya tafin min dashi ba." "Madina, har abada wannan Yaron bazai taSa koma wa hannunsa ba, yanda ya nuna ba Wansa bane to bai isa ya amshe sa ba, inda da yanda zan yi ma bazai sake ganinki ba daga ke har Wan bare yayi tunanin zai ?wace shi, don haka ki cire wannan tunanin a ranki ma don bai isa ya amshi Khalifa ba." Duk da kalaman Umma but Madina ta kasa samun natsuwa, shiyasa washe gari ta bi Umma don kamar yadda Umman ta faWa ne zai iya dawowa ya yi musu wani abun, tsoron hakan ne yasa ta bi Umma gidan Hajiya.**** Kusan kwana uku kenan Mashkur bai samu ya ga Madina ba, tunda idan ya fita tun safe sai yamma yake dawowa, shiyasa yau da ya dawo a gajiye burinsa kawai ya sanya ta a ido, ba ?aramin mugun kewarta yake yi ba, abun mamakin ma har mafarkinta yake yi daga jiya zuwa yau, yayi kewar matsoratan idanun nan nata masu kyau da kashe masa jiki, yau ya so ya dawo da wuri but aiki yayi masa yawa, amma duk da haka bayan yayi wanka ya zauna cin abinci, a ransa yana tunanin zuwa gidan yanzu don bazai iya ha?ura bai sanya ta a ido ba yau, Yana cin abincin amma tunaninsa yayi gaba har murmushinsa mai kyau yake saki, wanda ya ?awata face Win sa, Hajiya wacce ta fito daga Waki ta hange sa a wannan condition Win, sai ta taho ta zauna a gefen sa tunda yana kan two sitter ne, sai da tayi magana sannan ya ankare da zaman nata a wurin, da sauri ya Waga ido yana dubanta, tare da yamutsa fuska yana cewa, "haba Hajiya, wannan sai ki tsorata Ni ai, inuwarki kawai fa na gani." "Eh inuwata ka gani mana tunda kana can ka saki leSe kana sakin murmushin mahaukata, ka lula wani tunanin na daban ina zaka san da zuwa na Likita?" Murmushi yayi yace, "Hajiya kenan." Sai ya Wan ja numfashi da furta, "tunanin aiki ne ba wani abun ba." "Af! Ai na san da haka tunda baka da sana'a sai zancen aiki, ka dawo gida baka huta ba maimakon ka samu ko runtsawa kayi; amma ka ?i, kana cin abinci ma baza ka bar tunanin banza dana hofi ba, wai meye amfanin aikin nan naku tunda Allah ya hore muku iyeyenku suna da arzikin da zaku ci kuyi matashi, amma kun hana kanku sukuni, wlh haushin wannan aikin naku nake yi sam bai da amfani, daga nakan har na Ansar da shi ko zaman ?asar ma ba ya yi. Yana tafe da idanu a tsakar ka sai shegen faWin rai kamar ana kaWa mishi ganga." Dariya yayi sosai yana cewa, "wannan kun fi kusa Hajiyata, but kin fi son zuciyarmu ta mutu ne sabida iyayenmu sun tara sun ajiye? Ai nasu daban namu daban dole mu fita mu nema, sannan kar ki manta dukka aikin nan namu taimakon jama'a ne ba don kuWi muke yi ba, ke dai kawai ki mana addu'a ba wai ki ce haushin aikin kike ba, kuma kin san da cewan taimako muke yi." Baki ta taSe da cewan, "ai Ni ban hana ku taimakon ba, amma abu Waya ya tsaya min a rai yanda ku ka ?i ajiye Mata kuyi aure sai zancen aiki aiki babu ?arewa, ga iyayenku goyan bayanku suke yi tunda har yanzu sun ?i matsa muku kuyi aure, ita wannan Nabeela da naga kamar tana yin ka naku ya zo Waya, na zuba ido in ji kun tayar da maganar soyayyar taku amma shiru baku da ninya ma, Ni na rasa mai kuke son ku zama ne Faruok, don Allah ku yi wa kanku faWa." "Hajiya, ita Nabeelan ne tace miki muna soyayya ko kuma zolaya ne?" "Oh! Nufinka ba soyayya kuke yi ba kenan? Kai Ni fa na zuba muku ido ne kawai inga inda labarin zai je, amma tuni na harbo jirgin ku, kuma tunda na ga kun kasa furta maganar shiyasa nayi maka yanzu don na gaji da ganin ku haka nan, Daddyn naku zan kira in sanar mishi abun da ke faruwa ko zasu fahimci halin da kuke ciki, ai ka ga na taimaka muku." Idanu ya zuba mata har ta dire maganar nata, sannan yace, "Hajiya, I'm serious fa Ni ban san da wannan zancen ba, in rasa wacce zan aura kuma sai Nabeela Hajiya? She's my sister fa kamar Khairiyya na Wauke ta, kar ki fara wannan maganar ma Hajiya don baza ta saSu ba ban taSa son Nabeela ba." Baki Hajiya ta ri?e cike da mamakin furucin sa, "kana nufin wai da gaske ba soyayya kuke yi da Nabeelan ba? Duk wannan sha?uwar taku dama duk ba ta soyayya bace? Ai kuwa in haka ne baku kyauta wa kanku ba, amma duk da haka sai dai idan kai ne baka sonta, don in har ba idanuna bane suke min kallon ba dai-dai ba; to tabbas Nabeela ita tana sonka." Shi da yake ya Wauke maganar da wasa ne shiyasa yayi dariya yace, "i think Hajiya to idanunki basu faWa miki dai-dai ba. I never loved Nabeela, I considered her like my younger sister Khairiyya, and now I have someone I love, in dai aure kike son in yi addu'ar ki ta amsu a wannan gaSar, domin akwai wacce ta shiga raina a yanzu, kuma ina tunanin Insha Allahu ita ce farin cikina muradin raina, fatana ki taya Ni da addu'a Hajiya." Hajiya tace, "ai ba wacce ta fi maka ?ar uwanka Farouk, Ni na tabbata idan ka so Nabeela baka faWi ba tunda rainonka ne, tarbiyyar da ke gare ka shi itama take dashi, su kansu iyayenku zasu yi farin ciki da wannan haWin musamman yanda suke ?aunarta, ba wacce ta dace da kai sai Nabeela, don haka Ni a shawarce Farouk mai zai hana ka so Nabeela, idan ma ada ba sonta kake yi ba; to a yanzu ka nuna mata soyayya ko don dacewan da ku ka yi, ka fi kowa sanin halinta yarinya ce mai hankali da natsuwa, ita wacce zaka dauko baka san halinta kamar ?anwarka Nabeela ba." Cikin yanayin da ya soma gundura da maganar yace, "Hajiya, kema ba ki san wacce nake so bane na san da kin fi Ni farin cikin zaSin." "Kai da Allah can, wace ce zaka so da zata fi min Nabeela? Ai duk wacce zaka so a bayanta ne koda ?ar uwanka ne, don kun fi dacewa da ita fiye da sauran dangi, balle na san bare ce tunda ada ka ?i dangi balle in ce a cikin dangi take yarinyar." "Yanzu Hajiya idan na faWa miki wacce nake so kina nufin baza ki amince da ita ba? Baza ki yi farin ciki ba koda Madina ce Macen da na zaSa?". [3/2, 9:13 AM] Oum?ahira: =؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎? ?? *RAYUWAR MADINA* =ا? =؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎?=؎? _Writing Story:_ *NAFISAT ISMA'IL* ? ?? _(UMMUDAHIRA)_ *SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT>???* *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION*

Chapter 35 of 55