kunya kuma ba ga Abbaty ba shi ya dace ya aure ta.....
kuka Hajja tafara Sosai tana cewa
"Abdulrahaman kun gaji dani kungaji dani agaban ku yaran ku suke nunawa ban isa ba Allah sarki Abdulsamad tun Halima tana y'ar tasisiya Haruna yaba sa ita godiya ma yamasa amma gashi ku kun nu na ni ban isa da yaran kuba......
Daddy yace "Hajja dan Allah ki dena fad'an irin wannan Magan ganun taya zamu gaji dake Insha Allah ki bamu nan da kwana biyu zamu shayo kan abun".
tana jan majina tace''
ni bawani wanaki da zan baku nagama yanke hukunci ba inda yarinyar nan Izzatu zata fita tana gidan nan yo Allah na tuba idan Izzatu tabar gidan nan ai na banu ai saide na bita abin da take min akwai mai yimin shi cikinku da yaran naku yanzu gashi bazawarai sun fara fito mata za su rabani da ita akan me bazanyi abin da yadace ba".
Agrif jan hannu Nasrim yayi suka fita
su daddy kuma suka zauna lallashin Hajja
"haba my wife nifa ban amsa ba kuma wllh duk yanda za ayi Sai de ayi bazan taba yarda ba".
cikin tsawa Nasrim tace
"ai wllh Kai ma da lefin ka yanzu ta isa ta tukari wancan bayahuden jikan nata da take tsoron sa ne tun shekarun baya da ya mata ta tas kaji ta sake masa magan yayi aure ne
wllh ban taba jin na tsani Izza ba sai yanzu wai duk wannan abin da ake ko ta d'ago kanta ta naji".
"Please Sadiya ko mutuwa kikayi bazan auri wata ba zan cigaba da renan soyayyar ki ta isheni".
numfasawa tayi tace'' to yanzu ya za ayi kasan matar nan idan tafara abu sai tayi shi yanzu zata sako sau Abu agaba har sai sun mata yanda take so".
shiru yayi can yace " kiyi hakuri nan da sati 4 zan gama aikin da yakawo ni ba dan Kamal magan daci bane ma da yanzu munci k'arfin aikin muna gamawa zan daukeki mutafi tunda kin gama karatun idan muka tafi ai basai ta ganmu ba ni yanzu jikin Aiban ne yafi damuna har yanzu bai dena aman bane?".
"Eh Wllh bai dena ba zazzabin ne ma ajikin sa itama Zeenat banajin dad'i a part din mommy ta kwana".
"Subbahanallah meyake damun ta".?
"Wllh ban sani ba mommy ce take gayamin jiya amm.....
kiran wayan Nasrim ne ya katse ta tana dubawa taga mommy ce tana picking mommy tace'' kizo ki same ni yanzu ke daya a sama".
jin yanayin muryar mommy yasa gaban Nasrim faduwa tace'' mommy lafiya?".
tayi maganan tana mek'awa tsaye
Agrif shima ya mek'e yace "lafiya".
Nasrim tace" mommy ce tace'' nazo ni daya ina zuwa".
tayi maganan tana ficewa
mommy ta zuba uban tagumi Nasrim ta shigo har ta zauna mommy batace komai ba kanta a k'asa
Nasrim tace "mommy dan Allah kece kadai kika san yanda zaki shawo kan daddy dan Allah karki bari ya yarda da abin da Hajja tazo dashi wllh zai iya zama babban matsala a gidan nan".
Mommy kamo hannun Nasrim tayi ta d'aga kai ta zubawa Nasrim idon ta da suka gama canza kalan ja
Nasrim tsorata tayi da ganin yanayin yanda idon mommy ya kumbura yayi ja cikin in nina tace'' mommy me yake damun ki akan maganan auren Izza ne wllh nim.....
"Nasrim ba wannan ne damuwa ta ba kinsan meye dalilin jinyar Aiban da Zeenat".?
'Ah Ah".
Ahankali mommy tace
"To GUBA aka basu".
"What mommy guba waye zai bawa yarana guba me nayi da za amin haka wa nacuta wllh bazan yarda ba".
tayi maganan a gigice tana mek'awa tsaye kamo hannun ta mommy tayi tace'' please Nasrim wani abun yafi gaban a bayya nashi dan idan baka iya kama barawo ba shi b'arawo zai kamaka ke lawyer ce kin san komai ki nutsu sosai bana son kowa yasan wannan batun dan idan meshi yasan mun sani zayyi kokari sake sirrace kan sa amma idan mun nuna bamu gane ba zamu fi saurin gano me lefin".
Kuka Sosai Nasrim take tace''mommy ina Zeenat ina Aiban din mommy mutuwa zasuyi ko"?.
cikin kuka mommy tace'' insha Allah Zeenat baza ta mutu ba dan yanzu an samu kan abin kuma ita bata ci dayawa ba kinsan ita bata wani cin abinci sosai so bai higa jikin ta kamar Aiban ba tana gidan Dr Hafsa anjima za adawo da ita amma Aiban kam sai adduar".
"yanzu mommy wa kike ganin zai iya min wannan".?
"Nasrim ke lawyer ce ke yakamata ki gano ko ma meye amma nafi jin duk wanda yaso ai kata hakan ba akan komai bane akan dukiya ne ganin bani da kowa sai ke ke kuma Allah ya al'barkace ki da y'ar dan haka ma kusan tan mu sune abin tuhumar mu".
Nasrim ta gyad'a kai tace
"Mommy idan ko hakane ba Aiban da Zeenat kad'ai za aso halla kawa ba hadda ni dake da sauran yaran".
"wannan shine tunanina nima Nasrim amma dan Allah dame muka raji mutane"?.
Nasrim tace "mommy bazamuyi saurin zargin mutane ba sai mun zauna da yaran mun binciki waya basu wani abinci ko sha zai iya yuwama ko a makaranta suka saya ko kuma wani akasin aka samu".
girgiza kai mommy tayi tace'' Ah Ah duk nayi binciken wannan guban me tsadane sosai da gayya aka saka kuma yana iya kaiwa watanni ajikin mutum bai fara amfani ba amma idan yafara yana kisa sosai".
"Mommy nashiga ukku dan Allah mommy kisan yanda zakiyi kar na rasa Zeenat ko Aiban Allah Agrif yafi sonsu fiye da su Khafulan ma".
" insha Allah zasu tashi amma inason ki kula dasu Khafulan Sosai duk yan da akayi yanzu su ake hari akan su zamu d'ana tarko zasu koma part dinki gaba daya akwai camara da za'a saka musu ajikin rigunan su kinga ke kina da kula sosai kuma part din ki ba ma'aikata ajiye wani batun kishin ki kula sosai da wannan matsalan".
"tab ai mommy batun kishi ma abin dubawa ne dan wllh zan iya kashe duk wani wanda yaso yakawo min cikas arayuwar aure na wannan *FURUCI NA NE* ".
"Nasrim baki da hankali meya hadaki da irin wannan FURUCIN baki san yana da illa ba wannan furucin naki ma zai iya janyo miji abinda bakya so din ai".
"Kai mommy ke dama haka kike bakya so ki yiwa mutum addua mekyu".
"Ummm Nasrim shifa rayuwa yanda ka daukeshi a haka zai zo maka musamman kishi duk ta yanda kika daukeshi ta haka zai zo miki idan kin daukeshi da sauk'i zai zo miki da sauk'i idan kika dauka da zafi haka zai zo miki ba wani adduar da zan miki Wanda zai canza k'addara sai muyi fatan yazo da sauk'i dan haka ki shafawa kanki lafiya ki dauki Izza amatsayin abokiyar zama dan Hajja bata magana batare data yishi ba..........
"to wllh mommy awannan karan ta tafka kuskure dan wllh inde Ina raye ni kad'ai ce matar Agrif".
"Nasrim wai dama haka kike amma abu kadan kice Allah yace annabin yace kina da sani amma kina takewa".
"Mommy inde akan kishin ne koma meye a fadam.......
Shigowar Mama da Aiban a hannun tana kuka ne ya k'ase su mek'ewa tsaye mommy da Nasrim sukayi Mama kwantar da Aiban tayi agaban su mommy tazube tana kuka "Dr Fanna shikenan Aiban ashe ciwon ciki bana tashi bane". Nasrim ma zubewa tayi tana d'aga hannun yaron tace'' mommy yamutu mommy Abdallah na ya tafi mommy waye ya aikata min haka meyake so awajena.......
Mama dafa Nasrim tayi tace'' Halima bar fad'an haka addua zaki masa Allah yasa macotane Allah da yabaki shi ya kwace muma duk zaman jiran sa muke ".
Nasrim fisgewa tayi tace'' Mama ba Allah bane baruwan Allah gub......
da sauri mommy ta rufe mata baki tana janta kan gado tace'' Nasrim kar na k'arajin kinyi magana ki barwa Allah".
"Cikin wani irin k"araji tace'' mommy bazan iya ba wllh d'ana d'ana Agrif ne yashigo a gigice yana " Ina Aiban din Ina yake Mama na shiga part din ki a na kukan mutuwar d'ana wllh bai mutu ba.........
Abu da daddy ne suka shigo sai Hajja da Ummu kowa yayi kukan rashin yaron dan yaro ne me fara'a da shiga rai irin de halin Agrif
**************************
*bayan sati 2*
Zainab de ansamu anshawo kan abin Al'hamdulillah da nisan shananta
ta warke amma har yanzu de ba tayi normal ba dan kullum ciwon ciki duk tarame abin tausayi tana part din mommy cikin kulawar ta sosai ko aiki ta dena zuwa in yakama taje office to tare suke zuwa tana kula da cita da Shanta sosai
**********************
" haba Halima Allah da yabamu Abdallah shi ya karbi abunsa kuma baga su Khafulan ba dan Allah kiyi aiki da taushidin ki shi k'addaran baya shawara da mutum idan zai zo
Ai kin ga misali ya Ummu taji da Aiban babba yarasu kinga tayi tawakkali".
"Abban Fayyat nasani inda rasuwa ta Allah yayi bazan damu ba amma gub........
shiru tayi tana tuno gargadin mommy nacewa duk kusan cinta da mutum kar ta gaya masa dan makusan tan sune abin zargin su duk da tasan da wuya Agrif ya cuar da ita bata zagin sa kwata-kwata sai de abin akwai daure kai to waye yake son ganin bayan su
"ki k'arasa mana kamar ya ba mutuwar Allah bane kawai wani da yake da ikon rayawa ko matarwa bayan Allah".?
"Ah Ah kawai Ina tunanin meye musabbabin jinyar Abdallah ne".
hannu ta ya jawo yana shafawa a hankalin yace' my dear kiyi Ima'ni k'aran kwana ne ajali ne Allah zai bamu wani ko....
shigowar message cikin wayan Agrif ne ya k'asar dashi wayan yana hannun kujera kusa da Nasrim a mamakin ce take kallon wayan tana kallon Agrif
cikin tuhuma
tace'' Izza!? .
hannun ta sa zata dauki waya yayi saurin dafewa cikin wani irin k'arfin da bata san tana dashi ba ta tun kud'a hannun nasa tana mek'ewa tsaye da wayan ahannun ta
taren da shiga cikin message din tana karantawa a fili
_kasan Allah ba wasa nake ba tun zuwan mu jiya ban sa komai abakina ba wllh abin da na jure a mijin baya yanzu kaina yawaye Ido na ya sake budewa bazan iya ba dole zaka waremin lokacin_
_gaskiya my heart sabo da kai na musamman ne a rai na kai d'aya ne a zuciya karik'e ka aje komai wuya na dau aniya_
Sai wanda da alaman
tun 23 minute ago ne
wanda shi yasake tunzura Nasrim inda tace
_da alaman muguwar ta hana ka d'auki wayan ko?_
da sauri Nasrim ta fice da wayan a hannun direct part Hajja cikin bugo kofa tayi Izza tana zaune kusa da Hajja tana b'are mata ayaba nata bata cikin wani irin zafi Nasrim ta cukumo Izza ta tsayar da ita tare da zuba mata zafafan Mari wani uban naushi ta Kai wa bakin Izza sai ga hakori nan atake ta canzawa Izza kamannu
Hajja komawa tayi gefe tana rusa kuka nata cewa Akira mata Abdulmajid ga yarsa zatayi kisan Kai so daya Hajja yayi yungurin shiga tsakanin su Nasrim ta tunkudata gefe nan take ta kama konkoso tana wayyo ta garya ni zata kashe y'ar mutane ku kiramin Abdulmajid ".
Daddy yana wajen aiki aiko daga Mama har Ummu da suka shigo kasa banbare Izza sukayi a hannu Nasrim gashi da k'er take sauke numfashi sai maza mutum hudu ne ma'aikatan gidan suka samo na saran kwatan Izza da tagama jigata kuka Baban Izza yasaka yana cewa "shikenan Hajiya ta kashe min Izza dama ita kenan dani".
sarkin gida ne yasa aka tarkata Izza zuwa asbiti
daddy da Abu zube suke agaban Hajja sai hakuri suke bata a kan tayi hakuri ta kafe dolle sai an daura auren Izza da Haruna in ba haka ba zata fita tabar gidan kuma sun rasa ta kenan har abada
Nasrim ta doka tsalle tace'' Wllh Wllh in ko akace za ayi haka saide cikin ukku a rasa daya koni ko Izza ko Harunan".
Daddy tashi yayi zai cakumo Nasrim tayi kofar fita da gudu sai da taje bakin kofar tace "aide rigiman duniya dame rai akeyi ko wllh muzuba dagowa wannan *FURRUCI NA NE* ba zan taba zama da kishiya ba".
tafice
Hajja tace'' to kaji ko Abdulmajid kaji de ko duk abinda ya samu Agrif ko Izza Nasrim ce ka sheda a matsayin kana alk'ali
Hajja tasa anyanke ranan auren Izza da Haruna wata daya
mommy ta numfasa tace'' amma Hajja da an yan ke auren da gaggawa yin auren ko da zuwa gobe ne dan asamu Nasrim ta hak'ura dan duk wannan abin da takeyi barazana ne idan taga anyi aure dolen ta zata hakuri".
Hajja tace'' sai de ta mutu amma Izzatu auren gata zan mata bazawaran da tayi shekara 5 ba miji zan yankewa aure kwanta daya a wannan zamanin da ciwon sanyi yayiwa mata yawa ai sai na gyare ta tsaf".
haka de aka tashi ran kowa ba dad'i
**********************
"Halima ki dauka wannan k'addaran mu ne k'addaran bata shawara da mutum da ban zabi hakan ba wllh Halima an biyo ta hanyar da aka fi karfina ne ba yanda zanyi ne Abu ya tilas tani kuma wllh k.........
"dagata Haruna bana son jin komai daga munafikin bakin ka kowa yayi abin da yaga zai iya".
"shikenan amma dan Halima kidena FURUCIN kisan Kai kiyi ta maimaita inna'lillahi'wa'ain'na'ilaishirajju kiyi abakota da Qu'ani kamar yanda kike da tabbas shedan yana son yayi galaba akanki ".
ajiyar zuciya ta sauke tana cije labe
ranan de kusan a zaune suka kwana daga ita har Agrif washe gari lokacin fitan sa aiki ma bayyi ba yafita acan yayi breakfast ma saboda masifar Nasrim gashi shima a mugun gajiye ya shigo cikin office din gakuma bacci da bayyi ba sai kawai ya kwanta yabar Kamal da aiki
Nasrim kam tadan bi hawaran Agrif dan kusan wuni tayi tana karatun Qur'an da yamma tana zaune tazuba uban takumi Humairah ta shigo rai a b'ace ta zauna Nasrim ta kalle ta tace'' Hummee yade.'?
Humairah iska ta fesar tace'' wani rainin hankali nagani a status din Izza da ya Agrif".
"Agrif kuma".
mek'a mata wayan Humairah tayi Nasrim hannu na rawa ta k'arba
na Izza ta fara budewa
inda tarubuta wasu kalman soyayya a saman picture din Agri kamar haka
_ina yawan kaunar ka a zuciya ba shakka komai wuya ko duka alk'awar naka na dauka_
Sai na Agrif da yasa wa saman hoton Izza kalma kamar haka
_ko rana da wata zasu dena haske gimbiya ta sai ke soyayyar ki har abada I love baby_
murmushi Nasrim tayi tana maidawa Humairah wayan tace'' tabbas rana dawata zasu dena hasken kamar yanda yafada wllh cikin mu sai wani yadena ganin gaske a yau ba gobe ba".
Humairah tace'' subbahanalla Nasrim wannan ba kalman musulmi mai cikekken imane bane".
dafa kafadan Humairah Nasrim tayi tace'' Aisha kenan ke kin sani a fannin kishi Imani na yana da mugun rauni komeye zan iya ai katawa a yanzu jina nake nida gawa daya ne ni Agrif zai tozar ta".
ta k'arashe maganan tana daukan wayan ta cikin sauri da samo hoton Izza dana Agrif ta hada ta kansale da Jan rubutu ❌ sannan ta rubuta *RI JF* ta daura a status din ta tayi murmushi ta haura sama Humairah tace'' dan Allah Nasrim kar kiyi abinda zaki janyo mana nadaman a family".
bata mata magana ba ta k'arasa hawa steps
da sauri Humairah ta fito taje tayi Ummu bayanin abinda ya faru Ummu murmushi tayi tace " bawani abinda zan iya yi amma anjima zanje na mata nasiha Nasrim akwai taurin kai".
Humairah tace'' gaskiya Ummu wllh ba amata adalcin ba bawara yaje waje yasamo ba da ya auri Izza data gama sanin sirrin ta wllh kishin yanzu ba irin daya bane danasu Mama da mommy kuma Ummu wllh seriously ba wani batun sai anjima ki tashi muje yanzu ki mata nasiha ni wllh in yakama ma araba auren ta hakura ta barwa Izza din in yaso Allah ya bata wani da wannan munanan FUFUCIN da takeyi".
mek'ewa Ummu tayi tace'' to tashi mu tafi
"haba Nasrim kamar ba me ilmi ba to meye kishin da zaki ta da hankalin ki kituna fa kece tamu ba wani gata da ni'iman da Allah bai miki ba dan ya jarrrabe ki da kishiya sai kiyi butulci".
"Ummu ki gane kishiyar fa na cin Amana ne nifa naga Izza da Baban ta da gawa agaba ruwan sama yana dukan su nasa daddy ya dauko su duk wani mataki da Izza ta taka da sa hannun na da temakona amma tarasa wanda zata ci amana sai ni".
Ummu dafa kafadan Nasrim tayi tace'' Nasrim ki dauka amatsayin k'addara ba cin Amana ba zakiga riba Insha Allah kiyi misali da zaman hjy Aisha da Dr Fanna mana Wllh muna zaune agidan nan duk kan mu muna zaune tsakanin Dr Fanna da Aisha sunfi kusanci har Ina ganin kamar ni sun wareni ko da Abdulsamad ya rasu Hajja tace'' daya daga cikin mazajen mune zai auri Dr Fanna wllh nazaci nawa mijin za a bawa saboda yanda Dr da Aisha suke k'awance amma sai Allah yasa Abdulmajid ne mijin kuma alak'an Dr da Aisha k'aruwa yayi bai ragu ba wani abun ma sai suyi su binne ban sani ba kinga ba fa basu da kishi bane sun danne abun a rai ne kawai dan shi kishi ta yanda ka daukeshi haka zai zo maka kiyi hakuri ba abinda Izza zata rage ki dashi kuma nasan Insha Allah nima zan sa Ido akan zaman ku Baban gida zai kwantan ta adalci a tsakanin k.........
cikin b'acin rai Nasrim tace'' shikenan Ummu nagode".
Ummu bata gamsu da yanda Nasrim ta amsa abin ba gashi kuma gaban ta dare ne komai zai iya faruwa dan haka sai
tace'' ko za muje ki kwana a part dina gobe sai kizo".
murmushi Nasrim tayi tace'' lah Ummu ba komai ba abinda zai faru insha Allah".
"Ummu tace'' Yawwa Nasirisiya ta Allah yamiki al'barka."
bayan fitan Ummu Nasrim kicin ta shiga kwalin wuk'a ta dauko sai da ta zabi adda wanda yafi kaifin da tsini ta dauka ta zaga baya ta fara gogawa ajikin wani dutse ahankali take gogawa Khafulan da yake sama yana cire uniform din islamiya ya hango mamyn tasu a baya yace "kai bro gata can tana wasa adda ko Abbamu zata kashe muguwa ce".
Fayyat ya lek'a yana kallon ta yajuyo ya kalli Khafulan yace " mamy kake cewa muguwa Allah idan nagirma sai nasa an daure ka kullum kanayi wa mamy rashin mutumci".
"Eh nayi din karama mata mana ai itama batason Papa na bayahude take ce masa".
Fayyat yace "to tafada din".
shima Khafulan yace
"To nima na fada din daga nan suka kama kokuwa Allah yatemaki Fayyat shima yana da k'arfi dan haka dai dai suke karawa Khaldum ne dama bawan Allah ba ruwan sa
A office ko Agrif sallahn azahar ne kawai ya tashe sa bayan ya dawo daga sallan ya d'auki wayan sa ainda ya ajiye tun zuwan sa bai ma tsaya duba yawan Miss call da message din ba yasan Nasrim baza ta kirashi ba sai wannan na cacceciyar Izza tsaki yayi yana kashe wayar gaba daya batare da duba cikin saba ya maida ya ajiye sai asannan yafara aikin sa shine har sha biyun dare tukun ya tattara tarkacen sa yarufe office din ya fito yasamu drive komai akasalance yakeyi Allah Allah yake idan yaje gida yasamu Nasrim tayi bacci
Nasrim ko tasake hawa dam duk atunanin ta Agrif yana wajen Izza dan Izzan ta sake daura wani sabon status da yake nuni da suna tare har tana ikirarin tare zasu kana a hospital din
Yana bude kofar falo yace
"Inna'lillahi Halima bakiyi bacci ba".?
"banyi ba sai na aiwatar da abinda nake son na aikata".
"Halima kin gane nima a cikin damuwar nake wllh bansan wani mafita ba da nasani da nayi nima inda akwai hanyar da za ayi nagujewa auren da nayi amma kemeye naki shawaran".
Murmushi tayi tace''
Ummmm huuuu maza kenan har Kai kana da bak'in magana ka taba kaiwa bayan magaruba a waje amma yau saboda masoyiyar ka tana asbiti shine kaje kasata agaba kuna daura status na cin zarafina wllh bani kuka tozar taba kanku".
"Status kuma wani irin status".
kallon sama da k'asa ta masa tayi dariya ta shige ciki shi kuma ya jefa kan sa kujera there'siter lumshe ido yayi yana "Lahaulawalakkuwata'lillah'billah" .
bayyi auni ba kawai yaji an yankeshi a hannu a firgice ya mek'e kafin ya Ankara ta sake yankan sa ahannu
"Halima Halima Halima."!!!!!!
ganin zata masa illa yasa ya yi kanta gadan gadan
Tana nunashi da wuk'an tana ja dabaya tace'' inde dole sai kayi auren nan to zan kasheka inyaso a fanshi ranka da nawa".
"Halima ki saurara ni wllh bani da niyar auren nan zan miki bayani".
ni wllh bawani bayanin da zaka min ba kace ko Rana da wata zasu dena haske sai ita ba".?
"yaushe na fad'a mezanyi da wata Izza da har zan furta wannan akanta".
"a bayyane kafada yanda duk duniya zasuji shine dan kazo gabana......
gani da gaske take yada Agrif yin waje da gudu itama biyo sa tayi amma Allah ya temake sa yafice yarufo kofan ta waje yasa annu a al'jihun sa yana zaro wayan ya kira Kamal a take Kamal yafito a nasa part din yana tambayar sa lafiya
Agrif nuna masa annun sa dayake jini yayi yace " kaga hannu na Nasrim ce tamin haka tana ciki wai sai ta kasheni".
Nasrim ta ciki sai dukan kofar take
Kamal ya numfasa yace " Agrif duk lefin kane ai ba ka kyauta ba ko zaka fara d'okin Izza kabari tazama matar ka mana amma wllh nima banji dad'i abinda ka aikata ba".
"me na aikata Kamal wani d'oki na nunawa Izza yarinyar da ko kirana ta bana dauka".
Kamal yace "status din da kayi da ita ba doki bane".
cikin mamaki da rashin sani Agrif yace " ban gane status ba" ?.
yace yana duba wayan sa yace karo da status din da bashi ya d'aura ba kuma a wayan sa "what!? meye haka Kamal wllh bansan dashi ba ni bani na daura ba wllh ni bani da wani hoton Izza a wayata meyake faduwa".
Kamal yace"ban gane ba ta yaya wani zai d'auki wayan ka ya d'aura maka status".
cikin gigicewa Agrif yace
"Wallashi Kamal ka yarda dani ba tare muke da kai ba yau kaga ma nayi amfani da waya
" a silent fa na sata".
Kamal yace" ai shine nima abin yaban mamaki ina zuwa nasamu Humairah tana kuka ita take gayamin ga abinda yafaru wllh ban yarda ba Saida ta nuna min na yarda".
"Kamal me nayiwa mutane suke son ganin bayana da matata".
ganin yanda jini yake fita Sosai a hannu Agrif Kamal yace muje hospital
bayan su dawo daga asbitin
nasrim ta gama buge bugen ta wullar da wuk'an gefi tana maida numfashi dak'er Kamal ya shawo kan Nasrim tayarda ta shiga bedroom din ta Kamal yaraka yana kwantar mata da hankali tashiga wanka Yana zauna tafito sanye da rigan baccin har sai da yaga ta kwanta yaja blanket ya rufeta yafita
shima Agrif din Kamal dinne ya rakashi bedroom din sa
Kamal yace"shikenan Haruna ta hakura har ta kwata ma kaima kayi kwanciyar ka amma dan Allah idan da matsalan kayi saurin kirana dan FURUCI Nasrim Yana bani tsoro
************************
" da a suba Nasrim tana farkawa taji gaban ta Yana wani irin faduwa sai kuma ta kejin buga kofa kamar ana kuka kuma kamar kukan yaran ta da ta gudu tayi d'akin nasu tana bude kofar taci karo da Fayyat da Khaldum a kwance cikin jini an musu yankan rabo sai bige bigen kofar batdroom din d'aki a ke jitayi komai ya tsaya mata ahankali tayi kofar ban dakin tace'' waye aciki !"?
"mamy Dan Allah kar
ki kasheni na dena miki rashin kunyar wllh dan Allah kin kashe Fayyat da Khaldum !!!
"Khafulan bani na k'ashe suba dan Allah ka bude kaga yamin da kaske fa sun musu waye ya kashe su".
"Mamy kece kece da wuk'an da kika wasa d'azu kika kashe su bazan bude nima ki kashe niba".
Nasrim da gudu taju ya ta fita dakin Agrif nan ma me zata gani shima gaba daya an gama cakeshi da wuk'a juyawa tayi da gudu ikon Allah
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 40