Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
maganan Nasir ya fisgoshi yayi bathroom dashi sai da suka shiga yaturo kofar yace "kasan ni ba tsoro nake jiba idan kayi magana ko kamusa to dai dai yake da tonan asirin komai dama ni shi nake jira........ ji sukayi Nasrim tana wani irin buga k'ofar kamar zata karya tana cewa " ya Agrif kasan wacece Nasrim awajen kishi amma kamin haka kashigo min da k'aruwa har d'akin aure na ka manta nace duk randa kaso wata to za ayi biyu babu wllh kashe ku zanyi". Agrif yana ji yana gani har muryar Nasrim ya dashe amma ba halin yafita lekawa yayi ta bulin mukuli yaga hannun Nasrim har yakumbura dan bugu jinginuwa yayi jikin kofar yana maida numfashi shi kam Ina ma zai mutu yahuta da wannan rayuwar Ina ma zai iya kisa za zai kashe Nasir kawai ya huta in yaso shima akashe shi sai de shi ko Marin mutum bayason yi balle ya illata mutum ko cinnaka bai taba kashewa ba". azabure Agrif ya mek'e jin wani irif yana cewa wllh nas...…... *To masoya mu kasance cikin pages na gaba 10 Ina jin dadin comment din ku ngd sosai da soyayyar ku* *Taku b JATTKO* [4/8, 1:47 PM] Batul Adam Jattako: *FURUCI NA NE* *BATUL ADAM JATTKO* *Marubuciyar* *DAMA TA* *AMFANIN SOYAYYAR* *NOW* *FURUCI NA NE* *10* jin shiru yasa Agrif lekawa ganin Nasrim yayi akwance plates kamar bata numfashi cikin wani irin razana yayi kan Nasir yana cewa "wllh Nasir ni zan zama ajalin yaruwar ka idan har Nasrim ta mutum wllh Kai ma zaka mutu ka kasheta ka kasheta Nasir..... Nasir fizgewa yayi a hannun Agrif yabude k'ofar ba alaman numfashi atare da ita ga hannun ta duka biyu jini yakeyi dan yatsar roban tama ya cire acan gefe da sauri ya d'agata cak yayi gaba da ita cikin hanzari yake tafi ya Agrif naya binsa abaya har wajen parking spot duk da dare ne a kwai driver da yake idon sa biyu dan duty duty sukeyi ganin Nasara yasa da sauri ya mek'e jikin sa na rawa ya bude a katin a jiyan mukullayen motan yana ganin motar da yaga Nasir ya tsaya ajikin sa cikin saurin ya dauko key din da sauri ya nufi motar Yana budewa Nasir jiki na rawa yasa Nasrim aciki Agrif zai shiga Nasir ya masa kallon sama da k'asa alaman dubi halin da kake ciki sai a sannan Agrif yaduba jikin sa ashe daga shi sai towels ne komawa yayi da baya cikin sauri. duk gudun da drive yakeyi amma Nasir sai fada yake masa yana danna k'irjin Nasrim dan yabata temakon gaggawa shi yamafi jin abin cikin ta idan akace cikin nan ya zube to ya zanyi tabbas k'aryasa ta k'are dole Nasrim da Agrif zasu ci bulus yana nadaman meyasa yayi haka ma bayan shi likita ne yasan k'a'idojin renan jiki a take gumi yafara yanko masa addua yadin gayi yarabbi ka kare abinda yake kin ta ka karemi gudan jinina dan cikar burina idan zai zube ya Allah ka hada har da ran ita Nasrim din ka dauka na huta nakoma mutum sak yarabbi ka temakeni ko da suka isa hospital din bai yar da da aikin Dr din ba da kansa yashiga da ita emergency room sai da ya tabbatar ta farfado daga suman ya mata alluran bacci ya duba sosai komai normal tukun ya goge gumin fuskar sa ya yarfa mata yana mata mugun kallo afili yace "akaro na farko zanso kirayu saboda d'ana badan shima da daga wannan suman kin zarce kenan." yafita tare da rufo k'ofan da k'arfi a k'ofar emergency din yasamu Agrif a sugunne yana ganin Nasir ya mek'e tsaye rai amugun bace yace "last Wornig da zan maka daga yau kada ko hannu kaya sake guskuren taba jikin matata mahaukaci dabba d'an akuya k'azami irin ka mashayin giya mazinaci". tsororo Nasir ya tsaya yana kallon Agrif tunda yake a duniya ba ataba masa zagi haka ba saide shi yayiwa mutum irin wannan zagin amma yau shi Muhammad Nasir 3 A full a keyiwa irin wannan zagin". manyan idon sa da yagama rinewa kalan ja yaware akan Agrif amma tsabar b'acin rai yakasa furta komai kawai gyad'a kai yayi yayi gaba driver yana ganin sa yamek'e tsaye amma hannu kawai ya mek'e masa alaman yabashi key gudu yake a mota sosai har ya k'araso gidan iris yarage ya buge Aminu sojan da yake on duty a bakin get ajiyar zuciya Aminu yasauk'e afili ya furta " Al'hamdullah daka kashe banza". bibbiyu bibbiyu yake taka steps din har yakarasa hayewa har cikin bedroom dinsa waya ya dauka cikin b'acin rai yakira Ansher khan yarinyar da yazo da ita ita take masa shidima yar India ce Ansher tana ganin Nasir ahaka gaban ta yafadi ta fara addua Allah ya kubutar da ita a duka da cin zarafin sa amma bai mata magana ba sai jefa rabin jikin sa iya kafadun sa yayi akan gado iya gugun sa kuma a k'asa ya dafe kansa da ya kejin kamar zai rabe gida biyu kalaman Agrif ne yake dawo masa mahaukaci dabba d'an akuya k'azami irin ka tafin hannu sa yabuga agoshin sa afili ya furta yanzu zaka fara ganin halin dabbobi yanzu zaka zan a mahaukanan ma akwai nagaba yanzu ne zaka san Nasir mashayin giyane yanzu ne zan k'azance". ya k'arashe maganan yana nunawa Ansher ta kalmin sa alaman tacire Ansher duk da batajin me yake fada tabbasa tasan ransa abugun b'ace yake dan haka jiki na rawa ta fara cire takalmin sa sannan sa tacire masa wandon jis ta barshi daga shi sai boxes mek'ewa tayi tayi hanyar bathroom dan hada masa ruwan wanka ***************** ahankali take bude idon ta har taware shi akan Agrif da yake yake rik'e da hannuta me drip daya hannu kuma ya dafa kansa jin kamar tana motsa hannun ne yasa ya bude Idon sa wani irin kallo tsana yagani a idon Nasrim ahake wani da bara ya fado masa ya fashe da wani irin dariya Nasrim kallon sa tayi cikin muryan ba wasa tace'' kayi me isar ka wata k'ila shine dariyar ka ta k'arshe aduniya so nawa nake gaya ma zan iya yafe komai banda kishi Agrif ko a ina take yau sai tasan tayi da 3 A full tayi da three brother ..... dariya Agrif ya cigaba dayi kawai ya zaro wayan sa a cikin aljihu sa yafara danne dannen sai gashi ya danno wani gu ya fara rubutu duk abin da yarubuta sai wayar ta fassara da magana kuma da muryar macce yana cigaba da dariyan ya mek'a mata wayan yace " gata ki hukun ta ta ita ce kishiyar" taki. itama dariyar tayi tace'' Allah Yaya ka cuceni amma zan rama'. ta k'arashe maganan tana karban wayan ahanun sa itama rubutun tayi tana rubuta abu yana fassarawa tajuya muryar namiji ta juya na macce kuma yare kusan dari ukku ne aciki duk Wanda kazama shi zai maka kallon sa tayi tace'' my heart Ina son wayan nan yayi kyau sosai". ''kin samu jeki na baki". yace yana cigaba da dariya yace "wai dama da gaske ne zaki iyayin komai akan kishi". ajiye wayan tayi tana mek'awa zaune tare da cire drip din hannuta tace'' ai wllh inde akan kishine zan iya yin abin da yafi haka ma na kasheka na kasheta a fanshi ranku da nawa na yarda". sauke numfashi yayi yana girgiza mata kai yace " Ah ah my dear kidena irin wannan FURUCIN bana salihan bayi irin ki bane kefa malamace kuma lawyer ce nasan kin san illar irin wannan FURUCIN ki dena abin da nasa ni Haruna nakine har abada bazan miki kishiya ba". da asuba ya nemi sallama suka koma gida ba wanda yasan a asbiti suka kwana da safe an hallara a dining room Hajja ta kalli kowa tace'' wai shi wancan bayahuden me yake cine ko yamanta dokar gidan nan ne dole mutum ko bazai ciba yazo ya i'bi gaisuwa". Abbaty yace " ki kirashi mana" Kamal yana danne dariyar sa yace "ah ah baza ta iya ba jiya sunyi fada Humairah ma danne dariyar tayi tace kai jiya naga masifar ya Nasir ashe yana dogon magana kunga yanda ya tsuye Hajja kuwa tayi fiki fiki da ido.... "Abdulmajid a gaban ku yaran nan suke cin mutumcina kuna kallo suna min dariya". Abu yace kai Kamal meye haka Humairah uwar tawa kike yiwa haka ashe duk abinda Hajja kake cewa kun mata kunayi". Kamal yace' sorry Abu". Hajja tace" au da baku yarda ba ko to Wllh yanzu ba yauba Kamal tashi kabar min parlour na kai da rubbebiyar matar ka Abdulsamad ne yagina min ba uban ka ba kuma bana son k'ara ganin dogin k'afar ka a bangare na Kai badan kaci albarkacin sunan uba na ba wllh a gidan ma gaba daya zan koreka ita kuma sililiyar matar ka taci albar kacin cikin jikin ta". shiru Kamal yayi yana sa kansa a k'asa daddy yace " me kake jira tashi kafita ke kuma Humairah karki k'ara Kamal ya fice yana dariya k'asa kasa yace muda za abamu encin kowa yazauna a part dinsa ma aida yafi mana wannan tsarabe tsaraben bayan angama breakfast mommy ce tafara tashi dan ko wanka batayi ba gashi zata fita wajen aiki Hajja ta kalle ta tace'' Fanna ki koma ki zauna ina da maganan". Mommy komawa yayi ta zauna "Fanna jiya bayahuden d'anki duka na ne kadai bayi ba anan falon ya karemin tas akan na gaya masa gaskiya musamman akan shigo mana da fisararrun matan turawa da yakeyi gida toni bazan d'auki wannan iskancin ba tun wuri ki gaya masa nayi magana da babban murya yane mi matar aure da zata masa dukkan shidiman sa tunda yanace sai mata ne zasu masa komai wai bayason aikin namiji shiba waliyi ba dole wata rana wani abu ya gifta tsakanin su dan haka keda yake ganin ki da gashi to kigaya masa na basa nan da wata 6 idan bai samu matar aure ba to ni ina da wanda zan hadasa aure da shi Maryam din Bellon Dardum zan bashi dan tana da kalan tur............. Nasir da yake shigowa ya k'arashe mata maganan da cewa "in yaso nayi abin da zanyi ko? Yana kallon cikin idon Hajja ya zauna a kujeran da yake facing da ita yaci gaba "ni Nasir zaki yankewa hukunci Hajja kinsan abin da kike fada kuwa? ni d'an kine ubana kika Haifa bani ba kuma yanzu yana ina bayanan dan haka Allah da ya hadamu yaraba ikon ki da isarki ya tsaya a iya yaran ki da su Aiban da suka ga zasu iya d'aukan amma ni ni nake yankewa kaina hukunci rayuwata ce idan naso na kwana da mata dubu meye naki baki da Lada baki da zunubi kuma ba kabari daya za abunne mu ba kin zauna sai zafgawa mutane iko kike ai ba mommy zaki aika wajena ba ni ya kamata ki kira kisa idon ki cikin nawa ki gaya min ni bayahude ne kiga aikin yahudawa... Abu ne yayi k'arfin halin dakatar dashi haba Nasir Hajja fa uwace agaremu idan ba idon uban ka ai mu gamu bamu can canci kazauna kana fadan haka a gaban mu ba........... da sauri ya katse Abu da cewa "saurara Abu ina mutuk'ar jin nauyin ku kai da daddy amma bana son ana shiga rayuwata zan iyayin komai me yasa da Hajjar take fadan magan ganun a kaina bakayi mata magana ba yanzu zata bude baki tacewa d'an ka Agrif bayahude ne agaban ka ko zata ce masa mazinaci saboda ni ba ubana bata shayin komai Kai tsaye ta furta min duk b'atan cin da yazo bakin ta... duk kowa yayi shiru yana sauraron sa ko kyakkyawan motsi bameyi sai Nasrim da tunda yafara take zaf ga masa wani irin harara kasa daurewa tayi cikin b'aci rai tace'' Abun kake gayawa magana haka wllh mutum idan bai daraja iyayen mu ba muma bazamu daraja shiba idan kai ba bayahud.... da katar da ita Agrif yayi da cewa " kece me baki ki bari ya gama wannan alama ne da yake nuni da Koda uban sa Abdulsamad yana raye zai iya c..... bai k'arasa ba yaji wani irin sauk'an mari a fuskan sa cikin b'acin rai Abu yace " lalle Agrif a gabana kake K'iran sunan dan uwana wannan yazama na farko kuma na k'arshe... dafa k'unci Agrif yayi yana kallon Abu shi tunda yake Abu bai taba daura hannu akan sa ba sauk'owa yayi k'asa yazuba guiwowin sa cikin sanyi murya yace"Abu kayi hakuri wllh ban fadi haka dan naci zarafin Abba ba sai dan dakatar da Nasrim dan nafi kowa sanin waye Nasir amma dan Allah kuyi hakuri". Hajja tace'' bawani kai yanzu Agrif a gabana kake kama sunan Abdulsamad yoko uban ka Abdulrahaman ya isa ya kama sunan Abdulsamad kai tsaye kowaye yamuku Kai Yana dawa kuke fantamawa k'unci kun batse da gumin sa shi yaje ya kwanta dama bazaku ambace shi da al'kairi ba sai Sherri ni kullum d'ana da al'kairi nake ambaton sa.. nan ko Hajja tafara zagin Agrif duk haushin Nasir ta huce akan sa daga k'arshe Abu yabata hakuri dak'er ta hak'ura Nasir ya doka tsaki ya fice ******************** Nasir yana zaune abakin gadon mommy tana ta shirya masa kayan tafiyar sa dan yanzu ansamu cigaba a nasiyar da mommy ta masa yadena yawo da mata sai da tagama hada masa kayan tazo ta zauna a kusa dashi tayi shiru tana son tayi masa magana tana tsoron abinda zai biyo baya gane hakanne yasa ya ajiye wayan hannun sa ya fuskan ceta sosai yace "mommy akwai damuwa ne? numfasawa tayi ta gyad'a kai". "kamar na me ba?". numfasawa tayi tace "my son dama akan maganan Hajja najiya ne my dear nima gaskiya burina kenan naga kayi aure kaga fa Aiban kanin kane amma yanzu matar sa har takusa haifuwa Agrif sa'an kane yayi aure Kamal sa'anka ne yayi Ayman Ramadan aliyu duk abokan....... "da kata Mommy wai meye naku na sai nayi aure ne? Ummm duk su Wanda kike lisafamin zuciyar mu daya dasu ko ra'ayin mu daya ne wai meye acikin auren banda bak'in ciki da damuwa gaskiya mommy kiyi hakuri ki dena min wani zance aure kawai ki din gamin adduar idan Allah yayi zanyi zanyi". "shi kenan my Son". tayi maganan cikin sanyi murya Nasir jikin sane yayi sanyi bayason ganin mommyn sa cikin b'acin rai hannuta yakama yace' mommy ki kwantar da hankalin ki inde aure ki ke so zanyi kuma ko banyi ba kin kusa rike jinina insha Allah". arazane ta ware idon ta akansa tace'' ban gane ko bakayi aure ba kuma kace na kusa rik'e jinin ka?". murmushi yayi yasaki hannu ta yana mek'ewa tsaye zaunar dashi tasake yi cikin raunen niyar murya tace'' baka ban amsa ba Nasir kamin alk'awarin bazaka aikata Zina ba fa".? "Mommy kenan ai shi halin mutum saka riga yacire yafishi wahalan canzuwa". " cikin in nina tace'' Nasir kana nufin kazama mazinaci". "kai mommy bincike fa haramun ne kisa a ranki nayi so daya ko biyu kuma yazama na k'ashe amma mommy dan Allah kimin addua Allah yamin maganin damuwata". Mommy mek'ewa tayi tsaye tace'' nashiga ukku ni Fanna Nasir nasan Kai ba mak'aryace bane mai fad'an gaskiya duk d'acin sane amma ban sanka da karya ba me yacanza min kai".? ganin mommy cikin damuwa yace "Kai mommy idan baki sanni da k'arya ba ai kin san ni dayi miki wasa bazan taba zanzawa ba aure zanyi insha Allah". ajiyar zuciya mommy ta sauk'e tace " Al'hamdulillah wllh har kabani tsoro".? "ammm mommy da Baba Nasuru fa zan tafi akwai wani likitan kwakwalwa kwararre ne da namasa bayani yace " in kai shi ko za a dace". cikin jin dad'in tace''yawwa my Son dan al'barka Allah yasa adace burina kenan naga suwaye iyayen Halima". "Ameen". Yace tare da fara tafiya mommy ta dau jakan sa dawasu tar kacen sa ta tafara binsa abaya sai da suka fito babban parlou Zahira tayi saurin k'arban kayan hannu mommy ganin har ya doshi parking space yasa mommy tace'' my Son ba zakayi sallama da mutanen gida bane bama ku gaisa ba ai tun da baka fito breakfast ba ". dan yamutsa fuska yayi sai kuma yayi part din Ummu ita kuma mommy ta zauna a compound jiran sa cikin takun sa na isassun maza ahankali ya murd'a handle din bakin sa d'auke da sallaman na nasa naciki ciki Wanda bakowa ne yakeji ba balle a babban falo irin wannan Agrif yagani da Nasrim suna baje akan kujera there'siter cup ne ahannu sa da cokalin a ciki yana kaiwa bakin ta kallo daya yayi wa Nasir yajuya yana iban kunun madara me kauyi yana kaiwa bak'in Nasrim juya kanta tayi cikin shagwaba tace'' Allah Yaya nide ciki na zai fashe ". " Please my Honey daga wannan shikenan". "to nide sai kamin alk'awarin zaka shafa turaren first night din nan Allah wancen bashi bane". Agrif dan juyawa yayi yana kallon gefin da Nasir yake a tsaye kamar ma bai san da suba nanko kunne sa yana wajen ya juyo yace " idan kina tare dani baki da damuwa zan shafa". dariya tayi Wanda yasa kumatun ta duka lomewa ta wangala baki shi kuma ya zuba mata murmushi Nasir "yayi afili ya furta zanyi maganin ka yanzu". yanda bazasu jima Yakalli me'aikin Ummu da take ta jera masa sannu yace' Ummu fa".? cikin in nina tace'' tana falon sama". cikin sauri ya fara hayewa steps din Ummu tana zaune ana saka mata lalle ak'afa tana ganin sa ta washe baki tana cewa " d'an mommy shirin kenan". zama yayi kusa da ita cikin ladabi yace " Ummu zan tafi". " to Nasara ko gani kafi mutum sai bayan shekara ko ". murmushi yayi yace " gamu nan de". ya k'arashe maganan yana mek'ewa ita kuma Ummu sai fatan alkairi take masa har zaifita kuma sai yajuyo yace' Ummu dan Allah kiyiwa Agrif magana yafara wasa da aiki har nayi mai magana bai jiba yanzu tare yakamata mukoma amma yace a a". Ummu tace'' Zainab ba kince Agrif yana falo ba kiramin shi "baka ban amsa ba meye dalilin ka na wasa sa aiki".? shiru Agrif yayi a zuciyar sa yace tanan kuma ka bullo afili kuma yayi saurin cewa "Ummu kiyi hakuri Nasrim ce bata d'an jin dad'in kuma gashi tana buk'an tan temako na". jin jina kai Ummu tayi azuciyar ta tace gaskiya ne tunda ana auren yatafi yanzu kuma gashi ko sati bayyi ba yakoma zai iya shiga hakki ta gaskiya amma ya suka iya badan makaran ta ba da sai suna tafiya da matan su afili kuma tace'' hakane sai de kuyi hakuri na dan lokacine idan sun gama makaranta kowa yana iya tafiya da matar sa . ta kalli Nasir ta cigaba to Nasir kaji uzurin sa amma hakan bazai hanashi tafiya ko da zuwa gobe ne ba tunda yanzu bai Shirya ba goben ya bika". Nasir bai so hakan ba yaso yatafi k'afar sa k'afar Agrif yanzu idan ya kyale shi tunda yau baya nan Agrif zai iya kasan cewa da Nasrim amma a afili kuma yace"shikenan Ummu amma daga goben kar ya kwana anan akwai aiki acan yayi maganan yanayin gaba ko adawo lafiya masu aiki da Ummu baya amsawa a falo ya tarar da Nasrim tana bacci kallo daya yayiwa wajen ya fice Azuciyar sa yana cewa yanzu zaki huta na dan lokaci kafin ki haifamin yaro na insan matakin d'auka akan ki adaren ranan zaune suke a parlour Agrif sai operation din laptop din sa yake Nasrim da tagaji da jiran sa kawai sai tayi mek'a cikin yamutsa fuska tace'' my dear bacci". d'ago kansa yayi yana kallon ta cikin tausayin kan su yace'' zaki iya zuwa ki kwanta zan dan k'arasa wani dan aiki ne". Nasrim kallon sa tayi gaskiya zuwa yanzu kunyar ta da kawaicin da take masa yafara takurata gashi gobe zai tafi yau din ma ba alaman zai kasance da ita bata San sanda yafurta "na gaji na gaji". afili ba ahankali ya janye hannun sa kan laptop din ya d'ago yana kallon ta idon sa cikin nata sunkuyar da kansa yayi ganin bazai jurewa ganin taba amma duk da haka yafi tausayi kansa dan aganin sa yafita shiga takura bak'aramin dauriya yake ba wajen control din kansa awajen ta sosai yake buk'ata kasan cewa da ita yana cikin wannan tunanin bai Ankara ba yajita a jikin sa sosai ta cusa kanta cikin cinyoyin sa tana gyara kwanciyar ta tare da daukan k'afafuwar ta ta d'aura a saman kujera there'siter lumshe ido tayi tana sauk'e numfashi asan da tajita a cikin lafiyeyyen cinyoyin sa shima a nasa ban gare kasa control din kansa yayi wani irin har bawa gaban sa yayi take jikin sa yafara rawa cikin in nina yace " Nasr Nasrim dan Allah ki sassautawa zuciya ta da gan-gan jikina sha'awar ki zayyi ajalina zai sa nasa b'awa alk'awarin da na dauka miki bazan taba kusan tarki ba har sai kin yarda ba sha awarki nake ba........ sai kuma yayi shiru bude Ido tayi tana kallon sa can ta numfasa tace'' nifa Yaya Agrif ban San meye naka nayin wannan alk'awarin ba bayan ni da ka daukarwa ban amince dashi ba idan na amince zan shiga hakkin ka" . "ah ah Nasrim ba wani hakki na da yarage baki ban ba kin min komai kawai de nayiwa kaina alk'awarin hakan ne". afusace ta tashi zaune cikin b'acin rai tace'' bawani kan ka da kayiwa alk'awarin kayiwa mala'ikan naka ne wancan bayahuden Wanda tun randa kafada nagane ba wai dan Yana sona ya maka fadan ka kusanceni katafi ba nasan so nane kawai bayayi najima da sanin bayason ka rab'e ni kai nafa san ba kai ba duk wani abu da zai min dad'i arayuwa bayaso mutumin da yarabani da uwar data haifeni zai so wani abunda yasoni ne ya hanaka mu kasance tarene saboda bayason mu samu kwanciyar hankalin idan ba haka ba meye ruwan sa da shiga tsakanin mu wllh bana son sa bana son sa nida shi bazamu taba hada wani halak'a ta y'an uwan taka ba idan kaga munzauna dashi to agaban Allah ne ya mana shisabi". ta k'arashe maganan tana mek'awa tsaye shima mek'ewar yayi yakamo hannun ta cikin kalan tausayi yace "come down my dear sister wllh bawai dan shi bane ..... katse sa tayi da cewa "Kai da bak'in ka kagaya min haka kuma ai naji da kunne na kana cemasa ka dauki duk wani umarnin sa amma ban da saki ba zaka sakeni ba duk da ni ban yarda iya dokan da ya kafa maka bane baza arasa wani ba". ta k'arashe maganan tana fisge hannun ta tayi gaba zubewa yayi awajen yana maida numfashi afili yake furta Allah ya isa Nasir wllh kashiga hurumina ita ma Nasrim tana shiga d'aki ta kulle kanta ta fad'a gado a yau kam ta kai k'ololuwar buk'ata amma tayiwa kanta alk'awarin ba zata sake nunawa Agrif ba zata zuba ido taka k'arshen sa sai de haka kawai taji tana son sanar da Humairah ko zasu samu wani mafitar dak'er bacci ya dauketa da sofe bata fito ba sai da lokacin breakfast yayi ta Shirya cikin wani riga da siket na atumfa bak'i me manyan ganye ja d'inkin pitate ne yayi mutu k'ar zama ajikin ta takalmin ta plate ja ta taura Jan mayafi tayi kyau sosai ahankali take taka steps din atunanin ta zata ga Agrif a parlour tunda baya d'akunan sama sai de taga wayam har zata juya ta shiga small parlou sai taga wani takanda akan center tables ahankali ta k'arasa ta dauka "Kan uba!!!!!. tace a lokacin da takarasa karanta sak'on Agrif kamar haka _my wife afuwa nayi tafiya akaro na biyu batare da sallama dake ba dan Allah kiyi hakuri nima ba haka na tsara mana rayuwar muba amma zai wuce_ ******************* bayan wata 5 Allah ya sauk'i Izza lafiya ta haifi yan biyu duk ka mata zo kaga murna awajen Hajja da mutanen gidan amma Izza da Baban ta basu so haka ba sunso samun maza aranan suna yara sukaci sunan Ummu da mommy

Chapter 13 of 40