Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
aure, insha'allahu ranan jumma'a za'a daura auren sai ayi buki ranan asabar tareda na *Haleematus-Sadeeya* da Na ALLAH, tunda dama su anriga "an daura auren su, cikin miliyoyin mamaki *Habeeb* yace... *_Don Allah kuta yani da addu'a bani da LAFIYA pls_*๐Ÿ‘. Muje zuwa A *_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya) Tareda โœ๐Ÿฝ ๐ŸŒนMeenart๐ŸŒน [7/2, 11:47 PM] My Ameena: ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ _*KYAUTAR ALLAH CE*_ _(Labarin Sadeeya)_ ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ 2โƒฃ7โƒฃ WRITTEN By ๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ OR ๐ŸŽ *MEENAT* ๐ŸŽ SADAUKARWA *GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)* ___________________ ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_ ___________________ ~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~ โœ๐Ÿฝ _*Bismillahirrahamanirraheem*_ "Abba kana nufin ni *Habeebullah* aka daura ma aure da *Haleematus-Sadeeya* tanan gidan?..Abba yace itafa, wani irin farin ciki ne yarufe *Habeeb* wanda tunda yake bai tabajin irin saba sai ranan, "Yayinda matsanancin mamaki yaciga mutanan dake falon musamman su Adda Mamu, saidai kuma wani abun mamaki banda Hajiya da Inna da kuma Hajiyar su *Harees,* sukam da'alama dama sunsa da maganar. itakam *Deeya* zumbu tamike daga jikin Hajiya yayinda taji gabanta yayi wani irin azababben bugawa, kyawawan idonun ta take warewa cike da firgici abunda kunnu wanta sukaji, cikin tsoron tace Sweet *Feeya* kema kinji abunda naji Abba yace"?..kafin duk *Feeya* tabata amsa, taji Abba Na cewa tabbas an daura muku aure tun tsawon wani lokaci wadda nasan zakuyi mamaki jin haka, kuma nasan zakuso kuji shin dawani lokaci aka daura Auren, Adda Mamu ce tace gaskiya Abba zamu so muji murmushi yayi zayayi magana kenan sai sukaji, kukan *Deeya* tana cewa shikenan itakam ta mutu tunda aka aura mata Hmm *Habeeb* shida baya SONTA, shida yake duk...takasa karasawa saka makon wani irin tsawa da Baffa yadoka mata, Wanda yasa gaba daya falon akai tsit domin ba'a taba jin yadaga murya haka ba, Cikin bacin ran yace *KYAUTA* ashe baki da hankali bansani ba..., Dasauri tafada jikinta Hajiya tana kuka tace Hajiyar mu nikam banason Hmm *Habeeb* tunda shima baya sona, cikin tsawa Baffa yace ke! *KYAUTA* ki kiyaye ni kinji ko?.. Kuma muddun nasake jin kince tak! sainayi kasa-kasa dake agurin nan, Kai kaga mun marar kunyar yarinya. Sake rungume Hajiya tayi tana kuka sosai jikinta sai rawa yake, Wanda hakan yasa jikin Hajiyar yai sanyi, domin batayi tsammanin jin haka daga bakin *Deeya* ba, saidai kuma idan akai la'akari da yadda babu jituwa tsakanin ta *Habeeb* din, cikin karfin hali tace to kiyi shuru hali dubu na zansan yadda za'ayi kinji ko?.. kai ta gyada, tareda sake lahewa jikin Hajiyar saikace yar mage. Shikam *Habeeb* mutuwar zaune yayi, yayinda kirjinshi ke miliyoyin bugawa, kallo daya zakayi mashi ka hango tsantsar tashin hankali a tare dashi, Abba ma jiki shi yayi sanyi cikin kwantar da murya yace kiyi hakuri *Sadeeya*, tun ranan da'aka haifeki na bukaci Baffan ki daya ba Na ALLAH auren ki idan Allah yaraya ki, Amma sai Baffan ki yaimun wani irin halacci wanda bazan taba mantawa dashi ba, domin kuwa cewa yayi ai Na ALLAH shine d'ansa ke kuma 'yata ce don haka ga sadaki yaciro acikin aljihun shi yace yana nemar wa dansa auren 'yata, jin dadi abunda yaimun yasa nace na bashi yace to yana neman alfarman da'a daura auren nace mashi ba damuwa don haka atake aka daura aure ku, ida ni nazamo waliyin ki shi kuma yazamo waliyin Na ALLAH kuma Alh Al-mustafa shine sheda KO" ba haka akayi ba?..Baffa Al-mustafa yace haka akayi, To saidai kuma bamu san haka abunzai kasance ba da bamuyi saurin yanke hukunci ba, amma ki kwantar da hankalin ki tunda baki son Na ALLAH za'a raba auren, cike da tashin hankali *Habeeb* ya kalli Abba, yayinda Baffa yace haba Alh ai hakan bazaya taba yiyuwa ba, aure kam tsakanin ta da *Habeebu* anriga andaura shi, kuma ita ba ta'isa tasa'ara ba shi ba; kuma KO" bayan raina tace zata tilasta araba auren tada *Habeebu* ban yaf... Dasauri Abba yace haba mlm Yusufa meye haka kake kokarin furtawa?.. Cikin bacin rai yace bari Alh yau *KYAUTA* ta batamun rai matuka, yace to kayi hakuri ai abun baikai na'ayi mata mugun lafazi ba domin akwai kuriciya atareda ita; Baffa Al-mustafa yace kwarai kuwa kayi hakuri ita kuma abita ahankali insha'allahu komai zayayi dai-dai ne. yace to yanzu idan akwai sauran bayani sai ayi Abba yace "eh to inaganin kamar babu sauran wani abayanin ko mlm Yusufa?.. yace "eh to saida kuma ban saniba KO akwai me magana?.. kowa yace "a ah Abba yace to shikenan Mlm Yusufa ayima na Addu'a, nan Baffa yarufe taron da addu'a yayinda kowa yatashi jiki bakwari su Adda mamu sukaya masu Hajiya sallama suka tafi, lnna rai bace tanufi part dinsu inda Baffa da *Hafeez* suka rufa mata baya. Duk farin cikin DA *Feeya* takeji na cewar Hmm *Harees* zaya zamo mijinta nan da sati daya duk ya gushe, saka makon ganin halin da *Deeyar* ta take ciki Haka shima *Harees* duk sai yazama wani irin domin shima baiyi tsammanin jin haka daga bakin *Deeya* ba, saidai kuma idan akai la'akari da irin abubuwan da *Habeeb* yake mata dole zata Ce baya SONTA, jikin bakwari yabi bayan *Habeeb* saidai kuma gayi yayi dasauri *Habeeb* din yabi bayan Abba zuwa dakin shi, don sai shima yabi baya Baffa su. Dai-dai lokacin da Abba zayashiga dan madai-daicin falon dazaya sadashi; da dakin shi sai yaji kamar tafiya abayan shi don haka dasauri yajuya *Habeeb* yagani baice masa komai ba ya shiga falon, shima *Habeeb*; yashiga zama Abba yayi akan kushin yayinda *Habeeb* ya zauna kusada kafar Abban. Cikin sarkewar murya yace Abba meyasa kuka aura mun *"Sadeeya* tun tana jaririya?..Abba yace munyi laifi ko?...yace a ah Abba ba nufi na kenan ba, yace to meka ke nufi?..yace kawai inason nasan dalilin kun nayin haka, Abba yace *ZUMUNCI* shine dalilin dayasa mu kayi haka wanda muna son yadore, har jikoki saidai inaga hakan bazai yiyuba, yace Abba saboda me zakace" haka?..yace saboda *"Sadeeya* bata sonka shiyasa ma zan raba auren naku, Dasauri yace Abba don Allah kar karaba Auren nan yace saboda me?.. yace saboda Ina SONTA Cikin mamaki Abba yace kana SONTA fa kace?.. (Abunda yasa Abba yai tambaya saboda yana zaton KO" shima *Habeeb* bayason *Sadeeya* ne, kamar yadda itama tace bata son shi; koda yake ita harda kuruciya). Yace Abba Ina SONTA sosai irin Wanda bansan iyakar shi ba, nasan itama wata rana zata sonni idan tagane ni me SONTA, domin tun ranan da'aka haifeta zuciya take SONTA kuma har yau ban daina jinson ta" yaragu a zuciyata ba, shuru Abba yai yana kallon shi zuciyar shi cike da mamaki yace amma baka taba gaya mun ba, koda yake kai mutun ne me tsananin zurfin ciki, wanda ni har tsoro zurfin cikin ka yake bani, ayya na Allah zurfin cikin nan baya cutar dakai kuwa?.. shuru yayi bai Ce komai ba, Abba yace don Allah karage zurfin Cikin nan koda yake nasan ajininka yake amma karinga yin kokari kana furta wani abun dake damun ka kaji ko?.. cikin sanyi murya yace to Abba zanyi saidai don Allah Abba kar karaba auren nan, kuma na yimaka alkawari zan riketa" amana kuma insha'allahu ta sanadin Auren nan zumunci mu zaya sake karfi fiyeda yanzu, Abba to Allah yasa yace ameen yanzu idan akai sallah zaka tafi ko?..yace Insha'allah, yace to ka kwantar da hankalin ka kazamo mutum me adalci kayi aikinka da gaskiya da amana, saikaga al'umma suna kaunar ka. yace to Abba nagode, yace ba damuwa kaje Allah ya tsare hanya insha'allahu wani sati idan kazo zaka tafi da matarka, amma kayi kokarin sanar da "Murjanatu tunda ita duk yadda akaso taringa tsayawa gurin mitin din "takiya, ZUCIYAR shi cikeda farin ciki yamike tare da cewa to Abba sannan yafita. ****** Part din shi yanufa koda yashiga kwance ya'iske *Jana* akan kushin tana aikin daddana Waya, tsaki yayi tareda zama a kushin yace ki tashi inason zanyi magana dake; tashi tayi tareda ajiye wayar ta maida hankali akan shi, ba tareda bata lokaci ba yafada mata maganar auren shi da *Deeya.* Zumbur tamike cike da tashin hankali tace kan uba, dasauri yace I hope dai bakan ubana bako?.., bata saura reshi ba ta cigaba dacewa wannan ma ai maganar banza ce, zumbur yamike tareda doka mata tsawa Wanda yasa takoma ta zauna ba tareda ta shirya ba, yace wake maganar banza iyayena?.. tace to aini bance su" ba amma dai wannan cin amana ne ya za'a daura maka aure, ni matarka bansani ba, tsaki yayi yace bakiji abunda nafada maki bane ko?.. tace wannan ma ai rainin hankali ne taya za'a Ce tun tana jaririya za'a daura maku aure, kawai dai cutata akesonyi shiyasa za'ace haka kuma bazan yadda ba sai "anraba auren nan don wlhy ban shirya zama da kishiya ba eheee, Yace abunda kuma baki isa akanshi ba kenan kinji KO?.. don haka banason surutun banza dama, nashigo nafada maki ne so kuma nafada maki do haka na fita hakkin ki, kuma ranan asabar zata" tare sannan yafita yabarta tana ta masifa dasauri tadauki wayar ta, tanufi sama kamar mahaukaciya tana kiran layin shafa kawarta. Koda *Habeeb* yafita gurin *Harees* yanufa zaune ya'iske shi falo yazabga uban tagumi, yana ganin *Habeeb* yai sauri yamike ya tareshi, tareda cewa dan'uwa na biyoka saina ga kashiga gurin "Abba yace "eh dai-dai lokacin da suka zauna, *Harees* yace to ya'akayi ne?.. nan *Habeeb* yafada masa yadda duk sukayi da "Abba fuskar shi dauke da farin ciki, yace Alhamdulillahi! yanzu ka kwantar da hankalin ka insha'allahu komai zaiyi dai-dai ne, kawai dai abunda nakeso dakai shine duk wani abunda kasan kana yimata Wanda yasa take ganin kamar bakason ta to ka daina, kajata" ajikin ka sosai wanda ta haka ne zaka dasa son ka acikin ZUCIYARTA" kuma baza kasha wuya gurin yin haka ba domin itadin "yarinya ce, kagane ai?.. Cike da _confidence_ *Habeeb* ya daga kai tareda cewa insha'allahu, nan dai suka cigaba da fitar su suna cin kin fitar ne sukaji kiran sallah don haka suka nufi masallaci. ***** Dakyar Hajiya tasamu *Deeya* tayi shuru, kwance take akan gado saidai duk Rabin jikinta akan cinyar *Feeya* yake, wacce daga lallashin *Deeyar* itama tabuge da kukan Cikin sheshshe ka tace sweet *Feeya* ai kema kinsan hmm *Habeeb* bayasona tunda sai yayita mun tsawa da zaremun idon nan nashi masu ban tsoro kuma d'an abu kad'an idan nayi mashi sai rankwashi ni, ko ya murd'e mun kunne da baki ta karashe fadi cike da tausayi kanta, Cikin kwantar da murya *Feeya* tace to kiyi hakuri kinji my sweet *Deeya* ai yanzu bazai sakeyi maki haka ba tunda ke matar shi ce, batace komai ba saidai baki data turo tare da sake gyara kwanciyarta ajikin *Feeya.* _Nikam nace Oh! su *Deeya* sarkin son jikiโ˜บ_ Suna haka sukaji kiran sallah azahar don haka suka tashi suka nufi toilet don suyo alwala, bayan sun idan da sallah suna zaune jugun-jugun ko hijab basu cire ba, saiga *Hafeez* yashigo suna hada ido da *Deeya* ya watsama ta harara, domin haushin ta yakeji ta batama Baffan shi da lnnan shi rai. yace *Sadeeya* zonan tareda juyawa yafita tashi tayi tabi bayan shi, rai bace yace saiki samu sawan zuwa Baffa nakira jitayi gabanta yafadi, zata koma daki dasauri yace ina kuma zaki?. tace zankira sweet *"Feeya* ne tara kani, hararan ta yayi tareda cewa ba sweet ba chingam dalla mlm ki wuce ki tafi ke kadai, haka tawuce jiki bakwari. Da sallama tashiga falon nasu" Baffa dake zaune akushi ya amsa casbi ne ahannun shi yanaja da'alama daga masallaci yake, yayinda lnna ke zaune gefen shi zama tayi kusada kafar Baffa tace sannu Baffa ina wuni?.. lnna ina wuni shuru ba wanda ya amsa har sau uku basu amsa ba, kawai saita fashe da kuka tana cewa don Allah kuyi hakuri kar kuyi fushi dani wlhy bazan taba samun nutsuwa ba, idan har kuna fushi dani Baffana na tuba bazan sake bata maka rai ba lnna ta kiyi hakuri, ji sukayi duk tausayi ta Yakama su, hakan ne yasa Baffa ya dagota ya zaunar da'ita tsakiyar su yace ya'isa zamu hakura amma da sharadin bazaki sake cewa baki son *Habeebu* agaban mutane ba musamman gaba iyayansa, lnna tace to bashirman ma bace. Cikin kuka tareda rike hannun lnna tace nadai na, Baffa yace to sai kuma kin amince da auren dake tsakanin kuda shi; idan kuma bazaki amince bato ba zamu hakura ba kuma babu mu, babu ke dasauri ta kwantar da kanta akafadar Baffa tace na amince amma kace yadai nayi mun zalu ta karashe fadi tareda turo baki, ido lnna da Baffa suka hada sukayi murmushi domin sun hango tsabar kuruciya atareda 'yar tasu, kanta Baffa yashifa tareda cewa to shikenan zance afada mashi kinji *KYAUTAR ALLAH* Mu?.. tace to. Suna haka saiga *Habeeb* yashiga da sallama lnna ta amsa fuska sake, tace ah *Habeebu* ne?.. kanshi duke yace "eh domin yau wani irin kunyar su yaji yakama shi, *Deeya* kam jitayi gabanta yafadi don haka saita sake gyara kanta akafadar Baffa, Baffa yace *Habeebu* kashigo?.. yace "eh Baffa dama nazo nayi maku sallama ne zan tafi abuja yanzu, Baffa yace Allah sarki tafi yar yatashi kenan?. yace "eh yace to Allah yatsare hanya, yace ameen lnna ma tayi masa addu'a Sannan yatashi yafi. Baffa yace tashi kijeki yi masa Allah yatsare hanya, cikin shashsheka tace to tareda tashi tabi bayan shi shikam yana fita ya tsaya gefen kofa kasan cewar yaji abunda Baffa yace", tana fitowa taganshi tsaye itama ta tsaya bakin kofar dukar dakai tayi gabanta sai faduwa yake Cikin sarki war murya tace... *_Barkan muda jumma'a_* Muje zuwa A *_KYAUTAR ALLAH CE_* (Labarin Sadeeya) Tareda โœ๐Ÿฝ ๐ŸŒนMeenart๐ŸŒน [7/2, 11:47 PM] My Ameena: ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ _*KYAUTAR ALLAH CE*_ _(Labarin Sadeeya)_ ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ 2โƒฃ8โƒฃ WRITTEN By ๐ŸŽ *AMEENA UMAR Su*๐ŸŽ OR ๐ŸŽ *MEENAT* ๐ŸŽ SADAUKARWA *GA SADEEYA SADEEQ UMMU (Haidar)* *Wannan page din nakune nabaku kyautar MASOYA* *KYAUTAR ALLAH CE a duk inda kuke musamman yan group Dina na ZUCIYATA CE* *Inayinku irin sosai din nan Love yours* ๐Ÿ˜˜ ___________________ ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_ ___________________ ~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~ โœ๐Ÿฝ _*Bismillahirrahamanirraheem*_ Umm! umm!! Umm!!! dama Baffa ne yace" nazo nace maka Allah ya tsare hanya, kyakkyawan murmushi yayi tareda mika dogon hannun shi yajata zuwa faffad'an kirjin shi, saida yaji wani irin yarrrrrrrr! ajikin shi tareda bugawar zuciya amma haka yai mata lafiyayyan runguma, tareda sauke ajiyar zuciya me nauyi. ita kam ido tawaro cike da tsoro kirjinta kuma ya cigaba da bugawa yayinda jikinta yadauki rawa, saboda tunda take ba wani D'a namijin daya taba rike mata hannu to balle kuma rungumeta ta hakan yasa jikinta sake daukar rawa, tareda wani irin tsoro saka makon tunawa da maganar Hajiya don kaka sai kawai ta fashe da kuka me cike da tsoro. tareda cewa wayyo Allah na don Allah Hmm *Habeeb* kayi hakuri kasa keni ka daina tabani kaga"Hajiyar mu tace" idan muka bari namiji ya tabamu zamuyi ciki, tafadi tareda kokarin tureshi daga jikinta ido ya rintse saka makon jin kukan ta har cikin zuciyar shi, don haka saiya sake rungumeta sosai cikin sanyi murya yace *Leemah* ta kiyi shuru babu abunda zai faru, "Hajiyar mu tana nufin namijin da ba muharramin kinba, ni kuma kinga mijinki ne don haka babu komai. Sannan *Leemah* ta "amatsayin ki na matata bazaki zokice mun Allah ya tsare hanya ba sai ance kizo kice mun umm?..batace komai ba sai mutsumutsu da takeyi wanda so take kawai ta kwace kanta daga gare shi, domin ita bawai ta yadda Da abunda yafada bane, saidai kuma takasa don haka sai tayi tamo tana sauka ajiyar zuciya tareda shakar daddad'an tura ranshi, Sannan kuma kirjinta bai daina bugawa ba haka kuma jikinta bai daina rawan dayake ba. *Habeeb* kam yana jinta amma yakasa sakinta din kamar yadda tabu kata, asalima sake rungumeta yayi sosai domin yanayin dasu ke ciki yai masa dadi matuka, shi bai kima ace su dauwama haka ba, ahankali yace *Leemah* ta bakice komai ba wato hakan yana nufin da gaske baki *SONA* KO?.. Cikin rawar murya tace to ainima baka *SONTA,* Dasauri yadago kanta tare da zutsura ma kyakkyawar fuskar ta ido, yace waya fada maki banason ki?.. dukar dakai tayi cike da shagwaba tace to bakai bane sai kaita yimun tsawa da zare ido da rankwashi, har da matse mun baki kuma fa akwai zafi ta kareshe fadi cike da yanayin tana shagwaba. Murmushi yayi tareda cewa to kiyi hakuri kiyafe mun, amma nidai nasan ina sonki sosai irin son da bayaga "Hajiyarmu babu wata mace dana kema irin shi matsayayin ki acikin zuciyata me girma ne *Leemah ta*, dasauri tadago kaita kalle shi cike da mamaki! murmushi yayi yace kina mamaki! jin haka ne?..kaita gyada alamar "eh, yace *Leemah ta* kenan karkiyi mamaki! da lamarin ubangiji, domin ni tun ranan da'aka haifeki *ZUCIYATA* taka mu da kaunar ki, ido๐Ÿ˜ณtazaro cike da matsananci mamaki! yace tabbas abunda nafada maki ba karya bane kuma ki tambayi *"Harees,* kuka tafashe dashi, cikin gigita yajata ya rungume tareda cewa me yafaru *Leemah ta??* cike da shagwaba tace to ba kai bane kace tun ranan da'aka haifeni ka kesona amma kuma sai, kayita yimun zalu, yace to kiyi hakuri kodama karfin hali nakeyi kuma daga yau bazan sake ba kinji?.. batace komai ba sai mamakin shi daya darsu cikin zuciyar ta, har tana fadi aranta wai yau ita ce Hmm *Habeeb* yakece ma yana son har da bata hakuri akan abubuwan da yai mata, tab! lallai yau za'ai ruwa da kankara. Cikin sanyi murya yace *Leemah ta* kinyi shuru kodai baki yafemun bane?... Cikin cool voice din ta tace nayafe maka amma kar kasake, dariya yayi tareda cewa to nagode kuma bazan sake ba insha'allahu to amma kefa; yanzu kina sona?.. tace nima bansani ba, murmushi yayi tareda cewa to shikenan ni Zantafi amma inason kiyi mun Addu'a kinji?.. ba tareda tadago Kai ba ahankali tace Allah yasa tsare hanya, yace yauwa *Leemah ta* ameen amma pls kibarni naga kyakkyawar fuskarta ki, yafada tareda sa hannun yatallabo fuskarta dasauri ta lumshe ido, Kuri yayi yana kallon tsantsar kyau irin na *Deeyar* *Feeya*, *KYAUTAR* lnna da Baffa hali dubun Hajiya๐Ÿ˜€, "Ahankali yace *Leemah ta* bake son ganin fuskata ne?.. cike da shagwaba tace to ni idonka tsoro yake bani, baki yabude tareda yin dariya yace Kai *Leemah ta* idon nawane yake baki tsoro?.. tace "eh, yace to bude idon ki ki kalli kwayar idona idan kikayi haka shikenan bazaki sake jin tsoro ba, "ahankali ta bude idon tareda tsura mashi Su, shidin ma ita yake kallo zuciyar shi cikeda matsanancin kaunar ta, tsawon lokaci suna haka can saita dukar dakai ba tareda tace komai ba, Shikam ajiyar zuciya yayi tareda cewa to *Leemah ta* zantafi meki keso nasiyo maki idan Zan dawo?.. tace ba bukomai, yace Kai *Leemah ta* bakison komai fa kikace?.. tace "eh yace to shikenan amma ni idan nadawo zakiyi mun jagwalgwalon nan me dadi?.. dasauri tarufe fuska tana dariya, shima dariyar yayi tareda sake rungumota jikinshi yace Allah akwai dadi jagwalgwalon nan umm umm Ina sunan shi yauwa natuna alalan kwai KO?..yafadi tareda kashe mata ido daya, murmushi tayi tareda daga Kai alamar "eh. yace yauwa to zakiyi mun idan nadawo?.. tace "eh yace nagode to bude ido muyi sallama, tana budewa yasake ta tareda yi mata kiss agoshi sannan yace byeeee!, tareda wucewa tagefen ta, baki tabude cike da mamaki aranta tace oh๐Ÿค”wai dama haka Hmm *Habeeb* yake very simple amma sai yai tayiwa mutane masifa, tana tsaye har yashiga part din Hajiya Sannan tashiga falon. Mamaki ne Yakama lnna da Baffa ganin yadda tashgo fuskarta dauke da farin ciki sabani yadda tafita, kamar ba'ita ne taci muka ba, fuska sake tace Baffa Hmm *"Habeeb* yatafi Baffa yace to madallah yanzu zonan ki zauna kiji yafadi tareda muna mata gurin data tashi, Bamu su taje ta zauna cikin hikima irin tasu ta manyan mlm yaimata nasiya me kashe jiki, dangane da auren *Habeeb* dake kanta, Sannan ta tashi tafita zuwa part din Hajiya. ******* Bayan *Habeeb* yashiga ya sallami Hajiya Sannan yafito yanufi part din shi, saidai wani abun takaici shine koda yashiga bai'iske *Jana* ba sai me aiki dasu juinor, dagudu sukazo sukai mashi oyoyo, lili mama yadauka tareda Shafa kam Junior, yace Ina momin ku take?.. Junior yace tafi unguwa lili mama kam baki ta tabe tareda cewa Dad shine kuma bataje dani ba, yace Sorry bari nakira ta koda yakira layinta akashe, tsaki yayi tareda cewa my lili wayar ba tashiga yanzu dai kunci abinci?..suka ce "eh, Yace to ni zanshiga wanka amma idan nafito zan tafi abuja so kuje part din Hajiyar mu idan zan dawo me zan siyo maku?.. dauri sukace yeee! Dad sweet and ice cream zaka ciyo mana inji cewar lili mama; Junior yace Dad har da biscuit, yace to tareda sauke lili maman suka fita da gudu. Dakin sa yashiga ba tareda bata lokaci ba yashiga wanka, bayan yafito ya shirya cikin hadadd'en suit blue yai masa kyau sosai Sannan yadauki wata yar karamar jaka baka tareda wata babba itama baka cewadda da'alama kayan sawan shine acikin, sannan yadauki wayoyin sa yafita. Direban sa yana ganin shi yafito yai sauri yakarbi jakar kayan yabude but yasaka, sannan yasaka karamar jakar abaya tareda bude masa mota yashiga, masu tsoron shima suka shiga ta su motar Sannan sukaja suka fitada dudu ZUCIYAR *Habeeb* cike da KAUNAR *LEEMAR* shi. ********** *Jana* kam lokacin data hau sama tana kiran layin shafa kawarta bai jeba, don haka sai kawai tadauki gyale da key mota tafita bata tsaya ko'ina ba Unguwar su Shafa inda take aure, ahar gitse tashiga gidan shafa nagani ta tace lafiya naganki haka?.. zama tayi jagwaf tamkar kayan wanki tareda cewa hmm! kedai bari inafa lafiya ke kinji irin masifa data sameni rana tsaka kuwa?..ido shafata zaro cike da tsoro tace ke! meyasa me ki?..tace kishiya wani uban asharar Shafa ta yanko tareda cewa BABBAN masifa kuwa "shi *BB* ne yai aure kuma yaushe?.. Nan tafada mata komai aikam cikin masifa tace aibe'isa ba wlhy wannan aicin amana ne, don haka tashi muje nakaiki gurin wani hatsabibin mlm sunan shi mlm dare me abun mamaki, bamusu *Jana* ta tashi yayinda Shafa ta dauki gyale ba tareda Neman izinin mijinta ba suka fita. Saida sukayi tafiya sosai kamar zasu fita cikin garin Bauchi tukun sannan suka shiga cikin wani daji, shima saida sukayi tafiya me nisa sannan suka tsaya nesa dawata bukka me lullubeda ganyayyaki sannan suka fito suka rufe mota suka karasa gurin bukkar da kafa. Shafa tace da *Jana* karki ga gurin babu mutane shi baifaye aiki da rana ba saida daddare, amma idan irin na gaggawa ne to yanayi da rana tace nagane, dai-dai lokacin da suka isagurin bukkar Shafa tarera kirari sannan suka shiga cikin bukkar. Bakine mutumin wul yana sanye da bakin kaya zaune a saman bakin buzu, gaba daya tarkacen dake gaban shi bakake ne babu fariko daya, ya kalli Shafa yace kinzomun darana tsaka kuma kinsan bana aikin rana, tace ayi hakuri mlm dare a taimaka kawata ce take da matsala, yace meke tace da'ita?.. Nan take *Jana* ta koro masa bayani ba tareda bata lokaci ba yai yansur kullen shi, sannan takalli *Jana* tareda cewa kinyi sake domin kuwa son wannan yarinyar yayi matukar tasiri acikin ZUCIYAR shi, wanda bayan son uwarshi babu na wata ya'mace acikin ranshi, ke bari nafada maki gaskiya niko d'igon kwayar zarrar SONKI ban gani acikin ranshi ba, Dasauri tace wlhy mlm karya kake "mijina yana sona kuma babu wata mace data keda tasiri a ZUCIYAR shi idan bani ba. Cikin bacin rai yakalli shafa yace shafa'atu tunda nake aiki ba'ataba karya tani ba sai yau, wacece wannan ita har ta'isa nayi magana ta karya tani?... Cikin rawar jiki Shafa tace don bakin aljani mlm kayi hakuri,

Chapter 11 of 42