Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ƙayatattcen murmushi ya fara faɗin. "Zeezeena zo ki sha lemun da kika yi ta tuna mun a waya na saya, sarkin son lemu". Khadijah ce ta ce. "Baba ni kuma ina inabi na?". "Mamana na sayo maki kema ai, ban manta ba, duk kuzo ku sha". Ya yi maganar yana yankawa Zainab lemun zakin da ya ɗauko. Yana yanka lemun yana kallon cikin plate na fruits ɗin, idanuwansa kamar suna yi mashi gizo ne, dan bai ga inabin Khadijah a ciki ba, kuma itace ɗaya ya sayo inabin dama, wa ita kaɗai, ita kaɗai ya sayawa, dan ita kaɗai take shan inabi a gidan, Zainab lemu take so, ita kuma mamansu Apple, kowa da abin da ya fi so, shiyasa idan ya tashi saya yake sayowa kowa nasa, baya manta na kowa, shi kuma kankana yake sha shi da Haidar, sun fi sonta. "Maman Zainab kin rage wasu fruits kin saka a cikin fridge ne?". Ya yi maganar yana miƙawa Zainab lemu. Tana kan zuba masu white rice and beans ɗin a cikin plate ta bashi amsa da. "A'a ban rage komai ba, dukka fruits ɗin ne kenan". Dawo da kallonsa a kan Haidar ya yi kafin ya ce. "Haidar malam Sani bai saka mana inabin Khadijah da kuma abarba ba". "Any kuwa? Kamar fa ya saka a ciki, naga lokacin da ya ɗauko ya saka". Haidar ya bashi amsa. "To amma ya babu a ciki?". Baban ya sake jefa masu tambaya fuskarsa da alamar damuwa, dan shi mutun ne da baya son ko da sunan wasa ƴaƴansa su ji cewa kamar yana yi masu banbanci a tsakaninsu, da yasan babu inabi da ba zai bawa Zainab lemun nan ba har sai ya sake fita ya sayowa Khadijah nata, sai ya dawo ya basu a tare, dan komai a tare yake yi masu, yana nuna masu cewa dukkansu ɗaya. Shiru maman Zainab ɗin ta ɗan yi na ƴan sakani kafin ta ce "E akwai inabi fa, dan na ɗauki itace ɗaya ma na haɗawa Hauwa a cikin fruit dana ɗeba mata". Da sauri ya ɗago kai tare da watsa mata wani irin kallo mai nuni dacewa meyasa zata yi hakan?, domin kuwa inabi guda ɗaya ya sayawa Khadijah ita kaɗai. Amma duba da yaran suna nan sai bai yi magana ba, ya yi shiru, har cikin ransa sam bai ji daɗim hakan ba, sai ma ya ji duk abincin ta fita mashi a ransa, ya ji babu daɗi sosai, ya sayowa ƴaƴansa abu ta wani ɗauka ta kyautar kamar ya aiketa, in da ma kankanarsa ta kyautar ba zai damu ba, amma na Khadija takwarar mamansa guda, gaskiya bata kyauta mashi ba. "Kiyi hakuri mamana, bari Yah Haidar ya je ya sayo maki wani yanzu nan, jeki ɗaki ki ɗauko kuɗi a wajen drawer ta ki kawo mun". Ya faɗa cikin sanyin murya, daga jin yanayin maganarsa kasan sam bai ji daɗin abin da maman nasu ta yi ba, ita ma kuma ta lura da bai ji daɗin ba, duk sai ta ji babu daɗi ita ɗin ma. "A'a ta bar kuɗin da akwai kuɗi a jikina bari na sayo mata da shi". Cewar Haidar. Taɓe baki maman Zainab ɗin ta yi tana mamaki, yau Haidar da kyauta, sam baya taɓa masu kyautar ko Naira biyar ɗunsa, idan kaga ya bawa su Khadijah kyautar wani abin ci ma ba kuɗi ba to wlh sai idan babansu yana nan, eyes service gare shi, in babansu baya nan ko tsinkensa basu ci. Allah mai iko, kaga dayawa idan kana raye. Miƙewa ya yi ya fice daga parlourn, sai hakuri baban nasu yake ta bawa Khadijah, ta dai ce mashi to, amma ji take kamar zata fashe dan haushi, sai ta ji ta kara tsanar wannan Aunty Hauwar. (Masu suna Khadijah idan suka tsaneka ka shiga uku😅 kome zaka musu ba zasu ga farinka ba😅 in sun riga sun saneka fa to sai dai ka yi hakuri ka rungumi sorry ka kyalesu😅 ina ga dalilin cinye masu abubuwa da Aunty Hauwa take yi yasa suka tsaneta😅) Abincin suka fara ci cikin nutsuwa, maman Zainab ba dai iya girki ba, ta kware sosai, idan kana cin girkinta idan ka yi wasa sai ka fara zuba santi ba tare da ka sani ba, saboda daɗi da iya tsara girkin. A wannan hali Haidar ya dawo ya samesu, bai samu inabi ba, masu fruits na unguwar tasu duk basu kawo inabi, kun san yana da tsada, ba kowa yake sayansa ba, hakan yasa ba kowani mai sai da fruits yake kawo shi ba, sai manya masu sayarwa. Jin cewa ba'a sami inabin ba yasa Khadijah ta fashe da kuka tare da miƙewa ta bar abincin nata, fuuu ta nufi cikin ɗaki. Kallon maman baban nasu ya yi, irin kallon nan na ke kika jamun, ita ma shi take kallo, irin kallon nan na kayi hakuri. Bai ce da ita ko uppan ba ya miƙe ya bi bayan ƴar tasa dan ya rarrasheta, ga shi kuma dare ne, idan ya ce zai je neman inabi a yanzu sai ya hau mashi ya fita cikin gari ta wajajen kasuwar tasu, zuwa wajen kawai ma 500 naira ne kuɗin mashi, dawowa ma haka, bare kuma daren nan kunsan kara kuɗin mashi suke yi, gaskiya maman Zainab dai bata kyauta mashi ba, kuma idan bai nemo wannan inabi ba Khadijah dai ƙaramin aikinta ne ta yi mafarki, shi ma dai ba zai iya yin barci cikin daɗin rai ba, dan yasan waye Khadijah bagensa, sarkin zuciya da rigima, dole dai anemo inabi, kuma tsautsayi ne tasa yau ya sayi inabin guda ɗaya, sau da dama biyu ko ukku yake saya, zaka gansu a jikin itacensu ba'a cire ba an sako mashi guda uku, to yau sai malam Sani ya saka masu guda ɗaya tak, Mama ta bawa Aunty Hauwa, aiki babba kenan, akwai rigima. Nikuma dole na dakata da rubutu a nan, Maman Zainab baki kyauta mana ba, shiyasa ake son a rinƙa tambayar mutun abu idan ya kawo, ba wai ayi gaban kai ba.....….😌😒 *Masu buƙatar littafin TRIPLETS daga farko harshen su yi mun magana ta wannan number tawa, 08161390581.* 🤍PRINCESS TEEMA taku ta amana🔥 Share fisabilillahi 👏 ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍 🤍🔥𝗥𝗔𝗪𝗔𝗡𝗜𝗡 👑 𝗭𝗔𝗟𝗜𝗡𝗖𝗜🔥🤍 🔥CROWN OF INJUSTICE🔥 𝗠𝗔𝗟𝗟𝗔𝗞𝗜𝗡 ❤️‍🔥FATEEMA ZAHRA MUSA ❤️‍🔥 (❤️𝑷𝑹𝑰𝑵𝑪𝑬𝑺𝑺 𝑻𝑬𝑬𝑴𝑨🔥) 🔥🤍T🔥🤍T🔥🤍W🔥🤍......💻 ❤️𝑫𝑨𝑻𝑬 3/7/2024.....✍️📚🌹 🤍𝑺𝑻𝑬𝑷 1......✍️📚🔥 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ E____________6🔥 Kwance ya isko Khadijah kadina kadin Allah a saman ƴar madaidaiciyar bed nasu 6 by 6. Gadon a shunfuɗe yake da zanin gado mai kyau lunin pink color da ratsin baki, tsab da shi, sai kamshi ɗakin nasu ma yake yi, ga drawer kayansu mai ɗan girma a gefe guda, sai drawer bed ɗin da suke jera kayan kwalliyarsu da kuma mayukan shafawarsu. Sai wani irin kuka take yi, irin kukan nan da idan mutun zuciyarsa ta hasala sosai, sai ka ji yana wani irin kuka kamar mai sifirin..........😅 To haka Khadijah take wanan kuka. A bakin bed ɗin ya zauna tare da sanya hannu ya ɗagota yana mai bata hakuri. Cigaba da kuka ta yi abinta, tana yi tana wani irin jan numfashi alamar fa ta kai kololuwa wajen jin haushi. "Mamana ta shi ki je ki ɗauko hijabinki mu je bakin kasuwa a tare mu sayo wani inabin kin ji?". Ya faɗa cikin sigar rarrashi. Maƙe mashi kafaɗa ta yi, da kyar ta iya cewa. "Ni baba ka bari sai gobe, kada ka fita da daddaren nan, kaga ranar ma da ka fita sayowa Zainab magani masu kwacen waya sun tareka a hanya ko? Tom ka bari sai gobe kawai ka dawo mun da shi daga kasuwa". Tana magana wasu hawaye suna gangaro mata, kai daga jin maganar tata kasan ba daga cikin zuciyarta ya fito ba, ta faɗa mashi hakan ne kawai dan son da take yi mashi, bata son waɗan nan gurɓatattun mutane masu kwacen wayar su yi mashi illah, dan a wancan karon da suka tare shi har sun buge shi da sanda a hannu, sannan suka kwace mashi waya, haka hannun nasa ta kumbura tsawon sati biyu baya zuwa kasuwa, baya fita ko'ina, da kyar ya samu hannun ta yi sauki, shi ne yasa yanzu da sun yi sallar issha dai sun shiga kenan, zasu rufe gidan abinsu, a lokacin da abin ya faru Khadijah ta sha kuka kamar ba gobe, dan tana tsananin son baban nata, yana kyautata masu over. "Amma mamana ki bari naje a sayo maki, dan nasan kina so, ga shi ma kin kasa dai'na yin kuka, kawai ki barshi bari na je na saya maki". Cikin sauri ta kai hannunta a saman face nata ta fara goge hawayen nata tana faɗin. "Baba ga shi nan ai na dai'na yin kukan, ni dai ka bari sai gobe ka sayo mun". Ƙaƙalo murmushin dole ya yi tare da sanya nashi hannun ya fara tayata goge hawayen yana faɗin. "Tom shikenan, gobe idan Allah ya kaimu guda biyu zan sayo maki, yanzu tashi muje mu ci abinci ko?". "Baba Allah bana son wannan Aunty Hauwar, haushi take bani, kullum idan ta zo gidan nan sai mama ta bata abubuwanmu ta tafi da shi gidanta". Ƴar murmushi ya yi kafin ya fara bata amsa da cewa. "Haba mamana, kada ki zama mai rowa mana, menene dan mamanki ta bawa wata kyautar abu? Ai lada zamu samu, kin ga wannan Aunty Hauwar taku? Mamanku bata da kawa biyunta, tare suka taso unguwa guda, a tare suka yi wasan kasa, a tare suka yi karatu, Allah da ikonsa kuma sai ya kawosu aure gari guda, kin dai san mamanki bata da kowa a nan ko? Iya ƴan uwana kawai ke gareta, nata ƴan uwan babu ko mutun ɗaya a nan, to haka ita ma wannan Aunty Hauwar, bata da kowa sai ƴan uwan mijinta sai kuma mamanku, kinga dole zasu kaunaci juna su kuma haɗa kai da juna dan su ɗebewa junansu kewar iyayensu da ƴan uwa, dan haka ki dai'na cewa kin tsaneta kin ji ko? A matsayin ƴar uwar mamanku take, ku ɗauketa tamkar kawu Sadiq naku, ba kuna son Kawu Sadiq ba?". Da suri ta gyaɗa mashi kai tare da faɗin. "E baba muna son kawu Sadiq sosai, kullum baya taɓa dawowa gidan nan ba tare da ya kawo mana abin kwalama ba, amma shi Yah Haidar sam baya bamu komai, sai shegen masifa ya iya, shiyasa ni nafi son kawu Sadiq nawa". Shiru baban nata ya yi, har cikin ransa bai ji daɗin maganarta ba, ransa ya sosu, amma ya zai yi? Gaskiya take faɗa, dan Khadijah bata karya, Haidar ɗin shi ya jawa kansa. Nasan zaku so sanin wanene Haidar a gare su, wanene kuma Sadiq, to Haidar dai ɗane ga babbar ƴar babansu, wanda tun yana ƙarami baban nasu ya rike shi, a tare suke zuwa kasuwa, yana taya shi sayar da kaya, mutun ne shi mai irin halin mata, akwai shi da gulma, ga shegen iya eyes service, idan babansu yana nan zai kulasu, a bayan idanun babansu kuma sai hantararsu ya iya yi da zagi, baya wani kulasu, maman nasu ma ba wani ɗaukarta da daraja ya yi ba, ta rike shi tun yana ɗan shekara 8, yanzu har ya kai 18 years a duniya, amma hakan bata hana idan ta yi mashi ba dai'dai ba ya yi mata rashin mutunci, ga shehen kai gulma cikin dangi, ya ja ayi ta zagin Mamansu Zainab ɗin a kan ta mallake babansu, abu dai babu daɗi, yanzu duk ƴan uwan mijinta basu sonta, kuma duk wannan Haidar ɗin shi ne sila, ya je yana kwasan duk sirrin gidan yana kaiwa dangi, har da karawa da karyarsa son ransa. Shi kuma Sadiq kani ne ga maman nasu, yaron kirki, ko da yake dama dole ya zamana yana kaunarsu Zainab ɗin sosai, saboda ƴar uwarsa, tun da aka aurota tana amarya ta taho da shi, dan bata da kanwa mace, sai shi kaɗai, shi ne ta roki babanta lokacin tun yana da rai, ta roƙe shi ya bata Sadiq ɗin, da kyar aka yarda aka bata shi, a lokacin yana da shekaru 7 a duniya, ta rike shi har yanzu ya kai yana da 17 years, yaron kirki mai yin komai tsakaninsa da Allah, yana kaunar su Khadijah ɗin sosai, ko fita ya yi waje zai sayi abu, to ba zai dawo cikin gidan ba sai da sweet ko biscuits, ya kawo masu, su yi ta murya, yana kyautata masu sosai, duk abu mai kyau idan ya gani zai saya masu ya kawo masu, ko kaya ya gani a kasuwa an kawo sabbi masu kyau, da kuɗinsa yake cirewa ya saya masu, wani lokaci har faɗa yake yi da Haidar ɗin akan hantararsu Khadijah ɗin da yake yi idan babansu baya nan, kullum kuma idan suka yi faɗa sai Haidar ɗin ya yi mashi gorin cewa wai iyayensa basu da karfin rikesa ne yasa suka haɗawa kawunsa wato banansu Zainab ɗin kenan nauyi, wai yazo yana cinye masu arziki shi da ƴarsa, wani lokaci har ikirarin cewa sai ya yi sanadiyar barinsu gidan daga shi har ƴaƴar tasa Haidar ɗin yake yi, shi ala dole ana cinyewa kawunsa kuɗi, saboda jahilci, bai san me ake nufi da mata ba!. Wani lokaci har kuka Sadiq ɗin yake yi ya ce ba zai zauna a gidan ba zai koma garinsu, dan yana da zuciya, Mamansu Zainab ɗin ce take bashi hakuri ta yi ta lallaɓa shi, ta ce mashi idan ya koma ya barta ita da waye zata zauna? Waye zata gani ta ji daɗin rayuwa? Ya sani ƴan uwan mijinta duk basu sonta, idan ya tafi ya zata yi da rayuwarta?. Da haka take lallaɓa shi ya yi hakuri ya zauna. Shi Sadiq ya yi karatu, yanzu haka yana Ss3, shi kuwa Haidar tun daga primary 4 ya fasawa malamin English nasu kai dan bai yi class work da aka basu ba malamin ya zane shi, shi ne ya fasa mashi kai da katako ya gudu ya bar makarantar, tun daga lokacin ya ce ya ajiye karatu, ba yadda ba'ayi da shi ba ya koma makaranta, amma fir yaki yarda, har canza mashi makaranta banansu Zainab ya sake yi, amma sam yaron nan yaki, ya ce shi neman kuɗi zai yi, ga jahinci a cike da kai, shiyasa yake gulmace gulmace da tsugudidi tare da kananan maganganu, da ace yana da ilimi ya yi karatu, da sam ba zai yi wannan shirme ba, yanzu yana nan babu boko babu Arabic, shiyasa a haukarsa yake ganin cewa wai Mamansu Zainab tana cinyewa kawunsa kuɗi ne ita da kaninta Sadiq, to bai ma san me ake nufi da mata ba, ba ilimi, matar ma wadda ta haifawa kawun nasa ƴaƴa har guda biyu, ai ta wuce wasa. Allah ya gani baban Zainab yana iyaka bakin ƙoƙarinsa wajen ganin ya kyautata masu, daga Haidar ɗin har sauran ƴan uwansa, shi yake ciyar da Mamansu Haidar ɗin, dan mijinta dai sai a hankali, bashi da ko sisi ba aikin yi, hakan tasa baban Zainab ɗin yake ɗawainiya dasu, amma duk basu gani, sai suce Maman Zainab tana hana shi ya taimaka masu, ta kanainaiye komai ita da ƴan uwanta. A kasuwa duk wani harkar kuɗi da lissafi da Sadiq baban Zainab yake yi, dan Haidar kam kan fanko ce, bai san komai ba, hakan ne ma yasa ƴan uwan baban Zainab ɗin suka dage a kan lallai maman Zainab asiri ta yi wa ɗan uwansu, wai tun da harta harkar kuɗi a kasuwa da Sadiq kaninta ake yi, Haidar ya zama bare saniyar ware ɗan kallo, ita dai maman Zainab sai dai ta toshe kunne kawai baiwar Allah, shi ma Sadiq ɗin yanzu dan dolensa ya ko yi toshe kunnensa, baya kula kowa, idan maman Haidar ta isko shi a kasuwa, zagi da cin mutuncin kala kala take yi mashi, idan ta gama sai ya ce Allah ya bata hakuri kawai, dan bai san me zai cigaba da ce mata ba kuma. Wannan shi ne kaɗan daga cikin tarihin Sadiq da Haidar, to mu je dai zuwa. "Baba ya ka yi shiru?". Cewar Khadijah. Doguwar numfashi ya ja tare da saukewa a hankali. "Babu komai mamana, muje parlourn ki ci abinci ko?". Kai kawai ta gyaɗa mashi alamar to suje. Miƙewa ya yi tare da riƙo hannunta ya sauketa kasa, sannan suka nufi parlourn. A yadda suka bar Zainab da Maman Zainab haka suka dawo suka samesu, kasancewar baban nasu yana nan ne yasa Haidar ya ce. "Khadijah uwar rigima, daga cewa ba'a sami inabin ba har kin fara kuka". Cewar Haidar sarkin eyes service. Wata uwar harara ta wurga mashi ba tare da ta amsa mashi ba, yanzu haushin kowa take ji, har maman nata da ta bawa Aunty Hauwa wannan inabin, ita ma duk haushinta take ji. A baki baban nasu ya rinƙa bata abinci yana rarrashinta, yau an yi sa'a ƴan mutunci suna gaba goshi, dan haka sai ta hakura ta ci abincin, ba musu. Bayan sun kammala ne suka zauna yin kallo kaɗan, ita kuma Maman Zainab ta hau tattare kayan abinci. A cikin wannan daren ta yi wanke wankenta, ita bata barin kayan abincin da aka yi anfani da su da daddare su kai wayewan garin gobe, a daren take wanke su tsab, haka kayan wanki, waɗan da aka cire a ranar bata taɓa bari ya kai gobe ma bare har ya taru mata sosai, a ranar take wanke su abinta, so haka ta wanke kayan abincin nan fes tare da dawowa ta sake yin mopping na parlourn sosai, sannan ta kunna buner ta zuba turaren wuta mai daɗin kamshi kafin ta haye saman sofa kusa da baban nasu ta zauna. Wani American film suke kallah a MBC, sun nutsu tsit kamar babu kowa, ita kuma Khadijah kaf hankalinta baya a kan Tv, sai tunanin islamiya take yi, dan an kara masu karatu yau, kuma da daddare ne kawai take samun damar yin karatun, da safe zasu tafi makarantar boko, ba zasu dawo ba sai karfe uku, idan suka dawo kafin su ci abinci su yi wanka haɗe da shirin islamiyar, karfe huɗu ta yi, dole islamiyar zasu wuce a dai'dai wannan lokacin, so babu time, yanzu haka Khadijah tana primary 2 a makarantar boko, ita kuma Zainab primary one zata shiga yanzu, suna da ƙoƙari sosai, saboda kula da suke samu daga wajen iyayensu, babansu ba wai ɗan kasuwa bane kawai, degree gare shi a fannin electric engr, kuma ya fito ne da first class, kawai yanayin kasar ce tasa ya zama ɗan kasuwa mai sayar da atamfofi, lace, shadda, da dai sauransu, babu aikin yi, ya gama karatu bai sami aiki ba, shi ne ya zaɓi ya fara kasuwancinsa kawai, ya tattara result na makarantar ya ajiye a gefe guda. Mammansu kuwa ta gama secondary school nata, tana da ilimi dai'dai gwargwado, sannan macece mai ilimin addini, ga saukin kai da tausayi tare da fawwalawa Allah komai nata, so a takaice dukkansu daga maman har baban duk ba jahilai bane ba, suna da ilimi, shi ne yasa suke kula da karatun su Khadijah sosai da sosai. Sai misalin ƙarfe 9:30 su Khadijah suka miƙe suna yi wa iyayen nasu sai da safe, dama already sun rigada sun sani, karfe 9:30 suke shiga su kwanta, saboda tashi zuwa makaranta, tun suna yara mamansu ta tsara masu tsari mai kyau na rayuwa, wani abin ba sai ance su yi ba, sun riga da sun saba yi. "Mamana kada ku manta ku yi addu'ar kwanciya, nima zanzo in yi maku nawa idan zamu shiga". Cewar babansu. Da to suka amsa mashi tare da wucewa cikin ɗakin nasu. Wata riga da wando mai laushi sosai Khadija ta ɗauko masu daga cikin drawer saka kayansu, iri ɗaya ne kayan launin navy blue. Miƙawa Zainab nata ta yi, karɓa ta yi suka hau canza kayan ba ɓata lokaci, kayan barcinsu ne. Bayan sun canza Zainab ta haye saman gado, ita kuma Khadijah ta ɗauko takardun islamiyarsu tare da ɗauko littafinta na Nahhu ta buɗe shafin filul mahdi dan ta kara duba karin karatun da aka yi masu. Ta ɗauki a kallah minti goma tana ta karanta wannan filul mahdi'n kafin ta rufe takardar ta mayar cikin jaka, sannan ta mayar da jakar mazauninta, a lokacin har Zainab ta fara zuba barcinta abinta. Zama ta yi a tsakiyar gadon ta fara karanta kulhuwallahu kafa uku, falaki da nasi suma kafa uku uku, sai ayatul kursiyu kafa ɗaya, sannan amanar rasulu shi ma kafa ɗaya, ta tofa a hannunta kafin ta shafa a jikinta gabaɗaya, ta juya ta shafawa Zainab ma, kamar wata babban mace, bayan ta shafa mata ne ta jawo masu bargo, dan garin akwai sanyi sosai, gari ne na damina, Khadijah tana tsananin son Zainab over to over wlh, ita kaɗai ce ke gareta. Su kuma iyayen nasu, sai da suka kai har karfe 11 suna kallo, sai da suka ƙarisa kallon wannan film ɗin, shi ma Haidar saboda tsabar gulma yaki wucewa ɗakinsu, yana nan a tare suka ƙarisa kallon, sannan ya miƙe ya nufi ɗakin nasu yana yi masu sai da safe. Mamance kawai ta amsa, baba bai amsa ba, dan shi har ga Allah baya son wannan hali na Haidar, kawai ba yadda zai yi ne, ya yi iyaka bakin ƙoƙarinsa a kan yaron nan ya canza hali, ya koma makaranta lokaci bata kure mashi ba, amma sam yaki yarda, ya zauna sai shirmen banza da wofi yake yi, yana mayar da kansa irin local matan nan masu shegen tsugudidi. Ga shi babu halin baban Zainab ɗin ya kore shi daga gidan, dama yaya lafiyar kura bare ace ta yi zawo? Yanzu ma ana cewa maman Zainab ta yi mashi asiri ta mallake shi, to ina ga kuma idan ya kori Haidar? Ai shikenan abu ya sake kwaɓewa, sai aje ayi ɓatattciya da dangi, zaman lafiyarsa kawai ya cigaba da bin Haidar ɗin da idanu har lokacin da zai girma hankalin manyantaka ta shigesa, wata kila a lokacin zai iya gane dai'dai da ba dai'dai ba. Miƙewa baban Zainab ya yi ya je ya rufo masu kofar parlourn bayan tafiyar Haidar ɗin kenan, dama already ya rufe masu kofar gida kam tun tuni, suna dawowa daga sallar issha suke garƙame kofar gidansu, saboda tsaro, akwai gurɓatattun matasa ɓata gari a unguwar tasu sosai, shi ne yasa basu wasa da rufe kofar gida. Kowannensu ɗakinsa daban, baban nasa daban, ita ma Maman nata daban, amma dayawa lokuta a ɗaki ɗaya suke kwana, inma na maman or na baban, a dai ɗaki ɗaya suke kwana, yau ma ɗakin baban suka wuce a tare bayan sun kashe kayan kallon nasu tare da wutar parlourn haɗe da tattare komai nasu, suka shiga wajensu Zainab suka yi masu addu'a, sannan ne suka nufi ɗakin barcinsu. A suba ta gari............ ♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥︎♥♥︎♥︎♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥ 🏞️Forest🏞️ Tun da Kamran ya yi wannn barci bai farka ba har washegari da safe, abin abin ban mamaki mai rikitarwa, ko da ya farka kuma ya jima sosai idanuwansa biyu ya kasa motsawa, jikinsa duk wani irin azabbabben ciwo yake yi mashi, duk ya ji wani irin tamkar ba shi ba, kamar wanda ya sha kayan maye overdose suka sanya shi barci, jin jikinsa yake yi tamkar ba shi ba, kamar an canza shi, da kyar ya iya samun dama ma ya waro idanuwansa waje, wani irin nauyi idanun nasa suka yi mashi, da farko ma ji ya yi tamkar an manne mashi su da super glue, sai da ya yi da gaske ne ya iya buɗesu. A hankali hankali ya fara kallon wani irin jiri jiri tana ɗebarsa daga kwance, saman ɗakin nasa ne ya fara juya mashi kamar fanka. To me ya sami Kamran ɗin mu?. Dishi dishi idanuwansa suka fara ganin masa, like idan mutun yana ƙoƙarin sumewa, haka zai

Chapter 7 of 75