duk gidan sunfi kama dashi da ganin yanda fatar sa take shek'i kasan ba k'ananun kudi ake kashe masa ba bakin kilas ne a idon sa saide yanayin sa ba kamar na da ba yau ba far'a'an nan da haba haba da mutane kana ganin sa kaga me damuwa Baba Yakubu ne yafara masa kirarin da yasaba yace "barka da zuwa Alhaji Haruna sarkin tsafta Haruna kan d'aki bane hannu daya ya dauka ba a kaida d'a nabiyu a gidan 3.A. full nd'ororo an baka kabawa yaran baya Haruna kafi k'asan randa yawan wanka kai jarumi kake meson mutum kake".
hannun kawai ya jinjina masa ya fara takawa wanda da dane yadin ka wahe baki kenan yana nagode Baba Yakubu dan ko Nasara idan baba Yakubu ya fara masa kirari sai yasa shi murmushi balle Agrif sarkin fara'a ahankali yake takawa
Nasrim tayi saurin damk'e hannun
Zahra da hannun ta daya dayan kuma ta dafe k'irjin ta tace'' Zar gaba na faduwa yake"!
Zahra tace''
"Kinji kifa meye abin faduwar gaba bayan gashi gaki yazo lafiya zo musauk'a ya shigo".
Nasrim tace''kema kinsan part din Hajja zai wuce kibari sai ya shiga sai muje".
Agrif direct part din Hajja ya wuce kamar yanda al'adan gidan yake duk wanda yazo daga tafiya a nan yake sauk'a tun kafin ya k'arasa shiga parlourn ya fara rage suit din sa yarik'e a hannu sai farin riga da yabari
Hajja tana zaune akan wani lallausar kilishin ta idon ta cikin farin glass ta sunkuyar da kai tana karatun wani littafin da yagama tafiya da hankalin ta k'afar ta akan tum-tum Barira tana shafa mata man zafi ya shigo ciki-ciki yayi sallaman dan haka ba wanda yaji balle Hajja da tayi nisa a karatun ta har ya k'araso ya cilla kansa kan kujera there'siter bata jiba sai da Barira tace" barka dazuwa yallabai Agrif".
hannun kawai ya d'aga mata
sai asannan Hajja ta d'ago ta kalleshi ta tabe baki tace'' zama da mad'aukin kanwa dama ance shiyake kawo farin kai karasa halin d'auka sai na wannan bayahuden sallama ya gagare ka Haruna".
ta k'arashe maganan tana cire glass din idon ta tare da ajiye littafin
tsaki yayi yace". ko nayi sallaman amfani me zai miki dan Allah Hajja me kike nema a duniyar nan ne yanzu littattafan addini yaka mata agani a hannu ki ba wai novel ba ko mu jikokin ki bama karantawa".
"Haruna ka kiyayeni kar kaga ina raga maka saboda girman sunan ka awajena haka nace maka bana karanta littafin addini kalli can duk sune yoni ban dama Hajiya sabuwa tacemin littafin yayi dadi da ma'ana Wllh rabona da nayi karatu har na manta idan bana addini ba".
sake jan tsaki yayi yace kinji fa Hajiya sabuwa fa baza ta wuce sa ar Ummu ba amma da ita kike k'awancen karatun litafin soyayya".?
"Eh fadi kan ka tsaye ta dalilin littafin ma kuka san juna ko haramun ne labari nefa tamkar ta tsuniya yake gashi kuma kewa yake daukewa mutum meye a cikin jin labari inba nishad'i ba Hjy Bilkisu Funtuwa ta girmeni ma ba littafin ma take rubutawa ba k'arewa ma wata rana ai sai labari kuma zan bari gaba daya ma".
Agrif kwantar da kansa yayi ya lumshe idon sa yana sauraron yanda zuciyar sa take bugawa anya ? bayyi kuskuren barwa Nasir soyayyar da yarayu da shi shekaru shatara ba kuwa anya yayiwa zuciyar sa adalci kuwa to ma meyakai shi wannan gan gancin
Hajja yaji ta katse masa tunanin da cewa "to ai sai katashi min kaje inda ake zabbarin ganin ka an hada maka duniya kaje kai kam ai kaga ta kan ka yarinya rawan kai da kisisina tamkar uwar mata wannan ai idan Amina bata tashi atsaye ba ita ta haifawa d'a nasan juyaka zatayi sosai kamar waina acikin tanda".
shide bai kula taba ya mek'e dama hakan yake buk'ata dan adole yashigo dan kar ya tsaba doka dan yasan sai ta tara family meeting akan yazo bai sauk'a a ban garen taba
ahankali ya mek'e yafara tafiya yaji nata cewa"ikon Allah ni Lami Haruna da abinda yake damun ka je kagama cin abincin kazo kasameni".
Direct part din mommy yayi Yana tafiya very slow ma'aika suna ta masa sannu amma ko hannu yakasa d'aga musu har ya shige ciki
a hankalin ya murda handle din kofar ajiyar zuciya ya sauk'e da wani irin k'amshin d'akin ya ziyaci hancin sa idon sa yafara warewa akan komai na d'akin ko a ina yaga gyaran Nasrim zai gane tsaftan ta ya ban banta dana kowa afili yace "anya idan na cireki acikin rayuwa ta zan iya sarrafa shi tabbas inde zan cigaba da jin abin da nake ji yanzu to nan gaba kad'an za arasani ni nasan rayuwata na sadukar ba soyayyar kiba
jikin sane ya k'ara very slow a lokacin da ya tura kofar bedroom din nan ma k'amshin sa da ban dana parlourn kai tsaye bathroom ya wuce ya sakar wa kansa shower ya dafe bango yana sauraron yanda ruwan yake ratsa jikin sa yajima a haka sannan ya d'aura towels yafito adan gurguje ya shirya cikin k'ananan kaya t-shirt bak'i me dogon hannu da wando maroon ya dauki wayan sa ahankali yake taka steps idon sa akan wayan sa yana karanta message din Nasara yana sake jadda da masa alk'awarin su dan tun yana jirgi yake ta tura masa tsak'o baya Ripley ga ya dameshi da kira ba ya d'agawa bai taba ganin Nasir ya damu akan abu haka ba wannan shi ya tabbatar masa da lalle Nasir ya damu da Nasrim wannan shi yake k'ara k'arfafa masa gwuiwar ya bar masa kawai Allah yasa hakan shi yafi alkairi
zai shiga part din Ummun sa yaji anan shirin ta da i'k'aman sallan zuhur bayan yadowo daga masalaci yashiga yasamu Ummu zaune akan sallaya sai da yajira ta shafa ya tsak'o k'asa cikin ladabi yace "Ummu an wuni lafiya".?
"lafiya lau kadawo lafiya"?.
jin jina kai yayi
"tace'' to yayi kyau abinci fa.?
sosa k'eyar sa yayi yana murmushin da kana gani kasan a iya fuska ne
itama murmushi tayi tace'' dama nima na fad'a ne kaje inda aka hada maka delicious".
mek'ewa yayi yana cigaba da murmushi
Ummu tace'' amma kamar akwai damuwa ko kafin kazo kunyi abin da kuka saba ne kai da mutumin naka ko?". bai juyo ba ya girgiza kai yana cewa
"a a Ummu bakomai".
jin jina kai tayi tace'' ai dama kai da Nasara ba mejin kan ku kuma hakan yafi duk rintsi kuyi kokarin rik'e tsrrin junan ku dan idan kuka tona a sirin juna tanan shed'a'nun mutane zasu samu nasaran raba kan ku".?
"to Ummu mun gode in sha Allah ba komai kuci gaba dayi mana addua".
tace'' muna cikin yinta kullum Allah ya hada mana kan ku ya muku albarka yabaku zurua ta gari".?
"Ameen".
yace tareda k'arasa ficewa yana karanto addua azuciyar sa ta yanda zai tunkari Nasrim da salon
bakin sa d'auke da sallama ya shigo main parlourn Mama durk'usawa yayi ya gaida Mama ta amsa tana masa kirari "lafiya lau Baba Haruna gafi k'asan randa yawan wanka".
hawa kujera yayi yana murmushi yace", Hjy Mama me dinbin iyayi a ina kika zamu yaro haka''?
ya k'arashe maganan yana shafa kan wani yaro da baifi shekara shida ba
tace "la Agrif daman baka san Haydar ba ai d'an wajen marigayya Zainab ne yafi sheka 3 agidan nan ni aka bawa".
Agrif ya bude baki zayyi magana yaji sautin takalma kos kos ahankali bakin sa d'auke da addua ya d'aga kai wani irin bugawa gaban sa yayi tana tsakiyar Zahra da Humairah ajere suke takawa wajen sauk'owa daga steps din cikin sauri bai san sanda ya mek'e tsaye ba baki bude da gudu Humairah ta rungume shi yana murmushin bai san lokacin da yace "wahhh my heart kinga zata karya miki ni ko".
Nasrim tace'' Allah Yaya tunfa dazu muke ta faman jiran ka".?
"Tode yanzu ba gani gaban kiba ai sai yanda kikayi dani".
ya k'arashe maganan yana cire Humairah ajikin sa
yace "Hummee ke bakya girma kinga Nasrim ta dena fodowa mutane jiki ita dau girman".
dariya akayi har Mama
sannu dazuwa suka masa ya amsa yana shafa cikin sa idon sa akan Nasrim yasake cewa nifa welcomen din abinci kawai mutum zai min ya burgeni".
Nasrim tace'' ai Yaya baka da matsala da wannan".
tayi maganan tana jan hannun sa wani slowly kasala yaji ya rufeshi a sanda sanyaye kamshe turaren ta ya doki hancin sa jin tattausar tafin hannuta cikin nayi yasa gashin jikin sa wani irin mek'ewa har sai da yaji kamar yafadi a hankali yazame hannun nasa cikin nata ya sunkuyo dai-dai kunneta yace my sweet sister idan kina irin wannan gan gancin na rab'an mutum fa za'a iya samun matsala ke baki san daban kike da kowacce mace ba".
ya mutsa fuska tayi tayi gaba a slow yabita abaya gyara masa kujera tayi tace'' Bismillah ko".
har yanzu face dinta ba walwala
zama yayi idon sa akan ta ita kuma ta fara budude masa tana zuwa kan tuwon *d'alayi* yace" yawwa sis sannu da kokari Allah yabiya ki zubamin *d'alayi* ko sai kunun *mordom* sai *garabiyya* da dendero yan komin *denderon* na fara da dashi".
Humairah da Zahra dariya suka fara sukace dama ai munsan duk wannan shidimar baifi kaci kala biyar ba".
shide bai ma jisu ba ya shagala da kallon santala santalan y'an yatsun Nasrim wanda yasha jan lalle
sosai yaci tuwon d'alayi da miyar ganyen daddawwo kusan shi yacika masa cikin
ya d'ogo yana kallon Nasrim yace my heart missing you so much nayi missing girkin ki".
har yanzu ba walwala a face dinta tace' "ok girkina kawai kayi missing bani ba ko".
yana murmushi yace" am sorry I really nafi yin missing din girkin ki ai ke kullum muna tare a waya ai kema bakiyi missing din nawa ba tunda daga zuwana kin fara min fushi".
cikin turor baki tace ''ba kai ne kace ni ina da ban banci da sauran mata ba towai ni meye ban bancin nawa haka fa Yaya Kamal da ya Abbaty da ya Aiban ma suke min zasuyi hugging kowa ban dani ko kusa dasu nazo sai sudin ga ja baya".
cikin sanyin murya yace"bazaki gane bane Nasrim".
yajuya yana kallon su Humairah ta suke ta ciye-ciye yace to sarakunan ci mu zamu wuce ya mek'e tsaye yana cewa sister zokiji
direct parlourn sa suka suce
bayan ta zauna akan kujera one'siter shikuma ya zauna a wanda yake fuskan tarta there'siter cikin dauriya yace" da gaske bakiyi missing dina ba ko.'
yayi maganan can cikin mak'ok'oron sa cikin wani irin amon da ya ruguza duk kan garkuwar jikinta
ido ta zuba masa bata san yanda zata masa bayani yanda yake acikin yarayuwar taba
cikin sanyin murya tace" Yaya I really missing wllh bana second 10 ban tunoka cikin rayuwata ba bacci nishad'i duk sai da tunanin ka yake tasiri ba sai nace kai daya ne a Raina ba nasan kasan da haka tun jimawa bani da burin da yawuce n....
da katar da ita yayi dacewa
nasan da haka NASRIM ni anawa ban garen har yafi yanda kike jina ina ga nafi mommy da daddy sonki shiyasa ma nake son yazama kece ta farkon Wanda zan furtawa farin cikin abinda yajima a rayuwata Nasrim najima ina cemiki inason na gaya miki abu mai mushimmanci to yanzu lokacin yayi Nasrim ina neman soyayyar y'ar uwar ki k'awar ki wato IZZATU ke nake son ki sayo min soyayyar ta dan kinfi kowa kusanci da ita Nasrim Ina son Izza ta zama matata uwar y'ay'a na dan All......
awani irin razane ta m'eke jitayi kunnuwar ta da kwakwawan ta sunto she dif
shima me k'ewar yayi yana sun kuyar da kansa
cikin rawan murya yace" what happens to u
kamar bakiyi barin ciki da abin da nazo miki dashi ba ko batayi ba? Wllh idan kika ce batayi bana barta har abadan ki canza min da duk wacce ki kaga tayi".
itama cikin rawar murya lip dinta na rawa tace'' seriously Izza kake son"?
cikin cool voice yace " sure".
"Yaya kasan me kace kuwa Izza fa".
baya yayi ya jefa kansa cikin cushion ya lumshe idon sa yana danne wani abu da yake taso masa can
yace" Nasrim shifa baki dan aike ne duk abinda ya furta to daga zuciya ne
Sure ina son ta".
Nasrim ja tayi da baya da baya har taje tsakiyar parloun tajuya dawani irin sauri ta fita shiko daya ke idon sa alumshe yake bai san ta fita ba dan yasan a yanda zuciyar sa take idan yaci gaba da kallonta komai zai iya faruwa jiyake kawar yajata ya gungumo ta yake keji
Nasrim a dai-dai babban parlourn suka kusan cin karo da mommy da shigowar ta gidan kenan daga wajen aiki da gudu ta k'arasa ficewa ko mommy bata gani ba amma taji murya ta tana cewa lafiya
bata juyo ba kai tsyaye part din Hajja ta nufa bata tsaya a k'asa ba tawuce sama Hajja da take zaune da wasu bak'i tana ta fad'an ke marar hankali wannan gudun fa kin ibi k'ugu kamar wata uwar mata".
bata kula taba ta wuce bedroom din Hajja direct zubewa tayi akan gadon Hajjan
har yanzu kuka yak'i zuwa mata wani irin bugawa zuciyar ta take mata gaba daya tunanin ta ya d'auke cikin k'an k'anin lokaci kanta da jikin ta yad'au wani irin zafi wani irin kar karwa takeyi
Hajja da tama manta da Nasrim ta shigo sai da tashigo alwalan magariba taga mutum kwance akan gadon ta sai wani irin karkarwa takeyi ja Hajja tayi da baya tace
"la'ilaha'ilallahu me zan gani ni Mariya dama wannan y'a tana da mutane boye ban sani ba nabari ta shigo min dasu d'aki dan mugun ta har kan gadon bacci na yau nashiga ukku a gidan nan inane gun kwana na na gadona tun na Abdulsamad na hana acan zamin wani dan idan nazo kwanciya kullum sai na tuna dashi na masa addua Allah sarki da hannun saya kafamin gadon nan kafin ya kwanta dama shine zaki shigomin da mutanen boyen ki
Ina Barira Barira".!
ta k'arashe maganan tana kwallah wa me'aikin ta k'ira amma tana sake ja dabaya wai tana tsoro
da sauri Barira ta shigo tana
cewa " Hajja Mama lafiya".?
''ina ko lafiya an shigo min da masifa".
ta nuna Nasrim da bata cikin hayyacin ta
da sauri Barira ta hau gadon tana dafa Nasrim ta zaro ido cikin tsoro tace'' Hajja wani irin zazzabi ne ajikin ta kamar garwashin wuta" .
Hajja tace'' zazzabi ko far fadiya kiga yanda take girgiza gadon nan ba ita daya bace Kira uban ta ya nemo me ruk'iya".
da sauri Barira ta fita takira Mama atare suka shigo dasu Humairah Mama kuka tasa a sanda ta dafa jikin nata haka zahra da Humairah jiki na rawa Habiba takira family doctor din su
Dr yana auna BP dinta yace" subbahanalla Hajiya ya akayi jinin ta yayi mugun hawa lokaci daya haka me yasame ta da girma haka".?
cikin kuka suka ce basu sani ba
haka aka wuce da ita hospital
********************
a hankali ta bude idon ta da take jin ya mata nauyi idon ta ne ya sauk'a akan nasa yana rike da hannuta wanda ake mata k'ren ruwa dashi shima idon sa akan ta juyawa tayi tana kallon sauran mutane mommy Mama Ummu da Abu da daddy
Daddy yayi saurin cewa "daughter daughter ya kika ji jikin naki me yake damun ki meye damuwar ki me kike so".?
Murmushi tayi tare da tura lips dinta na k'asa cin bakin ta ta matsa a hankali tace
"Daddy kawai dama jinayi kaina yana min ciwo amma yanzu banajin komai dan Allah mutafi gida".
Mama tace'' damana fada bawani abin da yake damun Nasrim to meye ma zai dameta kawai fa rashin bacci ne ni nasan kwananan tana ta faman shirye shiyen zuwan Agrif bata zama sam itace wankin kai da kitso kunshi shekaran jiya fa da kanta ta tafi kasuwa wai baza a mata yanda take so ba gashi agarin burgr Agrif y'ata zata sawa kanta ciwo".
dariya sukayi amma banda Agrif da mommy ita mommy daya ke likita ce tabbas tasan da akwai abin da yake damun ta
Nasrim kallon hannu Agrif dayake cikin nata tayi a hankalin ta zame hannun ta tasa daya hannuta ta finciko drip din yafice kafin wani ya yunkura yace wani abu har ta sauko Abu yace" subahanallah ya haka Halima?".
"Abu bana son hospital din mutafi gida".
Daddy da Abu za suyi magana mommy ta dakatar dasu da cewa "a a Abu mu tafin kawai bawani abu zan kula da ita ko agidan ne".
part din mommy aka wuce da ita har cikin bedroom din ta da misalin Sha daya na dare bayan kowa ya watse mommy ta zauna abakin gadon tana kallon Nasrim da tayi sanyi sosai tace'' what is it you're doing Nasrim
kau da kanta Nasrim tayi cikin sanyi murya tace"
everything happens to meye ma bai faru dani bane mommy amma ke ba uwar data dace tasan damuwar y'arta bace".?
"Why zaki fadamin haka Nasrim me kika nema kika rasa a wajena".
Mommy so so na rasa soyayyar ki mommy kin fison wani daban bani ba tun ina jaririya kika yakice ni ajikin ki kika nisan ceni ban jima da sanin wai kece kika haifeni da cikin ki ba azatona Wanda kike so shi kika haifa nikuma Mama ce uwa ta to mommy nasamu labarin yanda keda da'n ki kuka azaftar dani ina tuna wani lokaci da yazo kikace kar na sake shiga part dinki har sai ya tafi idan gaisuwa ne namiki idan mun hadu wajen cin abinci a parlourn Hajja tun daga lokacin na dena zuwa part dinku sai de idan na ganki na gaisheki kin taba damuwa da wannan wani lokacin zamuyi kawana 3 bamu hadu ba musamman san da muke secondary kafin kutashi mun tafi idan mun dawo kungama cin abincin dare kowa yakoma part din sa kwanaki nawa nakeyi bangan kiba so bawani shak'uwa da yake tsakanin mu wanda zaki ji damuwata ba
bakya sona Agrif ne yakare rayuwata daga sherrin da'nki kuma yanzu gashi shima Agrif na rasa shi shikenan".
"Nasrim please finish ba dogo magana na tambaye kiba because ban taba ganinki cin wannan yanayin ba Nasrim ba uwar da zataki y'ar data haifa ina da nawa manufar na janyewa a jikin ki but bazan iya jurewa ganin ki haka ba mek'e damun ki Nasrim hankali na a tashe yake akan ciwon da naga yana barazanan samun ki Nasrim zuciyar ki cefa ta kusa bugawa wanda tsananin nisan kwana ne yake sa mutum ya tashi tabbas wani abu ne yafaru dake me girma Nasrim bani da kowa sai ke da Nasir a kullum burina Allah ya hadamin kan ku kuso junan ku shine buri na kuma ni nasan duk dare gari zai waye wata rana shida kansa zai furta yana son ki dan shima bashi da wanda yafiki a rayuwa Nasrim ki gaya min damuwar ki?.".
ta k'arashe maganan cikin kuka me tsanani tare da rungume Nasrim din tasa ta ajikin ta sosai
Nasrim ajiyar zuciya ta sauk'e jinta ajikin mommy taji wani sanyi aranta wanda sai yanzu taji hawayen data kasa fito dashi tun dazu ya fara fitowa da k'arfi
cikin kuka tace'' mommy ya Agrif yace bani yake soba Izza yake so mommy idan yasan bani yake soba meyasa ya zalinci zuciya ta ya dasa mata son sa b.....
awani irin zabure mommy tayi tare da mek'ewa tsaye tace''me !?
Izza a a wllh ko kaffara bazan yiba ke yake so ya gayamin wannan tun ranan da aka haifeki kuma ko kwana nan maya gayamin ke yake so bari na kirashi".?
tayi maganan tana daukan wayan ta dayake kan bedside da sauri Nasrim tada katar da ita
"Mommy ya riga ya furta Izza yake so kuma yace har cikin zuciyar sa har yana cewa _shi baki dan aike ne abin da yake cikin zuciya yake furtawa_
wllh mommy na hakura dashi ko yanzu yace ni yake so bazan so shi ba ni ina da kishi bazan auri wanda ya furta yana son wata ba ki min addua Allah yabani wanda zan so shi fiye da shi kuma wanda bazai min kishiya ba".
Mommy tace'' gaskiya ni ban yarda da wai baya son ki ba saide da abinda ya can za masa ra ayi".
Nasrim tace''mommy kyan ta yagani".?
"tsak'i mommy tayi tace'' Izzar banda farin fata me ta isa ta nuna miki ke abu nawa kika fita idan ana maganar kyau ta isa ta tunkaro inda kike ma dade abin da ya sauya Agrif amma ba wai kyanta ba kuma har yanzu Agrif yana miki tsananin son".
ta k'arashe maganan tana danna wayar ta da nunawa Nasrim wani pic din ta ire iren wanda Agrif yake daurawa a status din sa da kalaman soyayyar da yake daurawa Nasrim duk da tun ranan daya d'aura ta gani amma jitayi yanzu ma tana son sake karanta kalman da yarubuta kamar haka
_ME RIGUNA DUBU HALIMA AI KWALLIYAR KICE ME HALI DABU HALIMA AI MARTA BAR KI CE
sai wani da yasa
BURIN HARUNA HALIMA ARA NA KE DAYA CE A ZUCIYA KIRIK'E KI AJIJ DADI WUYA NA D'AU ANIYA_
sai wani wanda ya rubuta
_i na son ki na yaba da halin ki k'yan jiki da suran ki_
Sai na gaba wanda yarubuta
_masoyiyya ta nada kyau kuma bataji da kai hakan ne yasa ake mini barka sonki ya cikin jikina buri na dare da rana_
dade sauran su dama mommy yana daurawa dake dauka ta adana a wayan ta dan tanan take samun pic din Nasrim ajiyar zuciya Nasrim ta sauke tace "mommy ya cutar dani da kalaman da suka fi wannan ma". Mommy tace
"dan de kince ko yabar Izza bazaki soshi bane da sai nayi yan da nayi kika sameshi amma tunda kikace na miki addua in Sha Allah zan miki Allah yasa hakan shi yafi alkairi kuma nafi damuwa da kicire komai aranki ko agidan nan kar ki nunawa kowa komai kibi abin ta yanda yazo miki kuma ki samu Izza ki gaya mata kamar yanda yace kinji".
"to mommy amma a yanzu ba sai gobe ba zan kira Izzar na sanar mata".
da wani irin k'arfin gwuiwa ta mek'e tafita
a parlour n Hajja ta samu Izza kamar yanda ta zata tana aikin nata wato kallo
kama hannun ta tayi suka tafi k'aramin falon Hajja cikin dauriya da nusuwa ta mata bayani
komai amma tayi mamakin ganin farin ciki a face din Izza kuma ba musu ta amsa tayin soyayyar Agrif bayan tasan yanda Nasrim take son sa
a wannan daren de Nasrim bata wani samu baccin kirki ba
*****************
Washe garin tashi tayi cikin walwala dan tasa niyar danne abin sosai a ranta a hankali take takawa duk inda ta gif ta ma'aikata suna mata sannu cikin murmushin take amsawa
Part din su ta nufa kusan cin karo sukayi da Zahra da Humairah su zasu sauk'o ita zata hau kama hannu su tayi sukayi saman a k'aramin falon saman suka zauna cikin nusuwa ta musu bayanin sak'on Agrif
Humairah tayi tsalle ta dire tace ina wllh bazai yuwuba da Ummu zanje na hadashi...
hannun ta Nasrim ta kamo tana murmushi tace'' a a Hummee Ya Agrif duk yamin bayani kuma na gama gamsuwa dasu dama can nice nake ganin kamar son aure yake min ashe son yan uwan taka ne Itama Izzar tun jiyan wajen karfe Sha biyun dare na k'irata muka zauna na mata bayani kuma ta gama gamsuwa".
Zahra tace'' ta amince fa kika ce bayan tasan shine zabin ki bazata iya sadaukar miki shiba."
Humairah tace'' ai ni shiya sa dama can Izza ba wani burgeni take ba wllh fuskar salihai kawai take yabawa a zuci ba haka bane in ban da munafuka sarai tasan yanda kike son ya Agrif mutum ko awa daya yayi dake ai zai san matsayin sa awajen ki balle ita da muke Kwana mu tashi tare" .
Murmushi tayi cikin rashin damuwa tace "Please come down duk Wannan ya wuce nawa ne za ayi soyayya kamar acinye juna amma daga k'arshe ba za'a auri juna ba balle nida bai
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 40