Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuma neman afuwar rashin zuwana akan lokaci". ta k'arashe maganan tana sun kuyar da kai alaman ladabi ga Kotu kotu tace ta bada dama "shedata ta faro Barrister Izzatu Mustapha". kotu ta buk'aci Izza tafito Izza ta mek'e ta shiga gajeren d'akin katakon na bada sheda bayan malamin kotu yasa ta rantse akan zata fadi gaskiya ta gabatar da kanta tace'' aranan 7 ga watan 3 da misalin karfe 3 na yamma Ina kwance a cikin d'akina Habubakar Abdulmajid Haruna Kamal ya kirani a waya yace min izza Ina son kawo k'arshe rigiman gidan nan ta hanyan gaggauta auren ki da Agrif kamar yanda Mommy tace idan akayi aure Nasrim zata hakura ni kuma banason ganin tashin hankalin Nasrim dan haka ina son yanzu ki daura hoton ki Dana Agrif a status kiyi yanda zaki tunzura Nasrim na yau daya idan ta tada rigima dole za ayi auren yau ko gobe kowa ya huta atake na gamsu da shawaran sa na daura dan ni bani da burin da yawuce na aure Agrif saboda son da nake masa na abince na daura hoton Agrif Haruna dan na tunzura Nasrim bayan na daura sai kawai naga Ripley daga wanda ban taba tsammanin ba wato masoyina Haruna Abdulrahaman Haruna shima ya maida min da kalaman soyayya naji dadin da ban taba jiba aranan har na dinga Kiran sa bai dauka ba kawai sai da asuba muk............ sai tayi shiru ta kasa karasawa tana kokarin danne kukan amma ita takasa da sauri Barrister shashid ya mek'e tsaye yace'' objection my load ashe wadan nan hotunan Izzatu ba Haruna bane ya d'aura mun gano haka ne ta hanyan boyeyen cc camera din da yake cikin office din ina son kotu ta bada umarnin asaka wannan memory din dan". kotu ta buk'aci a saka memory din aiko saiga Kamal tun farko shiyazu bawa Agrif maganin bacci bayan minnuna kadan bacci ya fara daukan Agrif tashi yayi yakoma kan kujera three siter ya kwanta yana cewa Halima rigima bata barni nayi bacci ba jiya naso na gama aikin nan cikin kwanakin nan na dauke abata mubar k'asar wannan nacecciyar tsohuwar ta huta. ya k'arashe maganan yana rufe ido sai Kamal ya d'auki wayar Agrif yanata aikin a cikin sa Stop Barrister Fu'at Jiji ya danna yace'' my load kuma wayan Haruna yayi setting din ta yanda duk Wanda yayi amfani dashi to zai gani bayan Haruna Abdulrahaman ya koma gida Halima ta masa barazana kamar yanda dazu aka gani alokacin da akaje kashe shi an dauki wayan anyi amfanin dashi tawaje tura tsak'o bayan makashin ya k'ashe Haruna ya mek'awa alk'ali wayan alk'ali yagani sannan ya nuna a fili kowa ya gani to tes message din a wayar Habubakar aka tura dan haka muna tuhumar Habubakar Abdulmajid dashi yayi kisan nan k""""""""" cikin zafi Barrister Zayyat ya mek'e yace "objection my load ya barrister Fu'at zai daura lefi kai tsaye ga wani daban bayan ga Wanda ake zargi". Alk'ali yace'' barrister Fu'at ka kiyaye amma kotu tana buk'atar Habubakar Abdulmajid Haruna da yafito yayi bayani meyasa ya tunzura Halima Abdulmajid Haruna ta kashe mijin". Kamal tun ganin Humairah yaji komai ya tsaya masa cak yafito bayan ya fadi sunan sa yace'' kamar yanda na gayawa Izzatu Mustapha nayi dan a gaggauta auren ne dan y'ar uwata tasamu dangana shine dalilin..... cikin zabura Humairah tace'' objection my load ba shine dalilin ba dalilin da yasa ya tunzura Halima Abdulmajid ne tayi kisa kuma sai suka satan ta huce shine shi kuma yayi amfani da FURUCIN TA yaje ya kashe mijin ta da yaran ta". "Objection my load Barrister Aisha tana.... kotu tace'' Barrister Zayyat kabari shedu suyi bayani Murmushi Humairah tayi tace'' nagode my load ahankali Humairah ta taga gaban Kamal tace'' Habubakar Abdulmajid Haruna adaren 7 ga watan 3 da misalin karfe 12 kana ina".? ajiyar zuciya ya sauk'e cikin karayar murya yace" ina part dina marigayi Haruna Abdulrahaman dan uwa na kuma mak'ocina ya kirani nazo sun samu matsala shida matar Halima Abdulmajid". "Ok Habubakar da kaje a wane yanayi ka samesu.? Kamal wani irin hura hanci yayi tukun yace'' na samu Haruna a k'ofar main parlourn gidan hannu a yanke sai jini yakeyi anan yamin bayanin tsakanin sa da matar sace ita tayankeshi ganin yana zubar da jini Sosai yasa na yashi asbiti bayan mun dawo sai dana rakashi har cikin gidan sai dana ga komai yayi normal na koma part din na kawai da azuba ina Shirin fita masallaci Halima matar Haruna ta shigo da gudu tana cewa sun mutu sun mutu waya kashe su Koda mukaje nida matata sai muka samu Haruna kwance an caka masa wuka acikin". ya k'arashe maganan yana sakin kuka Humairah tace'' to Allah yaji k'an sa malama Habubakar kaman yanda muka kamaka dumu-dumu da amfani da wayan marigayi dan ka tunzura matar sa kuma gashi kasamu yanda kake so haka mun kamaka dumu-dumu da kashe dan uwan ka Haruna ta hanyar basaja da kayan matar ka bayan ka kashe suka cusa kayan..... Barrister Zayyat yace'' objection my load Barrister Aisha tana son daurawa Wanda nake karewa lefi kai tsaye bay.. buga k'ararrawa alk'ali yayi yace'' barrister Zayyat yashe ka zama lawyer sheda ai Habubakar sheda ne yashigo cikin shari'a ne kawai ka kiyaye".. Barrister Zayyat ya sunkurar da Kai alaman girmamawa yace'' sorry my load". Alk'ali yace'' barrister Aisha kici gaba da tambaya". godiya Humairah tayi tace" my load muna da sheda da zai tabbatar wa kotu Habubakar ne yayi kisan". Kotu tace''tana buk'atan shedan". Humairah tace'' muna buk'atar Fatima Kabala Wanda aka Kira da Fatima fitowa tayi ta shiga gajeren d'akin suka jera da Izza bayan malamin kotu ya rantser da ita aka buk'aci ta gabatar da kanta tace''sunana Fatima Kabala ni budurwa Habubakar Abdulmajid Kamal ce Wanda ya maida tamkar matar sa ina da y'a daya dashi bayan ciki da muke zubar wa ba adadi a ranan 8 ga watan 3 ranan da akayi suturan dan uwan sa Haruna yaje min cikin wani irin murna Yana shikenan nayi gaba nayi gaba Nasrim za a kashe ki ni zan hau kan dukiyar ki lefin ki daya Nasrim yawan haifuwa inda ke daya ce nasan dole ni zan gajeji amma ki kazo kika saki ciki kike ta haifuwa kina so dukiya yazama na yaran ki to mutuwa zakiyi yaran naki ma biyun da sukayi saura ko basu mutu ba zasu zama iko na nine komai nasu kai dole ma nakashe wancen shegen Khafulan din kar ya zame min dan *Zaki* anan gaba Sai na kalleshi tace'' Kamal kasan me kake fada Nasrim za a kashe Nasrim kake murna sai yake gayamin ai shi kudi yafi masa kowa a gidan nan in banda uwar sa gowa ma yamutu sai nace masa kenan Kai ka kashe Agrif da yaran sa dariya ya fashe dashi yace Sosai ma kuwa ni nadauki kayan matata irin Wanda Nasrim tasaka na bawa Mama ta rufe fuskan ta taje ta kashe su kinga munyi amfani da FURUCIN TA yanzu kowa a daukan sa Nasrim ce takashe mijinta da yaranta biyu yake nan ko Mama ce ta kashe su". alk'ali yace'' Fatima kina da shedan ne akan abinda kike fada"?. Fatima tace "yallabai bazanyi k'arya ba kuma ga video dana masa asan da yake fadan hakan da nayi video ne dan na masa barazana nayi ta cin kud'in sa to sai binciken wani d'an uwan su Nasir yabi ta kaina shine yace ya tsaya naje nasamu Aisha Humairah na bata da naba ta shine tace nazo da kaina kotun na kawo karb'an wayan Fatima akayi aka cire memory aka saka ajikin tabkeken TV na cikin kotu sai ga Kamal daga shi sai gajeren wando atsakiyar bed yana ta zuba zancen yayi kudi an gama komai Video ma ba daya bane harda ranan da yakwashe kudin mommy a gidan ma yayi amfani da laptop dinsa gashinan komai afili shiru Kamal yayi Alk'ali yace'' Habubakar ka yarda shedan fatima". Kamal yace" Eh. Alk'ali yace "lawyer me k'ara kana da tambaya da zakayiwa Wanda ake zargi a yanzu ko wani sheda ko hujja".? Zayyat ya girgiza kai yace'' babu my load". Lawyer Halima Abdulmajid ko akwai wani shedan". Barrister Fu'at Jiji yace'' my load aranan 30 ga watan 7 matar Habubakar Abdulmajid ta tsinci kayan baccin ta da takalmin ta da shijab dinta Wanda iri daya ne dana Halima amma ita Halima tama bada takalmin da shijab din rigan baccin ne kawai yarage munkai doctor cin da suke binciken sun tabbatar mana da jinin da yake jikin kayan yayi dai-dai da na Agrif da yaran kuma ita Wanda ake zarki ga kayan baccin ta ahannun hukuma ba ko d'igon jini ajiki my load idan aka hada da shedan da Izza ta bayar da Wanda fatima ta bayar zai tabbatar mana da Habubakar shiya kashe mijin k'anwar Sa ya d'aura al'hakin kisan a yar uwar sa muna rok'on kotu ta duba wannan Lamar ta yankewa Kamal da duk Wanda ya hada hannu sukayi kisan nan wato mahaifiyar hukuncin kamar yanda Shari'a musulumci ta tanadar Barrister Fu'at yacigaba " Still sheda na gaba boyeyen CC camera wanda Muhammad Nasir yasaka yana hassaka komai na gidan banda bedroom da bathroom". Brr Fu'at Jiji ya bada memory ai wannan memory ana sakawa jikin kowa yayi sanyi tan take duk kule kulen da Kamal da Mama sukeyi ya bayyana har zuwa inda Kamal ya lalata CC na asali har zuwa yink'urin kashe Baba Nasuru da cewa da yayi akama Humairah dade duk muna furcin yafito nan jikin kowa yayi sanyi Humairah tace'' my load sai shidan mu na k'arshe Habubakar Abdulmajid mijina ne uban d'ana amma yau kwana 5 da yasa aka kamani akan wai sai na bada wadan nan kaya ni kuma na hana nasha wahala ahannun Wanda yabawa aikin wadan nan ciwokan jikina duk su suka min kuma sun isa sheda nasha wahala tayi maganan tana nuna ciwukan fuskan ta dana hannun ta taci gaba dacewa kuma sauran jikina ma akwai sai ayau dabara ya fadomin nace sufadi abin da Habubakar ya basu ni zan ninka musu sau 3 ko fiye da haka sufadi duk abinda suke so nabasu subar ni sai suka yarda suna fadamin kidin na basu number Yayana Adamu Abdulrahaman Abbaty nace su Kira subani shi Yana daukan wayan nace anyi kidnappin dina amma kar yagayawa kowa yakawo abinda suke buk'ata sukace million 100 sukeso atake ya tura musu kudin ni kuma nace su kiramin Habubakar Abdulmajid wanda yasa aka kamani muyi magana suka kiramin shi a video calls ga memory din video call da mukayi dashi nayi saved ta mek'e memory aka saka atake fuska Humairah da Kamal ya bayyana murmushi Kamal yayi yace'' barrister Aisha Abdulrahaman Haruna my sweetheart wife haka kyakkyawar fuskar ki ta koma kai amma banso ba ganin ki ahaka ba dama ban dauki video call din nan ba my dear ki bada wadan nan kayan a kasheki cikin sauk'i dan Ina son rushin ki yasamu salama bana so su cigaba da baki azaba kwara ki tadda Agrif da shegun yaran acan kifa da masa ranan Wednesday zakuyi bak'uwa Halima ki gayawa Agrif zanyi amarya". sai yakece da dariya cikin kuka Humairah tace'' dan Allah my dear ka temakeni nifa matar kace uwar d'an ka kuma y'ar uwar ka kada ka kasheni na k'ona kayan Ina son ka bazan tona maka asiri ba dan Allah kar kasa akasheni". dariya yasake kecewa dashi yace my wife inaga kin yarda da kirarin da baba yakubu yakemin ne ko *KAMALUDDEEN DA WAYO BA HANKALI* shine zaki min wayo irin naku na lawyer to ko baki fad'i inda kayan yake ba kin gama yawo yace kibawa Gagare wayan mek'awa Gagare tayi yace'' kai Gagare cika aiki nan da 2 minutes banason ta Kara nunfashi ni na tafi naga yanda za'a rataya ran Halima good bye I love you with all my heart my Hummee". ya k'arashe maganan yana k'ashe wayan kotu kowa sai jinjina kai yake mommy ta rasa ma mezata Dr Hafsa murmushi tayi ta gyad'a kai tace'' Al'hamdulillah rabbil izzati waassalamun alarmursalin waalhamdul lillahi rabbil alamin". Barrister Fu'at Jiji yace''my load da wad'an nan kyawawan hujjojin da shedun muke son Kotu mai alfarma ta wanke Halima Abdulmajid Haruna daga lefin kashe mijin ta da yaran ta ta hukunta wanda suke da al'hakin kisan". Alk'ali ya jinjina kai yace'' barrister Zayyat kana da abin fada".? girgiza kai barrister Zayyat yayi yace babu my load". Alk'ali yace'' bisa k'orarun shedun da aka kabatar agaban kotu kotu ta tabbatar da Habubakar Abdulmajid Haruna shida mahaifiyar sa su sukayi ki......... mek'ewa tsaye Mama tayi tace'' wllh alk'ali ba d'ana bane yayi kisan kai nice nice nasaka kayan surukata naje na kashe mijin Halima da yaran ta Kamal temaka min kawai yayi wllh d'ana bai taba kisa ba so daya yayi yunk'urin kashe Baba Nasuru amma Allah bai bashi sa'a ba wllh nice nice". Barrister Zahra da tunda aka fara fadan lefin Kamal jikin ta yayi sanyi balle yanzu da akace k'anwar Babata kuma marik'iyar ta wanda ta dauka amatsayin uwa wanda a dalilin tane ta tashi acikin gidan three brother Ita take fadin ita tayi kisa wani irin k'ara tasaka ta zube awajen atake aka dauketa aka fita da ita Nasrim girgiza kai tayi tace'' Ah Ah Mama ba ke b'ace Mama keda ya Kamal bazaku tabamin haka ba idan kun shirya hakanne dan ku kubutar Dani ni wllh bazan yarda ba Mama ke nasani amatsayin uwa ya Kamal ne gatana ba zakumin haka ba Ah ah wllh alk'ali kar ka yarda Allah sun daukane saboda so da kaunar da suke min". Kamal ya d'ago kai yace " please daddy please Nasrim tabbas Mama ce ta cuceni ita ta koyamin wannan ak'idar tun ina yaro Mama meyasa bakiyi tunanin wata rana zamu iya fad'awa cikin wannan halin ba Mama a rayuwa duk Wanda ya yarda akwai Nasara to ya yarda kwai rashin sa Mama mesa kika cusamin ak'idar hassada Mama meyasa kika saka na zama me irin halin k'abila Wanda ya kashe dan uwan sa ciki daya saboda duniya Mama kin sa naci amanan family na Mama idan Abdul ya girma yaji labarin abin da nayi bazai soni ba bazai min addua ba mama da kin bani tarbiya kamar yanda duk uwata tagari take bawa yaron ta da banzama me fuska biyu ba da banci Amanan d'an uwana ba........... buga k'ararrawa alk'ali yayi yace'' kusaurara nan ba d'akin ganawa bane d'akin Shari'a ne ganin yanda masu lefi sukayi saurin bada kansu ba tare da sun wahalar da Shari'a ba Kotu ta yankewa Hajiya Aisha kukuncin kisa ta hanyan rataya Sai Habubakar Abdulmajid wanda yasa hannun sa akayi kisan kotu ta yanke mishi hukuncin shakara 25 agidan yari da huro mai tsananin kasan cewar wannan shine babban kotu na k'asa ba daman daukaka k'ara sai idan wanda aka yanke wa hukuncin suna da wani hujja na kare kai akwai daman kawo kwarafi cikin kwararun hujja idan aka kawo kwarafi ba tare da hujja sahihi ba to akwai hukunci na wahalar da Shari'a sannan kotu ta wanki Halima Abdulmajid ta kuma bada umarnin sakin ta ayanzu akwai Tara na kazafin da akayi mata akan kamal da Hajiya Aisha zasu biyata taran dubu d'ari takwas bisa adalcin''. ya k'arashe maganan yana buga k'arfi Maga takadda yace'' my load bayan andawo daga hutun rabin awa a kwai karan Izztu Mustapha wanda teke karan mahaifin ta wanda ya kashe mata mahaifiyar ta shekara 12 da yawuce". Alk'ali ficewa yayi ta k'ofar sa sai kuma kotu ta kacame da koke koke yan sanda kuwa atake suka kama Kamal da Mama sai kuka suke kotu ta kacame cire (akwa) din hannun Nasrim akayi aka mayar hannun Mama Nasrim rik'e Mama tayi gyam sai kuka take tana cewa wllh ba Mama bace dan Allah ni kumar ni ku saketa wllh ba...... rungumota Dr Hafsa tayi tana cewa "please Halima finally su Mama sunyi kuskure ne". Barrister Zayyat ya mek'awa Barrister Fu'at Jiji hannun yace'' congratulations my friend". shima hannu ya mek'a masa suna sakarwa juna murmushi barrister Aisha Abdulrahaman ta mek'ewa Izza itama suna sakin murmushi ina tharee brother basu ma tsaya sauraron k'aran Izza ba duk waje sukayi komai rashin ima'in mutum dole idan yaga daddy saiya tausaya masa Kai har Hajja da kowa ma dan Nasrim ahannunAbbaty ya kamata suka fita da ita ahankali Humairah ta taka inda Kamal yake ta jefa idonta cikin nasa tace'' my husband *Kamaluddeen da wayo ba hankali* badan naga Baba yakubu hankali sa yatashi yana ta faman kuka ba dashi zan kir'a yamaka wannan kirare kasan kirarin mu three brother abakin baba yabubu yafi dadi Ummm Kamal na jima Ina bibiyar ka duk kanayi cikin *WAYO* da kace kana zaune kana jira nayi wani FURUCI akan Izza ka gama da ida kana zaman jiran na Khafulan to kawai dan Khafulan ya daki Abdul sai nace sai na kashe sa sai kuma reshe ta juye ko to duk aikin *NASARA NE NASARA KO GONI KAFI MUTU NASARA ME WUYAR FADANCI NASARA GOSHIN GIRGI ME WUYAR KARAU* murmushi tayi tace'' ummmm karna cika ka da surutu ana jiran ka saki na nake buk'ata dan na samu Wanda yake waje ba na gidan prison ba ai ni naso da bakaga ratayar NASRIM ba naga naka amma badamu zamuga na jatuma kace da ita ta gaida habila da hamana da fir'auna". cikin muryar tausayi yace'' Humairah Ina son ki bazan taba sakin kiba dan haka dole ki jira na fito i love you with all my heart ya k'arashe maganan yana murmushi". kamashi yan sanda sukayi aka fice dashi haka Mama ma tana ta kuka tana cewa abar ta zatayi magana da mijin da Mommy da Nasrim amma Ina basu bata dama ba dak'er aka cusa Nasrim cikin mota sai ihun a bar ta taje gun Mama da Kamal take wllh basu bane sun daukawa kansu ne dan su kub'utar dani'. haka de aka jata akasaka ta cikin mota *Three brother house* Big problem kenan Daddy daga kotu bai zo gida ba sai tes daya turawa Hajja na yawuce jidda kawai wajen Abu Mommy zaune ta rakka uban tagumi duk wanda suke zuwa murna ko nace jeje ba abari suna shiga ciki inba najiki sosai irin su Dr Hafsa ba kuka take sosai tayi tayi ta shawon kan Nasrim amma ta kasa to yanzu duk ranan da taji ta samu labarin abinda Nasir ya mata zata ce gwara na Kamal kenan gashi dole Nasrim tasan hakan tunda magana ya bazu ko ina kuma dama Kamal ne yabaza afili ta sake cewa Allah ya isa Nasir Nasrim da dan shegen ". Ayman ne ya shigo shida Aliyu bayan sun gaisa da Mommy Mommy tace''Ayman Aliyu Allah ubangiji ya muku albarka yasa kufi haka kune kuka zame min komai ku kuka tsaya min da nemam lawyer alokacin da kowa ya guje mu". Aliyu yace'' Ah Ah Mommy ai duk wannan aikin Nasir da Hajja ne shi ya tsaye muku Mommy Nasir yasha wahala Sosai Nasir ne ya saka aka temakawa Nasrim asan da take gidan prison Hajja ita ta fara gano waye kamal Hajja ita t.......... katse sa Mommy tayi da cewa '' Ayman idan kana son farin ciki na kar ka sake min maganan Nasir yanzu ni neman da zan masa na shiga kotu ne zan makasa kotu duk abin da yamin wllh bazan yafe masa ba...... Hajja da take shigowa ne tace'' nima zamuyi zaman kotu dake ki nemonin jikana idan yazo gida sai ki makasa kotu Allah yabawa ne sa'a sa'a yo mu agaya mana kotu kotun sukutum na haifa eshe *To masoya mu hadu a 23 dan jin dame Hajja ta temaka ya Shari'ar Izza da babanta zai kasan ce Mama da Kamal zasu yarda da hukuncin* *Ina Nasir* *Kamal zai saki Humairah ko sai dole tajirashi kamar yanda yace* *Allah sarki Zahra na miki kuka* *Bj* *FURUCINA NE* (rikicin babban gida) *_________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *_________________________________* [4/8, 1:48 PM] Batul Adam Jattako: *FURUCINA NE* ( _rikicin babban gida_ ) *NA* *BATUL ADAM JATTKO* *23* dariya Ayman yayi yace "Kai Hajjar mu Allah yabar mana ke wato ke ba alk'alin bama kotun sukutum kika haifa". "yo ai gaskiya ne Aymanu ya zata koremin jika kuma tazo tana wani cewa ita zata kaishi kotu ai ga hanyar kotun". ta k'arashe maganan tana zama a k'asa sunkuyar da kai Mommy tayi Dr Hafsa tace'' Hajja muna godiya sosai da kokarin ki Allah ya K'ara lafiya da nisan kwana". Ayman ya kalli mommy yacigaba " Mommy kiyarda Nasir shi yayi komai kinga da farko Hajja ce tagano gomai". Hajja tace'' ai ita bata masan me take ba yo ai dana biyewa fañna da duk zuri'a ta ba shafe tareshin su Aisha zatayi ba y'ar matan nan gata de mutum a furka me rai yana kallo ni mairo". Dr Hafsa tace'' Hajja to ya akayi kika gano ta".? "Ummm ai tun ran da nace sai na hada auren Izza da Haruna naga murna a tattare da ita kuma abin da yafi dauremin kai yanda Nasrim tacigaba da haukan bataso amma Aisha shiru kakeji bata ce komai ba bayan Nasrim maganan ta kad'ai takeji da kaina na Kira Aisha nace tabawa Nasrim hakuri ayi abinnan yariyar nan Izza tana da biyayya kuma wllh tana mutuwar son Haruna tun tana takaba na gano hakan har mafarkin sa take duk Ina sane to kawai dan jikata ce agidan sai nazama meson kai bayan ALLAH yace kayi temako a inda kakeda ikonyi musamman sunnan manzon Allah ba Lada zan samu ba amma Aisha da alaman ma zuge Nasrim take daga nan nagano sai abin da yasa zargina yasake k'aruwa kuma ranan da Haruna ya mutu Nasir yazo yake gayamin shifa yana tunanin ba Nasrim bace tayi kisan shiyasan duk Wanda yayi kisan akai abinda yake son kuma ganin bayan Nasrim yake son yayi shine yayi kisan a kan gab'an FURUCIN ta nace masa to wakake zargi kai tsaye yace Kamal tare dabani hujjojin da misalai sai yace inde da gaske Kamal ne to Hajja ba makawa akan dukiya zayyi hakan dan Kamal b'arawo ne sosai bashida Amana bama ganin dai-dai a ai'kin sa kawai muna kyaleshi ne sabo da ai yafi wani abin duniya awajen mu sannan idan Kamal ya tara dukiya mezayyi dasu ba three brother zai kawo ba zuba basa idon da mukayi yasa yana yanda yake so gsky Hajja ina mugun zargin sa da boyeyen hali yanzu de nasaka an saka CC TV na boye da farko dole sai mun sako daddy a binciken ke kuma abin da nakeso dake kinuna bakya goyon bayan Nasrim da Mommy ki dage akai abin kotu sannan ki tunzura Mommy ta fadi wani abun sai kawai daddy ya saki Mommy kinga idan shi yakeyi idan aka saki mommy jikin sa zanyi sanyi idan dan dukiyar Mommy yakeyi zamu gane Tode haka akayi kuma yana kunna bin CC TV din Ina ganin duk munafurcin da Aisha da dan ta suke kullawa sati 3 da rasuwan su Agrif Humairah tazo min da kuka tana cemin wai Kamal ne yayi kisan kayan ta yasaka yayi kisan gasunan yanzu Faiza mai'aikinta tafito dasu anan muka sake tambatarwa Nasir yace takoma tayi zaman ta kamar bata gani ba komai yazo k'arshe amma sheda mukeso dumu-dumu anan Nasir yace to muma Hajja murikita musu tunani ta hanya amfani da FURUCIN Mommy muce tabaki guba a gefe daya akasaka guban aka bani naci gefin da ba guban sannan na gauraya na fara birgima ai kunga yanda hankali Kamal da uwar ya tashi suka fara tunanin basu kad'ai bane masu kulla kullan kuma kunga ita Fanna ta tsira da bamuyi saurin amfani da FURUCIN nata ba su zasuyi dashi kuma ni zasu kashe alokacin tunda nice Fanna tayiwa FURUCI a kaina NASIR da iyawan sa da Basiran sa saida yabi diddigi ya kawo wani babban malami mai suna malam K'aura ashe bokane shi yake koya musu komai ashe tun Aisha tana budurwa take aiki akan gidan nan tayi ta asa sosai amma mun rufawa malamin a Siri tunda yamana alk'awarin ya

Chapter 25 of 40