and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
Ba *MUTUM* bace toh" wacece...? yace aljanace ido ta zaro๐ณ tareda cewa aljana kuma...? yace "eh Hajiya bakiga tsananin kyan datake dashi bane...? ajiyar zuciya tayi tareda sakin murmushi tace naganta tun dazu tabbas ita din kam kyakkyawa ce sosai tubarakallah masha'allah, saidai kuma ni banga wani Kaman datayi da'aljanu ba,
Da sauri yace gaskiya Hajiya yarinyar nan aljanace domin kyantan yayi yawa, da dai taga zaya cigaba da zuba mata wauta irin wacce kana ji zakasan cewa "eh shidin *D'AN FARI NE*, don haka saita daure fuska tareda cewa don kyanta yayi yawa shine zakace ita din aljana ce..? Cikin sanyi murya daganin yadda taba rai yace toh" Hajiya ai naji ance sune keda tsananin kyau fiyeda mutane,
tace kaga nifa banason wautan banza idan bazaka tayasu murna da *KYAUTAR* da ALLAH yabasu ba, toh" karka sake alakanta masu 'ya da aljana, shin wai kamanta tsawon shekarun da sukaiyi suna neman haihuwar ne...? yace a ah Hajiya toh" amma ita wannan din kamar ba mutun ba wlhy dana kalle ta saida naji tsoro, 'kura masa ido tayi na tsawon wani lokaci sannan tace hmm...toh" KO" mutun ce ita KO" ba mutun bace suna sonta haka tunda itadin *KYAUTAR ALLAH CE* da yabasu,
Daga haka kuma batasa ke cewa komai ba saidai kawai ta tashi ta'ajie jaririyar saman gado sannan tashige bayi,
shikam *Habeeb* da sauri yaje yadauki jaririyar da Hajiya ta ajiye shuru yayi nadan wani lokaci yana kallonta can kuma sai yace wannan dinma kyakkyawa ce sosai, saidai waccan tafita kyau,
toh"๐ค amma kuma meyasa ke banji irin abunda naji agurin waccan ba...? baki yatabe tareda ajiye jaririyar yanufi shashin shi.
************
Ranan suna jaririyar lnna taci suna *Haleematus Sadeeya* wanda Abba ne yai mata huduba da sunan wato sunan mahaifiyar Baffa wanda hakan ba karamin dadi yaima Baffan ba, ita kuma jaririyar Hajiya taci suna *Safeeya* wanda Abba ne yaba Baffa Yusufa umarni yasa mata sunan da duk yakeso toh" shine yasa mata *Safeeya* domin yana son sunan sosai shiyasa yasa mata, hakan nan dai aka gama suna cikin kwanciyar hankali, yayinda suka cigaba da rainon yaran su cikin kwanciyar hankali.
*_Bayan wata uku_*
Dayin suna Hajiya tana zaune saiga Inna tashiga da sallama tana rungume da *Sadeeya*, Hajiyar ta amsa sallamar fuskarta daukeda fara'a tace ah! Innan *Hafeez* kinshigo...? tace "eh zan shiga wanka ne shine nace bari na kawota, Hajiya tace toh" kawota idan kin fito sai nashiga tace toh" tareda mika mata *Sadeeya* dake ta sharan bacci abunta sannan Inna tafita, *KYAUTAR ALLAH* kenan hakanan Baffa yake cewa itama lnna saboda alkunya *KYAUTAR* take kiranta.
*Habeeb* ne shida *Harees* suka shiga falon Hajiya tsaye suka isketa tana jijjiga *Sadeeya* dake tafaman kuka ga kuma *Safeeya* kwance itama sai faman kukan take, da sauri *Harees* yanufi gurin *Safeeya* ya dauke ta tareda cewa Kai! yaran nan duk kun gigita mana Uwa, tace hmm! kadai Bari tun dazu kuke kukan nan nayi lallashi har nagani amma basuyi shuru ba, ga kukan nasu dazaran daya yafara sai kuma daya shima yafara, tafadi ne tareda mikawa *Habeeb* *Sadeeya* tareda cewa karbi *KYAUTA* kaita nasan yanzu lnnan tafito wanka,
jiyayi gaban shin yafadi sakamakon tunawa da abunda yaji lokacin da yafara daukar ta, kasan cewa tun ranan be sake daukar ta ba sai yau don haka cikin fargaba ya karbeta aikam tuni yaji irin abunda yaji din lokacin daya fara daukar ta, ahankali yace yah! ilahi! dai-dai lokacin da Hajiya takarbi *Safeeya* daga hannun *Harees* inda shikuma yace ma *Habeeb* muje daga can sai mutafi KO...? Kai kawai *Habeeb* ya gyada domin wani irin yakeji ajikinsa, aranshi kam fadi yake meyasa duk lokacin da yadauki *Sadeeya* saiyaji wani irin Abu nayawo acikin ajikinsa,
toh" wai *MEYE HAKA NE*...?
Suna fita dasauri ya mikawa *Harees* ita tareda cewa karbeta shikam *Harees* karbanta yayi ba tareda tunanin komai ba, *Habeeb* yace da kadauketa me kaji..? yace banji komai dasauri yace da gaske bakaji komai ajikinka ba..? yace "eh dasauri yasake karban *Sadeeyar* wacce har tayi shuru, amma saboda karban ta da *Habeeb* din yayi daga hannun *Harees* dasauri yasata saki kuka wanda hakan yanuna taji tsoro
ne,
shikam *Habeeb* abunda yake gudu shi yaji don haka jiki asanyaye yasake mika ta gurin *Harees* aran shi ko fadi yake wato shi kadai yake jin hakan kenan, kallon shi *Harees* din yayi tareda cewa menene...? cikin sanyi murya yace ba komai don Allah jeka kaita gurin lnnan kadawo mu tafi yace toh" bayan *Harees* din yakaita yafito sannan suka nufi shashin su yayinda jikinta *Habeeb* asanyaye.
*******
Sannu ahankali *Sadeeya* da *Safeeya* suka girma inda suka taso gwani sha'awa kamar tagwaye kasan cewar komai iri guda ake yi masu, Abba ma tagwayen Hajiya yake kiran su domin idan ka kallesu farar daya sai kaga kamar suna kama saidai *Sadeeya* tafi *Safeeya* kyau sosai, sun taso cikin tarbiyya me tsafta takowani bangare daga gurin lnna har gurin Hajiya wacce suke kira da Hajiyarmu, gawani irin kauna dasuke yiwa junansu naban mamaki gasu da dan kare wayo komai tare sukeyi, kasan cewar halayyarsu kusan daya saidai sun dan ban-banta tawasu gurare kadan,
kamar *Sadeeya* tanada matukar tsoro kamar farar kura ga d'an karen tsokana, sabanin *Safeeya* da batada tsoro kuma batada tsokana amma zama da *Sadeeya* yasa ta'iya sosai saidai kuma batada karfi amma tanada juriya, ita kuma *Sadeeya* tanada karfi saidai batada juriya domin abu kad'an sai yasata kuka, gasuda d'an karen shagwaba musamman ma *Sadeeya* wanda ita shgawabar a jininta yake.
Abangaren *Habeeb* kuma bai daina jin abunda yakeji ga me da *Sadeeya* ba muddun yaganta sai yaji faduwar gaba idan kuma har yai kuskure yadauke ta sai yaji wannan abu nabin jikinsa wanda yarasa dalilin dayasa yakejin hakan, tunda yagane haka sai yake gujema ganinta musamman ma kwayar idonun ta dasuke bashe tsoro toh" balle kuma daukar ta shikam tuni yadaina,
shekaran su *Sadeeya* biyar *Habeeb* da *Harees* suka gama degreen suna farko akan business administration wanda Abba yasa suka karanshi, toh"bayan sun gama ne sai ya shirya masu zuwa U.K don suyo degree su nabiyu akan ra'ayinsu inda *Habeeb* zaya karanci fannin siyasa shi kuma *Harees* zaya karanci fannin lafiya.
Lokacin ana gobe zasu tafi *Habeeb* yana dakinshi tsaye gaban madubi yana kum din kanshi yayinda *Harees* ke wance saman gado yana kallon shi, can sai *Harees* din yayi murmushi me cike da zolaya yace nidai don Allah mlm mu tafi haka nan tun dazufa kake faman wannan k'ak'ale-ka'ka'le saikace mace, hararan shi *Habeeb* yayi zayayi magana kenan saiga *Sadeeya* tashiga dakin da gudu ta rungume *Habeeb* ta baya tareda cewa Hamman *Harees* kaga Hamman *Hafeez* zaya dukeni ko,
_azaton ta *Harees* din ne_ domin shiyana sakar masu fuska sosai sabanin *Habeeb* da ko" kadan ba yasakar masu fuska, dasauri kuma cikeda tsoro tasaki *Habeeb* din sakamakon hango *Harees* din datayi tacikin madobi yana zaune saman gado yanata murmushi domin dai yasan yau akwai dirama tsakanin *Sadeeya* da *Habeeb*,
Wanda tuni yasaki kum din hannun shi dai-dai lokacin *Hafeez* ya biyota da gudu ran shi bace har zaya shiga dakin sai yafasa ya tsaya bakin kofa, saboda wani irin kallo da *Habeeb* yaimashi, cikin bacin rai yace ita cefa ta bata mun littafina shine ta gudo nan, yarinya aizaki fito ne sai nayi maki duka kuma ance *_KYAUTAR 'BERA_* ๐sannan yajuya yatafi, aikam tuni tafara bubbuga kafa yayinda hawaye yafara gangaro wa akan beauty fice dinta,
_Domin ta tsani bera arayuwar ta tun wani rana da Hajiya zataje store debo abinci sai *Sadeeyar* tabita, toh" shine beran yafad'a ajikinta saboda tsanani tsoro saida numfashi ta yadauke na wucin gadi, sannan tasaki kuka tareda cakume Hajiya to shine tundaga ranan take mugun tsoron beran,_
Cikin kuka tace Hamma *Harees*
kag.....kasa karasawa tayi saboda wani irin tsawa da *Habeeb* yadoka cikin matsanancin bacin rai yace....?
Muje zuwa
A
*_KYAUTAR ALLAH CE_* (Sadeeya)
Tareda
โ๐ฝ
๐นMeenart๐น[7/2, 11:28 PM] My Ameena: ๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
_*KYAUTAR ALLAH CE*_
_(Labarin Sadeeya)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
1โฃ3โฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT* ๐
SADAUKARWA
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)*
___________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
___________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
Subhalallahee! *BB* meyasa meka..? da karfi yake kiran sunan shi tareda girgizashi saidai ina ko kadan *Habeeb* bai motsa ba, cikin tashin hankali *Harees* yatashi yabude mota dai-dai lokacin da Musa drive yanufo gurin dasuri, _kasan cewar yana hango duk abunda yake faruwa_ yace subhalallahi! yalla'bai *Hareesu* meyasa meshi..?
Cikin tashin hankali yace bashi da lafiya taimaka mun musashi cikin mota, suna kokarin sa shi amota saiga su *Safeeya* sunfito zasu tafi school _Dama su musa drive kejira_ don haka dasuri suka nufi gurin,
Cikin tsoro suke tambayar meyami Hamman *Habeeb*..?, nan *Harees* yafada masu" yace su shiga gida sufada
dasauri yashiga motar yatayar yanufi asibiti da *Habeeb*.
Dasauri *Sadeeya* tanufi part dinsu tafadi itama *Safeeya* ta nufi part dinsu ta fadi, kusan alokacin daya Abba da Baffa suka fito cikin tashin hankali, Baffa yace Alh ashe *"Habeebullah* baiji dadi ba..? Abba yace nima yanzu nan *Safeeya* tashiga take fada mana waima harma *Hareesu* yatafi dashi asibiti, yace "eh haka *KYAUTA* tace mun,
Musa dake tsaye gefe cike da jimami yace gaskiya yallabai *Habeebu* bashida lafiya sosai don ko motsi bayayi, cikin tashin hankali Baffa yace subhalallahi! toh" Alh mutafi asibitin mana, Abba yace toh" musa mutafi yace toh" Alh nan da nan suka shiga mota harda su *Sadeeya* da jikinsu yai sanyi ganin yadda aka dauki *Habeeb* baya numfashi.
Cikin sanyi murya *Safeeya* tace Abba muma za muje mu gaida Hamman *Habeeb* din, yace a ah yan'biyun Hajiya banda rigima kuda zaku tafi makaranta, gashima kun kusan makara kubari idan Ku tashi makaranta saikuje Kunji KO..? suka ce toh" dai-dai lokacin da Musa yashiga school din su wato alfurqan, banyan ya sauke su sannan ya nufi asibiti.
*****
Su Abba suna'isa asibiti anafito dashi kasan cewar koda *Harees* ya'isa dashi dakin taimakon gaggawa akaishi, wanda sun dan sauki lokacin kafin su samu numfashi sa yadawo dai-dai, baya ankai shi dakin Hutu sai Likita yanemi ganinsu Abba don yasanar dasu abinda yake damun shi,
Inda yafada masu cewa *Habeeb* yana daya daga cikin mutanan dake da karfin sha'awa, sai kuma yake shan magunguna don su rage masa karfin sha'awar, saidai kuma saka makon shansu dayake sosai shine sukai masa yawa har suka haifar masa da matsanancin ciwon mara, kasan cewar maganin sun daina yimasa amfani,
Idan kuma har bai daina shansu ba zuwa gaba zasu'iya haifar masa da mummunan matsala, dasauri Baffa yace subhalallahi likita Insha'allah hakan baza yafaru yace "eh bamu fatan hakan yafaru, shidai Abba bai Ce komai ba, sai
Baffa ne yasake cewa toh" yanzu Likita wani irin magani ne zaya ringa amfani dasu wayan da bazasu haifar Masada matsala ba..?
yace mace ne maganin matsalar sa, Baffa yace Likita ban gane bafa...? Abba kam murmushi yayi domin tuni yagane abunda Likita yake nufi, shima likitan murmushi yayi, yayinda *Harees* ya dukar dakai kasa cike da kunya yana faman sosa keya alamar tuni yagane abunda Likita yake nufi, likita yace ina nufin aure ne abunda yaka mata yayi domin shine maganin matsalar shi dazaran ya kusanci matar toh" shikenan babu wani sauran matsala,
Baffa yace "Oho nagane toh" amman dai yanzu babu wata matsala zaya farfado lafiya lau KO...?, yace "eh ba matsala mun bashi taimakon dayaka mata kuma insha'allahu zaya barfado normal zaku'iya ma tafiya dashi, Baffa yace toh" madallah mungode sosai, sannan suka fito.
Suka nufi dakin Da aka kwantar da *Habeeb* din har lokacin bai farka ba, Abba ya kalli *Harees* sai yai murmushi Cikin zolaya yace mlm Yusufa nikam yau abun nan yaban mamaki yace meke nan fa Alh..? yace toh" muda muke da likita sukutun agida amma kuma saigamu acikin asibiti toh" wai ya'kayi haka..?
Murmushi Baffa yayi tareda cewa gaskiya kam,
Cikin murmushi *Harees* yace Abba aini yau tsabar rikicewa mantawa nayi ni likitane, Abba yace toh" shikenan mu zamu tafi kaga Abbanka bai saniba, ni kuma zanje nashirya natafi office so aibabu wani abu KO..? yace "eh Abba yace to shikenan tunda litikitan ma yace bawata matsala idan yafarfado kaga sai kutaho , yace toh" shikenan Abba sannan suka fita.
Cikin sanyi murya Baffa yace Alh shin har sai yaushe ne za'a ba bam....dasauri Abba yakatse shi da cewa lokaci na nan zuwa in Allah ya yadda, yace toh" shikenan Allah yanuna mana lokaci Abba yace Ameen, suna tafe suna fira har suka isa gida yayinda kowa yanufi part dinsa.
*ASIBITI*
**********
Su Abba ba su dade da fita basai *Habeeb* yafarka, *Harees* yace masa sannu ya amsa da yauwa ina ne nan...? *Harees* yace asibiti, yace waya kawoni..? yace ni yanzu masu Abba suka tafi gida cikin mamaki yace meya faru dani..?
Cikin kosawa da tambayoyin *Harees* yace kai kam aidama karatun jarida kayi, haba wannan irin tambaya haka nan dai yafada masa duk abunda yafaru harda abunda Likita yace.
tsaki *Habeeb* yayi tareda saukowa daga saman gadon, yana kokarin saka takalmi sannan yace toh" nagode da tona mun asirin dakayi saika tashi kamai dani gida, cikin mamaki *Harees* yace" don nakawoka asibiti shine natona maka asiri...?
yace "eh dai-dai lokacin da yabude kofa zaya fita yana cigaba dacewa saboda baka tsaya gida kayi mun taimakon da kasa ba bani a U.K ba, sannan kuma aikasan magunguna kala-kala basaika siyomun ba amma duk baka yiba, saika wani daukoni ka kawo asibiti gashi nan yanzu kowa zayasan abinda keda muna ,
*Harees* dake biye dashi a baya yace shin wai Kai bakaji abunda nace maka Likita yafada bane..? kafin haka nima banasha fada maka cewa ka rage shan magunguna ba...? saboda zasu iya haifar maka da matsala, dai-dai lokacin da suka higa mota *Harees* yatayar suka tafi, yana cigaba dacewa
sannan kuma ni banga abun bata raiba, don ansan halinda ka ke ciki wanda hakan shi zayaba da damar asamo maka mafita cikin sauki,
Dan dai yanzu na tabbatar za'ace kafito da mata aimaka aure, toh"๐ค yanzu kaida baka kula yan mata idan akace kafito da mata ya zakayi kenan...? yafadi yana kashe masa ido๐, hararanshi *Habeeb* yayi tareda cewa ban saniba kajiko..? yace ai zaka sani ne idan akace ka fito da mata nan da sati biyu๐.
Koda suka'isa gida part din su Hajiya suka shiga sunyi ake lnna da Hajiyar su *Harees,* sun shiga gaida shi Cikin jin kunya *Habeeb* ya amsa gaisuwar sannan suka tashi suka nufi part din su, suna shaga *Harees* yace ka kwanta kahuta nizan tafi office.
*Bayan kwana biyu*
**********
Da misalin karfe 11:00Am na rana lahadi Su *Habeeb* ne suka fito cikin shirin su nazuwa kaima abokinsu ziyara dake zaune a new makama estate,
*Harees* yace mushiga muji kiran da Baffa yakeyi mana kafin mutafi ko...?
yakara she fadiyana kallon *Habeeb* yace "eh,
Zaune suke gaban Baffa Kansu duke akasa cike da ladabi suka ce Baffa ga mu, gyaran murya Baffa yayi sannan yace shin kunsan dacewa duk daraja da mutuncin mutun Da mutane" suke gani, dazaran ance baya da iyali
Shikenan daga ranan darajarshi tazube "a idon "mutane kuma bazasu sake mutun tashi ba,
Don haka abunda nakeso daku shine kowa nan ku yafito da matar dayake son ya aura, domin dai lokaci yayi da yaka mata Ku ajiye iyali kun jiko...?, har *Habeeb* zatayi magana sai kuma yayi shuru,
Cikin ladabi *Harees* yace toh" Baffa Insha'allah zamu fito dasu yace yau Allah yaimaku albarka suka Ce ameen sannan suka fita.
Tunda suka fito har suka shiga mota suka nufi inda zasu babu Wanda yace komai, yayinda *Habeeb* yake tuki ahankali can sai *Harees* yace toh" wai da me zakace ma Baffa..?
tsaki *Habeeb* yayi tareda cewa hmm! aini wani irin kwarjini Baffan yaimun shiyasa nakasa Cewa komai, murmushi *Harees* yayi yace ai Baffa kam akwai kwarjini sosai, toh" wai yanzu ta'ina zamu fara..? yace hmm! kodai ta'ina zanfara,
Da saurice bangane ba..? yace toh" kaifa kanada Safeena kuma tana sonka kaine dai baka sonta, murmushi *Harees* yayi yace aiba wai banason taba ne "eh yesss! Ina sonta saidai kagane akwai wadda nake matukar so fiyeda "ita, kamar yadda kaima kake matukar son wata
fiyeda yadda kakeson kanka,
Wani irin wawan burki *Habeeb* yaja tareda kallon gefen da *Harees* yake, cikin matsanancin mamaki yace...?
Muje zuwa
A
*_KYAUTAR ALLAH CE_*
(Labarin Sadeeya)
Tareda
โ๐ฝ
๐นMeenart๐น
[7/2, 11:28 PM] My Ameena: ๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
_*KYAUTAR ALLAH CE*_
_(Labarin Sadeeya)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
1โฃ4โฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT* ๐
SADAUKARWA
*GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)*
___________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
___________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
โ๐ฝ
_*Bismillahirrahamanirraheem*_
"Kai tunda muke dakai ka taba jin nace maka ga yarinyar danake so...? hararan shi๐ *Harees* yayi tareda cewa haba don Allah mlm wannan wani irin abune haka sonake ka kashemu tun ba mukai ga cimma burinmu ba,
"Dasuri yace kaga mlm dalla ka fadamun "wace yarinya ce" nake matukar so fiye da kaina eye..? *Harees* yace ban saniba, harara *Habeeb* yasake watsa masa tareda cewa ah! tunda abun kulin sharrine ai baza kasani ba, wani irin kallo ya watsa masa sannan yace kaga mlm banason _pretending_ fa,
"asukule *Habeeb* yace anyi _pretending_ din kaji ko..? tsaki *Harees* yayi tareda cewa Oho Kaidai kasani waikai sarkin yan *ZURFIN CIKI KO..?* kag mlm idan zaka fito kafadi abunda ke cikin *RANKA* kafito kafada, idan kuma bazaka fadi ba Kai kasani,
*Habeeb* yace "eh bazan fadi din ba kaji ko..? yace toh" shikenan ka cigaba da ajiye shi acikin *RANKA,* saidai kuma kasani idan Kai wasa watara na zaka iyarasa shi, muddun baka fitar dashi ansani ba kuma na tabbatar alokaci dakai yunkurin fitar dashi yariga yaimaka babbar *ILLA A ZUCIYA*,
Cike da jin haushi yace waikai ina ruwanka dani ne...? yace da ruwana tunda ni dan uwanka ne kuma shakikin amininka ne, amma tunda kace ba ruwa na toh" aje'a hakan saidai kasani nidai Ina nan akan bakana nason wacce" nafada maka lokaci kawai nakejira yayi na baiyya na mata zallar kaunar danake yimata",
tsaki *Habeeb* yayi tareda cewa kadaiji kunya wlhy, da sauri *Harees* yace ah! yanzun kam banji taba saidai ko zuwa gaba idan na'ajiye girmana gefe kila naji, cike da mamaki *Habeeb* yace ita" kunyar...? yace "eh ita din, kaga yallabai kaja mota mutafi kuma anjima zamu gidan lnna "Hafsatu muga "Safeena mudai-daita, don haka saikafara Neman wacce za'a aura tun yau don idan aka tsayar da maganar mu bazan jira kaba,
_"lnna Hafsatu kanwar Mahaifiyar *Harees* ne "Safeena yartace" tana matukar so *Harees*, shine dai bai damu DA ita sosai ba_ .
tsaki *Habeeb* yayi tareda tada motar yace kaidai kasani kuma kada Allah yasa kajirani din mlm duk ka wani cika ni da surutu.
"Akan hanyar su ta koma wa gida ne *Harees* yaketa cewa *Habeeb* ya tsaya zayayi fitsari, amma Yaki tsayawa saida yace don Allah ka tsaya kasan fa babu kyau mutun yarike fitsa saboda yana yiwa mutun illa, duk da haka *Habeeb* bai tsaya ba saida suka shiga Unguwar wintin dada sannan *Habeeb* din ya tsaya gefe titi,
Da sauri yafito yanufi gefen kwata ya tsugun'na.
Doguwa ce fara tana da kyau balaifi saidai tana da yar kiba kadan
wanda yanayin jikin nata yanuna idan zata samu Hutu zatayi irin kibar nan ne mara fasali, sayen take da uniform din islamiyya riga da wando da hijab shekarunta zasu kai 18 to19, tunda ga nisa *Habeeb* yake kallonta ta madubin mota har tazo kusa da shi zata wuce, ahankali yaleka ta wundon motar ya cigaba da kallon bayanta,
Wato tafiya take ahankali saidai a yadda take takun tareda motsa jikinta, zaka fahimci cewa tana yinsa ne domin daukar hankalin duk wani d'a namiji, gyaran murya *Harees* yayi Wanda yasa *Habeeb* juyawa dasauri suka hada ido daure fuska *Habeeb* yayi, shikam *Harees* murmushi yayi tareda cewa yaaa! kodai..?
Da sauri yace kodai me..? yace ah! kar kadamu Ina zuwa, dasauri yabi bayanta sallama yayi mata ahankali tajuyo ba tareda ta amsa sallamar ba sai yatsina fuska datayi saidai kuma gani kyakkyawa saurayi yasa tasaki fuska,
Yace sannu ko..tace yauwa yace don Allah kiyi hakuri na tsayar dake kan hanya tace lah! ba komai , yace dama inason magana dake ne saidai ban saniba ko" Unguwar nan kike..? tace "eh ga gidanmu ma can tafadi tareda nuna wani kujajjan gida me da kali duk ya faffashe, yace toh" kije gamu nan zuwa kofar gida sai muyi maganar tace toh".
********
Gurin *Habeeb* yakoma yace masa don Allah yazo yara ka shi, ba musu yafito ya kulle motar sannan suka nufi kofar gidansu yarinya, tsaye suka isketa suna hada ido *Habeeb* duk sai ta rikice domin wani irin kyau tagani da kwarjini atare dashi lokaci guda kuma sai taji mugun sha'awar shi ya dira zuciyarta,
Bayan sun gaisa sai *Harees* yace yasunan mlmar..?.tace Murjanatu amma a nakira Na *JANA,* yace masha'allah mlma murjanatu ni sunana *Harees* dan'uwana kuma *Habeeb* KO" kice *BB smart,* yaganki ne yaji kinyi masa ma'ana yana sonki kuma da aure dafanta Zaki karbeshi hannu babbiyu, Dasauri tace badamuwa na amince,
yace Alhamdulillahi toh" Bari nadan Baku gurin KO..? tace toh," ya kalli *Habeeb* dayayi sororo yana kallon shi yace zanjiraka amota, baijira abunda zayace ba yawuce, ahankali *Habeeb* ya kalli *Jana* wadda yarasa meyasa yaji wani abu game da'ita tun lokacin daya hango ta, murmushi yayi Wanda yasake gigita *Jana,*
karo na farko kena arayuwar sa daya taba tsayawa da budurwa, don haka duk sai ya rikice yarasa abunda zayace can saya tsinci kanshi yaname ce mata inafata dai baki yiwa wani alkawarin kanki ba..? Dasauri tace "a ah yace toh" shikenan ai kinji abunda dan'uwana yace KO..? tace "eh, yace toh" kibani dama naringa zuwa gurinki idan mun fahimci juna saina turo magaba tana, domin bana son adauki lokaci tace badamuwa Na amince,
yace toh" nagode sannan yasa hannun aljanu yaciro kudi da baisan konawa bane yamika mata, tareda cewa ga wannan sai mun dawo anjima, jikina rawa takarba tana godiya sannan ya'iske *Harees* suka tafi gida.
*Wacece Jana*
Kamar yadda tace asalin sunan ta kenan Murjanatu Sani kawayenta ne suke kiranta *Jana,*
Mahaifinta mlm Sani _shoe maker_ ne wato me gyaran takalma talakane shi talak saidai yanada wadar zuci sana'arsa kenan gyaran takalmi kuma dashi yake ciyarda iyalinsa,
matarsa daya Dije ya'ya'nshi uku Jafaru shine babba kuma shi ma sana'ar yake don baiyi karatu ba ,sai Binta ita tayi primary school Bayan tagama aka kukuta akai mata aure, sannan *Jana,* mahaifisu sani shushaina yana'iya bakin kokarin sa nagani yabata tarbiyya, saidai sam *Jana* bata dauka, domin ita banajin magana tana da mugun son abun duniya gata da high test domin tasha cewa, kamata yayi ace ita yar gidan masu kudi ce ba yar gidan talakawa ba,
tagama primary da kyar tashiga secondary tanayin junior wec tadaina zuwa, takama bin gidajan kawaye da dakin samari musamman idan ta shirya zuwa islamiya, *Jana* kenan indai zaka bata kudi to" zata baka jikinta kayi yadda kakeso dashi so biyu tana zubar da ciki, ganin hakan ne yasa mahaifina yace tafitoda miji aimata aure takiya don haka sai ya kyale ta, tanada wani saurayi guda da take bashi kanta yayi yadda yakeso ba tareda yabata kocici ba,
"Wani lokacin ma ita kebashi kudin domin tana mugun son Ado saidai tanajin aranta bazata'iya auren shiba, domin shindi talaka ne ita kuma tace gaskiya bazai yiyu'a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 42