Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ma munyi arzik'i tunda ai za a dan ba mu. Na ce ka san Allah ba wani wanda zan bawa ya min wayo saidawa zan yi mu raba kudin ku tayani tono shi mun sha wahala dama da buhu a wajen mu za mu zuba goruba wanda zamuyi saraba da shi bamu ciko goruba ba muka sinto gol. Yahaya ya ce kai amma kai Abdulsamad kana da sa'a ka san yanda mutare suka hawalan neman wannan sama da shekaru amma kai ka samu nima na sheda wajen ko zai sake tsurowa". da kyar suka dauramin a ka ban ma koma cikin gari ba suka rakoni tasha ba wani wanda ya kawo wai gol ne a buhuna haka har na samu motan kano su kuma suka koma cikin gari na musu alk'awarin idan na saida zan raba kashi biyu na basu daya ina zuwa nayiwa su baba da brother bayani Baba yace kar mu gayawa kowa kafin a san abin yi muka cusashi k'ark'ashin gadon Hajja amma da safe danaje shagon me alewa na wanda nake sari nasan yana da amana kawai naji zuciya ta ta aminta dana gaya masa ina gaya masa yace" to kar ka sake gayawa kowa a take yabarwa yaran sa jiran shago muka shiga motarsa mukaje sabon gari wajen wani abokinsa yana zuwa Dubai sarin gol ya masa bayani da farko bai yarda ba sai da oga Kabiru yayi da gaske alh sa'idu mai gol yace mu je ya gani ai ya san danyen gol da yana da hotonsa ma amma yanzu ya rasa muna zuwa gida Baba bai tafi shagon dinki ba saboda ba ya dan jin dadi brother suna makaranta dan alokacin suna level one 100 da ganin yanda Hajja da Baba suke harara na na san basu so na zo musu da mutane nide dama haka Allah ya yi ni da wutan ciki inde a gun kudi ne Alhaji sa'idu da oga Kabiru sun gaisa da baba san nan suka masa bayanin abin da suka zo gani Baba yace" na dauko dak'er na mirgino shi dan sai a sannan naji nauyinsa nake ta mamakin meyasa jiya ban ji wannan nauyin ba abakin kofa na barshi Alh Sa'idu ya tashi yazo ya gani wani irin ja da baya yayi yana rufe bakin sa yana salati sai da yagama mamakin sa ya zauna yana fitar dashi na temaka masa muka fitar yace malam Haruna wannan fa ba karamin abu bane anya zamu iya fitar dashi a k'asan nan kuwa?." Baba yace "to yaza ayi kenan".? shiru alh sa'idu yayi can yace "shikenan bari na kira wani balarabe abokin kasuwancina a Dubai yabamu shawaran yanda za ayi atake yafito da wayarsa ya kira shi yace shima abokin nashi yace to bari yakira wani uban gidansa me company k'era gol yana kiransa bayan ya kashe wayan ba jimawa aka kira wayan Abdallah ne daga Dubai yace sun gama magana da uban gidansa gobe zasubi jirgin India sabo anan ne kadai yake da register na bita da danyen gol ta India idan yashigo na Nigeria zai iyacewa da abinsa yashigo bawanda zai tuhumeshi hakan ko akayi bayan kwana biyu sai gashi shi ma da yagani tsora yayi da girman gol din musamman ma da fari ya fi yawa atake yayi mana bayani ai wannan dukiyar zai sayi campanyn sama gaba daya bashi da kudin da zai iya sayan sa amma idan mun yarda tunda yana da company sarrafawa sai asarrafa in yaso sai mu ba shi ladan sa mu saida kayan mu ladan da zamu ba shi ma ya isa ya K'ara k'arfin jari shima kasancewar da turanci yake maganan sai da yagama nayiwa Baba bayani yace ba damuwa Allah ya sa me albarka ne bayan su Abdallah sun koma masaukin su a dare Baba yamin nasiha sosai ashe wasiya yake min bayan mun gama cin abinci ya ce "Abdulsamad ina son magana dakai Abdulsamad duk da kai da yan uwan ka rana daya aka haifeku amma karigasu zuwa duniya dan kai anan gida aka haifeka su kuma ya gagara muka je asbiti shiyasa nake cewa kaine BABBAN GIDA kuma alama ne da Allah ya nuna kai ne jagoran su to ina son kayi hakuri da yan uwan ka kamakar yanda na sanka kar ka canza wannan daukaka da Allah yake shirin yi maka na mallakan dukiya kar yasa ka dauki kan ka daban dasu ka rike zumunci ku kamar yanda kasaba tun kana yaro ka sadaukar da naka karatun kake nemaka kawo musu sun shiga karatun kai kuma gashi baka shiga ba karike zumunci kar abin duniya ya rudaka ka canza daga Abdulsamad dina me sadaukar da farin cikin sa akan na yan uwan sa Allah yasa albarka cikin rayuwar ku." nace" Amin Baba in sha Allah zaka sameni fiye da yanda kafada." Baba yace" nasani Abdulsamad ba kai nake jiba sherin macce nake tsoro matar da zaka aura ni a son samu nama ka auri Halima itace zatafi dacewa da rayuwan ka" . na juya na kalli Halima da take wanke wanke a kusa damu wanda alokacin bazata wuce shekara 10 ko 9 ba nace "Baba Halima kuma." yace"eh ita ina tusayawa yarinyar bata da kowa sai mu kaga Baban ta har yanzu bai dawo hankalin sa ba kai nake son ka auri y'ar nan kariketa amana na yarda dakai Halima tarbiyar muce nasan zata dace da kai ". cikin kunya nace amma Baba kaman tayi min yarinta nifa nan da shekara 3 zanyi aure kaga lokacin nacika shekara 20 kenan". Murmushi yayi yace"kabari nan da shekaru ukku kagani idan zata ma yarintan amma na nemi alfarman karin shikara 2 kaga ta isa aure a wannan lokaci". nima murmushi nayi nace "to Baba na gode". A washegari muka kama hanyan Dubai nida Abdallah da ogan sa Albaty da kuma alh sa'idu mun isa lafiya ba jimawa aka fara aikin sarrafa gold wanda ya yi matukar ba da mamaki dan farin diamond din da yafita ciki me daraja ne wanda a lokacin anci shekaru ba a samu irinsa ba kuma kinsan turawa da larabawa da shi suka amfani ana bugawa a jarida ba jimawa yan sari daga k'asashe da dama suka fara rububin companyn dinmun samu riba fiye da zaton mu, wanda yanzu tun muna hade da Albaity yanzu mun raba kuma Allah da ikon sa nawa company shine akan gaba bayan company na babba na bubai ina da reshe a America ina da reshe a Englan ina da reshe a saudia a an Nigeria ne nake jin tsoron budewa amma ni na aikin gina babban companyn k'era mota mashin da yawanci kayan da akeyin sa da k'arfe Dr Fanna nayi mamakin yanda dukiya ta yake ta hayayyafa agareni kinji yanda akayi nayi yaro yayi kudi kinji tarishi na kenan a tak'aice". Murmushi ta yi ta ce" saura abu biyu ne ban sani ba yanda aka yi Halima ta zo gidan ku da mutuwar Baba". Sai da yayi shiru na yan second yace " Dr tun zuwana na daga Dubai na farko ban samu Baba ba sai tarin wasiyoyinsa duk wannan dukiyar Baba bai san dashi ba, ita kuma Halima ai inaji ta gaya miki da bakinta hatsari mota sukayi da babatan wanda yayi loosing memory akwai wani Alh Musa a tsohon anguwarmu kofar na'isa a gabansa suka yi hatsarin mutum ne me tausayi komai da shi akayi na ceton ransu Alh Musa ya kashe kudi sosai akan Halima dan saida aka canza mata fuska alokacin baza ta wuce shekara 2 a duniya ba shiko Babanta aka ce zai warke ahankali dalilin dawowar Halima gidanmu mutuwar Alh musa ne wanda wasu mutane da ba a san su waye bane suka dirka gidan sa suka kashe shi shida matarsa bayan sadakan bakwai yan'uwansa suka zo suka koro Baban Halima da Halima da alokaci bata wuce shekara 5 ba waje suka ja gidan suka rufe shi Baban a nan kofar gidan ya zauna ita kuma Halima dama tana shigowa wajen Hajja da yake Hajja bata da ya macce tana son y'ay'a mata shiyasa ta jata sosai ajiki ta tasa ba tana shigowa shine da aka korosu ta shigo gidanmu tana cewa Hajja ai wasu mutane sun rufe musu gida Hajja tana jin haka ta san yan uwan Alhaji Musa ne shiga d'akin Baba ta yi ta gaya masa Baba ya je ya sanar da Mai anguwa aka zo daukan Halima da Babanta Hajja ta ce ita zata rike Halima har sanda tunanin babanta zai dawo haka ko aka yi Mai anguwa yawuce da Babanta ita kuma Halima ta zama yar Hajja". Dr Fanna tace "Allah sarki Allah ya jikan Halima ya raya Nasir yanzu ina shi Baban nata".? Abdulmajid yace"yana nan acikin gidanmu dama da zamu taso Hajja tace mutaso dashi yana part din sa damasu kula dashi". Dr Fanna kallon agogon hannuta tayi tace "to Alhaji zan wuce sai da yamma a kula min da yarona kar ganin sabon yaro adena yayin nawa dan naga Hajja sai doki take" Murmushi yayi yace"keko ba dole tayi doki ba saifa yanzu aka mana k'anne Allah ya sa Aishan Abdulmajid mata haifi namiji kin ga 3 brothers ya samu kenan, sai ke kuma idan kika tashi kifara da macce sai ku sake Haifa mana mata masu kai daya to ya zaki aureni? zaki zauna da yan uwa na zuciya daya? Murmushi Dr Fanna yayi tace "wacce macce 3 brother's zai yiwa tayin aure taki Koda na wuni daya ne amma kasa a ranka wllh ba kudin ka nake soba wasiya Halima ne da kuma son ka da yamin shigan ba zata dan tun rasa Sharif ban yi zaton zan samu wanda zan so kamar shi ba sai gashi harma fiye dashi Allah yasa kai kamin ko da rabin s....... Sai kuma tayi shiru tana mai da kanta daya gefen a hankali yatashi yafita a motan yana murmushi ya kama murfin motan zuciyar Dr Fanna sai bugawa yake adduar nasara take ta karantowa ta ji kamar daga sama yace "zuciyar ABDUL tun yana yaro yake son auren yar barebari mai irin zanen ki me irin sanyin halinki me irin sanyin muryan ki amma nabi zabin Baba na auri Halima sai gashi a karo na biyu Allah Ya bani fiye da zabina gaskiya na san dalilin biyayya da umarni iyaye ne ya sa Allah yamin wannan babban kyautan amma ba wai dan na cancanta ba tun kallon farko dana miki naji kece matar mafarkina FATIMA ZAHRA kisa aranki Abdulsamad naki ne". Yana gama fadan hakan ya mata murmushin sa me tsada tare da kashe mata ido daya ya rufo kofan ya juya cikin takunsa na ingarma ya fara tafiya kasa rufe baki tayi wai ita Fanna emeka 3 brother's yake gayawa wannan kalaman anya ba mafarki take ba mutumin da saide taga sunansa ajikin gidajen Mai ko kwalin taliya ko muhun sugar omo shikafa dade sauran su 3brother's dafe kirjinta tayi yanda yake bugawa kawai jira take taji ta farka daga baccin da takeyi shi ma Abdulsamad yana shiga yayiwa Hajja da yan uwan sa bayanin wacece Fanna da farko Hajja ta nuna kamar bata gamsu da d'anta ya auri tubebbiya ba amma da taga yanayinsa ta gane yana sonta kuma ta tuna da asalin saurayin Fanna din Sharif yanda yayi soyayya na shekaru da ita kuma suka shiya shirin aure batare da sanin iyayen saba shine ta tsorata kar shima Abdul yayi tunanin haka tunda yana da daman da zai ajiye mata dari gashi ba mazauni bane tsoron haka yasa ta amince ayi auren amma har ga Allah ba dan taso ba. A ranan suna jaririn Amina ya ci sunan Haruna Baban su A'A'A Hajja zo kaga mu a gun hajja a take tace akirashi da Agrif Hajja tsohuwar makaranciyar litatafan hausa ce dan haka tasan suna kala_kala dan har yanzu hajja karatun hausa novel takeyi har irin na online duk tasan marubuta shiyasa ko kallon yaranta sukayi tasan me suke nufi ita take koya musu yanda zasuyi soyayya ma A ranan da Nasir ya cika wata ukku a ranan aka daura auren Dr Fanna da Abdulsamad ba wani shagali akayi ba a washegarin ranan ne kuma Aisha matar Abdulmajid ta tashi da nak'usa tasha wahala Dr Fanna tace amata cs amma Hajja da yan'uwan Aisha suka hana wahala tayi wahala har suma Aisha takeyi sai da sukaga abin bazai yuwuba suka saka hannu aka turata d'akin theater ansamu nasara ceto uwa da jaririta amma ansamu babbar matsala a mahaifarta wanda yariga ya fashe ba wani dama sai de a fitar dashi Allah saki Aisha kowa sai da tausaya mata haifuwar fari a cire mahaifa kowa ya ji sai yace Allah sarki Allah yasa albarka arayuwan d'an data haifa. Ranan suna yaro ya ci sunan Muhammad Albaity ogan gidan Abdulsamad dan Hajja haka ta ce ba abin da za a saka wa albaity dashi sai de susaka masa me suna ana kiransa da Kamal bayan warkewar Aisha gida ya koma yanda yake kowacce tana kula da nata ɗan yanda ya namata Fanna ta ajiye aiki saboda kula da d'anta da mijinta duk da yawanci bayanan yau yana can gobe yana can wani abin mamaki Nasir yana kara girma kaman nisa da Dr Fanna yana bayyana abin yana bawa kowa tsoro dan Abdulsamad de b'aki ne ita ma marigayi Halima kak'ace sosai amma Fanna fara ce sosai irin sol din nan farin ibo din nan idon sa hancinsa duk rin na Fanna ne kullum Hajja cewa take ikon Allah tsabar son da Fanna take yi wa Nasir ya sa har kamanninsu yana son ya zo daya in dai ba ido na ba ne wllh sak *Bayan shakara biyu* Amina ta sake haifuwa wannan karon ma danta namiji sunnan Baban Hajja Habubakar sadik aka masa alkunya da AIBAN . AIBAN na da shakara biyu Amina tasake haifuwa shima namiji sunan Baban Amina aka sa wato Adamu ana kiran shi Abbaty har wannan lokacin Fanna ko batan wata ba tayi ba tun abin baya damunta har ya fara damunta dan Hajja tafara k'ananun magan ganu tunda yaran suka fara wayo suka gane Nasir ya fita daban acikin su yana da wani irin zafin zuciya ga rashin tsoro da rashin kunya idan ba mommynsa ba ba wanda yake ragawa ba wanda ya isa da shi inde yana gu to sai de kome ayi yanda yake so dan shikara 6 amma tamkar dan shekaru 20 haka yake diler kowa a gidan iyayensa ma ba ya raga musu balle ma aikatan gidan hatta Hajja shayin sa take balle su Kamal da Agrif ko abu aka ba da baya wajen to ba za su dauka ba sai sun jira ya zo ya gama jan ajinsa ya d'auki nashi su d'auka har ga Allah Abdulsamad ba ya son halin d'an nasa sai de ba shi da lokacin zama da shi wani halin nasa ma bai sansu ba tunda bai fiye zama a k'asan ba. Baba yabubu me gadi kam yaron tausayi yake bashi kuma bayan mommysa ba wanda yasan halin Nasir sai Hajja da yabubu me gadi. Yau ma kamar kullum sun taso daga islamiya duk kansu ukku kowa akan kekensa a tare suke tuk'awa Bodyguard dinsu ne a gefensu sun sanya su a tsakiya Agrif kam wani fisari yake ji sosai tun a makaranta amma bai isa ya wuce Nasir a gaba ba dan ahankali suke tuk'awa kuma a tare ko ataku daya wani bai isa wuce wani ba har suka zo bakin get Baba Yakubu yana ganin sa yafara masa kirarin da yasa ba "A a barka da zuwa NASARA nasara ko gani kafi mutum NASARA me wuyar badanci Nasara goshin jirgi me wuyar karo kafe kekensa ya yi daidai inda Baba Yakubu yake Kamal ma yatsaya cak shida bodyguard din shi ko Agrif fisari ya gama matsansa dan haka da sauri ya masa kan keken alaman ya yi gaba cikin wani irin tsawa Nasir yace "What Agrif"................. Ba Agrif da ya gama jika jikinsa da fitsarin b hatta bodyguard din da Baba yabubu sai da suka tsorata dan yanda yayi tsawan kaman ba yaro ba *To masoya mu je zuwa don ganin FURUCINA da wane salo yake tafe kar ku manta taku Batul mai baku kala ce* [4/8, 1:47 PM] Batul Adam Jattako: *FURRUCI NA NE* *NA* *BATUL ADAM JATTKO* ```Marubuciyar``` *DAMA TA* *AMFANIN SOYAYYA* ```NOW``` *FURRUCI NA NE* *_________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_Domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *_________________________________* *Page 2* "Agrif fitsari kake yiwa mutane a wando? Banza, wawa, jaki, dabba. Wani irin kuka Agrif ya fashe dashi ga kunya ga tozarcin zagin Nasir, yayi jifa da keken ya shiga part ɗinsu da gudu cikin tsananin kuka. Kamal ya fashe da dariya irin na yara shima ya sauka a keken ya barta a nan shi ko uban-gayya wani dogon tsaki yaja shima yabar nasa keken ya shiga part ɗinsu. Su kuma bodyguard ɗinsu suka dauki kekunan suka kai ma'adanar sa kamar yanda al'adan gidan yake bayan Isha kowa ya haɗu a dining table har Alhaji Abdulsamad da yaran suke kira da Abban mu yana wajen, dan idan yana ƙasar yana kokarin yaga ya zauna cikin familyn sa. Abdulraham kuma suna kiransa Abu sai Abdulmajid Dady, Amina ummu Aisha Mama Fanna mommy. Mommy ce ta hanga ta ga ba Agrif a wajen cikin mamaki tace "Ummu yau ina Agrif ne". "Amina tace "ai yau abin akayi a hanyar makaranta da kuka ya shigo nayi nayi yayi shiru yaƙi yanzu haka har zazzabi yazo masa nabashi tea da magani ya sha ya samu bacci." Mommy ta kai kallonta wajen Nasir da ko ajikin sa har ya fara cin abincin sa tana son tayi masa magana dan tasan dashi akayi faɗa amma tasan tana masa magana yanzu zaiyi zuciya yabar abincin, kuma Abdulsamad yana wajen tasan shima faɗa sosai zai masa dan haka ta rufa asirin, dan haka tayi murmushi tace ayya Allah sarki yarona lalle yau gidan nan ba lafiya, Baban gida guda akwance?" Aiban yace "Mommy ya Nasir ne ya masa duka yayi fitsari a wando". Abba yace" duka kuma? Nasir ban hanaka faɗa da yan uwan kaba dama baka daina ba?". Ko ɗaga kan sa baiyi ba kamar ba dashi ake ba Alhaji Abdulsamad ya fusata sosai yace"Kai NASURUDDEEN ba da Kai nake ba?" Abu yace "haba Alhaji ka bisa a hankali mana kasan fa Nasir baya son hayaniya kuma ni nasan baya faɗan rashin gaskiya, san nan ko kashe shi zakayi tunda baiyi niyar magana ba to ba zai yi ba abin da ya faru ya wuce." Abba yace" haba Malam bakwa ganin yanayi yaron nan ne idan yatashi a haka bazai mana daɗi ba. Yakamata a din ga tsawatar masa dan dai ni ba mazauni bane. Ya juya ya kalli Dady Abdulmajid yace "alk'ali ya kamata kusa ido akan yaron nan fa wlh akwai abubun da yake sam bana gamsuwa dasu akan sa. Yaro sai yanda yayi damu? Yakamata yasan mu ne gaba dashi." Murmushi Dady yayi yace "zai daina." wani dogon tsaki Nasir ya ja tare da ture cup ɗin tea ɗin tare da gangara shi hannun Aiban. Da yake yana saman tablen ɗin yasamu yanda yake so dan dama yayi ne dan ya ƙona Aiban da shi ne ya gayawa Abba abinda ya haɗasu da Agrif. Wani irin ihu Aiban ya callara yana yarfa hannu da sauri Abba ya cafko Nasir ya figo wayan da yake jikin DBD yadinga sula masa ko tari baiyi ba bale yayi kuka kawai wani irin huci yake da sauri Hajiya tashiga tsakanin su. "Abdulsamad kashe tilon ɗanka zaka yi akan abinda ba laifinsa bane? Ai shi Aiban din shine munafiki ai duk inda mutum biyu sukayi faɗa sai ansamu laifin kowa. Da yake Agrif ɗan uwan sane yaki faɗan laifin sa, sai na Nasir ai gwara da ya ƙona munafikin, ai ni da nasan haka Aiban zai zama munafiki da ban sa masa sunan ubana ba suna mai daraja Habubakar w.... Abba yace ''haba Hajja bai kamata ana barin yaron nan yana taka kowa a sanda yaga dama ba, ni idan aka min haka ba'aman adalci ba, ni ina can wajen da zan rufamana asiri ni da ku da dangin mu. Ɗana yana cikin matsala yanzu ne Nasir yake lokacin da za'a nuna masa dai_dai da ba dai _dai ba saboda gaban sa." Hajja tace" amma sai ka kamashi da duka sai kace kisa yayi?" Abba numfasawa yayi ya jefar da wayar, yayi hanyan waje Mommy da Mama suka kama hannu Aiban suna ganin kawai shagwaɓa ne da gulma irin nasa ba wani ƙonewa da yayi. Dan shayi ya huce mommy tace "sannu Aiban yanzu zai daina ciwon ko?" Ummu tace "kai Dr. kinsan fa halin Aiban dama son asani ne bawani. Kuma nima ruwan tea din ya taɓani ba wani zafi". Ai ko Hajja tafara masifan to azo a kai mata jikanta asbiti, Abdulsamad ya fasa masa jiki. Mommy ma da taga jikin nasa ranta ba karamin bacci yayi ba tace "Hajja kawoshi muje na shafa masa magani". Cikin bacin rai tace "gafara can ba a gaban ki yarinƙa jibgar sa kamar an aikoshi daga sama ba? Ai da ke kika haifeshi da baza ki bari hakan ta faru ba baki san ciwon haifuwa ba. Ɗan da shikenan a wajen Abdulsamad har yasa hannu ya dake sa, nima nasan hanyar asbitin ba dole sai ke ba. Idan kinga Nasir ya koma ɓangaren ku to Abdulsamad ne yabar ƙasan nan." Ba Mommy ba hatta Mama da Ummu basu ji daɗin abinda Hajja tace ba duk da ba wai yau ta fara faɗa ba. Mommy idon ta ne ya wani irin cicciko wa ita ba wai gorin haifuwar ne damuwarta ba yanda Hajja take nunawa kamar ta gaza a kula da Nasir shine damuwar ta, bayan yanzu ita a duniya ba abin da take so fiye da Nasir ko da yara ɗari zata haifa dukkan su batajin zasukai darajan Nasir, kuma indai ciki ne yanzu ma tana dashi kuma bata jin aranta ya kai Nasir. Saurin ficewa tayi dan bata son hawayen da take ɓoyewa ya zubo. Taɓe baki Hajja tayi tace" jita gwalmaɗaɗɗiya dama wannan ƙugun naki ina zai iya daukan ciki mace kamar muciya duk ƙashi, abincin cikin ta ma a ƙa'ide yake wai ita likita. Aure kusan shekara bakwai bako ɓari. Yo ina ta tsaya taci ta koshi balle cikin ya zauna awan nan shafaffen cikin nata tubabbiya kawai" suma sauran mata haka suka zame rai a ɓace suka fice suka bar Hajja tana ƙolotun kiran sule driver yazo ya kai mata jikan ta asbiti. Ita kuma mommy tana shiga part ɗinsu direct bathroom ta shiga ganin Alhaji a zaune da laptop ɗinsa akan gado bata bari ya gane yanayin fuskar ta ba, kai tsaye ta wuce bedroom kwanciya tayi lub cikin bathroom ta dai_daita shower a dai-dai kanta, ta jima tana tariyo rayuwar ta, to ina mahaifin ta? Ina dangin sa tasan dai duk inda suke musulmai ne me yasa shi bai ɗauke ta ba? Da duk wannan abin bai faru da ita ba, da ba'a kira ta tubabbiya ba. Allah sarki mommyn ta Emeka tasan tana cikin damuwar rashinta tunda bata da wani ɗa sai ita anya lokacin zuwanta wajen uwar ta baiyi ba kuwa? ko ya take uwa uwa ce kuma tana da haƙƙi akanta, taja dogon lokacin tana tunanin tana shafa cikin ta tasaki murmushi a fili tace Hajja "Fanna ba juya bace kwanan nan zaki sheda hakan. Ajiyar zuciya ta saue lokacin da taji knocking ɗin kofan bathroom ɗin ya tsanan ta tasan Alhaji ne dama tasan dole zai biyota yace zasuyi wankan tare ita kuma tana son keɓantuwa shiyasa tasa sakata,

Chapter 2 of 40