uwa na yamiki ni naki dan uwan yana bani dukkan kulawa amma ni nawa ya kasa".
ajiye cup din hannu ta tayi akan Center table cikin murmushin k'arfin hali tace'' dan uwan ki fa kikace ni kin cireni cikin family kenan ko sannan ni ya Agrif bai min komai ba ni yanzu na ganshi da Ido ma nake so ina mugun zargin kaina da wasu abubuwan ni yaka mata naji kunya saboda kar yazamana tsilan auren mune yasa hakan ta faru dashi ban san dalilin tafiyar saba".
kafin Hummee tayi magana har iyayen sun taso suma
Hajja ta k'asara kan tum_tum dinta tadan k'ishin gida sanna tayi kyaran murya hakan yasa mommy daddy Abu da Kamal da kowane yake shirin fita acikin su komawa ya zauna akan kujera dan sun san magana zatayi
sai kowa yanutsu tace''
"Fanna Ina son ki kiramin miskilin d'an naki wanda in ba kiranki ba bazai dauka ba sai yaga dama dan na san a wajen sa kadai zamu samu labarin Agrif yasan inda yake tabbas duk inda Agrif yake da sanin Nasuru".
hannu mommy ta saka acikin jakan
ta zaro wayan ta tare da danna kiran ta mek'awa Hajja
Hajja tace'' a a ba sai kin bani ba saka a handfee".
Nasir da yake a kwance duk abin duniya ya ishe shi tun randa ya *sadu* da Nasrim bai samu sauk'i ba kamar yasa a sato masa ita yayi ta kasan cewa da ita yake ji danta canza masa duniyar sa sosai sai juyi yake akan makeken gadon sa dan a da shi ba mazinaci bane Nasrim ma yayi ne dan yasa Agrif ya tsaneta amma badan wai yana ra ayi ba sai kuma yajefa kansa wata duniyar da bai taba tunanin zai shiga cikin taba mamakin kansa yake da k'ara tsanan Nasrim dalilin ta ya fara aikata zina gashi ya zame masa masifa wai shi Nasir ne har ya wayi gari ya
afkawa yan matan da suke masa aikin tausa da sauran shidimomi wanda ada yake kallon su kamar maza jinsu yake tamkar jinsin sa bai taba ganin su amatsayin mata ba
amma sai gashi dumu dumu yatsici kansa da farko Raddeka y'ar India ya fara afkawa bai ji komai ba sai b'acin rai sai yasake afkawa dayan silinyan y'ar k'asan turkey ce nan made baiji wani sauki ba daga
k'ashe ma koran su yayi gaba daya agidan
gashi shi yana mugun tsananin matan turawa baya harka dasu kawai zuciyar sa tana bashi shawaran ya sato Nasrim ya kulle ta a d'aki me duhu yayi ta amfani da ita idan ya gaji sai yasan yanda zanyi da ita tsaki yayi ganin Wannan shawaran bayyi ba bai isa daukan fansan ran mahaifiyar sa da mahaifin sa da suka rasu adalili ta ba abin da ya shirya tun yana yaro shine dai-dai da fansan sa amma yanzu yazo ya ajiyeta yana amfani da ita ai zai iya fad'awa soyayyar ta abin da baya fata kenan afili yace Nasrim lefin ki yayi mugun k'aruwa aguna bayan na iyayena yanzu kin sani na aikata babban tsab'o wato ZINA Nasrim kifara hukun ta kanki kafin ki fad'a tarko na kifara yankan Naman jikin ki kina cinyewa kafin na juyo kanki
yana cikin wannan sun batun yaji wayan sa yana Ringing kuma ring din mommy ne
cikin dan masifa masifa ya d'aga Yana cewa
" haba mommy kinsan fa mu anan dare ne meyasa idan zaki kira b'akya duba lokaci da muke ciki anan ne".
"Please wait my Son kar ka kashe min waya tambayar ka zamuyi ina Agrif"?.
"Mommy kin san me kike cewa kuwa Agrif kike tambaya nafa waya ban ajiyar sa ummmm".
Hajja tayi saurin cewa"rasa kunya beran tan-tan mommy ta kama baka kyale ba to Agrif muke nema nasan kasan sarai inda yake ai dakai dashi nasan shegu biyu ne wake da shinkafa ya dirkawa yarinya ciki a daren farko mun sha wahalan jinyar b'arnan da yayi mata yugu-gudu har da d'inki ya farka ta ya gudu to ka binciko mana inda yake yanzu ga ciki ya bullo dan h..........
Nasir da har zai kashe wayan amma jin wannan kalaman na Hajja yasa hannu sa yafara mugun rawa cikin in in na yace " ciki ciki ciki Hajja Nasrim tayi daren farko mu amma Hajja dan Allah yatake yanzu tana lafiya ko Hajja dan Allah ki kula min da ita kafin gobe nazo dan Allah duk abin da take so abata amm kawai bawa Mama nasan tafi kula da ita ciki nan Hajja naw".
ji yayi anzare wayan ta bayan sa
Agrif cikin murna yace "Hajja Nasrim tana da ciki ki kace".?
Al'hamdulillah Allah na gode maka da ka nuna min Wannan ranan Hajja taya zan gudu in bar amarya ta da gan-gan akwai dalilin Wanda ita ma tasani amma insha Allah gobe zanzo kuma kuzuba ido cikin second ni k'adan zan goge dukkan lefina awajen Nasrim akula min da ita kafin goben amata albishir da tukuicin na musamman".
ya nagama fadan wannan ya kashe wayan tare da jefashi saman bed yajuyo zai fita
Nasir yace my friend ya kaga DAMA TA na biyu ya cika saura na ukku in sha Allah shima zanyi Nasara kamar yanda nayi nasara samun budurcin ta da samun cikin ta
yanzu saura ta haufanin da me kama dani sak kaga Koda ban fada ba za adasa ayar tambaya ayan Kai da ita kuke bak'ak'e ".
Agrif ya taka har inda Nasir yake ya d'aga kafan sa daya ya d'aura abakin gadon cikin murmushin k'arfin hali yace " hakan zai iya kazan cewa ta haifi d'a namiji kamar yanda ka buk'ata saboda Allah yana bawa masu tsabon sa dama amma kasani sab'on Allah guba ne da zayyi ta yawo ajinin ka musamman na ZINA har jiko kin ka Nasir ina matsayin ka kana yawo da lefi kwarara Zina cin amana to kasani bayan shika bawani lefin da take da girma awajen Allah kamar Zina duk lafin da mutum yakeyi tamkar guguwa take yana yawo amma idan yasamu Zina to rumfa yake kamawa yadin ga jifguwa ta yanda ba k'aramin tuba bane zai rushe she".?
Wani irin Dariya Nasir yayi sai kuma ya daure fukka yacin Izza yace " Eh nasani na sab'awa ubangijina amma kasani zai yafemin dan Wannan shine lefina na farko a duniya kuma ba shirka nayi ba wannan shine zai bani damar nayi yanda nake so da Nasrim da duk Wanda ya rabeta".
Agrif yace baka isaba inde ina raye ganin Nasrim sai yafi karfin ka balle ka cutar da ita in Sha Allah kayi na farko kayi na k'arshe ".?
murmushi Nasir yayi yace "ni Nasara har akwai wani abu da zan soyi ya gagareni dan uwa har yanzu da birbishin son ka a zuciya ta shine yasa nake raga maka amma har yanzu baka makara gaba daya ma ka tsaki Nasrim zamu koma kamar da".
Agrif yace " kai wawane a yanzu ko nace na bar maka Nasrim baka isa ka siyi soyayyar taba s.....
katse sa yayi cikin sauri yace kai kanka kasan bawani soyayya da bazan iya tsiyan sa ba ciki har dana auren mata dubu da zayyiwu ka taba jin wanda yace baya sona a duniya ai tare muka tashi daga kan iyayen mu yan uwa mu abokan mu ma ai'ka tan mu duk wa sukafi so kaga banyi niyar nl bawa mata dama su soni bane".
Agrif yace " haka ne nasheda anfi son ka amma kasani ba so bane tsoro ne duk Wanda kaga yace yana sonka to wllh ba sonka yake ba tsoron ka kawai ake ai kai baka isa ka siyi zuciyar mutane da soyayya ba sai de ka tsiyi tsoro da Izzar ka amma kasani
matan da zasu soka ba irin Nasrim bane mata irin su Nasrim kudin ka mulki ka sarautan ka duk baya d'ad'asu da k'asa kuma na baka dama ka zaga duk duniya ba zaka taba samun irin Nasrim dina ba Nasrim tawace dan ni Allah ya halicce ta".
Nasir yace ''Agrif kudi ba abin da baya tsayawa mutum kai yanzu ba matar ka na nema a daren farkon ka ba meyasa baka dauki mataki ba saboda kasan na maka nisa ne sabo da ni goshin jirgi ne me wuyar karau".
Agrif yacije lefin sa abin yana k'ona basa rai amma ya danne cikin murmushin yace
"ban kyale ka dan Ina jin tsoron kaba Nasir na kyale kane saboda Abu biyu ko ukku
Na farko narufa maka asiri ne saboda idan bawa ya rufa asirin wani bawa Allah zai rufa masa nasa na biyu inason Allah yabani garabasan da yake bawa masu hakuri musamman Wanda aka zalinta wanda yana da k'arfin ramawa amma yazuba ido to zai ga sakayya Kai kanka kasan ka zalinceni amma na cinye ba dan bani da k'arfin ramawa bane wllh baka fi karfin komai ba ciki harda hukunci ".
Nasir dariya yayi yace" karfin ramawa ai zanfi son haka dan zakafi bani k'arfin gwuiwan sanin inayi da namiji Agrif tun farko nafito na nuna maka akwai illa a rayuwar ka muddin ka aure ta amma ka aure ba tare da daukan wani matakin ba Kai kan ka san ni babban bak'iyin kane tun daga randa ka aure ta meyasa baka dauki mataki ba dama baka shiyawa hakan ba ai nayi zaton ka shiya ne wawanci ne Allah Ta'ala ya nuna maka mak'iyin ka amma baka nemi hanyar ts'ira daga sherrin saba na gaya maka tun farko ni nafison katona min asirin sabo da cikar wata DAMA TA tawa barin abin ahaka wllh ni ba rufa man asiri kayi ba zaifi min dadi idan kowa yasan cewa cikin jikin Nasir ba naka bane nawa ne kuma nafison ka fada da bakin ka za afi yarda ".
Agrif yace" ai nasan kafi son a haramtanin ita shiyasa bazan taba tona asirin hakan ba zanjira har sai sanda Allah ya sauketa lafiya na mayar da ita cikekkiyar matata zamuyi rayuwan da ba wasu ma auratan da sukayi".
cikin wani irin dariyar mugunta Nasir yace " ni Nasir na maka alk'awarin inde ina numfashi a duniya Nasrim bazata taba jin dadi ba wanda ya rab'u da ita ma bazai ji dadi ba kai meyasa ka kasance me taurin kai ne mommy da cikin ta ta hafi Nasrim amma da nace bana son ganin ta da Nasrim rabuwa tayi da ita takoma wajen Maman Kamal da zama sai kai kayi taurin kai ka aure ta ba abin da ban gaya maka ba dan haka wllh yanzu ma nafara k'unta ta maka Wannan kad'an ne manyan na nan zuwa
duk da yanzu ma Al'hamdulillah Allah yabani sa a biyu na farko dauke budurcin ta wanda nasan har iya karshen rayuwar ka sai de kayi manage da ita amma fanko ce ita bazawara ce sai na biyu Allah yabani daman ajiye d'a a maran ta wanda hakan na nufin ni zata fara haifawa d'a ba kai ba duk san da zakayi sex da ita sai ka tuno ni na fara shan romon farko duk sanda ta Haifa maka d'a sai katuno nawa ne babba
murmushi yayi tareda dafa kafadan Agrif yaci gaba dacewa
Yanzu dama ta ukku nake rokon Allah yabani wanda dashi zanyi AMFANIN Nasrim ta haifamin d'a namiji me kama dani.....
hhhhhhhh yayi dariya tare da jefa kan sa cikin kujera yaci gaba wllh Agrif zanyi abin da dakan ka zaka fito kanunawa Nasrim ni ta haifawa d'a ba kai ba zanyi AMFANIN da DAMATA wanda kai kanka kasan bana sake dashi kuma kasan duk abin da na furta to sai nayi shi ko yayi kyau ko kar yayi nide ba Wanda ya isa ya dakatar dani Agrif ba a tsabawa umarnin Nasir da kab'atawa Nasir gwara ka sab'awa ubangijin ka yana sonka zai iya yafe maka ka bari mu hadu gobe a 3brother kaga abin da zan iya da wanda bazan iya ba ko zan baka mamaki....
hada yatsun sa yayi ya bada sauti k'as k'as yace " Agrif ka sani NASARA baya yafiya baya furta abin da ba zayyi ba kajira saka mako".
ya tashi yashige bedroom din sa
dafe kansa Agrif yayi yana ta mai maita Hasbunallahu wa ni' imal wakin
Kwana a k'asan nan bai kama shiba dole yariga Nasir zuwa Nigeria yanzu ya zauk'a akasan Dubai din dama dan ya dauki wani documents din sa a gidan Nasir din sai yasame sa yana wannan wayan azabure ya tayi yayi han yar waje...
gida kuma Hajja cikin mamakin kalaman Nasir na cewa _Nasrim ta samu ciki adaren mu na farko dan Allah kulamin da ita kafin gobe nazo_
cikin mamaki tace "Abdulmajid me hakan yake nufi me kalamun Nasir yake nufi ko de................
*dir k'ashi To masoyya ankusa fa shiga RIKICIN BABBAN GIDA ya Nasir da Agrif zasu kasance wake da nasara sai naji comments din ku mu hadu a page 8 insha Allah sosai nake jin dadin comment din ku Allah yabar kauna*
*Bj*
[4/8, 1:47 PM] Batul Adam Jattako: *FURUCI NA NE*
(```Rikicin Babban Gida```)
*NA*
*BATUL ADAM JATTKO*
```Marubuciyar```
*DAMA TA*
*AMFANIN SOYAYYA*
```NOW```
*FURUCI NA NE*
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
*Page 9*
Dama wannan bayahuden shi yamin haka shi ya rabani dakai na shawon sati shida alokacin da nake buk'atan ka akusa dani shiyasa ni dama banga lefin ka ba dan Allah Yaya kane mi wani ai'kin a wani'gu tunda baya sona ka aureni bazai bari muji dadin rayuwar mu ba ai kagani tunda ga yanzu ya turaka aiki adaren furkon mu mun jure yaga ba riba shine yanzu yafito a file yake maka barazana daka sake ni ko".?
ajiyar zuciya Agrif ya sauk'e afile bakin sa yana furta "Al'hamdulillah" tunda bataji kan zancen ba duk da shima hankalin sa atashe yake amma cikin son wantar da nata hankalin yace " come down ki fashin ta my dear ni nafi kowa sani waye Nasir ba zance yana farin ciki da auren mu ba kuma bazance yana b'akin ciki ba dan da baya so wllh yasan hanyar da zai biya yaha auren amma Nasir mutumin kirki ne ba yanda kike daukan sabane".
cikin rashin yarda da maganan nasa tace'' mutumin kirkin ne zai umarceka daka sakeni har kana cemasa zaka d'auki duk sharadin sa ni kawai kagaya min wane sharadi ya gindiya maka har kake masa alk'awarin ko yatsa na bazata taba ba?".
cikin in'ina
yace
" amm amm dama randa zan tafi Bai San na karbi budurcin ki bane kawai Hajja tasa mommy ta kirashi tana tambayar sa ni anan tagaya masa kina da ciki shine yake fadan na zaliceki wai jikin ki nake so nak'asa hakura har naje na dawo haka na turmujeki da gajiyar biki to danaga ya zauki zafi dayawa sosai har yana gani kamar wata rana zan iya juya miki baya shine na masa alk'awarin dana miki randa zan tafi ai namiki alk'awarin bazan sake neman wani abu ajikin kiba har sai kin shekara agida na dan ki yarda ba jikin ki nake soba abin da yafaru k'addaran ce
to wannan shine saradin Nasir shi yana fadane akan ki
ki yarda dani Nasir yak'i yake akanki Nasir masoyin kine na boye ke kike nuna masa k'iyayya".
tabe baki tayi tace'' ummm to Ina ruwan sada rayuwar mu nide wllh ban karbi wannan sharad'in ba".
Agrif yace" nima bawai na karbi sharad'in sa bane ah ah yazo akan gab'an alk'awarin da na miki ne bazan kusan ceki ba in Sha Allah har sai lokacin da na dauka yayi danna nuna miki ke nake so bawani abunaki ba".
Nasrim wani irin kallo ta masa tana tabe baki ta wuceshi
sai data haye kado taja blanket ta rufe rabin jikin ta tace'' ni kuma ban yarda da wannan alk'awarin ba ni kayiwa lefi kuma nayafe maka saboda isanka a waje na kai harma kafi".
tana gama fadan haka ta k'arasa jan bargon ta ta shige ciki
Agrif dube dube yafara da alaman yana nemam inda aka tsak'ala CCcamera ne amma bai gani ba
cikin muryar shagwab'a tace''
"wai me kake nema ne ".?
diri diri yayi yace
"amm sweetheart ki kwanta kinga kina buk'atan hutu bari ingama shiryawa ina zuwa".
yace tare da ficewa daga shi sai towels akugun sa
yana taka steps wani message din yasake shigowa Nasir din ne de da sauri ya bude gaban sa yana fuduwa yafara karantawa
_banason kabawa kan ka wahala wajen neman CCVT Dan zaka b'ata lokaci kane dan ko da ido dubu aka halicceka bazaka gani ba_
a slow yake takawa
d'akin k'asa yashiga ya zauna abacin gadon yana dafe kansan
shima
Nasir abangaren sa rufe laptop din sa yayi ya mek'e yana murmushi yafita da saurin sa yafice direct part din su Agrif ya nufa cikin rashin far gaba saikace gidan sa haka ya haye har sama direct bedroom din da yake zaton anan Agrif din yake yanufa murda handle din yayi ya shika Agrif duk da bai d'ago ba amma yasan Nasir ne dan idan ya doshi gu k'amshin turaren sane yake sallama
karasawa yayi har inda Agrif yake abakin gadon shima zama yayi abakin gadon yasa hannu ya cire tagumin Agrif cikin sanyi murya yace"
My friend banso muka zo wannan matakin da Kai ba naso ka dauki shawara ta tun farko kara bu da ita amma ka nace banso kyakkyawar halak'ar mu takoma haka ba dan kasan kaine abokin shawarata kai kafi kowa sani na duk damu ukku muka tashi Amma kasan bamu shak'u da Kamal kamar kai ba agani na na isa dakai ni me baka shawara ne san nan nafi k'arfin komai awajen ka".?
Agrif sake matse hannun sada yake cikin na Nasir yayi cikin k'unan zuciya yace "Nasir kafi karfin komai awajena nasani shine dalilin na na barmaka NASRIM tun farka a zatona da gaske son ta kake duk da nasan bazan jure rashin taba nima amma na bar maka dan kafi karfin komai awajena ashe kai bason Nasrim kake ba nikuma ina sonta bilhakk'i bazan yarda da abin da zai cutar da ita ba dan Allah Nasir Nasrim taci darajan son da kake min kabari mu zauna lafiya".
girgiza kai Nasir yayi yace' ah ah wllh bazan iya ba Agrif bazan iya kwatan ta maka yanda zuciya ta take min barasaza a kowacce second game da Nasrim bane tayi mugun shiga yaruwata yanda bazan iya kwatan tawa ba wllh bazan taba barin ta
ta huta ba".
numfasawa Agrif yayi yace
"Nasir ka bani mamaki duk da nasan halinka duk abin da kace zakayi zakayi da kace bazaka bari nazauna lafiya ba ban zaci ta wannan hanyar zaka bullo ba duk atunani na k'untatawar taka zata tsaya a iya korata a aiki ne tunda Kai ne me campanyn amma ashe abin naka ya zarce nan Nasir ina tausayin ka aranan da zakayi nadaman abinda ka aikata kana musulmi ka aikata zina da matar aure kuma baka sirran tashi ba kanunawa wanda yake auren ta saboda ka isa kasani wllh Allah shine ishehhe Nasir wani irin zuciya Allah yabaka da baka sawa aranka akwai ranan shisabi awai randa ikon ka kudin ka baza su maka amfani ba Nasir ban zaci isar taka har takai ka dauki CC camera kasaka a d'akin aure ba har kana barazana dashi kasani mala'ikun Allah ma idan ma'aurata suka keb'e kansu juya musu baya sukeyi basa ganewa idon su tsiraicin ma'aurata Nasir me namaka ?me Nasrim tamaka? Wllh Nasir ka jefani cikin wani irin k'uci wanda ko fitar rai bana jin yafishi ciwo why".?
ya k'arashe maganan yana dafe goshin sa saboda kansa da yake masa zugin ciwo
Nasir mek'ewa yayi tsaye yana juya baya yana murmushi me dauke da b'acin rai yace
"Agrif duk yanda zaka kwatan ta zuciyar ka bata kai tawa ba wllh nafika shiga cikin k'unci
Dan Allah ka temaka kar kayi yunk'urin bawa Nasrim kowane
irin farin ciki a karo na biyu zan zo maka da buk'ata idan kabi insha Allah zaka tsira da mutumci ka idan kayi gardama irin na baya to saka makon zaifi haka muni".
cikin dauriya Agrif yace" me kake buk'ata"?.
sunkuyawa yayi cikin taushin murya yace
" Ina son ko dan yatsar ta kar ka taba har ta haifamin yaro na sannan ina son mahaifar ta yazama a tsarkake yake shine dalilin saka cc camera idan ka k'arya alk'awarin nasani".
Agrif yace
"wannan sharad'in ai nariga na dauka amma dan Allah kacire CC TV a bedroom din mu bazan kusan ceta ba sannan ba maganan na baka yaro Dan koni nabada ayanda Nasrim ta tsane ka bazata baka d'an taba sannan shara'a musulumci ta halak tamin cikin jikin Nasrim".
wani irin kallo Nasir yabi Agrif dashi ya d'aga kafada yace' ai dama Kai zumane sai da wuta to wllh ni dakai zanga me nasara zan tona asiri komai ma yafaru ba uban kowa zanji kunya ko tsoro ba".
shima Agrif cikin b'acin rai yace "amma ai na yarda da sharad'in kana farko bazan hada shimfida da ita ba dan haka kamin uzurin ta haifun idan ta amince zata maka shikenan amma da sunan ni zan maka kyautan sa dan Allah idan kana kaunar iyayen ka kar ka fallasa zaka zubar da mutumcin gidan mu hakan babban abin kuyane zaka janyowa three brother abin fad'a aduniya kasani gidan mu shaharatren gidane aduniya ".
cikin rashin damuwa yace
"ni duk wannan bai dame ni ba na tsabawa mahaliccina ma balle wani abu da wani bawa me zunubi aka zai fada akai na ba wannan ne damuwa taba damuwa ta ka kula da sharadina kawai".
Agrif yace"shikenan naji zan kiyaye amma dan Allah ina son na d'an kwanta na huta".
murmushi Nasir yayi ya nufi kofa atunanin Agrif fita zayyi sai yaga yasakawa kofar key kuma yazare ya jefa acikin aljihun sa ya tako yana murmushi ya fada bed din yana jan blanket yace "good night".
ba aja dogon lokaci ba bacci ya dauke Nasir
Juyowa Agrif yayi Yana kallon fuskan Nasir afili ya furta "anya ko Nasir kai mutum ne kana nufin kwana zakayi a part din mu wannan wacce iri yar rayuwa ce"?
tashi yayi yafara safada marwa a d'akin ba abinda yake tunawa irin Nasrim tabbas yaga sha'awar kasance wa dashi acikin idon ta mezai ce mata bai gama wannan tunanin ba yaji ana murda handle din kofar da k'arfi gaban sane yaji yafadi sanda yaji muryar ta tana cewa Yaya "Agrif anan kake ne dan Allah kabude min wllh bana iya kwana ni kadai tsoro nakeji".
ta k'arashe maganan tana dafe maranta dan wani irin murdawa yakeyi duk kwana kin nan hakuri takeyi ta rasa wane irin abune yake damunta tabbas cikin jikin ta yana da son a sadu ga magunnuna da aka dura mata yau ma Mama sai da tabata wani shiyasa take jin mugun sha'awa
Ji shiru yasa tace'' dan Allah Yaya kabude"?
tayi maganan tana jij-jiga kofar da k'arfi
bude Ido Nasir yayi yana murmushi yace "kaji jarababbiya ko"?
Nasrim da sauri ta koma d'akin ta
ta dauko wayan ta Saida tazo dai-dai kofar da Agrif yake ciki ta danna k'ira dan azaton ta kobaya d'akin ne aiko taji waya yana Ringing aciki amma har ya katse ba adauka ba
tabbas tasan duk baccin da yake zai ji wannan bugun k'ofar da k'ira da take masa
Afili ta furta "yaya Agrif me hakan kenufi"?.
Nasir yace'' ka bata amsa da cewa kai kana tare da wata yau ba zaka samu daman budewa ba kana da buk'uwa".
cikin razana Agrif yace" ah ah bazan iya ba Nasir cikin sharad'in mu ba wannan'.
mek'ewa yayi tsaye yana cigaba da murmushi sa
yace "ni zan iya yayi bakin k'ofar
Agrif bai ankara ba yaji Nasir ya canza muryar sa ya koma irin na mata sak sai ka rantse macece yace "ke balla gaza da baki san waye mijin naki bane to ki koma da jaraban ki tunda har ya gaiyatoni har gida ba zan hakura ba ban saba da kwana ba namiji ba".
cikin k'araji nasrim tace'' wacece ke......?
sakeyin muryar matan yayi yace' keni bani da wannan lokacin idan nagama aikina na tafi ki tambayi mijin ki".
Agrif zayyi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 40