Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)* __________________________ ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_ __________________________ ~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~ โœ๐Ÿฝ _*Bismillahirrahamanirraheem!!!*_ _NOT EDITS_ Yanzu saboda Allah hali dubu na tun dazu kuka dawo amma kika gagara shigowa kibasu nono su sha ko?...wai meyasa kikeyin haka ne umuh?.. kodan kinga suna da hakuri shiyasa ko?.., hum to bari kiji nafada maki ranan da duk kika cikasu, suka ture maki zaki sani ne ke bakisan halin tagwaye ba ko?..dasauri ta'isa gurinta cike da tsoro tace wayyo Hajiya ta me sukeyi?.., hararan ta tayi tareda cewa bansani ba nidai karbeshi kibashi yasha, tun dazu yake tafaman kuka karban shi tayi tareda turo baki sannan ta zauna yayida Hajiya fuskar ta had'e, taduka tadauki *Haneef* dake kwance akan dan keken shina jarirai yanata butsul-butsul da hannun dakafa da'alama shima nonon yakeso. Cikin wantar da murya *Deeya* tace eyya yi hakuri hajiya ta karkiyi fushi dani, kinga ko muna kan hanyar dawowa ne sai "sweet Hmm na yakirani yace" gashinan zuwa shine nashga na hada masa abinci, saida ta zauna sannan tace hum sarki me sweet hmm to Allah yakawo su lafiya, murmushi tayi tace ameen Hajiyar mu dai-dai lokacin da take kokarin ciro nonon, tana fadin sorry *Haleem* din mom *"Feeya* karbi kasha kafin mom dinka tazo tayi mun masifa nabar mata yaron ta yana kuka, bata gama rufe baki ba saiga *Feeyar* tashigo, da'alama maganar tafada akunnan ta domin kuwa cewa tayi aikin kyauta dakika barmun yaro yanata kuka, kallon ta *Deeya* tayi cike da mamaki tace wai dama kina labe ne?..hararan ta *Feeya* tayi tace "eh ina laben ne, tace to dai labe ba kyau "eheee don haka gara mutun yadaina ato yakareshe fadi tana dariya kasa-kasa, tsaki tayi tace ke ni rabani dawani labe labe kina nufin tunda muka dawo sai yanzu kika shigo zakiyi feeding din su?..hajiya ta mike tareda mikawa *Feeya* *Haneef* tace aikam sai yanzu tashigo, karban shi *Feeya* tayi yayinda Hajiyar tashiga daki tabarsu. kallon *Deeya* tayi tace wai da gaske sai yanzu kika shigo?..koda yake da gaske ne tunda gashi nan har wanka kikayi kika chanja kaya, tace yes! na tsaya hadama sweet hmm abinci ne shiyasa so bayan nagama nayi wanka to yaki kaga wanka?..ta fadi tareda dage mata Kira daya, tsaki tayi tace to bakiyi kyau ba dariya tayi tace dadin abin badan mutun nayi ba nayine sbd sweetie na, Wanda na tabbatar idan yazo yagani zaya yaba eheee, tace to ina ruwan wani eye?. tace ah! da duwanshi mana tunda gashi nan yakushe tafadi tareda yin gwalo, tace ke! na kula dake gaba daya kinfi damuwa da "Hmm *Habeeb* akan twice dina KO?.. tace Kai tawan ashe dai kinga ne, tace ke! *Deeya* watakullaha! takarashe mata da fadin hayyismakuntum my dear muji tsoron Allah adik inda muke, ke! kwarai da gaske nafi damuwa dashi sbd "shi nafara gani kafin su" ke! ni kyaleni da zancan yaran nan naki haka, ki fadamun inda kika barmun my "Affan boy?.. tace ban saniba idan kuma za'a shakeni ne sai na fadi inda yake to bismillah, tace ah! name ai zancen shaka be ta shiba kawai saita fisge nonon ta daga bakin *Haleem* aikam yasaki kuka dakarfi kasan cewar har yafara bacci, Dasauri tace wai meye kikeyi haka ne?..tace Oho! mlm amsa mun ina boy dina yake?..tace to dalla "yana gurin lnna ta sai ki bashi ya sha ko?., tace Oh! yanzu naji batu sannan ta cigaba da bashi nonon tanayi mata dariya, itama dariyar tayi tana fadin kai my sweet *Deeya* baki da dama sannan suka fara fira. Bayan tagama bashi yai bacci saita kwantar dashi sannan takarbi *Haneef* shima tana cikin bashi yai bacci, don haka ta tashi ta kwantar dashi dai-dai lokacin wayarta tayi kara tana dubawa taga *Habeeb* Ne, murmushi tayi tareda dauka video calla ne, kafin duk tayi magana yace my honey *Leemah* mun shigo fa, tace to alhamdulillahi Allah nagode maka daka dawo mun da my sweet Hmm lafiya, u are highly wlcm my real one lallausan murmushi yayi yace thanks dear, itama murmushi tayi tace sai kun karaso yace Ok tareda kashe wayar. Sannan ta kalli *Feeya* wacce itama kallon ta take gira daya ta dake mata tareda fadin, yadai mom din twice matar dr to nifa zanje natari habiby na don haka ga yaranki nan, Kai ta girgiza tace to sarki me habiby sai kin dawo amma fa akulamun da hmm na da kyau, murmushi tayi tace karki damu hakan aifarilla ne tace Oh! my sweet *Deeya* Allah ya shirya ki dariya tayi tace amin tareda nufa hanyar fita dai-dai lokacin da Hajiya tafito tace ah! ita kuma Ina zata?..tace hum Hajiyar mu kyale ta Hmm *"Habeeb* ne ya'iso shine zataje tarban shi, cike da farin ciki tace oh! hali dubu na kenan shidai wannan hmm din ba'a hada shi da kowa ba, tace shima aibe hadata da kowa ba domin idan kanason ganin bacin ran shi to kataba *Leemarsa,* yanzu zaku kwashi yan' kallo, murmushi tayi cike da jin dadi tace to aigara haka, tunda kulawar da be samu da ba yanzu yana samu aidole yaki hadata dakowa tace gaskiya kam hum ai wlhy sai yanzu hmm yasan yayi aure, tace aikam to Allah yabada zaman lafiya da zuri'a dayya ba, tace amin, kudai ta kula da mazajen ku dariya tayi tace to hajiyar mu, tace yauwa sannan ta zauna suka fara tattaunawa tsakani y'a da Uwa. *_Bayan kwana biyu_* ****** Ranan lahadi da misalin karfe 7: 30am na hango *Jana* tana tazabga uban sauri kamar mahaukaciya sanye take da zani daban riga daban, hijab din datasa yayi cumun-cumun kamar an kwato shi abakin akuya, kallo daya zakai mata kaga ne bata cikin hayyacin ta tana tafiya ta waiwaye kamar mara gaskiya, Sosai take sauri kamar zata tashi sama saida tayi tafiyar kusan awa daya da rabi sannan ta'isa anguwar su akafa, kamar koda taushe tashiga gidan ba tareda sallama ba direct babban falon tanufa Baba yana zaune yana kallon Labarin safe, kai yad'aga ya kalle ta sannan ya girgiza kai, yace ai sai ke wai sallama Murjanatu sai ta gagareki sai kace ba yar musulmain ba?..Allah ya shirya ki, zama tayi tana fidda numfashi kamar tayi tseren gudu fuska had'e yace lafiya ki kazo mana gida haka tunda uwar safiya ke! ashe bama nace Karna sake ganin ki gidan nan idan ba tareda yaron mutane ba?.. shine kikazo ba kuma tareda shiba sbd ban isa nafada maki magana kiji ba ko?..to tashi maza kifitar mun agida kinji ko?..Cikin tashin hankali tace baba kaimun rai wlhy bazan iya sake kwana gidan can ba sbd kullm sai nayi mafarkin wani katon mutun baki yana bina da wuka zaya kashe ni, yace Murjanatu kenan ke atunanin ki Allah bazaya hukun taki akan abinda kike aika tawa ba?.. hum to kinyi kuskure dole ne ki fuskanci mummunan hukunci agurin ubangiji wanda na tabbatar shine kika fara fuskata tun yanzu, hum ZINA fa kuma da aure akanki Murjanatu harda yaranki Kai ko bakada aure ai ZINA ba'a banyi bane, tunda Allah yahane mu da yinta amma ke kikeyi KO?.to kisani ni bazan zauna da mazinaciya agida na ba don haka tashi ki tafi gidan ki kuma ki, tabbatar kin kawo mun yaron mutane kinji. Cikin kuka tace Baba dan allah kayi hakuri har ado yadawo kuma wlhy na daina ZINA, yace dayafi maki alkhar dube kifa dan Allah dukkin lalace ke kodaga haka ma ai ya'isaki gane ZINA ba'abiyi bane, sai kuma yafara yimata nasiha me shiga jiki, cikin sanyi murya tace to baba inasan nafada maku wata magana amma sai agidan su *"BB* agaban shi da "iyayanshi harda yan'uwan shi dan Allah baba kaji?.. Shuru yayi yana kallon ta inda yahango nadama akwayar idon ta, cike da tausayin ta sannan yadaga kai ya kalli dija wacce tafito tunda zatayi tsaye tana jinsu yace tashiga ciki, kibata abinci ta karya sannan tayi wanka ta sake wasu tufafin dan banza muje da'ita gidan mutane haka ba, bari nakira yayan su yazo yakai mu tace to tareda tashi tashiga daki Dija kam tuni tashige daki. Waya yadaga yakira Abba Bayan sun gaisa yace mashi ga sunan zuwa shida iyalinshi don allah shima yakira iyalanshi sbd *Jana* zata fadi wata magana amma sai agaban Alh *Habeebu* da kuma su, yace to ba damuwa dama akwai meeting da sukeyi duk ranan yau da karfe 10 zuwa 11 don haka kowa zayazo Insha'allah yace to shikenan sai sun zo, yace to Allah yakawo su lafiya yace amin tareda kashe wayar sannan yakira jafaru yadama shi. ****** Misalin karfe 10:15am su *Jana* suka isa gidan su *Habeeb* direct part dasu Abba suka shiga sun'iske mutane cike duk kowa yazo amma banda *Deeya* da *Habeeb,* nan dai suka gaggaisa sannan suka zauna, *Jana* kam sai rarraba ido take alama *Habeeb* take duba. Abba yace wai yau lafiya har yanzu su na Allah basu shigo ba?. Kai *Hafeez* tashi ka dubosu,har da zaya tashi sai su kaji daddad'an kamshin turaren su wanda yariga su shiga falon, cikin nutsuwa suka shiga bakin su daukeda sallama *Habeeb* yana gaba rungume da *Haleem,* *Deeya* tana biye dashi rugume da *Haneef* sanye suke da wata ubansun shadda me ruwan gwal kallo daya zakai mata kane me tsada ce, irin dinki da wayayyu samari yanzu ke yayi, ita kuma dinki dogon riga tayi me stones work irin Wanda manyan mata yanzu ke yayi, yaran kuma sanye da wasu kyawawan riga da wando me ruwan ja da yalo gaskiya sunyi kyau sosai, yayinda suka dauke hankalin mutane falon suka kuma birge su sosai. Bayan sun gaggaisa da mutane sannan suka zauna yayinda kowa keson daukar twice kunsan suda farinjini saida kam tuni iyayensu sun karbe su, wato *Feeya* takarbi *Haneef* yayinda *Harees* yakarbi *Haleem,* gyaran murya Abba yayi haka ne yasa kowa yanutsu, sannan Baffa yayi addu'a bayan ya gama sai Abba yafadi abinda yatara su duk da sun saba, amma nayau akwai dalili sannan aka umarci *Jana* tafadi abinda takeson fad'a, Wacce gaba daya hankalin tayana kan *Habeeb* jitayi kamar taje ta rungume shi saboda so, sosai take kallon shi Mrs senato *Habeeb* kam be masan tanayi ba asalima hankalin shi nagurin Affan daya karba hannun *Hafeez* wasa yake mashi ahankali sai yanata wangale baki, tsawa Jafaru yadaka mata da fadi mlm kefa ake saurare aikam tayi firgigit tadawo hayyacin ta, domin tuni ta lula duniyar tunani sabuwar rayuwa itada *Habeeb* still idon ta yanakan *Habeeb* din tace... *_Kuyi hakuri nazo wannan page din yazama na kashe amma allah be nifa ba_* Muje zuwa A *_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya) Tareda โœ๐Ÿพ ๐ŸŒนmeenat Lufhat๐ŸŒน [11/9, 10:19 PM] My Ameena: ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ _*KYAUTAR ALLAH CE*_ _(Labarin Sadeeya)_ ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ 8โƒฃ7โƒฃ *_END_* WRITTEN By ๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ OR ๐ŸŽ *MEENAT* ๐ŸŽ *_DAGA MARUBUCIYAR_* *_DA SANNU_* *_ZUCIYATA CE_* *_AFSANA_* *_(Labarin na)_* *_KYAUTAR ALLAH_* *_(Labarin Sadeeya)_* SADAUKARWA *GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)* ___________________ ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_ ___________________ ~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~ โœ๐Ÿฝ _*Bismillahirrahamanirraheem*_ _NOT EDITS_ umh! ummh dama zan fad'a maku gaskiya cewa Junior ba d'an *BB* bane gaba daya falon aka dauki salati, *Habeeb* kam ajiyar zuciya yasauke tareda lumshe ido aranshi yana godiya da Allah yanuna mashi wannan Rana, yayinda dija ta mike zumbur cike da tsoro da tashin hankali tace me kika ce?...tace "eh wlhy dija da gaskiya nafada "Junior badan *BB* bane dan ado ne, aikam tuni tazube kasa sume,gaba daya falon yarikice da hayaniya, Binta kuka tasaki tareda dago dija tana Allah ya'isa tsakanin su da *Jana,* baba kam tunda tafadi wannan muguwar maganan kanshi ke kasa tsabar bakin ciki da kunya, jiyayi kamar kasa tabude yashige nan da nan su Hajiya suka rufe Dija ana yimata fiffita, dasauri aka dauko ruwa aka yayyafa mata saidai numfashin be dawo ba, cikin tashin hankali Abba yace da *Harees* yaduba ta kasan cewar dama yana zuwa da kayan aikin shi gurin meeting din, koda wani abin zaya faru, don haka yafara bata taimako cikin gaggawa. Ahankali baba yadaga Kai ya kalli jafaru wanda shima kallon Baban yake, aranshi yana rokon Allah yasa kar yashiga wani haki makamancin wanda Dija take ciki yanzu, yayinda zuciyar shi take cike da bakin cikin abin kunyar da *Jana* tayi azuri'arsu, lumshe ido baba yayi wanda banga ne nufin shi ba ga mamaki na jafaru naga yatashi da zafin nama yanufi *Jana,* kafin kace me yasakar mata barin makauniya wato yahauta da duka tako'ina aikam tafara ihun neman taimako wanda hakan yadawo da hankalin mutane gurin, Dai-dai lokacin kuma Dija ta farfad'o, cikin tashin hankali Baffa yace subhalallahi! jafaru meye haka kuma idan kaji mata ciwo fa?. rai bace Baba yace mlm yusufa bari ya duki yar banzan yarinya marar mutunci, baffa al-mustafa yace haba Alh idan yayi mata illafa?. cikin gigita dija tace aigara yayi mata kadake ta sosai shegiyar yarinya da haibuwar irin ku aigara farin ku, aikam jafaru yakara karfin dukan ta dakai mata shuri ta ko'ina, cikin tsawa Abba yace Kai! Jafaru kayi hauka ne kashe ta zakayi?..hakan ne yasashi barin dukan nata, yakoma gefe yana maida numfashi. Abba yace kowa yakoma gurin zaman shi ya nutsu Bayan kowa yakoma ya zauna, sai shuru yaratse falon sai sauti kukan Dija dana *Jana* ke tashi, gyaran murya Abba yayi sannan ya kalli *Habeeb* wanda hankalin shi kwance yake yima Affan wasa, tsawan lokaci Abba yana kallon shi yayinda yake nazarin abubuwa dayawa aranshi ahankali, yace Na Allah kaji abinda Murjanatu tace" KO?..cike da ladabi yace "eh Abba tuni naji hakan na shiyasa ma ai tazo ta dauke "shi takaishi gurin Baban shi, Cike "matsanancin mamaki kowa yake kallon shi musamman Abban da Hajiya dasu baba, wanda aranshi yake jijjina halin kirki irin na *Habeeb*. Abba yace na Allah tun yaushe kaji wannan maganar amma kayi shuru baka fada ba?..shuru yayi bece komai ba, yace shin na Allah koshine dalilin dayasa ka saketa?..cikin sanyi murya yace "a ah Abba bashi bane?..yace to menene? nikam zurfin cikin ka yafara bani tsoro irin wannan aisai ka cutar da kan ka, kasani irin wannan maganar ba'abin bari aciki bane, yace abba ai dan'uwa yasani yace ikon Allah amma mu ba musani ba?..yace kuyi hakuri Abba dama inajiran irin ranan yaune don haka yanzu zanfada maku abinda naboye maku, abba yace muna sauraren ka cikin nutsuwa yafadi komai tundaga ranan da ado yakira shi har da awon jinin da *Harees* yayi masu yakuma muna cewa Lili yarshi ce, amma Junior ba dan'shi bane inda yakareshe da fadin mutumin dayasa ce *Deeya* shine Baban Junior. Sosai mutane ke salati kowa yana fadin albarkacin bakin shi, Abba kam be ce komai ba domin lamarin yadaure mashi kai sosai dija kam da Binta sai kuka suke me cike da bakin cikin abinda *Jana* tayi cikin tsananin kunya baba yace don Allah Alh kuyi hakur... dasauri Abba yace "a ah Alh Sani kar kace haka dama can Allah ya kaddari hakan sai yafaru, Baffa yace haka ne nan yai tayi ma baba nasiha kai ya girgiza yace shikenan na gode mlm yusufa kai kuma Alh *Habeebu* Allah yaimaka albarka yanda ka rufa mata asiri Allah yarufa maka da zuri'ar ka baki daya, Alh mun gode sosai Allah ya'albarkaci zuri'ar ka gaba daya falon aka ce ameen sannan yamike yace to mu zamu koma su Baffa sukace to a sauka lafiya, Da sauri yafita rai bace yayida ahalinsa suka tashi suka bishi *Jana* kam fuska duk ta kumbure dakyar take tafiya sai wai-wayen bayan ta, take tana kallon *Habeeb* Wanda bema san Allah yayi ruwan tsiyar taba. Suna fita falon yakaure da hayaniya adda mamu tace Oh! daza'a hada mana zuri'a da bara gurbi, adda Rahma tace hum kedai bari *Feeya* tace ai aunty *"Jana* tayi asara arayuwar wlhy Kai Allah yasa Lilin Daddy bata nan, sosai suke fadin albarkacin bakin su su hajiya da lnna suma suna ta tattaunawa akan wannan al'amari, tsawa Abba yadaka masu shiyasa sukai shuru, ita kam *Deeya* ba tace komai ba asalima hankalin ta yana kan *Habeeb.* Ahankali yadaga Kai suka hada ido yasa kar mata lallausan murmushi ajiyar zuciya tayi tareda mayar mashi martani, dai-dai lokacin da abba yace kodai mene yari ga yafaru saidai muroki Allah yai mana tsari da shigowar irin su cikin zuri'ar mu, sannan Allah ya shirya su da'aikata wannan mugun aikin mu kuma Allah yatsare Mu da'aika tashi arayuwar mu, suka ce ameen yace yauwa Baffan *Hafeez* ayi ma addu'a mu tashi yace to. *_Bayan kwana biyu_* ***** *Jana* taji sauki daga dukan data sha gurin jafaru yayinda gaba daya kuma baba da dija sun fita sha'anin ta, abinci ne kawai yazama dole abata gashi yanzu sosai ruwa dake fita agaban ta me wari yakaru harta kai inta zauna kusada mutun yanajin warin, gawasu kuraje dake fito mata a jiki kome ya kwabe mata domin yanzu batada abokin shawara dama Shafa ce abokiryar shawaran ta da badala, to tun wani lokaci da mijin shafar yaka masu suna aikata madigo aikam yaima su dukan tsiya musamman ita Shafan sannan yasake ta ita kuma *Janar* yace idan takara zuwa gidan shi sai yasa yan'sanda sun kamata, don haka sukayi fada da Shafa kaca-kaa domin tace ita ne ta kashe mata aure, don haka rayuwar yai mata tsanani kuma gashi bata daina wannan mugun mafarin ba yanzu har da Junior take mafarki yana kuka yana kiran sunan ta. Kamar yanzu kwance take adakin ta ita kadai bacci take me cike da wahala firgigit ta farka sai gumi take tana zaran ido, takurarran hijab dinta tasa tafita batareda kowa ya saniba bata tsaya ko'ina ba sai gidan yari akafa don haka tayi mugun gajiya kasan cewar da ga unguwar su zuwa gidan yari danisa sosai, sannan dakyar daroko suka fito mata da ado. Yana ganin ta yace Kai shegiya tawajena haka kika koma meyasa me ki haka?.. ban zatayi dashi sai harara datake zuba mashi, dasauri yatoshe yace hum! *Jana* tusaki kayi haka?.. cike da haushi tace kashi nayi baki yatabe yace amma dai bakida lafiya ne ko?.. tace "eh yace ayya kema kin kusa mutuwa kenan, kamar yanda nayi mafarki da kaka ta kusan mutuwa cabbb, kuna nufin tun yanzu zaku mutu?..lallai aiki yaganku nikam ba yanzu zan mutu ba wlhy kuttt! idan na mutu yanzu ai banyi wa kaina adalci ba domin zuciyata cike takeda abubuwa masu yawa, musamman daukar fansa kuma ba makawa sai na dauki fansa don haka kinga mutuwa yanzu batawa bace ko?.. itakam bata iya ce masa komai ba sbd tsabar mamakin jin abinda yake fadi, yace haka ne KO?..Kai ta gyada domin lamarin shi tsoro yake bata yace yauwa kuda ku kashirya mutuwa yanzu sai kuyi ta mutuwa, amma kafin na kike gurin "kakata domin naji ajikina ita ce zata fara shurawa don haka kije unguwar jahun layi na biyu ki tambayi gidan "kaka Ladi masifaffiya, tabaki D'ana kikai shigurin "dija ta'ajiye munshi kafin nafito nan da sati biyu na karbe shi tunda kema mutuwa zakiyi, idan kuma ki kai kuskuren kai shi gurin shegen *"BB* nan na rantse idan nafito sai na kashe duk azuri'ar ku na kashe *"BB* sannan na dauko D'ana, ido tazaro cike da tsoro dariyar mugun ta yasaki tareda juyawa yakoma. Dasauri tafito tanufi unguwar jahun akafa kai aranan *Jana* ta wahala irin wanda bata taba yi arayuwar ta ba, Kamar yanda ado yace haka tayi abin mamaki ce mata akai yau tarasu yanzu ma aka dawo kaita, cike da tsoro ta shiga gidan Junior yana ganin ta yazo dagudu ya rungumeta bayan ta zauna sun gaisa dayan kalilan mutan dake zaman makokin, sannan tafada masu itane maman Junior dama tazo daukar shine makociya iyalle tace Allah sarki *Jana* ba tadade bata karbi kayan Junior suka tafi, Still akafa suka isa unguwarsu sun gaji sosai junior har da kuka yayi sbd tsabar gajiya suna shiga gida *Jana* tazube kasa sume, nan dija tayi kanta da gudu cikin tashi hankali ta dagota tana kiran sunan ta dai-dai lokacin da Jafaru yashigo dasauri, yadebo ruwa aka zuba mata amma bata farfado ba don haka suka dauke ta zuwa asibiti. Asibiti ikitoci sunyi nasara ta farfado, saidai cikin wani masuyacin hali, domin kuwa wani irin ihu take tana fisgan naman jikinta musamman gaban ta sai surutu take barkatai da likitoci suka ga haka sai sukayi mata allura bacci. *_Bayan sati biyu_* ***** Ayau asabar ne aka saki su ado yabito xuciyar shi cike farin ciki da kuma kudirin daukar fansa, saidai kuma baikaga daukar fansan ba rai yayi halinsa, domin kuwa yazo sallake titin dake gefen gidan yarn kenan sai wata babban tankin motar maita ta, takeshi murus sai tattara naman shi akai sannan akai mashi sallah aka kai shi gidan sa na gaskiya wanda yace be shirya zuwa yanzu ba, sai gashi yatafi bazato hum yaruwa kenan, kanataka allah natashi na Allah kuma shi ne gaskiya to Allah yasa muyi kyakkawan karshe amin, Koda labari ya'iske su baba hankalin su yatashi sosai to yaza'ayi haka rayuwata ke, *_su ado dai kam anzo duniya abanza ankoma awofi to Allah yai mana tsari da iri wann rayuwa._* A banga ranan *Jana* kam ba sauki sai agurin Allah hauka tubura, likitoci sunyi bakin kokarisu don ganin tasamu lafiya tunda sungano tana dauke da cutar HIV, sai suka dorata akan maganishi saidai kuma batashan maganin sbd fisge-fisgen datake, kwanata goma sha biyu asibiti suka sallame ta sukace suje suyina gargajiya. Kwanan su biyar da komawa gida tarasu rasuwa me cike da tsoro da al'ajabi domin rainta be fitaba, saida taringa ihu tana fisgan gaban ta tareda fadi duk abin da tayi arayuwa sannan taroki iyayenta gafara da yan'uwanta sannan tace ace *BB* da *Deeya* suyafe mata abinda tayi masu sannan ta cika. Sosai mutuwar *Jana* yataba iyayenta dasu *Habeeb Deeya* kam harda kuka tayi na tausayi ta, sunje gaisuwa baba yake fadawa *Habeeb* sakon *"Jana* yace shi aituni ya yafe mata allah yajikanta sannan yace yayi alkawari daukar nauyin karatun Junior, tunda ga primary har university, su baba sunji dadi sosai suna tasa mashi albarka, bayan ya cika su da kudi da abinci sannan suka tafi zuciyoyin su cike jimami mutuwar *Jana.* *_Hmm su Jana kam ayima duniya shigan zomo kasuwa, wato shiga da gudu fita da gudu batare da guzirin komai ba to Allah ya kyauta, yabamu ikon guziri na alkhairi amee._* *_Bayan shekara daya_* **** Haka rayuwa tamika tsakanin *Deeya* da *Habeeb* kwanciya hankali nutsuwa yawanzu a gares, sosai suke kaunar junan su tareda gudanar da soyayya su cikin aminci da yardan juna, batare da tunani sake faruwar wani abin duk dacewa ana samu yan wasu kalubale akan siyasar *Habeeb* din, saidai addu'ar iyaye data su had'e data al'umma dasu ke matukar taimako tana tasiri sosai akan su, *Haleem* da *Haneef* kam tuni aka yayesu kasan cewar da kansu suka daina shan nono, sbd sudi yarane masu kazar-kazar sunada kwarjini sosai da shigaran mutun tuni suke tafiyar su ko'ina basu cika zama part din suba, saina *Feeya* wacce sukayi matukar sabawa da'ita, sai kuma part din hajiya dana lnna. Ranan wata juma'a da misalin karfe 5:30pm, *Deeya* da *Feeya* ne zaune a falon *Deeyar* tun Bayan da suka gama tattaunawa akan business dinsu dasuke sanna sufara fira, kasan cewar yara suna part din Hajiya su kuma mazajen su sun tafi soro da gujun fulani kamar yanda su kasa ba, Sosai suke fira cike da kaunar juna da aminci sanye suke da wani aren fakista me tsada dakyau, riga da wandon pencil kala royal blue da ratsin yellow sai sukayi rolling da gyalen sunyi kyau sosai. *Habeeb* ne yashiga dai-dai lokacin da *Feeya* tace sweet *Deeya* mu kiyi family planning dakarfi yace what?..dasauri suka mike tareda fadin la! sannu da dawowa, harara yawatsa masu yace no wonder aketa kiran wayoyinku baku dagaba ashe kuna nan kuna shirya yanda zakuyi wa mutane illah ko?. Dasauri ko wacce ta dauki wayarta dake cikin silent taduba aikam miss calls dayawa,baki suka bude tareda zaro ido hararan *Feeya* yayi yace bar part din nan kona fasa maki kai har sai likitan mijinki yai maki dinki, aika dagudu tafita tana dariya. Wani irin kallo yaima *Deeya* sanna yajuya yanufi dakinshi cikin sassarfa Yake taka steps din, aikam da gudu

Chapter 41 of 42