*Habeeb* yace mafarkin wa...? *Harees* yana dariya yace ummmmh...kodai abar kaza cikin gashita kawai, tsaki *Habeeb* yayi tareda cewa kaidai kasani, *Harees* yace kaima kasani.
Yanzu dai ba wannan nan ba yakake ya kuma gajiyar kamfen..? yace lafiya gajiya kam akwaita sai kuma na yau da gobe, yace yau da goben ina za'aje...? yace yau liman katagun da kafin liman zamuje, gobe sai muje huturu da gudun fulani dama su sukayi saura,
yace "OK toh" Allah yabamu nasara yace ameen, saidai yau ma bazan samu zuwa ba saida gobe insha'allahu, dasauri yace jiya mafa bakaje ba yauma kuma bazaka jeba to" Ina zakaje...?
yace yi hakuri kasan jiya munyi tiyata dayawa shiyasa, yau kuma zankai mutane na Shopping ne kasan jiya bamu samu zuwa ba saboda me Daraja ta batada lafiya,
toh" shine Zan kaisu yanzu so kozaka rakamu...? ya karashe fadi cike da zolaya,
hararan shi *Habeeb* yayi tareda tashi yana cewa kasan aina saba rakaku so dole kafadi haka, kaga mlm ni zan shiga nayi wanka kafin mutane sunyi yawa domin najiyo hayaniya alamar sun fara taruwa so sai mun hadu anjima,
mikewa shima *Harees* din yayi yana cewa "OK sai kun dawo *Habeeb* yace "ok tareda shiga daki, shi kuma *Harees* yafita.
*Jana* tana nan inda take don haka KO" kallon inda take *Harees* baiyi ba yafita, saidai itace tabi bayan shi da harara tareda cewa maye kawai to" umma ta gaida ashsha,
Koda *Harees* yafita! ya'iske mutane harsun fara taruwa a harabar gidan part din su *Sadeeya* yanufa.
**********
Yan biyu kam sai misalin karfe 10:30am suka tashi brush su kayi sannan suka karya kumallo,
bayan sun gama su kayi wanka suka shirya cikin wata haddiyar doguwar rigar material, marrow color sai aka man na mata black din flowers awuyan rigan da kuma hannu rigan sai sukayi rolling da bakin gyale, kasan cewar su farare sai shirin yaima su kyau zasu fito kenan,
sai su kaji sallama *Harees* zaya shiga dakin.
jin muryar shiyasa *Feeya* tayi saurin boyewa akuryar gado, domin wani irin kunyar shi takeji musamman ma yanzu dayake kiranta me Darajar shi,
*Deeya* Ce ta amsa sallama tana cewa Hamman *Harees* ina kwana.. yace lafiya Queen of beauty, kun tashi lafiya..? tace lafiya qalau yace masha'allah toh" kun shirya kenan ko...? tace "eh, yace "ok amma ina me Daraja ta..yafadi yana duban dakin,
Cikin kun she dariya *Deeya* ta muna masa rigar *Feeya* da tafito gurin saurin boye wa, Cikin zola kuma tace Hamman *Harees* ai my sweet *Feeya* tace mutafi kawai wai yau ba zata jeba,
yace au haka tace"...? tace "eh yace "OK to ke mutafi kawai sai mufara zuwa gidan su "Mamu da gidan "Rahma sannan gidan "zakiyya, sai kuma yace kai!..amma yau zamu sha yawo har da gidan su little feena fa zamu,
tace yauwa Hamman *Harees* toh" mutafi yace "OK, Da sauri *Feeya* tafito tana cewa kai! my sweet *Feeya* yaushe na fadi haka..? dariya sukayi gaba daya,
ahankali *Harees* ya matsa kusada ita cikin sanyi murya yace toh" amma ai kince ba zakije bako...? cike da shagwaba tace "a ah nifa bance ba tafadi, tareda hararan *Deeya* dakeyi mata gwalo,
Yace hmm! wato kwalliyar ce bakiso nagani ko...? kanta yana kasa batace kamai ba saidai wasa da yatsunta datake tana murmushi, cikin rada yace toh" yajiki..? batareda ta kallo shiba tace naji sauki, yace nima naji sauki dariya tayi still bata kalleshi ba murmushi yayi tareda cewa kinfayi kyau sosai me Daraja ta, bari muyi selfee da sauri ta daga kai aikam tuni ya kashe ta da hoto,
dariya sukayi dukkan su sannan yace oyo mutafin ku suka bishi abaya yayinda *Feeya* take cewa *Deeya* keko...? aizan rama sukai ma lnna sallama tace masu sai sun dawo itama zata shiga gurin Hajiya sannan suka fita.
Motoci da mashina da Mutane ne cike aharabar gidan 'yan zuwa kamfe, wanda cikin lokaci kankani suka cika gurin, dakyar su *Sadeeya* suka ra'ba sukafi ta daga gidan saka makon mutane dake tafaman kai gaisuwa sukeyi gurin *Harees*.
*Habeeb* kam cikin lokaci kankani yai wanka yashirya yafito cikin wani ratsetsen yadi dark bulu me shara-shara domin har anagani farar vest din shi, saiya saka hula meratsin fari da bulu kasan cewar aikin rigar ma an ratsashi da farin zare sai yasa farin takalmi, gaskiya dressing din yayi masa kyau sosai,
Sai faman kamshi turaruka yake, wayoyin sa da wallet yakwasa dake saman durowar gefen gado tareda key motar da zaya shiga, cikin sauri yafita daga dakin.
jin takun tafiyar sa tareda kamshin turaran shi sune su kasa *Jana* sauri tashi tsaye tayi tana jiran fitowar sa, da saurin ta tari gaban shi cak! yatsaya tareda watsa mata wani irin kallon dayasa taja baya dasauri,
yace lafiya zaki tare mun hanya bakiji mutane awaje suna jirana bane...?
tace dama zanje gidansu Shafa ne, tsaki yayi tareda kallon ta sama da kasa, yace toh" ban yadda ba idan kuma har kika fita ba da izinina ba kamar yanda ki kasaba toh"keda Allah, sannan yabi ta gefenta yafita abun shi
Cikin takun kasaita.
Mutane naganin fito warshi suka taso Cikin sakin fuska ya tare su da gaisuwa yayinda direban sa yakarbi key
yabude masa tashiga, cikin kankani lokaci muten suka shiga motoci masu mashin suma suka hau dama tuni me gadi ya bude masu kofa sukayi tafita har suka gama sannan ya mai da kofa yarfe.
Itakam *Jana* *Habeeb* yana fita tasaki Dariya tareda cewa hmm! BB smart kenan aidole yau saina dangana kaina da Ado idan ba haka ba gaskiya akwai matsala
_*Nikam nace toh"Allah Kai mana tsari da matsala kowa ce iri ce ameen*_
Sannan ta hayewa sama dakyar ma take taka matakalar tana sakin nishi.
*****
Saida lnna ta tabbatar mutane sun watse aharabar gidan sannan tafito tashiga part din Hajiya, sai faman sallama lnna keta zubawa amma shuru ba amsa, hakan ne yasa tashiga,
mamaki ne yakama lnna ganin Hajiya zaune amma bata amsa sallamar ba, zama lnna tayi kusada ita tareda ta bata tace Hajiyar su *KYAUTA* lafiya...?
Ajiyar zuciya tayi tace hmm! lafiya qalau lnnan *Hafeez* yaushe kika shigo..? lnna tace a ah babu lafiya kam tunda ina tayin sallama baki amsa ba, tabbas *Hafeezee* na yafadi gaskiya da yace" kina cikin damuwa shin meke faru wane..?
Murmushi Hajiya tayi tareda cewa Kai! Inna *"Hafeez* bakomai kawai dai shirmen *Hafeez* ne, lnna tace "a ah Hajiyar su *KYAUTA* *Hafeezee* na baiyi shirme ba, domin kuwa alamunki yanu na kina Cikin damuwa don haka idan har zan'iya sani toh" ki fadamun kila inada shawarar dazan baki.
Hajiya tace hmm! dama dai ba komai bane yakeda muna illa irin abubuwan dasuke ta *FARUWA* tsakanin "Hamman su *"Sadeeya* da matar shi abun yanada muna sosai,
Inna tace tabbas nima abun yanada muna, saidai ba damuwa ce abunda yaka mata murin gayi ba, addu'a ita ce" mafita, shikuma *"Habeebu* ya cigaba da yin hakuri ita kuma Murjanatu" nasiha za'a cigaba da yimata tareda muna mata abubuwan daya kamata taringa yiwa mijinta,
wanda tasan su sarai amma kuma lalaci Da son
*Zuciya* sun hana ta aikata wa, Hajiya tace tabbas kuwa sune suka hana ta aikata wa, dai-dai lokacin da su kajiyo karar jiniya lnna tace Alhamdulillahi yau su Alh sun dawo dawuri, Hajiya tace "eh dama yace sanmako zasuyo
tace Allah sarki gashi ko har sun iso, tace "eh fa.
lnna tace toh" Hajiya abunda za'ayi kenan,tace toh"Allah yasa adace tace ameen. dai-dai lokacin Abba yashiga falon da sallama suka lnna ta gaidashi tareda mikewa tayi ma Hajiya sallama tafita.
Cikin son nan da ake cewa baya tsufa saidai masoyan ta su tsufa, Hajiya da Abba suka hada ido sukayi ma juna lallausan murmushi tace sannu da dawowa, yace yauwa tareda Kama hannun ta kamar yadda yasa ba suka nufi dakin shi cikin sanyin murya yace ya' akayi ne Hajiyarmu naga damuwa afuskar ki muje ki fadamun menene yafaru,
dai-dai lokacin da su kashi ga dakin ta taimaka mashi ya cire babbar rigar shi, hannun ta Yakama suka zauna a gefe gado yace fadamun mene damuwar...? tace kahuta mana tukun, yace aihutun ba zayayi dadi ba tun da ki na cikin damuwa,
Murmushi tayi
tace aiba wata damuwa bace dama dai akan abunda keta faruwa ne tsakanin Hamman yaran nan da matar shi, murmushi yayi yace toh" bana ce ki ringa yi masu addu'a ba...?
tace Ina yi amma abun ne yafara da muna sosai, yace karki damu da hakan kedai kawai ki cigaba dayi mashi addu'a komai zaiyi dai-dai ne insha'allahu,
saidai nasha fada maki auren Na" ALLAH da "Murjanatu kaddara Ne wanda yaka mata kigane hakan, kuma shi duk abunda kikaji ankira kaddara, toh" ana nufin jarabta wace duk wanda Allah ya jarabceshi da'ita tofa bashi da ikon yayema kashi harsai ubangiji ya yaye masa ita, koba haka bane..?
Ajiyar zuciya tayi tareda cewa hakane toh"Allah yaye masa yace ameen tareda tashi yana cewa Zoki hada mun ruwan wanka, tace toh"
Amma dai yanzu lokaci yayi da ya kamata a bashi
matar shi ko...?, dasauri yajuwo ya kalle ta Cikin tsanani mamaki yace...?
_Kut! ๐ณ dama ashe *Habeeb* yanada wata matar ,amma yake cin kwakwa agurin *Jana*_,tab! ๐ค
_nasan dai me karatu zaya ce toh" wacece wannan matar KO"...? ๐ toh."_
Muje zuwa
A
*_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya)
Tareda
โ๐ฝ
๐นMeenart๐น
[7/2, 11:46 PM] My Ameena: ๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
_*KYAUTAR ALLAH CE*_
_(Labarin Sadeeya)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
2โฃ1โฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT* ๐
SADAUKARWA
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)*
___________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
___________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
Me ki kace"?..tace nace ne yanzu kam lokaci yayi da yaka mata abashi matar" shi, kaga idan bai jidadi gurin wannan ba to" zayaji agurin waccan" domin na tabbatar bazasu taba taruwa su zama daya ba KO?...
Dasauri yadawo kusa da ita ya zauna Cikin tsanani farin ciki ya rike mata hannun ta sannan yace Alhamdulillahi!, abunda nadad'e ina jira ki fada kenan da bakin ki sai gashi yau kin fada din wanda baka ramin dadi naji dajin haka ba, kuma tabbas maganar ki gaskiya ce dakika Ce",
idan "baiji dadi gurin "wannan ba to zaiji agurin "waccan hakane, dama amfani auren mace fiye da daya kenan idan wannan ta kuntata maka waccan zata faran tamaka, don haka yanzu kifada mun da wani lokaci kikaga ya kamata abashi matar shi?...
tace umm to idan ba damuwa abarshi zuwa alokacin dana fada maka kwana kin baya, yace to ba damuwa haka din ma shine dai-dai Allah yanuna mana lokacin lafiya tace ameen.
yamike yana cewa wai yau Ina yan "biyun ki ne?... banji duriyar su" ba ko suna part din Baffan su ne?... tace sun tafi siyayya tareda "Hamman dinsu" *Harees* daga can kuma zasuje gidajen yanninsu" yace ah! lallai yau za'asha yawo to ita *Safeeya* taji sauki kenan?... tace "eh taji yace to Allah yakara sauki yakuma dawo dasu" lafiya tace ameen.
Koda lnna ta koma part dinsu ta'iske Baffa yadawo, _kasan cewar akwai wayandan ke daukar karatu agurin shi duk ranan asabar da lahadi,_
bayan ya zauna sai yake tambayar lnna tasamu shiga gurin Hajiya kuwa?... tace "eh yace to me yake da mun Hajiyar?.. nan ta kefada ma shi akan abubuwan dake faruwa tsakanin *"Habeeb* ne da "matar shi,
Baffa yace tabbas abubuwan Da "Murjanatu takeyi babu dadi Wanda dole ne ya damu mutane musamman yawon da takeyi ba tareda izinin "mijinta ba, saidai kawai a ita yimata addu'a shirya lnna tace to Allah ya shirya ta yace ameen,
tace yanzu kam lokaci yayi daza a bashi matar shi ko?.. murmushi yayi tareda tashi yace yau zamu sakeyin maganar da "Alh sannan yanufi daki.
********
*Jana* kam wanka tayi ta shirya sannan tazari key mota tafito Junior yana biye da'ita yana fadi Aunty *Jana,* zanbiki, _suma aunty suke kiranta kamar yadda sukaji su" *Sadeeya* nakiran ta,_
Cikin fada tace to bazanje dakai ba yaro sai shegen nacin tsiya dalla gafara kawuce katafi part din Hajiyar ku, fuska Junior ya kwabe kamar zayayi kuka tareda juyawa zai wuce sai kuma yajuyo yace Aunty *Jana* to ki siyo mun _chocolate da ice cream_ kinji?..
tace to da gudu yanufi part din yana tsallen murna, ita kuma tashiga mota tafita bata tsaya ko'ina ba sai unguwar ilela akofar wani dan madai-daicin gida naga tayi fakin, sannan tafito ta kulle motar tanufi cikin gidan wanda yake dauke da falo guda da dakuna biyu.
Ado ne kwance atsakiyar falon dagashi sai gajeren wando yayi sha yakoshi, ganita yasa yatashi dasauri yanufeta tamkar mayunwacin Zaki itama haka domin tuni tayi jifa da Jakarta tareda gyalen ta, gani nayi yana kokarin rabata da suturan jikinta yasa nai saurin fita ina furta au'zubillahi.
*_KE DUNIYA ina ZAKI da MU?.. wai shin meke damun wasu matan ne?...ace da AUREN KI kike aikata ZINA?... Wa'eeyazubillahi! wannan wani irin MASIFA CE haka?..., shin mazajan kune basa gamsar daku shine kuke bin mazan TITI?...shin ke ba mace bace?... bakisan yadda zaki koyar da mijinki yadda zaya ringa gamsar dake bane?... dole sai wasu mazan ne zasu gamsar dake?...KO" dayake na tabbatar wasu ba rashin gamsar dasu bane mazajan su" basayi, tsabar jarabace DA suka sama kanku, kai kaji wani komawa baya wai harda kudi wasu suke ba abokin facikancin nasu Wa'eeyazubillahi! da kudin Ku da Auren Ku kuke aikata ZINA innalilahi, wlhy duk macen datake aikata ZINA especially matan Auren to ta tuba tadaina idan kuma bata daina ba to tabbatar da cewa AZABA ME tsananin GIRMA tana nan tana jiranta ranan gobe KIYAMA, Allah kashirya masu aikata hakan ka, wayanda basu aikata wa ubangiji ka karesu ameen._*
Saidai su *Jana* suka dauki tsawon wani lokaci suna aikata masha'arsu, sannan suka sararawa Kansu sannan ta maida suturan ta, tadauki gyalen ta tayafa tareda daukar Jakarta tabude taciro bandir din kudi yan dari biyar-biyar tamiwa ado,
fuska daukeda farin ciki yakarba tareda cewa godiya nake me zakina, badan keba da yanzu Ina can agidan yari kuma gidan nan daki kasiya mun naji dadin sa kwarar kinga gashi Ina rayuwa ta hankali kwance, shiyasa nake rokon Allah yabarni dake *Jana* domin kina shayar dani farin ciki,
_Sata sukayi shida abokanshi sai aka kama su" shine tayi ta cuku-cuku harta fitar da shi, sai kuma gidan dayake suka koreshi shine tasiya mashi wannan gidan,_
tace hmm ainima rokon danakeyi kullum kenan Allah yabarmu tare yanzu dai Zan tafi sai nadawo, yace to amman don Allah kar kisake yin kwana biyu nan da bakizo ba jinayi kamar zan mutu, tace haka nan nimafa naji kamar Zan mutu saboda rashin jinka ajikina amma karka damu zansan yadda zanyi, yace yau to kiyi idan ba haka ba zanfara biyoki gida,
tace abunda yakamata kenan domin nima nafara gajia dayawon zuwa gurin ka saboda Baffa mlm yasamun ido sosai, tsaki ado yayi tareda cewa kibarni Da wannan tsohon" bafullacen zanyi maganin shi, tace yauwa dadai yafi kam domin yana takura mun sosai sannan tafito ta tafi gida.
_*Nikam nace to ALLAH ya shirya*_
*******
Su *Deeya* kam basu suka dawo gida basai karfe 3:30pm na yamma duk da sungaji amma haka sukayi wanka suka shirya suka tafi islamiyya, domin su basa wasa da karatu.
Sai karfe 6:00pm sannan suka dawo daga islamiyya, uniform suka cire sai suka sa riga da siket iridaya na wata atamfa, bulu me ratsin yalo basu daura dan kwalin kayan ba saidai suka dora wani bulun gyale me duwatsu akai, dinki kayan yai masu kyau sosai kasan cewar yadan kamasu kadan,
Bayan sun gama sai suka dauko siyayyar da sukayo zama sukayi kamar yadda suka sabayi, suka cire man shafawa sabulai daba turare da kayan kwalliya suma daban kayan kwalama suma duk daban har da pads dasuke amfani dashi idan period yazo shima sun core shi daban,
Wanda tun lokacin da suka fara al'ada, shine dasu kaje siyayya sai a karasa wanda zaya sauka pads din saboda tsabar kunya, ๐ saidai *Harees* ne ya daukar masu kuma har yanzu idan sunje siyayyar shine yake daukar masu pads din,
Bayan sun gama cirewa sun ajiye kowani agurin zaman shi sai suka kwashi _chocolates da sweets biscuits_ kun rabin Wanda suka siyo, zasu fita sai *Feeya* tace sweet *Deeya* ayi rige-rigen zuwa gurin Hajiyarmu, tace Oyo muyi ayoma sedi redi gooooo suka fita falon kasa da gudu,
lokaci guda suka fajikin Hajiya amma sai *Deeya* tace yeeee! narigaki *Feeya* tace to sarki ojoro ai tare muka iso KO" Hajiyarmu?..tace "eh amma dai ku daina gujegujen nan haka,
sukace to Hajiyarmu tareda sauka saman kafet suka zube _chocolate's da sweets da biscuits_ din, gani yawan _chocolate's da sweets da biscuits_ kala-kala yasa Hajiya zaro ido tace yanzu duk yaza kuyi da wannan tarkacen?..
sukace sha zasu yi tace lallai yaran nan da sauran ku, kunga baruwana da shirme kubani su duk nan, ba musu suka kwasa suka mika mata saidai sunata turo baki, guda biyar-biyar ta basu tace ya ishe su haka ba ruwanta da shirmen su sai idan zasuyi al'ada sai suyi tafaman fadin cikin su naciyo,
sannan ta tashi takwashi sauran tanufi sama tabar sunan zaune suna turo bakim
Sai kuma suka fara yiwa junansu gwalo daga nan kuma sai suka fara jifan junan su dasu sweets din
suna dariya,
*Deeya* Ce tajefi *Feeya* dawani _chocolate_ saidai tuni *Feeya* ta kauce majifar tana dariya, daidai lokacin da *Habeeb* yashiga wanda ga dukkan alama dawo warsu kenan,
Sai jifan yasame shi a kirji wanda kallo daya zakai mashi ka fahimci ran shi abace yake, ganin hakan yasa *Feeya* ta haye sama da gudu cike da tsoro, dasauri itama *Deeya* zata gudu yadaka mata tsawa aikam ta tsaya cak! yayinda jikinta yadauki rawa Cikin bacin rai yace?...
Muje zuwa
A
*_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya)
Tareda
โ๐ฝ
๐นMeenart ce๐น
[7/2, 11:46 PM] My Ameena: ๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
_*KYAUTAR ALLAH CE*_
_(Labarin Sadeeya)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
2โฃ2โฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT* ๐
SADAUKARWA
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)*
___________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
___________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
Ke! Ina wasa dake ne?... Kai ta girgiza ciki da tsananin tsoro, cikin abinda baifi secod ba ya'isa gaban ta wanda har saida suka ji numfashin juna tareda daddadan kamshi turaran su wanda ya daki hancin su alokacin guda, musamman *Habeeb* dayaji kamshi turaran ta har cikin kwakwalwar shi wanda yahaifar mashi da faduwar gaba me tsanani,
da karfi yarintse ido sai kuma yabude aikam tuni sunyi jajir haka ne yasa tayi saurin jada baya kadan, cike da tsoro ta kalle shi abunda tagani akwayar idon shi, yasa taji gabanta yafadi musamman data tuna da abunda tayi masa jiya, Cikin bacin ran yace shine kika jefeni dan baki da kunya ko?..
Cikin tsanani tsoro tace kayi hak.... ta kasa karasa wa sakamakon yatsun shi biyu dayasa yakama bakinta, yamatse aikam tuni taji wani irin rad'ad'en zafi ya bakunce ta wanda yasa hawaye suka fara ambaliya akan kyakkyawar fuskarta,
ahankali tadaga hannun biyu tana bashi hakuri๐domin babu bakin magana,
fuska ya daure๐ก tareda cewa aidama nace zan kamaki shine jiya kikai mun rashin kunya har da murgud'a mun wannan bakin saboda kin rainani KO?...yakarashe fadi tareda sake matse bakin.
gaba daya jikinta yadauki rawa saboda zafin data sakeji yaratsa ta, Cikin tsawa yace dalla daina kallo na, ahankali ta lumshe idonun ta masu daukeda zara-zaran gashi yayinda hawaye suka sake zubowa, tsaki yayi tareda kauda kan shi gefe yace idan kika sake murgud'a mun wannan bakin me Kama da gidan tsutsa saina sa wuka nayanke shi, sannan yasaki bakin tareda cewa bace mun agurin nan kona tattakaki, aikam tuni tahaye sama dagudu tana sakin kukan shagwaba.
Saman kun shin yafada tareda dafa kanshi sai kuma ya rufe ido ahankali yafirta yah ilahee, can kuma sai yasaki tsaki mtww tareda cewa nikam nagaji! da wannan abubuwan nagaji!! nagajiiiiiiii yakarashe fadi dakarfi, Hajiya dake tsaye akan shi tun lokacin da *Deeya* tashiga ita kuma tafito don taji dalilin dayasa mata ya' kuka, tace dame kagaji?.. dasauri yabude idanun shi Da sukayi jajir ya zuba su akan ta, tace nace dame kagaji?... shuru yayi ba tareda yace komai ba sai dai kallon ta kawai dayake yi da jajayen idon shi, zama tayi kusada shi tareda cewa idan har akan "Murjanatu kake furta kallamar gajiya to kayi maza kafurta istigifari saboda ka sabi ubangijin ka domin shi ya jarabeka da auren ta,
idon ya lumshe tareda furta Astagafurullah! astagafurullah!! astagafurullah!!!
tace yauwa. saidai meyasa idan an bata maka rai sai kazo nima ka bata mun rai, a miliyon ya bude ido cike da tsanani tsoro yake kallon ta me kunshe da tambaya?.., aikam tuni tabashi amsa da cewa tabbas bacin ran *"Sadeeya* da *"Safeeya* shine bacin raina, aduk lokacin da ransu yabaci inajinshi har cikin raina don haka banason abunda kakeyi masu" musamman hali dubuna, wanda narasa abunda yasa kake saurin sata kuka gaskiya kadaina banaso.
Idon yarintse yayinda yake jin wani irin abu yana yawo akahon zuciyar shi wanda yarasa kome ne ne, ahankali yafurta kiyi hakuri zan kiyaye saidai aduk lokacin da raina yabaci ina shigo wa nan ne domin naji sanyi araina, amma sai su kuma su sake bata mun rai wanda hakan ne yakesa nakeyi masu abunda suma ransu yake baci wanda bansa hakan yana bata maki rai ba, don haka ki gafarce ni sannan yatashi yafita.
Bin bayan shi tayi da kallo harya fita sannan tayi ajiyar zuciya ahankali tamike jiki bakwari, tanufi sama zuciyarta cike da tsanani tausayin halinda yake ciki.
*****
Dakin su *Deeya* tashiga har alokacin *Deeya* tana kuka yayinfa *Feeya* ke lallashin ta, zama Hajiya tayi agefen gado dasauri suka matsa kusada ita suka dora kansu acinyarta Cikin shagwaba *Deeya* tace Hajiyarmu kinga har yanzu bakina yana mun zafi, ahankali tasa hannun asama leben da haryayi ja abuga fara, Cikin sanyi murya tace sannu hali dubuna kiyi hakuri da halin "Hamman din Ku, amma kuma meyasa kukeyi masa rashin kunya bana hana kuna ba?...
tace nifa ban masa rashin kunya ba naje jifan sweet *Feeya* ne shine nasa meshi bansani ba, kuma nace yayi hakuri shine ya matse mun baki ta kareshi fadi tareda turo dan mitsitsin bakin, murmushi Hajiya tayi tace to yi hakuri hali dubu na, amma kuma kuringa kula da yanayin dayake shigowa, kunga wani lokaci yana shigowa ne ranshi abace sai Ku kuma kusake bata mashi rai, wanda banajin dadi haka kamar yadda banaji dadin abunda yake maku, ku kiyaye banason kunayi mashi rashin kunya kunji ko?...suka Ce to sannan ta tashi tafita.
*******
*Habeeb* kam rai bace yanufi part din shi direct toilet yanufa Bayan yayi wanka sai yadauro alwala yafito daure da tawul akugun shi, daya kuma ahannun shi yana goge Kai bai Shafa maiba saboda yajiyo kiran sallah don haka turaruka yafesa sannan yasa boxes tareda saka brown din jallabiya, sannan yafita zuwa masallaci.
dakyar *Habeeb* ya'iya tsaya wa akai sallar isha'i dashi saboda wani irin azababben yinwa dayakeji, don haka ko doguwar addu'ar daya keyi bai tsaya yayi ba to balle kuma daukar karatun da sukeyi bayan isha'i duk Ranan asabar da lahadi, *Harees* yana kallon fitar shi daga masallaci shima yai sauri tashi yabi bayan sa, yace lafiya naga ka fito yau ba zakayi karatun bane?.. dakyar yafurta zanje nadawo ne yace "OK tareda koma wa cikin masallacin shikuma yawuce.
part dinsu lnna yanufa da sallama yashiga lnna tana nad'e abun sallah ta amsa zama yayi a kushin tareda cewa lnna sannu da gida, tace yauwa *Habeebu* sannu da dawowa agalabaice yace yauwa lnna don Allah idan akwai abinci ataimaka mun dashi amma kafin nan idan akwa ruwan zafi a fara bani tukun, tace to *Habeebu* duk akwai bari na kawo maka yace to lnna nagode.
*Habeeb* baibar part din lnna ba saida yaci abinci ya koshi sannan yafita, koda yafito su Baffa suna
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 42