Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yace kingama magana domin kin hadani da masoyina amma badan haka ba da tabbas yau saina koya ma kawarki darasi me muni, Shafa tace bakin aljani yahuci zuciyar ka, Shafa tace da *Jana* ki bashi hakuri, tace Allah ya baka hakuri Shafa tace ke! cewa zakiyi bakin aljanu yahuci zuciyar ka, nan dai tafadi sannan yace tafadi abunda takesan ayi mata". Da sauri *Jana* tace mlm kashe "ta nake son ayi, yace bazata kasu agareni ba domin addu'o'in dake jikinta sunfi karfina da aljanuna idan kuma nace zan kashe "ta dakarfi to saidai aljanuna sukone ni dake kuma mu mutu, ido ๐Ÿ˜ณ *Jana* tazaro cike da tsoro tace.... Muje zuwa A *_KYAUTAR ALLAH CE_*(Labarin Sadeeya) Tareda โœ๐Ÿฝ ๐ŸŒนMeenart๐ŸŒน [7/2, 11:48 PM] My Ameena: ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ _*KYAUTAR ALLAH CE*_ _(Labarin Sadeeya)_ ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ 2โƒฃ9โƒฃ WRITTEN By ๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ OR ๐ŸŽ *MEENAT* ๐ŸŽ SADAUKARWA *GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)* ___________________ ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_ ___________________ ~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~ โœ๐Ÿฝ _*Bismillahirrahamanirraheem*_ Mutuwa kuma mlm?.. yace tabbas idan har mukace zamu kashe "ta mutuwa zamuyi, domin tsarin dake jikin "ta yanada matukar karfi sanna "ita kanta bata wasa da lbada, don haka yima irinsu" asiri yakamau nan take to sai anrasa rai nikuma banyi shirin mutuwa yanzu ba gaskiya. Cikin rawar murya tace nima gaski ban shiryawa mutuwa yanzu mlm yace to kingani, tace to mlm ka kyaleta kar akashe ta" amma kuma na tsaneta fa mlm banason "ta ko kad'an, don haka inason kayi "mata abunda zata zama da'ita da banza duk daya acikin gidan, Ina nufi kadasa tsana atsakan "su yaji "ya tsaneta sosai yaji aran shi bayason ganin ta kusa dashi. Mlm dare yace wannan abune me sauki yanzu aikin takanshi" zaya koma kenan?.., tace "eh mlm yakoma takan shi din domin yaci amanata, yace to bari mugani ta'ina zamu fara domin shima naga a tsaye yaka da ibada. Bayan yayi yan surkullen shi sannan yace inason kikawo mun gashin ganshi, KO rigarsa ke ko hular shice ki kawo mun, tace to mlm saidai akwai matsala yace menene matsalar?..tace yaune zaya tafi Abuja kilama yanzu yawuce, sannan maganar gaskiya mlm baya bari nashiga dakin "shi, saidai shi yashigo dakina idan yanada bukata ta, bayan yagama sai yafita sannan kuma baya barin komai nashi adakin nawa. "Wata mahaukaciyar dariya mlm dare yayi tareda cewa aina fadamaki kinyi sake yanzu kar kidamu Zan baki wani ruwan magani, ki ajiyeshi duk ranan daya dawo kizuba shi ta'inda zayabi yawuce Ina nufi ya tsallaka wannan maganin to shikenan magana takare daga ranan zaya tsaneta sosai dazaran yaganta zayaji ranshi yabaci sannan yadinga yimata masifa ke Bari kiji daga karshe mantawa dawata wacece ma kikace sunan "ta?.. tace *"Sadeeya* ana kiranta *KYAUTA* yace ba *KYAUTA* ba ko *SAMU CE* daga ranan zakiga abunda zaya faru tsab zaya manta da'ita", arayuwar shi kilama sai ya tambaye ki wacece ita" ke kuma zaya soki feye da kowace mace kilama harda uwarsa, amma da sharadi....tace mlm menene sharadin?.. yace daga ranan wata ma'amala ta'auratayya bazaya sake shiga tsakanin kuba, tace mlm ban game ba?.. yace zaya'iya rungumar ki da sumbatar ki amma kuma bazaya kusance ki ba, Dasauri tace kan uba mlm tayaya hakan zata kasan Ce Ina matsayin matarshi amma bazaya ringa saduwa dani ba gaskiya mlm bazan iyaba, saboda inada tsananin bukata. Dasauri Shafa ta dungure ta tareda yimata rad'a akunne, tace dalla gafar ke banza ce don be saduwa dake sai me?.. baga adonki ba sannan idan kina bukaran wasu mazan saina nemo maki, tace kin fasan idan "yadawo wani sati tare zamu tafi "Abujan tace shegiya shikenan sai kici karanki babu babba ka, tace "eh kuma fa haka ne. to mlm na yarda saidai fa shima yanada tsanani bukata, yace karki damu zamu dauke mashi bukatar shi zayaji bayaji sha'awa, tace yauwa shikenan ma nan dai yabude wata kwarya yadebo wani bakin ruwa yai wani siddabaru acikin sannan yazuba cikin wata bakar kwalba sannan ya mika mata. tareda cewa ki tabbatar dakin zubashi gurin da zaya tsallaka, akarba tareda cewa to mlm nagode yace kinsan makarin wannan sihirin?..tace a ah yace duk ranan daki kabari jikinshi Dana waccen "yarinyar yahadu to daga ranan asirin zaya karye, wlhy zaya so ta feyeda da ke! nafada maki gaskiya zai mata wani irin mahaukacin so ne wanda zaya zarce yi tunanin me tunani, domin alokacin zaya'iya aikata komai akan *SONTA"* don haka sai ki kula da kyau. tace Ina mlm aibazan taba yadda yaganta bama ba talle yata" yace to shikenan, sannan taciro kudi ajakarta masu yawa tabashi sannan suka fito suka tafi, saidai *Jana* ta maida Shafa gida. sannan itama tanufi gida koda ta tambayi me aikinta Ina *Habeeb* tace mata aiya tafi Abuja baki ta tabe tareda hawa sama, boyan kyau tayima kwalban maganin da mlm dare ya bata sannan tafito tazo zaman falo. ******* *Deeya* kam fuska sake takoma part din Hajiya har saidai Mamaki yakama *Feeya* tace my sweet *Deeya* me yafaru?.. Dariya tayi sannan tabata labarin abunda yafaru tsakanin ta da *"Habeeb,* (amma kuma bata fadimata cewa ya rungume ta ba har yayi mata kiss agoshi) ita kam *Feeya* ido zaro cike da matsanancin mamaki wai Hmmm *Habeeb* ne yakeson *Deeyar* ta tun ranan da aka haifeta tab! lallai ma Hmm *Habeeb* din nan. Sannan kuma ta bata Labarin yace" idan yadawo zatayi masa jagwalgwalon nan dasu kayi ya cinye masu aikam nan sukai ta dariya, har Hajiya ta'iske su Wanda hakan ba karamin dadi yai mata ba ganin yadda *Deeya* tasaki jiki, kamar ba 'itace tayi kuka dazu ba tason *Habeeb* ba. Cikin farin ciki ta tambaye su abunda sukema dariya?.. nan suka fada mata itama dariyar tayi tareda cewa Oh! yaran nan Allah ya shirya munku sannan tafita tabar suna firar su gawani sha'awa. *_Bayan kwana biyu_* ******* Su *Deeya* basufita ko'ina dama can suba masu yawon banza bane, kuma *Deeya* tasaki jiki abunta sosai tama manta da wai akwai aure akan ta; sai sha'anin su sukeyi itada *Feeya,* saidai kuma takasa mantawa da "abunda *Hmm Habeeb* yaimata abun ya tsaya mata arai tana yawan tunawa sai tayi murmushi, Ganin tasaki jiki sosai ne yasa Hajiya tafara gyarasu cikin hikima, haka itama lnna sannan su Adda Mamu suma suna yin nasu gyaran nasu na musamman, gefe kuma gasu goggo Lanti suma suna yin nasu kai abunda ba'acewa komai. Inna ce zaune adakin su *Deeya* yayinda suma suke zaune a gabanta "KO wacce hannun ta rikeda cup din glass wani, hadin magani ne tayi masu shine ta tsare su sai sun shanye, *Feeya* takusa shanye nata amma *Deeya* ko rabin cup ba tayi ba. Cikin yanayin tana shagwaba tareda yamutse fuska, tace don Allah lnnan Mu kiyi hakuri anjima zan sha kinji?..hararan ta lnna tayi tareda cewa ba zanyi ba saikin shanye shi tas! yanzu kinbani Kofi, ga yar'uwan kinan takusa shanye nata amma ke kin tsaya shiriri ta. tace to zansha amma ki karbi wannan kibani najiya din nan yafi dadi ko sweet *Feeya*?..Kai ka wai ta gyada batayi magana ba domin gaba daya baurin maganin yahade mata baki, Inna tace to sarkin kwadayi babu irin shi kun shenye tun jiya, don haka ku shenye yanzu ku bani Kofi na haka nan, dai suka shanye badan sun soba sannan tadauki kofunan ta tafita. "Ajiyar zuciya *Deeya* tayi tareda kwanta wa kan kafe tayi rigingine tana kallon sili tace don Allah sweet *Feeya* tashi mu gudu daga part din nan, idan ba haka ba anjima ma sake bamu zatayi tsaki tayi tareda cewa to aiko muje can part din itama Hajiya mu maganin zata bamu Cikin sanyi murya tace "eh kuma fa haka ne suma su Adda Mamu duk kanwar jace yanzu tashi muje gidan Hajiyar su Hmm *Harees* mu boye, bamusu *Feeya* ta tashi suka fita. *_Nikam nace a ah su Feeya ba'ajin kunyar sarakuwa_๐Ÿ˜€* Zasu shiga part din Hajiya shikuma *Harees* yana shigowa da motar shi yagan su" amma su basu gashi ba, murmushi yayi tareda cewa hmm! su me Darajata kenan duk yadda akayi sunzo 'boyewa ne, bayan yaifakin sannan yafito yanufi part din shi. zaune suka iske Hajiya a falon kasa bayan sun gaida ita ta amsa ciki farin ciki, tace yasu Hajiya sukace lafiya, Hajiya zamu kwanta idan azo Neman mu kice munyi bacci inji cewar *Deeya,* Dariya tayi tareda cewa to amma banda Hmm Ku KO?..dariya sukayi sannan suka haye sama dakin ta suka shige suka kudindine akan faffadan gadon ta *Feeya* tace ke nifa bacin gaske zanyi *Deeya* tace nima ai dai-dai lokacin da sukaji murya *Harees* yana cewa two brads, wato amare biyu dariya sukayi domin sunan na dasu yake. Dasauri *Feeya* tarufe da bargo tana dariya dai-dai lokacin da *Harees* yashiga kun nan shi makale da waa *Deeya* tace Hmm *Harees* sannu da dawowa, yace yauwa karbi nan mijinki ne yake son magana dake jitayi gabanta yafadi, bin wayar tayi da ido ba tareda ta karba ba yace ke karbi mana dasauri takarba jikinta na rawa. Shikuma yanufi gurin *Feeya* yana cewa me Darajata tashi muma muyi soyayar mu, Cikin jin kunya tace a ah nidai bacci zanyi yace to yi hakuri ki bude mun fuskarki nagani, ahankali tabude fuska ta na dariya yace yauwa ko kefa to me zan samu??. tace bakomai yace kai! haba kodan kiss din bazan samu ba?. tace kai๐Ÿ˜ณtareda bude baki saikuma taja bargo tarufe kanta tana dariya, Shima dariyar yayi tareda cewa bani mana zan koma office ne, tace nidai ba ruwa na idan "Hajiya taji ka dariya yayi yace to shikenan natafi tunda bazaki bani ba, Queen of beauty idan kin gama ki kawo mun wayar ina falon kasa sannan yafita. Ita kam *Deeya* tunda ta karbi wayar tasa akunne ba tace komai ba, sai *Habeeb* ne ke tafaman magana shi kadai, zaune yake acikin faffadan office din shi saman lallausan kujera me juyawa yayi release sosai akujeran idon shi rufe, Sanye yake da wata dakakkiyar shadda dark green dataji aiki kanshi babu hulla suman nan sai kalli take hannun shi daure da agogon gold, kafarshi kuma sanye cikin farin takalmi sauciki kamshin turare sai tashi yake ajikinsa, ahankali yake juya kanshi akujeran cikin cool voice din da harshan turanci yace *Leemah ta* kice wani abu mana umm?,. Inason naji sweet voice dinki ne da nayi missing kwana biyu, Cikin sanyi murya tace Ina wuni yace lafiya lau *Leemah ta* nayi kewarki sosai fa, fadamun kema kinyi kewata?.. ba tace komai ba sai faduwa da gabanta yake aikin yi, haka dai yaita janta dafira daga umh sai um-umm! take cewa. Daga karshe yace mata ranan juma'a yana nan zuwa kar ta manta da jagwalgwalon nan๐Ÿ˜‚,dariya tayi me sauti har saida yaji ta cikin waya, ido yarintse domin saida yaji wani irin yarrrrr! ajikinsa Cikin sanyi murya tace ai bazan manta ba, yace yauwa *Leemah ta* ki gaida mun da "lnna da "Baffa ki kuma kula mun da kanki kinji ko?.. Cike da kunya tace Hmm yace byeeee tareda yo mata kiss yace oya to nima kiyomun naji kinji?. *Leemah ta* dasauri tace um-umh tareda cire wayar daga kunnanta tana dariya, shima dariyar yayi tareda kashe wayar. Sannan taje takaima *Harees* wayar shi tadawo suka fara fitar *Habeeb* Da *Harees,* sai yamma lis suka koma part din lnna kasan cewar can suke da kwana, murmushi lnna tayi data gansu tace sannu ku *_yan gudun hijira_* (Littafin dr Zain) tace saidai kuma kun gudu amma baku tsira ba, ga sauran maganin nan ku zauna kushanye kubani ko fina. fuska suka yamutsa tareda zama sai kuma suka kalli juna suka kyalkyace da dariya. ******* Kwanci tashi a saran me rai yau alhamis kuma ayau ne su Adda Mamu suka shirya ma su", *Deeya* Da *Feeya* sister's night only family ne sai kawayan amare kawai, Wanda za'ayi yanzu agarden karfe 8:30pm na dare. "Amare sunsha gyara sungaji sunyi matukar kyau, sanye suke cikin wani hadadden bakin materi me ratsin ash color, dinki riga da siket ne irin me bajewar nan ne takasa kayan yadan kama jikin sun kadan, ta yadda sharp dinsu yafito gwanin sha'awa sai aka daura masu goggwaro ash color jaka da takalmi suma ash color, kai gaskiya amare sunyi kyau sosai kamar kasa ce su ka gudu. Sannu ahankali suka fito daga part din Hajiya suka nufi garden inda yan'uwa kejiran su, yayinda su Salma ke take masu baya har suka isa suka zauna akujerun da aka tanadar masu, bayan sun zauna sai Adda mamu tabude taroda addu'a sanna akafara gudanar da liyafar, Yayinda *Harees* yakoma gefe ya zauna yana video call da *Habeeb* wanda yakejin kamar yai tsuntsu yazo Bauchi, shima ayi sisers night din dashi saidai kuma ba hali, sai misalin karfe 10:00pm sannan aka gama kowa yatafi gidan. "Aban garan *Jana* kuwa duk wani abunda ake ba uwargida nafadar kishiya "an bata harda kayan daki saida Abba yasake mata wanda iri daya akai mata dasu *Deeya,* sannan Hajiya da lnna sunata lallashin ta to ba laifi ta dan sa ki jiki ana hidimar bukin da'ita. ****** Washegari Jumma'a akasa amare kalle kuma ranan za'a daura auren *Feeya* Da *Harees* bayan an sauko sallar juma'a, *Habeeb* kam yana idar da sallah juma'a yahawo jirgi yataho sai ce ma masu tsoron shi su iske shi gida, yana'isowa ana kokarin daura auren don haka ya tsaya aka daura dashi, bayan angama Sannan yashiga part din Hajiya, atunani shi su *Deeya* na can domin ita kawai yake so yagani, koda yashiga mutane cike a falon kasa sun ke waye Hajiya gaida ita yayi Sannan yace lna su *Deeya?* akace suna part din lnna, don haka yafito yanufi part din shi Domin yana jin kunyar shiga ne manta. Dasauri *Jana* ta tare shi tayi masa sannu dazuwa, Shafa ma dake kusa da'ita taimasa ya amsa fuska ba'annuri yanufi dakin sa, Shafa tace da *Jana* tashi muje ki zuba masa maganin daya fito "ya tsallaka, tace lna aina fasa na bari sai munje abuja sannan yadda zanji dadin gasama yar'isa gyada ahannu, dariya Shafa tayi tareda mikama *Jana* hannu suka tafa tace shegiya ashe dai kanki yanaja wani lokaci tace sosai ma kuwa, shikam *Habeeb* yashiga ya cire kaya yashiga toilet. Da misalin karfe 4:00pm amare da angwaye suka fito cikin shirin fulani wanda za'ayi agidan su *Harees*, sunyi kyau sosai ko wani ango yana like da amaryar sa musamman *Habeeb* jiyake kamar yamai da *Deeya* Cikin sa itakam duk kunya yacika ta, hannun ta yana cikin nashi amma jikinta rawa yake Cikin rad'a yace *Leemah ta* ki saki jiki mana, cikin shagwaba tace to nidai kasa kar mun hannu yace bazan iya ba *Leemah ta,* ahaka dai suka karasa gurin. *Jana* kam duk haushi yacika ta sai tsaki take da hare-hare kasan cewar taje gurin, cikin nutsuwa ake gudanar da fulani day din karfe 6:00pm angama. Karfe 8:00pm akatafi hadadd'en dinner da aboka nan su suka hada masu, wanda sukai ma suna da _only friends_ wato abokai kawai don haka dinner babu mutane sosai shiyasa tayi matukar kaya tuwa, daga abokai da suka saka kaya iri daya farar shadda da akaima aiki da bakin zare, sai kawaye Suma kaya iri daya suka sa bakin material, su kuma amare suka sa blue material, angwaye suka sa farar shadda sai akai mata aiki da blue zare, gaskiya sunyi kyau sosai dinner ta hadu sai karfe 10:00pm akagama, *Jana* kam cewa tayi bazata ne ba saboda ba zata'iya gani kayan takaici ba๐Ÿ˜ฅ. *_Nikam nace dataje da taga kayan takaici kam๐Ÿ˜‚_* Domin da'akace" *Habeeb* yaba *Deeya* cake abaki sai yasa abakinsa sannan ya rungumeta; yahade bakin su yasa mata cake din, kunya kamar zata kashe *Deeya,*๐Ÿ˜€ Koda suka dawo agajiye ana ina amare akai su dakin su ba'agansu ba, "Ashe suna can sun shige dakin Abba sun kwanta suna baccin gajiya, saida yashiga shi da Hajiya sai su kagan su" dariya sukayi zata tashi su sai Abba yace ta kyale su" sai gobe. **** Washegari akai masu jere, da misalin karfe 8:00pm na dare, Abba yace akai ko wacce dakinta; saidai me cewa sukai basu san wannan zancen ba, domin kuwa rungume juna sukai suna kuka gwanin tausayi ganin haka yasa Abba yace abarsu har gobe, idan su *Deeya* suka tafi Abuja dole *Feeya* ta yadda akai ta dakinta. Haka ko akai da gariya waye lokacin da zasu tafi dakyar aka rabasu, *Harees* ya rungume *Feeya* zuwa part din shi. *Habeeb* kuma yashiga da *Deeya* mota dazaya shiga kasan cewar *Jana* sun shiga guda itada yara dayar kuma masu tsoron sane, haka suka dauki hanyar zuwa Abuja *Deeya* na rungume jikin *Habeeb* tana sauke ajiyar zuciya. *_to readers kubiyo ni kuji wata wainar za'atoya a'Abuja_* Muje zuwa A *_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya) Tareda โœ๐Ÿฝ ๐ŸŒนMeenart๐ŸŒน [7/2, 11:48 PM] My Ameena: ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ _*KYAUTAR ALLAH CE*_ _(Labarin Sadeeya)_ ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ 3โƒฃ0โƒฃ WRITTEN By ๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ OR ๐ŸŽ *MEENAT* ๐ŸŽ SADAUKARWA *GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)* ___________________ ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_ ___________________ ~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~ โœ๐Ÿฝ _*Bismillahirrahamanirraheem*_ "Basu dad'e dafita garin Bauchi ba bacce yasace *Deeya* yayinda Direbobi keta sharara gudu akan titi, itakam tana kwance ajikin *Habeeb* abunta sai sharan baccin ta take hankali kwance, yayinda duk wani mutsin Da zatayi sai *Habeeb* ya gyara mata kwanciyar ta, tareda sake rungumeta ajikinsa sosai yana me shakar daddad'a kamshin turaran ta,yayinda yake jin zuciyar sa tana wani irin tsinkewa sai yana ji ajikin sa kamar akwai wani abun dazaya rabashi da ita. ****** Saida misalin karfe 5:00pm suka isa Abuja kasan cewar dama bawai sun tashi dawuri bane, kai tsaya _housing senetors_ suka nufa dake _Maitama_ gidan *Habeeb* upstairs ne dai-dai kofar gidan direbobi suka tsaya, _Alhamdulillahi!_ shine abunda *Habeeb* yafurta akasalce, Domin wani wani irin kasala ne yasauka ajikinsa tun lokacin da *Deeya* ta kasan ce kwance ajikinsa sosai yakeji wani irin matsanancin kasala, ido ya kurama kyakkyawar fuskarta me cike da haiba da kwarji gawani irin annuri datake fitarwa na musamman wanda wannan sirrine na amare. Shikam bai taba ganin wacce bacci yayima kyau irin *Leemar* shiba, idonsa yarintse yanajin wani irin *SONTA* yana ratsa shi, saidai kuma yanaji ajikinsa kamar wani mummunan al'amari zaya faru dasu, ahankali yafurta yah ilahee wannan baiwa taka tun ranan da tazo duniya nayi tozali da ita nakeji wani al'amari me girma game da ita, Wanda bansan ko menene shiba sai sannu ahankali na fahimci cewa "Ashe kaunar Ce kadasa mun a *ZUCIYATA,* nashiga wani ahali lokacin narasa yadda zanyi ta zamo mallakina; ashe ma bansani ba tuni ka mallaka mani ita; "Aranan dana fahimci haka nayi *FARIN CIKI* mara musaltuwa wanda har yanzu ina cikin shi, duk da cewa inajin tsinkewar zuciya amma hakan bazaya hana ni godia agare kaba Da wannan *KYAUTAR* dakayi mun, ta mallaka mun abunda *RUHINA* yake kauna gangar jikina ke *MURADI.* yah! Allah nagode! nagode!! nagode!!! saidai kuma inaji kamar akwai wani al'amari dazaya faru tsakani na da "ita; wanda kai kasani amma ni bansani ba domin bansan gaibi ba, saidai KO" menene zaya faru tabbas nasan *KADDARAN MUCE* nida ita don haka yah Ubangiji inarokon ka, kasa yazo mana da sauki ameen yah Allah. "A hankali yasa zara-zaran yatsunshi yana shafar cute fice dinta tareda fadin wake up sleepy beauty mun iso, ahankali tabude fararan idonta wanda KO" kuka tayi ba suyin ja to balle bacci, salati naji tayi tareda kura masa lumsassun idanun ta masu kashe masa jiki, lallausan murmushi yasakar mata tareda cewa, *Leemah ta* mun iso kinata bacci. "Ahankali tamike daga ajikinsa tajingina kanta ajikin kujerar dake gaban ta, wani irin nauyi taji kanta yanayi; hannun yasa yadago kan nata tareda cewa *Leemah ta* ya'akayi ne??..; batace komai ba saidai tayi rau-rau da ido zatayi kuka, Dasauri ya rungumeta tareda cewa "a ah *Leemah ta* karki yi kuka kinji fadamun menene??..Cikin rawar murya tace yanzu shikenan bazan sake ganin my sweet *"Feeya* ba, da "Hajiyarmu Da "lnna ta da "Baffa na ba?.. yace haba *Leemah ta* zakigan su mana, cike da shagwaba tace to sai yaushe?.. yace sai "an kwana biyu zamuje kigansu" kuma kafin muje baga waya ba sai kuringa gaisawa, dasauri tadago fuskarta dauke da annuri tace Lah! yauwa Hmm *Habeeb* inama Waya ta dakace nakawo zaka samun charge da games?.. (Kasan cewar jiya yasiya masu tsadaddun wayoyi masu kyau ita da *Feeya*) murmushi yayi cike da zolaya yace ayya aiko mun barota gida jikin charge, ido tazaro cike da shagwaba tace Kai! Hmm *Habeeb* jikinta charge kuma? yace "eh tace to yanzu idan zankira sweet *Feeya* dasu Inna fa?..yace sai na aramaki tawa, to idan zanyi games kuma fa?.. ta karashe fadi tareda turo baki. Dariya yayi tareda Kai hannun ya kama pink mouth dinta yace to sarkin buga games ga wayar kinan Cikin bag dinki, inajina ma anata kira kilama Sofee Ce" dariya tayi tareda karban jakar dasauri tana kokarin budewa sukaji "Ana kwankwasa glass din motar. *Jana* kenan wacce tacika tabatse tayi fam kishi kamar zaya kashe ta, gani tun dazu suka iso duk sun fito daga mota har da direban daya tuko su *Habeeb* tuni yadade da fitowa, amma su suna cikin mota basu fito ba, to KO" uban me sukeyi acikin motar Oho!. inji cewar *Jana* kenan๐Ÿคฃ. Jin shurun yai yawane gasu kuma tsaye suna jiran su", shiyasa ta kwankwasa glass din saboda irin me dubu, nan ne Wanda na waje baya ganin na ciki saidai kai dake ciki kaga shi nawajen, "Ahankali *Habeeb* yabude mota tareda zuro santala-santalan kafafunsa masu saye da bakin takalmi, hannun shi rikeda jamar *Deeya* hannun yamika mata bamusu tasa hannun ta takama, tafito ido suka hada *Jana* ta banka mata wani irin mugun kallon Wanda yasa gaban *Deeya* faduwa, Dasauri tadukar dakai kasa ahankin yadda balallai bane wani yaji tace, la'elaha'ella'antassubahanaka'inniku tun'meenazzalimeen, da gudu lili mama tazo tarike hannun *Deeya* tana dariya tace Aunty *Deeya* tale jamu kwana KO?.. dariya *Deeya* tayi tareda gyada Kai alamar "eh tace ada Kai KO" Dad? tafadi tana kallon *Habeeb* murmushi yayi tareda cewa yesss my lili, Sannan yakalli dan matashin direban dake tsaye yace Saminu a shiga da kayan ciki mana, Cikin girmama wa yace ranka yada'e ankai- tun dazu yace OK " mujen ku ciki KO?.. *Leemah ta* Cikin sanyi murya tace to hannun ta guda na cikin nashi, gudan kuma yana rikeda lili mama suka nufi cikin gidan. Cikeda takaici *Jana* taja tsaki mtww tareda Jan hannun Junior suka bin bayan su aranta kuwa tana fadi zakuga ne baku da wato. Tadaga kafa za shiga kenan sai kuma tafasa, Dasauri *Habeeb* yajuyo yakalleta yayinda yaji kirjin sa yafara bugawa, Cikin fargaba yace menene?.. bata bashi amsa ba saidai tasaki hannun sa, yayinda tadaga hannun ta duka biyu tafara jero Addu'a kuri yai mata da ido wani irin son ne yake ratsashi har yanajin tsigar jikinsa yana tashi, tadauki lokaci tana addu'ar sannan ta Shafa wanda tare suka Shafa da *Habeeb* harda lili mama data shafa tareda fadin ameen Aunty *Deeya*๐Ÿ˜€. Sannan suka shiga wani abun mamaki shine tsarin gidan kamar nacan Bauchi saidai akwai ban-banci kadan, babba falon kasa yana dauke da set din kushi manya-manya da kuma t.v bango da fridge sai d'a kuna biyu, _sukam bansa yasuke ba don banshiga ba,_ sai guda shikam wannan kicin ne domin gashi nan arubuce. Kallon su *Habeeb* yayi yace nan ne falo na ga dakina nan wancan kuma na Junior wannan kuma kitchen ne kungani ai so mujen ku sama na nunawa KO" waccen ku dakinta. Still hannun shi yana rikeda na *Deeya* suka nufi sama, falon saman baikai nakasa girma ba shima yana dauke da daku a uku sai set din kushi tareda table a tsakiyar falon, sai babban t.v bango da kuma fridge, dakin farko yace ke *Jana* gadakin ki ke kuma *Leemah ta* ganaki nan wannan kuma na my lili, Dasauri lili tace Dad ni wajan Aunty *Deeya* Jan kwana yace OK" Dasauri *Jana* tace gaskiys BB ni wancen dakin nakeso, wani irin kallo ya watsama ta tareda cewa tsarina kenan kuma babu wanda ya'isa ya chanja mun, kuma da wannan dakin da

Chapter 12 of 42