me sunan mommy itace babba ana kiranta Muwadda sai me sunan ummu Amina ana kiranta umdatu
Aranan sunan su Ummdatu Humairah mata ta haifi d'an ta namiji mesunan Abba Abdulmajid Hajja ta hana acanza dan haka da sunan sa ake kiransa
**********************
*Dubai*
Murmushi Agrif yayi yace
"Nasir tanan kuma ka b'ullo to ma in ba da aljanu kake son nayi aki ba ni daya nayi supervisor a k'asa she har 6 tare da kuma zuwa signing k'atsa 6 acikin wata daya kuma zuwa dakai bayan nawa aikin zaka had'amin aikin mutum shida ni nidaya".
kallon sa Nasir yayi sama da k'asa yace
" Ok ba zakayi ba"?.
mek'a masa file din Agrif yayi yace" Yes wannan aiki ai sai ku gauraye amma bana mu masu iyali bane".
ya ajiye file din ya juya zai fita yaji Nasir yace " lafiya lau Ummu sai dama inason kizama shedane Agrif yace zai ajiye aiki kinga kar aga kamar Koran sa nayi".
shiru yayi yana sauraron can yace " wai dan nadan raga masa nawa aiki dana Aiban kafin Aliyu yazo nikuma gaskiya ban yarda da wani na waje ba shine yace ai wannan aikin sai mu kauraye ok".
yace tare da mek'ewa Agrif wayan "Ummu barka da war haka".
"Agrif me kake son kazama ne kode zaka gaskan tamin maganan Hajja da take cewa idan ka auri Nasrim sai nadage ne tun daga yanzu ka fara wasa da aikin ka akan mace" .
"Ummu ba haka bane ki duba yawan ai.....
"rufemin baki kar nasake jin an kawomin k'aran ka akan aiki inaso ka kasance me aiki tukuru kamar Abban ku marigayi shi kad'ai yana iyayin aikin mutum goma bana son naji kace komai".
"Ok Ummu in sha Allah zanyi yanda kikace".
Daga fa Agrif yashiga very busy
Nasir yasamu abinda yake so dan ayanzu Agrif bashida lokacin kansa ma balle yasamu ya Kira Nasrim ko ta waya ne gaba daya yabircike cikin watannin nan yazama kamar mahaukaci kullum sai ya hau jirji ko shan shani bazai gaya masa yawo ba dama burin Nasir kenan ya kauda hankalin Agrif akan Nasrim
Nasrim ko tasake cika fam dashi yanzu tsayon 3 bako waya dan idan yasamu lokacin Yana dan kwada K'iran ta amma bata picking shima yafi son hakan dan bashida abinda zai gaya mata cikin Nasrim yayi wani irin girma kamar ba haifuwar fari ba watannin cikin 7 amma tana mutuk'ar shan wahala yamata mugun nauyi Hajja da sauran yan gidan Sarai sun gane ba d'a daya bane a cikin ta ganin yanda cikin yarabu kashe biyu kamar na yan ukku mommy Nasrim wanda komai ma yimata ake sallah ma azaune ko akwance fitsari atsaye dan ko gwada tsugunawa bata iyaye tunyana wata 5 ta tare part din Mama komai Mama ce take mata da kanta dan tana sha wahal sosai
*******************
bayan wata 2
duk mutane gidan suna kan dining table amma ita ta baze a tsakiyar parlourn da shirgin tuwon al'kama a gaba Kamal yana firfita mata kunun gyada sai faman lallab'ata yake yana mugun tausayin ta kamar yacire cikin yakeji yamutsa fuska tayi ta ture tuwon a gaban ta Kamal yace " sorry my sister sai me ki keso"?
hawayen data jima tana danne waye ya sirto mata da sauri Kamal ya ajiye cup din hannu yace
" sorry sis me yake damun ki".?
tace'' Yaya Kamal marata da cibiyata'.
ta k'arashe maganan tana kai hannun ta kan maran ta
da sauri Kamal ya juya ya kalli mommy ita ma mommy duk hankalin ta awajen yake dan haka taji abinda Nasrim tace'
Kamal yace " mommy maranta ne yake mata ciwo".? Mommy tace
"Son jikin tane ya janwo mata bana ce tana yawan motsa jiki ba tafa shiga watan haifuwa amma ita kenan kullum ajang'obe awaje daya waya sani mako labor take ta tashi tana d'an zagawa".
Hajja tace'' gaskiya yarinyar nan fa abin tausayi ce mijin ma gani nake baya kulawa da ita wane aiki zai hanani zuwa ganin matar sa ahalin da take ciki nikam wllh Agrif bai iya kula da macce ba sai de d'ir ka ciki daga ganin cikin nan magadan yan ukku ne aciki amma komai saide Aisha da Kamal su mata anya ko a waya yana k'ira kuwa".?
Mama tace'' sosai ma Hajja Yana k'irana" .
itane Nasrim ta kanta take yanzu Kamal ne yakama hannun ta tamek'e tsaye ahankali take tagawa Kamal yana rike da hannun ta
cikin wahalallen murya tace'' "Allah Yaya bazan iya ba marata".
tace tare da rek'e Kamal kam mommy ce tafara tasowa
duk suka taso suna mata sannu mommy tace'' Mama mukamata ko wannan bedroom din mushiga da ita
Safan hannu ta zaro acikin jakar ta suka kama ta suka shiga da ita bedroom din Hajja na k'asa mommy tana dubawa jikin ta yafara rawa cikin in nina a tsorace ta d'ago tace'' Aisha mutafi asbiti".
Mama tace'' Dr Fanna lafiya".
Aisha hannu da k'afane yake shirin fitowa dole sai munje can na haska idan yakama dole ayi cs ne saide na mata".
Kwantar da ita akayi acikin motan mommy tana bata temako haka suka k'arasa hospital din suna sauk'a wayan mommy yayi Ringing tauka tayi Nasir ne ko sallama bayyi ba yace'' mommy meye damurwa ne yajikin nata".?
Mommy cikin mamaki tace'' waya gaya maka kai kuma"?.
"Mommy yanzu ba lokacin wannan tambayar bane meyake damun Nasrim ".
Mommy tamasa bayani halinda ake ciki
cikin rawar murya yace" mommy mommy Dan Allah ku temake kar ku farka min Nasrim kubani two hours
ya k'arashe maganan kamar zayi kuka
hakan ko akayi mommy de tafara bata temakon gaggawa tana jiran zuwan Nasir da yace mata gashinan a private jet
yana sauk'e direct hospital din ya wuce cikin tafiyar sa kamar zai tashi sama yau ba tafiyar k'asaitan labor room din yawuce Hajja suna parlourn ko kallon su bai tsaya yayi ba ya wuce Nasrim tana ganin sa ta fara yun k'urin zata tashi da sauri mommy da Dr Hafsa suka mai data
cikin wahalalen murya tace'' mommy ku rufe min jikina mommy me wannan bayahuden zan min yafita".
Mommy tace'' haba Nasrim dan uwan ki ya damu dake tun daga Dubai fa yazo yanzu dan ya temaka miki".
"wa mommy ni wllh ko zan mutu idan wannan banzan ya taba jikina ban yafe ba kubar ni na mutu kawai."
ahankali Nasara yake takawa idon sa cike taf da hawaye afili yafurta mommy haka cikin Nasrim yaka haka yamai data haka yabata wahala mommy me yasa baku gaya min ba".?
ita ko Nasrim sai k'okarin rufe jikin ta take ganin zata masa tijara yasa yayi wani irin daure fuska ya goma Nasaran sa sak ya janye zanin da take k'ok'arin rufe jikin ta dashi ko safan hannu bai tsaya sawa ba ahankali cikin kwarewa ya tura hanun da k'afan cikin mommy da Dr Hafsa yan kallo suka zama suna mamakin yanda akayi Nasir ya k'are wajen sarrrafa k'arban haifuwa
shafa goshin ta yayi cikin taushin murya yace " ki yi Nishi".
kafin yarufe bakin sa taji nishin yazo da kansa sai ga d'a yafado zata sauk'e numfashi taji wani sabon nishin yana taso mata wani d'an dan ne yasake fadowa ba ad'au lokacin ba sai ga wani dan d'an
cikin kan k'anin lokaci Nasir ya yanke musu cibiya sai faman kallon yaran yake yarasa murna zayyi ko bak'in ciki yasunan yaran nan yan halak ko Haram ko y'ay'an k'addaran bai ta bajin yayi nadama kamar yau ba
jiyayi hawaye ya sirto masa atake yaji wani irin son yaran yashige shi
Mommy ta kalli Nasrim tace'' kiyi shiru kidena motsi dan mahaifar ki tasamu ta koma dai-dai".
Dr Hafsa sai kallon Nasir take da jariran ta kasa hakura tace "ikon Allah Dr Fanna kin ko ga yanda jariran nan suke kama da Nasir"?.
Mommy ta sake kallon jariran da Nasir yake shirin daurasu girjin Nasrim tace'' sosai ma kuwa ai kamar sanda aka fito da Nasir aka bani nake kallon su".
shide Nasir bayyi magana ba yafice gaba daya yarasa meyake masa dadi dan wani irin tausayin yararan da soyayyar su ya mugun shigar sa lokaci k'alilan
Ummm
Zokaga murna awajen Hajja da sauran mutanen gidan three brother
Agrif ba Wanda yagaya masa sai a status din Nasir yagani atake yabincika aka sanar masa ai Nasir nema ya karbi haifuwar aiko bashiri shima ya dauk'o jet din ana shirin sallaman su a asbiti yashigo jiki a sanyaye yake kallon kowa har aka shishiga mota aka fara watsewa shima motan daddy yashiga ana shirin shiga sallan magariba suka k'araso dan haka iyayen maza a masallaci suka tsaya bayan an idar da sallan Agrif yace " daddy Abu dan Allah ku gafirceni akan abinda nayi da wanda zanyi yanzu daddy ni Haruna nasaki matata Nasrim alokacin da take da ciki batare da sanin ita kanta ba gashi yanzu ta haifu hakan yanuna ta gama idda kuma yanzu inason Mai da auren mu dan haka ga sadakina amai da mana auren mu yanzu batare da sanin ta ba bana son iyayena mata su sani".
ya k'arashe maganan yana fito da kudi a al'jihun sa
yace ga sadakin ta malam liman dan Allah katayani bawa iyayenan hakuri nayi kuskure kuma zan iya daukan kowace irin hukunci amma banda na kin maida aurena a wannan lokac......
wani dogon ajiyar zuciya Nasir ya sauk'e yace " Al'hamdulillah anzo wajen amma Haruna kayi kuskure idan kana tunanin zan sake barin ka mallaki Nasrim dama so daya tak take zuwa mutum arayuwa Nasrim ta *saku* ba wani batun maida auren tunda ba iddar ka akanta ayanzu Nasrim iko na ce ni zan aur......................
*to masoya muje zuwa gar kuka ina gudu batare da na fayya ce muku kamai ba labarin FURCIN NA NE labarin ne me tsoyo Sosai shiyasa nake saurin dan kurzu cikin labarin kar ku manta rikicin babban gida ne ta ko ta Ina rikin zai b'ullo dukiya soyayya sai munshiga cikin labarin de Dan har yanzu shinfida ake*
*Sai naji comment din ku*
*ban baya ko cin gyara ko kwarafi 08062383027*
*Bj*
[4/8, 1:48 PM] Batul Adam Jattako: *FURUCI NA NE*
( _rikicin babban gida_)
*NA*
*BATUL ADAM JATTKO*
*11*
Ni nake da ikon aurar da ita awanda ya dace kai baka da ca da ita ba".
Agrif ko kallon idan Nasir yake bayyi ba ya cigaba
yace' "Dan Allah liman idan har baka bawa iyayena hakuri an maida auren nan anan yanzu ba idan munshiga cikin gida za a iya samun babban matsala Dan Allah ka dubi wannan buk'atan nawa".
Abu juyowa yayi cikin wani irin b'acin rai yana kallon Nasir yace' Nasir wakake son ka aurawa Nasrim".
kafin Nasir yayi maganan daddy yace " ah ah Abdulrahaman ba ayi haka ba idan akace baza amai da auren nan ba ba ayiwa Baban gidan adalci ba kayi duba da tsoron Allahn sa amasa adalci
yayi saki batare da sanin kowa ba sai shi sai zuciyar sa amma yaji tsoro Allah yakawo kansa dan a halatta masa matar sa bai kamata mu masa haka ba ida yacigaba da zama da ita ahaka wayasa amma tsoron Allah yasa yakawo kansa ni dama na san Baban gidan me tsoron Allah ne da bin dokokin sa kuma basai mun bincika dalilin sakin ba ni dama tun auren sa nasan cewa da abinda yake damun sa".
Abu yace" to yafadi akan me yasake ta shida ko zaman kirki bayyi da ita ba".
Murmushi daddy yayi yace "shi zurfafa bincike a tsakanin maurata ba zai kawo na matsa lahaba ba nide ya burgeni da yaji tsoron Allah nawane ake saki ukku amma matar da mijin su rufe abin su azauna ahaka ayita haifan yara shegu acikin gidan aure shiyasa zaka samu mutum da uwa da uba amma tantiri ya daddabi iyayen da dangi yawanci aka bincika ba y'ay'an sunna bane".
Man liman yace" hakane alk'ali ku kuke jin abubuwan da dama nima yaron ya burgeni Ina shawar tanku da amaida masa matar sa tunda dagani koma meye yayi nadama Allah yakiyaye gaba".
Abu de bai soba dan gani yake Agrif yana samun Nasrim a arahane yasa yake duk wannan abubuwan
Daddy ne da kansa yabada sadakin dubu shamsin mutane suka shafa fatiha wani irin kallon nayi nasa ra Agrif yadin gayiwa Nasir
sosai man liman yayiwa Agrif nasiha akan saurin sakin aure yana kawo da nasa kuma ba a saki cikin b'acin rai duk abinda matar ka tayi maka wanda yakama na sakine kada kayi alokaci kabari ka nutsu sosai kafin ka furta saki dan gujewa danasa".
Agrif yace" nagode Baba malam insha Allah aurena da Nasrim awanan Karan ba saki".
hakade kowa ya watse
sai Agrif da Kamal da Nasir da bashi da niyar tashi ma Kamal ne yafara mek'ewa yana kallon Agrif yace" Haruna kasamu dama fa daya dama Kai bayan tafiya da kayi kabar da harda saki kamata kwata kwata Nasrim bataji dad'i aure ba Dan me zaka maida had'in gida haka wannan ai yazama had'in muguta ni ina zaune da taka k'anwar lafiya amma ni tawa tana Shan wahala wllh badan Allah yariga ya k'addara rabon wadan nan yara har ukku a tsakanin kuba da bazan bari amaida auren ba".
dariya Agrif yayi yace " shegen sama wai Kai Yaya ko to nagode da naci al'barkacin yarana kaga tun daga yanzu sun faramin amfani Allah ne kadai yasan AMFANIN da zasumin zuwa gaba na gode Allah da ya bada yaran nan da sunana kuma har abadan sunanan zasu amsa".
Ya k'arashe maganan yana yiwa Nasir wani kallon k'eta
shima Kamal dariya yayi yace" amma fa mutumina kayi mugun iya zubi yara ukku lokaci daya three brother sun dawo congratulations".
ya k'arashe maganan yana mek'ewa Agrif hannu kama hannun sa Agrif yayi suka fita suka nar Nasara awajen
****************
Acikin gidan
sai da akayiwa jaririn wanka aka kin tsasu cikin fararen rigunan su over roll sai asannan kamansu sak da Nasara yasake fitowa Izza tace'' kai masha Allah yaran nan kyawawane amma mamaki na mugun kama da sukeyi da ya Nas ".
wani uban ashe Nasrim ta maka tace'' tam lalle Izza bak'ya So na zaki had'amin yara da wancen bayahuden Allah yasauk'e ba dangin iya bana baba suyi kama dashi mommy suka biyo wllh dan iska dan renin hankalin harda shigamin labour room ku........
shiru tayi asan da suka hada Ido dashi fuskar sa ba yabo ba fallasa cikin takunsa na isa ya k'arasa har cikin bedroom din bayyi musu magana ba yawuce bakin gadon inda yaran biyun suke kwance duk yabude fuskokin su da alaman babban yake nema shine ahannun Izza d'agowa yayi Yana kallon Izza da alaman ta mek'o masa shi da sauri Izza ta mek'a jiki na rawa durk'usa yayi da yaron a hannun sa ya fara masa sallama akunne sannan yamasa K'iran sallah sai kuma yamasa shud'uba yajuya ya mek'awa Humairah ahankal yafurta "sunan sa ABDULSAMAD amma za adinga kiransa da KHAFLAN".
sai yasake daukan me binsa shima yamasa kamar yanda yayiwa wancen ya mek'awa zahra yace " sunan sa ABDULRAHAMAN za adinga kiransa FAYYDAN
sai k'aramin shima yamasa kamar yanda yayiwa yan uwan sa yace " shi kuma ABDULSAMAD za adinga kiransa KHALDUM".
yayi kiss din yaro tareda fita dashi gaba daya a d'akin
wani uban ashe Nasrim tamaka tana dirowa a gadon Nasir da bai k'arasa ficewa ba yana jinta juyowa yayi ya mata kallon Ido cikin ido Wanda bata san ya zata fassara Shiba ya k'arasa ficewa yana murmushi
"Kan uba wannan wane salon renin hankalin ne shiwa meye hadin sa da yarana kai harda wani yimusu hud'uba dan iko har da fad'an sunan da za akirasu dashi wllh kayi kad'an tayi hanyar fita zata bisa Zahra ce ta rik'ota tace'' Ina zaki".?
"ki barni Zar d'ana zan karbo".
kafin Zahra tabata amsa Hajja tashigo da kwanon kunun kanwa da ludayi ahannu
tace'' ke kuma fa ko mutanen na kine sukaji k'arnin jini suka tashi kike wani fincike fincike".
Humairah ce tayi mata bayani tana dariya
Hajja tace'' ooyo aikin banza dan kinsamu ma Nasuru yanuna kulawan sa akan yaran ki kike wani falli kinga yanuna kulawa akan dan gidan Humairah da Kamal ne ko kinga ya taba d'aukan yan biyun Izza kema kinci darajan shak'uwa su da Haruna ne".
Nasrim muzurai ta bara da ido ta zauna a bak'in gadon tana gunguni
Hajja tace'' gashi kunnun kanwane saboda ya warkar miki da gun kwanciyar yaran da wankin ciki idan kinga dama kisha".
"ni kam gaskiya ba kunnun da zansha ai nasha maganin".
Hajja zatayi magana me aikin mommy Zahira tashigo ta zube a k'asa tace'' ranki shi dade Halima yallabai Nasara yace zan kai masa Khafulan da Fayydan".
Hajja tace''suwaye kuma hakan".
Zahira tace'' ban sani ba haka de yace".
dariya Izza tayi tace'' Hajja jaririn na ne mana".
Hajja tace'' gaskiya sunan yayi d'adi".
sai da Hajja ta dage Sosai Nasrim tabari Zahira tafita da yaran
Nasir yana zaune da Khafulan aciya a parloun mommy Zahira tashigo da yaran ahannu mek'ewa Nasir yayi tsaye cikin tsawa yace "ke baki da hankali ba zaki nemi wani yataya kiba zaki cukuy kuyamin yara kaman kayan wanki kika...
Mommy ce tamek'e ta karbi yaran daya bayan daya ta kwantar akan kujera tace'' Zahira jeki abinki". Jiki
na rawa tabar wajen . mommy ta kalleshi tana mamakin yanda ya damu dasu tace''sorry Abban su Khafulan."
murmushi yayi yace "mommy sunan yayi kyau dani daga yau kidena kirana da son sai Abban KHALDUM".
Mommy tace'' eh mana gashi nafara ai ka girma kazama Baba Allah de yanuna min naka yaran".
tsugunnawa yayi yana janye showel din da ya rufe fukan Fayydan yace "mommy bakiyi mamakin yanda jariran nan sukayi kama dani ba".
Mommy ta dauki Khafulan tana sake kallon sa sosai ta numfasa tace'' ai kowa mamakin yakeyi saide idan akayi la a'kari da uwar da uban duk ka jinin ka ne ba abin mamakin bane su biyo ka a na samun haka Sosai kai wani mafa kwata-kwata basu had'a dangi ba amma sai kaga suna fisgen kama".
"ajiyar zuciya Nasir ya sauk'e
yace" mommy ban taba son wani abu a duniya kamar wadan nan yaran ba mommy ina son kizama sheda na basu rabin kasona acikin dukiya ta sannan idan Allah yasa na mutu ban haifi wasu yaran ba na basu duk a bin dana mallaka a dukiya".
zaro ido mommy tayi tana kallon sa tace'' Nasir baka iya hausa ba cewa zakayi idan na mutu ban haifu ba amma idan kace idan na mutu ban haifu wasu yaran ba tamkar kana nufin kai ka haifi wadan nan kenan kuma gaskiya kyautar tayi yawa kade duba wani abu ka musu kyau tan dashi amma rabin dukiyar kafa zai iya zama wani abun da ban a gidan nan kaga Abdulsamad yaron Kamal shine babban amma banajin ko daukan sa ka tabayi ga yaran Aiban suma yan biyu baka taba d'aukan suba sai wadan nan zaka sa adinga ganin kamar kana nuna ban banci ne saboda su wadan nan jikoki na ne baza suyi duba da shak'uwar da yake tsakanin ka da Agrif ba saide ace dan ni kayi kaga ba dad'i dama Hajja tayi mugun sa Ido akan abinda Allah ya bani duk da ban rage su da komai ba kuma ban zag'e akai na nuna musu nawa nawane ba yanzu idan taji an bawa yaran Nasrim wannan babban kyauta zatayi magana". daure fuska yayi yace
"Mommy nide na basu kuma kar ta fasa tayi maganan naji".
Mommy tace'' ah ah son ai ba agaban ka zatayi ba".
kawar da zancen yayi da cewa "mommy yanzu wane Madara ya kamata afara daurasu kinga Faydan yunwa yake ji".?
yayi magana yana nuna mata dan yatsar sa da Fayydan din ya raruma zai kai baki
" ai Abban Khafulan nonon uwa shiyafi dacewa akan komai awajen jariri amma tunda sunyi yawa balalle ya ishe su ba NAN yaka mata a hada musu dashi".
*****************
a ban garen su Nasrim kuma
shigowa Agrif yasa su Izza dasuke da faman lallashin Nasrim ficewa a d'akin a hankali ya k'arasa yazuba guiwowin sa a k'asa sunkuyar da kan sa yayi itama batayi magana ba amma tayi mugun cin kunu rasa yanda zayyi yatun kare yayi can ya numfasa yace " hakuri juriya sune mataki na farko na nasaran komai a rayu musamman akan soyayya nasrin zan baki hakuri akaro na ukku wanda in Sha Allah shine na k'ashe wanda kuma ina sa sammanin yafiyar ki saboda girman SOYAYYA ta a zuciyar ki".
me makon ta bashi amsa sai kawai ta mek'e tsaye kamar zata shiga bathroom tafara wak'a cikin zazzak'ar muryar ta tace'' _ashe Wanda kayar da dashi wataran zai cutar da kai k'ashi nide rayuwa nake Sam Sam bani da jida kai kaicon wannan rayuwar Wanda ka so shi zai ba dakai shin dawa zaka yarda ne_
sauk'e numfashi yayi
shima yana mek'ewa kamo hannu ta yayi yace "Halima da kanki kawai zaki yarda ba mutane duniyar yanzu ba koni bance kiyarda dani ba dama kawai na keson kibani Nasrim jiya yawuce yanzu ma zay wuce wllh Nasrim aiki ne aka hadani dashi kuma aka d'au reni da umarni uwa wanda yazame min dole nayi amma bana jin akwai fitar nufashina da zai iya fitowa cikin k'oshin lafiya ba tare da tunanin ki ba ni na yarda da kaina bayyi dan na cutar dake ba"..
zama takoma tayi tana kallon sa tace'' Agrif ni bana fushi da kai tunda naganu matsala mu
kasan meye matsalan mu ne".?
girgiza kai yayi yace " nasan Wanda na sani amma ballene nasan wanda kika sani ba sai kin sanar Dani".
ajiyar zuciya ta sauk'e tace'' Nasir ne kuma saboda ni ya K'ara maka yawan aiki saboda baya son muji dad'in rayuwar mu meyasa dacan bai k'arama ba sai yanzu amma kai ka kasa yarda kullum k'okarin kareshi kake".
g'ada kai yayi yace" good naji dadin yanda kika gano manu farsa abin da baka sani ba shi zai cutar dakai wanda kasani kana da al'hakin shayo kan matsalan Nasrim a sharawa ta a halin yanzu idan muna son mu kasance dare dole sai mun hak'ura da karatun ki duk inda zanje muje atare".
"a a a ya Agrif ba zancen ajiye karatu na saboda shima yana daya daga cikin burina".
"to Nasrim so dayawa idan aka hada buri biyu to basa cika gaba daya sai an kashe wani araya wani amma ni zabin ki shine nawa".
"gaskiya na zabi karatu Yaya sabo burina ne tun ina yarinya nazama lawyer saboda na nemi hakkin cutar dani da wancan azzalumin yayi wajen ciremin yatsa sai dana girma na k'ara wayo nasan cewa alokacin da yamin hakan bai kai minzalin da za ayi Shari'a dashi ba amma duk da haka banji bana son zama lawyer ba saboda burin daddy na ne".
"Ok to Nasrim ni zan zame miki dukkan garkuwa wajen ganin cikar burin ki dan haka nidake zamuyi hakurin bin rayuwa yanda yazo mana dan haka meye matsalan ki game dani ayanzu bayan wannan"?.
"Yaya Agrif babban matsala ta shine bari da kayi wannan dan rai nin hankalin yake yanda yaso kana sane da cewa shi ya karbi haifuwa ta bayan ba muharramina bane sannan yazo yashigo min har d'aki batare da neman izzini ko sallama ba dan iko har yasawa yaran mu suna da bada umarnin sunan da zamu kirasu dashi cikin iko da isa".
murmushi yayi yana jawota jikin sa yayi hugging dinta Sosai atare suka saki ajiyar zuciya har sunaji bugun numfashin junan su
ahankali ya dan janyeta suna facing din juna yace " dan yakarbi haihuwa ba matsala bane wani can daban ma inde likita ne zai iya karban hafuwa musamman da matan suka kasa
zab'an suna kuma bawani matsala dan yanuna kulawa ga yaran mu kuma koda nine ita abinda zanyi kenan na maida suban su daddy tunda magadan sune".
shikenan amma sunayin da yabada akirasu dashi ne bazan Kira ba".
murmushi yayi yana shafa fuskan ta yace " wannan kikon kine na uwa my beautiful wife ke wallahi haifuwar ma wani k'ayatacciyar kyau ya karamiki anya bazamu koma part din muba".
ya k'arashe maganan yana Shirin setting din bakin su
salatin Hajja ne ya dawo dasu hayyacin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 40