Agrif yayi gyaran murya yace" yawwa Daddy abinda na manta ban fada ma ayi agaban ku nasan halin kishin Nasara zai iya cewa zai yanke min zumunci da sister dita to anan ne zayyi kuskure gwara kusani zumunci da Halima ba fashi".
Daddy yace" to kai Nasir kaji".
Nasir yace "to Daddy ni akuyane da bazanyi kishin matata ba saide ni bazanyi kishin Agrif ba saboda nasan amanan sa zan dimga masa kallon tamkar Kamal ne awajen Nana".
da dare Zahra Ayman yazo suka tafi bayan sunsha fira da Agrif duk da su dama shida Aliyu sunsan yana raye Zarrat ma yazo ya dauki Humaira suka tafi bayan sun raka Izza Part din ta
Nasir da Agrif
samun waje sukayi suka sake baje hajar fira har kusan shabiyun dare
Nasir ya kalli Agrif yace "bro kafa bar ƴar mutane ya kamata kaje,
kaga ni Nana wai tana jego komeye wani jego Hajja ta haɗani da Mommy ta hanani shiga ɗakin da take ma".
numfashi Agrif ya sauke yace " bros nayi missing dinkane sosai nasan my dear zatamin uzzuri ai tasan muna tare".
Nasir yayi murmushi yace " kai kana yabon wannan matar taka kuma da alaman tana mugun kulamin da kai bro gashi kayi kyau kayi ƙiba fresh dakai".
numfashi Agrif ya sauƙe yace "sosai Izza ƴar aljana ce yanzu na san nayi aure duk namijin da yake son ya morewa rayuwa to ya aure matar da sonta yafi nasa anan ne zaiga tattali nifa yanzu ko sarki saide yanuna min nauyin rawani babu ta inda ta gaza Allah yamin baiwa da mafificin baiwa da ya hadani da Izza Izza she's good komai nata nice nasan bazan taba nadaman samunta amatsayin mata ba".
Nasir yace "kaga nikam duk ta yanda taga dama takeyi dani juyani ake sosai nikuma idan na fito na rama akan ma'aikata".
dariya Agrif yayi yana dukan kafaɗan Nasir yace" ah nasan ka fa ai bazaka juyu ba duk da nasan soyayya ce take tafiyar da rayuwarka ɗan loop"
Agrif yace yawwa bro ni kana kula da harkan companyn Kamal kuwa Abbaty de yace a'iki yamasa yawa baisan halinda ake ciki game da company ledan saba amma wasu plaza din sa yace komai normal ko".
"Eh ina bincikene akan company gaskiya manager din ba mutumin kirki babe yana son kashe masa company amma gobe de zan gama dukkan binciken a canza manager din".
sunsha fira yanda yakamata duk da tattauna war tasu akan business ne
sai kusan 2 na dare yafito daga Part din Nasir din
Izza har ta gaji da jira tayi bacci Suhal ne ya tashi ya fara kuka daukan sa tayi tana shirin sashi a nono ya shigo cikin sallamar sa da ya tsaya a iya leben sa direct bathroom ya wuce ba tare da yakalli inda take ma bajimawa ya fito daure da towel ɗaya a ƙugun sa ɗaya yana goge jiki dashi ya wuce inda mirror sama sama ya murza lotion a jikin sa tare da fesa turare ya ware ido yana kallon yanda ɗakin yasha gyara kamar ba shiba gaba daya part din ma yabashi mamakin yanda aka canza masa fasali murmushi yayi yace "ni Haruna ɗan gatan Mommy ne nasan wannan aikin sai ke Allah yabar manake yace tareda meƙewa yasaka kayan baccin sa
ahankali ya sunkuya ya sakarwa lil Aiban da yake cikin gadon sa agefin nasu kiss yashafa kan Suhal da yake cinyar Izza ya hau gadon tare da gyara pillown sa ya shafa addua ya kwanta tareda jan bargo
ahankali ta kwantar da yaron akan gadon sa ta sauƙo daga gadon ta zaga gefin sa ta gurƙusa tare da jan barkon cikin rawar murya
tace "mijina yau ni kajuyawa baya kasanar dani lefina kamin hukunci daidai da lefina kar ka zabi azaf tar dani ta wannan ɓan gare bazan iya jurewa ba".
kallon ta yayi ido cikin ido yace
"Izza kina son kifara taurin kai ko".
hawaye ne ya zubowa Izza yarrr bazato tace "subbahalallashi ni ni taurin kai Abban Zeenat menayi".
cikin daure fuska yace " tun yaushe nake miki maganan gyara mu'amullar ki da Halima amma kikace sai munzu gida gashi munzu ina gani ko kallon inda take bakiyi ba Nasrim bata daga cikin jerin matan da zakiyi kishi dasu ita din ƴar kuwa tace jini na kuma bazan gaji da gaya miki arziƙin ta kike c............
da sauri ta rufe masa baki da tafin gannunta tana girgiza masa kai ga hawaye na surto mata
"my habibi baka fassara ni dai-dai ba ni na isa nayi kishi da Nasrim albarkacin ta fana keci wllh wllh Ya Agrif ko kai bazaka gayamin son Nasrin ba Nasrim itace ta inganta rayuwa ta adaliln ta muka shigo cikin gidan nan ita tazamar ni mutum wllh kunyar ta ne ya hana na mata magana ina mutuƙar jin kunyarta ne kuma tana min ƙwarjini sosai kuma kai ma kasha cewa Nasrim tana da ƙwarjini so dayawa Hajja da kanta tana cewa anya Nasrim da Nasir ba sha shatau suke shaba suna da ƙwarjini sosai ni bansan ta inda zanyi controlling kaina a gaban ta ba amma tunda umarnin mijina ne ko zan mutu sai naje na gana da ita awannan tsohon dare ba sai gobe ba.....
ta ƙarashe maganan tare da meƙewa a zabure
wani irin fisgota yayi ta faɗa jikin sa ya birkito da ita tayi ƙasa shi kuma a sama ya sakar mata nauyin sa gaba daya yakai bakin sa daf da nata numfashin su yana fita atare murya can cikin maƙoshi
yace " MAR'ATUSSALIHA kinsan meye sirrin ƙwarjinin N'N".?
girgiza kai tayi tareda rolling da idon ta
yace" sirrin shine falalar salatin Annabi Nasir a kullum yana salati sau dubu arana kin gade duk yawan aikin sa ayanda yake dinnan to bayan ko wacce sallah sai yayi salati so dari biyu istigfari dari kinga idan aka hada na sallah biyar zai bada salatin dubu istigfari dari biyar wannnan ƙa idar Nasir ne sai dana zauna da Nasrim naga itama tanayi kinga nima awajen su na zara wannan shine sirrin su kema ki gwada zakiga abin mamaki".
Izza tace "kwarai kuwa haka Nasrim take duk busy din da zata shifa sai tayi su koda zata bar sauran zazkar din ta kuma wllh sakacine amma tare Mommy ta koya mana wannan tarbiyar Mommy ne Allah yasaka mata da mafificin Alkairi".
ta ƙarashi maganan tare da ƙarasa manna bakin ta kan nasa
*Nasir*
murmushi yayi a lokacin da ya bude dakin ya hango Hajja akan gado sai munshari take zubawa
ahankali ya tako har bakin katifar tsayawa yayi kallon ta yanda take baccin ta cikin kwanciyar hankali ta rungumo Baby Ni'mra ahankali ya jaye Baby tareda daukan ta ya maidata kan gadon Hajja ya dauki pillow ya kara bayan yarinyar ya dawo ya shige jikin Nasrim cikin bacci taji kamshi sa da tattausar jikin sa wani gwuron numfashi ta sauke tareda shigewa jikin sa jin abin yafi karfin kamshi yasa Nasrim ta bude idon ta da sauri bude baki tayi zatayi magana yayi saurin daura yatsan sa akan bakin ta yana juyowa inda hajja take alama yamata da kar ta tada Hajja
ahankali ya kai bakin sa kusa da kunne ta yace" meyasa baki tsaya kin ci abinci ba kika gudu".
ahankali tace "banajin yunwa ne ".
ɗan marin kumatun ta yayi yace "Ah Ah kide fadi gaskiya ganin Agrif yasa kika tsorata kin zata za ace ki rabu da ɗan ɗanon zuman ki ko ".
"kana nufin kai baka tsorata ba Ya Rujjulussalihi na idan akace in rabu dakai ai kamar an tarwatsa rayuwatane toma tayaya impossible ni kai har abada taya zanyiwa wanda yaƙi kula wata saboda ni ya zabi yarayu ba aure duk saboda ni
taya zan maka butul ci akan wani Agrif da bai san meye soyayya ba nasan da kaine baza ka fansar wa wani niba darajata tafi haka awajen ka RUJULUSSALISHI".
girgiza mata kai yayi yace
"Nasrim gaskiya Agrif yana sonki yanada zuciya mai yau wanda ba kowane yake da shiba tabbas bazan iya kwatanta yin abinda yayi ba Nasrim Agrif ɗan Aljanna ne tun muna yara yasha hakura da abinda yakeso akaina kamar irin su abinci zabi na karatu abubuwa dayawa ya sadaukar min kinga muna yara Kamal tak yake jira nayi lefi tazo yafada amma Agrif yafini moye duk abinda ya zamana lefina ne Nasrim ni ban isa nasakawa Agrif abinda yamin arayuwa ba banida abince masa banida abin bashi sai adduar dacewa a wajen uban giji
ni sannan ina sonki ki manta da kin taba soyayyya ko zaman aure dashi ki zauna dashi amatsayin dan uwan ki nima nayarda dashi bazai cuceni ba nadauke duk wani kishina inde akan Agrif ne".
can cikin dare Hajja taji ƙafa da da hannun Baby yanata shurin ta azabure ta tashi tana ihon maciji ya haumata gado ta fara kururuwa tana cewa "dama saida nacewa Abdulrahaman yasa arage itacuwan lambun nan mucizai sun fara yawa agidan nan jiyama saida aka kashe a gidan Haruna gashi yanzu har kan gadona ke Nasrim kunnan wuta inaga muciji yasareni ma Halima ba magana nake ba kin min.............
bata ƙarasa ba Baby ta sandara kukan tsorata da ihon Hajja wani wawan numfashi Hajja ta saike
tace au ashema mai sunata ce Allah sarki takwara kece wannan sakaran uwar taki takawo ki bata sanar dani ba da nadanne ki fa".
ta ƙarashe maganan tana laluman ƴar har ta dauketa ahankali ta sauƙa tana laluman makunni wuta
Nasir murmushi yayi yana sake shigewa jikin Nasrim tare suke cigaba da dariya basu zaci Hajja zata kunna wutan ba kawai sai ganin ɗakin sukayi ya kaure da haske salati tafara tana tafa hannu ta dungurar da yarinya a katifar ta fita da sauri zuwa falo
tsabar bacin rai batayi ma la akari da dare neba ta daukin wayan ta ƙira Mommy tare da fashewa da kuka
Mommy meƙewa tayi dafe da ƙirji taba Innalillashi Allahumma ajirni fimusifati
da sauri Daddy yace Dr lafiya".
Mommy tace "Daddy ban garen Hajja ba lafiya". tace tayi hanyar fita aɗakin da sauri a tunanin ta wani abune yasamu Nasrim ko jaririyar ta
Daddy yayi saurin riƙe mata hannu yana cewa pls dr bawani abin da yafaru ki nutsu yace suna ratsa compound din gidan harzuwa part din Hajja
zaune take a palo akan kujera tana faman jijjiga kafa da sauri Daddy yace "Hajja lafiya "? .
"ina ko lafiya Fanna na ƙira ta fita min da tantirin ɗanta anan ni ina taƙama nakawo yarinya kusa dani wai danna kubutar da yaran nan daga saɓo ashe shi hoto yake daukana kodayake ita tafishi fitina gasu can manne da suna jinin biƙi bai tafi ba mahaifa bata koma ba".
wani dogon numfashi daga mommy har Daddy sukaja Mammy ta shiga ɗakin shikuma Daddy ya tsaya bada hakuri ita kuma Mommy ta wuce ciki
suko NN sarai sun jita dama ba baccin suke ba dariya suke mata ganin ta fita yasa suka dauki ƴarsu suka koma kan gadon Hajjan a tunanin su ko Hajjan tayi fushi ta barmusu ɗakin ne gaba ɗaya kawai sai jin muryar Mommy sukayi akan su tace "haba haba my son karasa wajen shigowa sai ɗakin Hajja gashi yanzu duk ta tadamana hankali ita ka kirata zuwa part dinka mana kumama kwana nawa ne za a baka matar ka am srry kayi kakuri ka fita kaga tana can tanayiwa Daddyn ku faɗa".
ta ƙarashe maganan tareda karɓan NI'MRA hannun sa ta kwantar da ita tana ɗagosa tana wurga idon neman inda yacire kayan sa dan daga shi sai boxer hango jallabiyar sa tayi a gefin katifan dauko masa tayi tana meka masa "saka ko de ni zan saka maka ne Habibi".?
turo baki yayi alaman shagwaba
Mommy ta kalli Nasrim tace "ok Ammin Aiban karbi ki saka masa daure my son idan gari ya waye sai ta ɗan leƙaka a part dinka ni zance na sata aiki ne kaji sorry".
"MOMMY nide banaso yanzu ne fa nake bukatar ta bana iya bacci sai ina jin bugun numfashin ta shi yake zame min AC kwana biyu bana iya rinsawa idan banji ni a j........
sai kuma ya kasa ƙarasawa ya tsaya yana kalon yanda kirjin ta suke sheki alokacin data ɗaga hannun dan karɓan rigan da Mommyn take meƙa mata sai da tazo zata saka masa hannun hahu wanda shine na ƙarshe cikin kunnen sa ta raɗa masa
" daka ƙarasa mana yaushe kafara jin kunyar Mommyn ka ka dubi tsabar idon ta kace mata kai bazaka iya bacci ba sai kaji tudun boobs a cikin hannun ka".
shi kuma cikin ƙarfi yanda Mommy zataji yace ƙinaga bazan iya hakan bane".
dasauri ta yanke zancen da cewa Mommy na ƙarasa saka masa
Mommy ta kama hannun sa tace "muje."
suka fito daidai lokacin da Hajja take cewa ni ƙaton gardin nan zai shigowa a sirara Daddy de sai bada hakuri yake
har suka fice tade kasa yiwa Nasir da yake ta faman jifan ta da harara magana har suka fita kafin taje tabi ta kan Nasrim din data raina kuma
washe gari tun kafin a fito breakfast Izza ta shiga har cikin bedroom din Hajja ta samu Nasrim tana shirin fitowa aɗan kunyace tayi sallaman ta shigo zama tayi abakin katifan tana kallon yanda Nasy tayi kyau sosai cikin doguwar rigan wani kwancecen super holland mai zanen ja da yellow da baki ya zauna das ajikinta hannuta ta sake kaiwa bayan ta tana laluman zip din da dauri Izza ta tashi takai hannuta taja mata zip din ta cikin mirror suka hada ido Nasrim tace " thanks"
Izza tace "not thanks".
dan gajeren murmushi Nasrim ta sakar mata
Izza tace "dama ke mai kyau ce basai na bata bakina wajen cewa kinyi kyau ba kin sha jin sa awajen mutane da ace company wannan atumfar zasu san dake da sun daukeki ki musu tallah ".
juyowa Nasrim tayi tana shafa kumatun Izza
tace "haba my gangariya ai kin fini kyau kefa farace kalan maza kalan zamani"
Izza kama hannun Nasrim tayi zuka zauna bakin katifar sun kuyar da kanta tayi sai gashi yar hawaye shiru Nasrim tayi tana kallon ta saida ta dau lokaci tana wannan kukan can ta ɗago idon cikin na Nasrim tace "Dan Allah sister kiyi hakuri wllh bansan shi aka auramin ba kunyar ki ce tasa nake guje miki nake ƙin kulaki dan Allah ki yafemin".
girgiza mata kai Nasrim tayi tana cewa
"Ah Ah Izzatu hakance tazo a kaddaran mu nima gashi kunyar Ya Agrif ya hanani sakewa ko gaisheshi banyi ba".
hakade suka ci gaba da fira har lokacin breakfast din yayi suka fito yaude ba lefi Nasrim ta dan ware har suna fira da Agrif anan Agrif yake cewa shi idan ya tashi da Khaflan Da Abdul da lil Agrif zai tafi switzerland su kuma su tafi da matan Zeenat Muwadda Musatat Ummda
yau kwanan Nasrim ashirin da biyar da haifuwa tuni am mata kyaran jiki na mussamman wanda ahalin yanzu babu lolacin da zan muku bayanin sa
Idan kuna son jin cikekken tsumi na binnau wanda ake binne shi yayi wata shida ko ukku wanda akeyiwa amare masu jego da uwar gida first class ku tareni cikin littafina na *MAI GURI YAZO*
*ɗan daurin kai*
misalin ƙarfe shaɗaya na dare ya shigo Nasrim tana zaune tana shafa mai Hajja tana gasa marar yarinya zama yayi daf da Hajja har idan ta motsa jikinsu yana gugan na juna ya zubawa jaririyar ido yanda idan Hajja ta daura mata yatsan ta mai dumi take wani lumshe ido kamar Uwar ta taji ummmm
murmushi yayi ya ɗaga ido ya kalleta yayi sa'a itama shi take kallo da hannu ya yafito ta tasowa tayi daga ita sai sleeping dress din ta amma maidan kaurine saboda yanayin jikin jego
tsugun nawa tayi tana kallon sa nuna mata Baby Ni'mra yayi yace "kiga abinda Baby takeyi".
Nasrim tace "zafi ko ai dama nagaya mata ya isa takiji kai ka gaya mata tunda tana tsoron ka zataji yarinya kwanta ashirin da biyar amma ba adena gasa taba".
murmushi yayi yace "ba zafi takeji ma ki kalleta sosai idon ta yana kama da naki idan kikaji miss ko".?
fincike hannun ta tayi ta juya tana hawa kan katifar ta
Hajja da tunda Nasrim tace tana tsoron Nasir ta bude baki tana kallon ta har taje ta kwanta
cikin ɓacin rai tace "ni Maryama ni nake tsoron wani abu wai Nasuru Uban sa Abdulsamat ma banji tsoron sa ba balle wani yo ni badan maraicin sa nake dubawa ba ya isa wani abu awajena".
Nasrim tace "kina fakewa da maraici de amma waye ya isa acikin jiko kin ki ya ratsa main parlour ki ya rasa free palo ya haura sama yaratsa falon sama ya shigo miki har cikin bedroom yanzu ko Daddy yana shigowa nan ne ba iya kar su palon sama ba amma ki zauna kina bakewa da guzuma kina harbin karsana ina aka tabayin ƙaton mayara kamar wannan".
ta ƙarashe maganan tana jan barkon ta
dariyan mugunta Nasir yayi ai dama yana meman kofar da zai hadasu faɗa wanda zata korata Part din Mommy ko Ummu wanda komai zai zomasa cikin sauƙi
yace " ke Hajjar kike gayawa haka uwar Three A full ashe bakida kunya Hajja ta wllh yariyar nan badan jego takeba wllh yau ba me rabani da ita agabana take zagar min uwar uba ".
ya ƙarashe maganan tare da daure fuska kamar irin da gasken nan yaji haushi
"rabu da ita dena ɓata bakinka shalele na maganin ta kishiya aure zaka ƙara".
"Ah Ah Hajja koranta zakiyi a part dinki".
kallon
ka raina ni Hajja ta masa tace kai yaro nifa kakar bariki ce yo ni zaka gayawa zamani wannene ban gani ba nifa duk wani salallaben soyayya kar nake kallon ku yo nida nake karatun littatafan hausa tun tala taini damu aka fara yanzu ma sa idon Agrif ne yasa na dena karatun dan kasani nasan komai ni kakar bariki ce'.
Nasir kansa ya kwantar a ɗaya cinyar Hajja yace "to ai barikin ki banyi amfani ba gashi kin kasa bawa lovers jikan ki abinda yake so Hajjata nifa duk duniya ba nida kowa bayan Mommy na sai ke ina son ki musamman da kikayi kama da Abbana akullum fuskar Abbana nake kallo a naki ina son Allah yamiki tsowon rai sosai kakata".
shafa fuskar sa tayi tace "nasani Nasuru tun kana yaro nake ganin tsantsan na so a gareka nima ina son ka fiyeda yanda nake son raina jikana nasan kana son matar ka kuma tasamu cikeken tsarki ka dauki amarka gata can yarinya cede ni sai nayi kwana arba'in ina gasawa yarinya mara saboda yayi kwari kasanta ya saba da dubi shiyasa kikokina basa boranci shiyasa ka mannewa Halima kaga itama Humaira mijin yagama susucewa a kanta ga Kamal can agidan yari yana haukan shide ko zai rasa komai bayason rasa Humairah da ita yake son karasa rayuwar sa idan yafito
Bayan shekara ashirin da biyu tuni kamal ya fita an aura masa wata yaranya a dangin Mommy yarinyar uwar ta shuwa ce baban ta kanuri kaf three brother ba mai kyanta ta haifi ɗanta namiji an saka masa sunan MALA yayan Mommy
ahalin yanzu Nasrim yaranta bakwai wanda haifuwar ya tsaya mata tun shekaru takwas tana da yara biyar da Nasir bayan auren su NI'IMA sai hasan da susaini wanda ake kiransu FAYYAT KHALDUM
sai mai sunan SHARIF yayan Mmomy sai mai sunan Alhaji Hamza abokin Abban Nasir wanda suke ƙira da HAZEEK
Izza yaranta shida wanda da Agrif harda yan biyun da ummda yakama tana da yara tara cif
sai humaira ita yaran ta hudu duk maza ABID RAYYAN AMRIN sai ABDULSAMAT dinta babba
Sadiyan Abbaty yaran ta shidda amma ita yanzu ma shayarwa take dan ta nafari mai sunan baban ta wanda suke kira da Marhaf shine suke soyaya da Rumana ƴar gidan Zahra yanzu ma batun auren su akeyi sai yarda ta ukku Iman
a cikin shekarun nan anyi rashin Hajja da Hajja Ta soro
yara matan Muwadda Musanat Zeenat duk sunyi aure Abdul ma yayi aure har lil Agrif shima yayi aure
rayuwar gidan abin koyi ne da ban sha'awa sabida inde macce aka haifa a three brother to ana yayeta awajen Nasrim zata tashi in kuma namiji ne wajen Izza
akwai haɗin kai da fashimtar juna sosai cikin family
Mommy ta kalli Khaflan da yake cika yana batsewa fuskan nan cike taf da kunci tace " tode kaji umarnin dana baka ko ".?
cikin ƙunci yace
"Amma Mommy ni wana taba cewa zamana haka yana damuna ni yaka mata na yan kewa kaina hukunci bawani daban ba".
"nade kaya maka nan da wata biyu auren ka da Iman".
da sauri Iman tayi saurin sun kuyar da kanta zuciyar ta yana bugawa lalle an hada ta da aiki Khaflan tayi ta maimaita sunan a zuciyar ta".
Hazeek ne ya sameta a kitchen tana ta faman hada coffee yace "Mami Papa yana jira fa".
ya ƙarashe magaban tareda ficewa ta kofar baya
a palon ta sameshi yana ganin ta ya meke tsaye yace "my Nan kin manta da asalin Babyn ki ko".
Rujuluss na tsaya lallashin Iman ne Allah nide Mommy bata kyauta min ba yaza ayi tace zata hada Iman mai hakuri da hankali da wannan yaron wllh Iman tana mugun tsoron Khaflan hadin bayyi ba".
kamo hannun ta yayi yace "niko nayi mugun yabawa da zabin Mommy akan kaina ma balle ɗana da yayi dace da yarinya mai cikekken nutsuwa da asalin kyau kuma naya mugun sonta fiye da yanda ni nake son uwar sa".
da sauri Nasrim ta rufe masa baki da tafukan hannun ta tace "no bawani namijin da zai so matar sa feye da yanda ni mijina ya soni duk gatan macce kar nake kallon ta amma my dear seriously fa Khaflan yafi karfin Iman because idon yaron nan a bude yake sosai yanzu makaga lallashin da nayi wa yarinyar
ga tana mugun tsoran sa".
"muna furcine irin na goggan ta marikiyar ta kin manta itama haka tayi ta burgan bataso kinsan ance idan daɗi yayiwa mutum yawa sai yace Allah gani kasheni badan Mommyn ta dage sai Iman din ba mutane nawa ne suka min maganan dan Allah ga ƴarsu nan ta kafe sai Khaflan kinsan de idan irin Iman dubu yake so my son zai samu ko".
dukan ƙirjin sa tafara tana cewa ni ni zaka cewa munafurcin mariƙiyar ta sai nace nafasa tunda gashi kayi furfura".
"furfura adone ki fasan man nima Babby dina ya huta da yawan matsa dama kin damar min shi".
ya ƙarashe maganan ya na daukan coffee dinshi yayi sama cikin sauri itama ta rufa masa baya tana cewa Allah sai nayi sati ban kulasa ba ai zanga mai damuwa
"psl my nn kona yau bazan iya ba ai kingane ". yayi magana yana ɗaga mata gira daya
tura baki tayi tare da fanko
ƙofar kafin ya shiga
Khaflan
aika Harun ɗan gidan Baba yakumu ya kira masa Iman iman ƴar wajen Sadiya da Abbaty ce
tana shigowa ta samesa zaune a kan cushion ya meƙe ƙafar sa akan santa table da remote a hannnu sa fuskan nan nashi a mugun murtuke Iman adduar ta dingayi ganta a ƙasa ta ƙaraso sallama tayi tareda duƙawa
tace "Big bro barka da war haka ta ƙarashe maganan bakinta yana rawa bai ko juyo ba a hankali ya sauƙe numfashi yana cigaba da kallon kwallon sa
Iman tun tana durƙushe jin ƙafarta yana neman sajewa yasa ta zauna tare da kwantar da kanta a kan hannnun kujera tasan tunda ya shareta sai sanda yaga dama
sai daya tabbatar tayi bacci ya sauƙe ƙafarsa a hankali yana murmushi ya taso ya durkusa a gaban ta ya zubawa kyakyawan fuskan ta ido yana murmushi
ahankali yakai hannu kamar zai shafa fuskar ta kuma yayi saurin janyewa
cikin taushin harshe
yace "nutsuwar ki kunyar ki hakurin ki kyawun suffarki zubin dirinki abin so da alfaharine ga ABDULSAMAD NASIR ABDULSAMAD
I love you with all my heart amma kidena tsorona ina son muyi rayuwa kaman friend to friend ina son muyi rayuwa kamar Mami da papa zamuyi koyi da rayuwar su abin birgewa hakan bazai samu ba sai kincire tsorona nima mutum ne kamar kowa im so sorry babu wata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 39 Chapter of 40