dake a gabanta Jaish ya ƙariso ya zauna a saman shinfiɗar da take ɗin kenan.
"Sannu da hutawa Momma".
Ya faɗa kansa na'a ƙasa yana kallon shinfiɗar, dama na gaya maku muguwar kunya ke gare shi, sam baya son haɗa idanu da mutane.
Gyara zamanta ta yi a in da ta kara dakewa a cikin alkyabbar.
"Jaish ka dawo lafiya? Ya gajiyar hanya ya kuma ka baro mun su Abbana?".
"Kowa yana lafiya Momma, and suna gaisheki sosai".
Bawan Allah ko part nasa bai leƙa ba, yana dawowa kawai iyayensa ya fara buƙatar gani, sune sama da komai a garesa, baya wasa da su kuma bi haɗasu da kowa ba, idan ba ya zo ya gansu ba ko wanka ba zai iya zuwa ya yi ba, shi ne yasa ya fara da fada ya duba daddynsu sannan ya taho wajen Mommansa, a kullum idan ya dawo daga tafiya haka ko daga office sai ya bisu ɗaiɗai ya fara duba suna cikin aminci kafin ya tafi ya je ya yi abin da zai yi.
"Ina amsawa ina Omar?".
Ta yi maganar tana kai hannunta saman kyakkyawar bakin gashin kansa, a hankali ta fara shafa kan nasa tana saka mashi albarka.
"Baka je part naka ba ko?". Ta sake jefo mashi wata tambayar tana mai do da kallonta a saman kyakkyawar face nasa.
Nisawa ya yi kafin ya bata amsa da. Omar yana gidan uncle Rahab babban yayanta kenan, sai ku ya ɗaura da cewa. "Ban je part nawa ba, ai kinsan ba zan iya zuwa ko'ina ba har sai na zo na ganki".
"Allah ya yi maka albarka my son, ina alfahari da ku".
Da amin ya amsa mata kafin ya ce. "Momma kina lafiya ba wata matsala in wuce part nawa?".
"Lafiyata lou Alhdulillah nake, amma da ka je gidan Yah Rahab ya kasami su Jannat?".
Shiru ya ɗan yi na a kallah one mint kafin ya ɗago da kallonsa ya ɗan kalli face nata kaɗan, sannan ya sake sunkuyar da kan nasa ƙasa, sai ƙoƙarin tuna su waye kuma su Jannat a duniyar nan yake yi? Amma ina ya kasa tuna su waye su, dan bai ma san da su ba a duniya, ƴaƴan uncle ɗin nasa ne da shi bai ma san da zamansu a duniya ba, su kuwa sun san da shi, har ma sun saka shi a cikin zuciyoyinsu, dan muguwar farin jinin ƴan'mata ke gare shi sosai, duk in da ya shiga sai ya shiga can cikin zuciyoyinsu, amma shi sam baya kula kowa. E babbar magana kenan, lallai Jaish ka cika cikakken ɗan duniya, ƴaƴan uncle ɗin nasa ne ma bai sansu ba.
"Ba dai su ma su Jannat ɗin baka sansu ba kam?".
Ta yi maganar tana aikin kallon face nasa da ya wani sunkuyar da kai ƙasa.
"Momma i don't know them". Ya bata amsa yana kai hannunsa ya riƙo nata guda ɗaya a cikin nasa.
Shiru ta yi a kan maganar su Jannat ɗin, dan tasan fin haka ma zasu aikata, dama ta yi sa'a suka san uncle Rahab ɗin kenan, kaɗan daga aikinsu su ce basu san sauran uncles ɗin nasu ba.
"Mommana zan iya tafiya?".
Yana magana ya ƙoƙarin cire mata wani dankareran tsadadden diamond ring da yake manuniyar yatsarta, zoben ya kama mata yatsa sosai ne, har ya fara cin namar jikinta.
"Meyasa zaka cire mun? Zoben Ummiee na ne fa".
"Ummm shi ne yasa kika ki cirewa har ya fara cin maki namar jikinki ko? Tom ni dai ba zan iya ganin shi yana ƙoƙarin cutar mana da ke na barshi ba, zan cewa Ummiee ta aiko maki da wani, dan nasan nata daban ne".
Ya kai karshen maganar tare da zare ring ɗin a hankali cikin dabara ta yadda ba zai yi mata zafi ba, tamkar ma bata san an cire ba, duk da kuma yake ya kama jikinta.
Murmushi kaɗan ta yi a cikin zuciyarta tana ƙara godewa Allah da ya bata ƴaƴa masu matuƙar kaunarta har haka, sun san farincikita ko bata gaya masu ba, haka zalika sun san bakin cikinta ko bata bayyana masu ba, sun san abin da take so da wadda bata so.
"Momma zan je na yi wanka na ɗan yi barci, inason gobe na fita office da sassafe, kinga almost 2 weeks bana nan, so yakamata na je office gobe dan naga me ake ciki".
"Jaish barci yamman nan fa bashi da kyau, idan ka yi shiri yanzu zaka tashi da ciwon kai".
"In Sha Allah zan kiyaye, but now am feeling to much of sleeping, zan yi kaɗan kin ji mommata?".
Ya yi maganar in a low voice sosai!.
"Tom shikenan, ka kula sosai Allah ya yi maku albarka".
Da Ameen ya amsa mata kafin ya miƙe tsaye rike da ring ɗin nata, sannan ya nufi kofar fita da wannan taku nasa cikin nutsuwa haɗe da fadanci. Da idanu ta bishi har ya fice daga cikin ɗakin, nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana mai kara godiya ga Allah a cikin zuciyarta.
Yana fitowa ya iske Aunty MieMie da Gimbiya Chuchu and Zunaira suna ta hirarsu, Yah Jawad baya wajen, tamkar zai tambayi Aunty MieMie ina Jawad yake? Sai kuma ya fasa tambayar yasa kai kawai ya wuce ba tare da ya bi ta kansu ba.
Ita ma Aunty MieMie bata ce mashi ko uppan ba, dan tasa da wuya ya amsa mata, Gimbiya Chuchu dama saboda ance mata yana cikin ɗakin ne yasa ta nemi waje a parlourn ta zauna, dan haka yanzu yana fita ta yi maza ta miƙe ta nufi cikin ɗakin da murnarta. A hanzarce auta ta miƙe ta rufa mata baya, suka bar Aunty MieMie ita kaɗai, gyarawa ta yi ta kwanta a samar sofar tare da fito da wayarta ta fara latsawa.
Dai'dai Jaish zai shiga cikin elevator wasu kyawawan ƴan samari suka fito daga cikin elevatorn, kyawawa ne sosai, da gani ba tambaya ƴaƴan Gimbiya Rahilarh ne, wato Momma. Ƴan samari ne da basu fi 13 years ba a duniya, kana ganinsu kaga twins, saboda tsannin kamannin da take a tsakaninsu ta yi yawa, ba zaka iya banbantasu ba, idan ka gansu ma zaka ce mutun ɗaya ne, dan fa komai sak suke kama.
Suna ganinsa suka ɗan ja da baya suna mai risinar da kai.
"Good afternoon Yah Jaish, ka dawo lafiya?". Suka haɗa baki wajen faɗar hakan.
Tsaresu da idanu ya yi ba tare da ya yi magana ba. Nan take suka sha jinin jikinsu suka fara ƴan kame kame.
Obaid ne ya ce. "Wajen momma zamu je dama". Sai kace an tambaye shi, tsabar tsarguwa ce kawai, da gani sun aikata wani abin da ba dai'dai ba, dan wlh idan kana neman ƴan rigima ƴan haɗa cakwakiya fitinannu marasa jin magana idan ka samesu kai kam ka gama komai, su ɗin number one ne a harkar rashin jin magana, sam basu son zaman lafiya, idan ƴaƴan sarakuna suka zo neman auren Gimbiya Sarina da Fanan, to da su Gimbiya Sarina take haɗa baki su kulla munafurci su kori ɗan sarkin, yanzu sau uku ƴaƴan manya manyan sarakuna daga masarautu daban daban suna zuwa neman auren Sarina ɗin, amma duk ta haɗa baki da su Obaid ɗin ta kori samarin, a cewarta babu class nata a cikinsu, suna da wani uncle mai suna Taheer kanin Mama wato matar king ta biyu, wannan uncle Taheer ɗin mutun ne mai izza da ji da kai bala'in girman kai na wuce misali, tun yana ƙarami yake cikin masarautar, yana nuna isa da zafin rai, ga jarumta, amma duk da haka sai da ranar su Obaid suka kusa saka shi kuka, kuma har yau babu wanda ya gane su suka yi mashi wannan ɗanyen aikin, kuma Sarina ce ta saka su, dan uncle Taheer ɗin yana bata haushi, yana takura mata da faɗa akan ta yi sallah ta dai'na taɓa waya, shi ne nan ta je ta sanya wata kuyanga daga cikin masu yi mata hidima ta ɗebo mata wani irin azabbabben mai mai zafi da aka rubuta rob a jikinsa, ɗan iskan zafi ke gare shi, haka ta kawo mata, saboda rashin imani ta saka su Obaid suka san ta yadda suka yi suka zubawa uncle Taheer ɗin wannan rob ɗin a towel da zai goge fuskarsa idan ya yi wanka, haka kuwa aka yi, dama ga shi jajir da shi kamar tsada, ai kuwa yana goge fuskarsa da towel nan ya kara yin wata uwar ja fuskar tasa, nan take face ɗin nasa ta yi ruɗu ruɗu kamar wadda ya sha marika a hannun maza irinsu commander ZAFAR, kan ka ce me idanuwansa sun yi jajir kamar jini, fitsari ne kawai bai saki a wando ba ranar, saboda azaba, sai da ya kwanta a gadon asibiti, saboda rub ɗin tana da azaba sosai, ga shi sun zuba dayawa a jikin towel ɗin.
Ƴan albarkar ƴaƴa har yau ba wanda ya iya gane su suka yi wannan aika aikar, sun iya haɗa sharri kamar ba jinin gimbiya Rahilarh ba su kam, babban abin haushin kuma muguwar shiga rai ke gare su, wlh idan ka gansu sai sun yi mugun burgeka, ka ji duniya kana kaunarsu, ga shi kuma idan suka yi laifi aka kamasu to fa ba za'a taɓa iya banbance wanene ya yi laifi a cikinsu ba, saboda tsananin kamar da suke yi, sai su yi ta rai'nawa mutane wayo, wannan ya ce wannan ne, wannan ma ya ce wannan ne, haka suke ruɗar da mutane.
"Me kuka aikata?".
Shi ne tambayar da Yah Jaish ya wurga masu.
Kallon juna suka yi, a tare suka haɗa baki wajen cewa.
"Yah Jaish bamu yi komai ba, daga part ɗin mummy fa muke"
Sam bai yarda da maganarsu ba, dan yasan hali, yasan basu zama shiru, basa ji, auta da take kanwarsu 11 years ma tana nan nutsatsiya kamar wata waliyiya, amma banda su, ba dan ba dan ba da na ce waɗan nan renon shaiɗan ne.......😅
"Idan na ji kun aikata wani abin Allah sai jikinku ya gaya maku".
Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya shiga cikin elevator abinsa.
Tsayuwa suka yi a wajen har sai da suka ga tashin elevator, sannan suka kalli juna suka kwashe da dariya a tare kamar wasu munafukai, tamkar masu aljanu a tsakar ka.
Dariya harda rike ciki suka yi, tamkar basu ne yanzu suke muzurai a nan ba. Sai da suka yi mai isarsu sannan Omaid ya ce.
"To mu idan ma mun yi laifi za'a iya gane mu ne? Ai ƙwaƙwalwar Star ne da mu, ba tunanin boss muke da shi ba, dan boss ne yake da ɗoɗaɗɗen ƙwaƙwalwa, a film kullum cikin rashin nasara yake saboda tunaninsa na banza, kullum shi ake kashewa ba actor ba, kafin mu yi abu sai mun yi tunani irin na actor, sai mun nemo hanyar da baza'a taɓa gane mumuka yi ba".
Dukar wasa Obaid ya kai mashi a shoulder ɗinsa yana faɗin.
"Amma kasan dai Yah Jaish and Yah Jawad they're acting like actors ko? Suma ba tunanin boss suke da shi ba, tunanin actors ke gare su, wlh tun da sun dawo sai mun kara dogon tunani ta yadda zamu rinƙa zulle masu".
(Ka ji wani zance, wai masu 13 years ne zasu yi wa mai 25 years wayo😂 kai jama'a su Obaid basu da kirki, kaɗan fa suka samu gadon kaifin ƙwaƙwalwar King Zuhair, amma har suke ƙoƙarin yiwa manyan kai waɗan da su suka gaji ƙwaƙwalwar da gaske wayo fisabilillahi 🤌😂 lallai kuna ruwa, mu muna gefa idan suka riƙeku zaku san cewa tunanin actors kuke yi, amma fa da gaskiyarsu, suna da kaifin basira sosai wlh, sun iya saka mutun a tarko su zulle su barshi)
"Kai Obaid mu wuce ciki hai, kada Yah Jawad ya isko mu a nan, kasan dai tun da ka kalli Yah Jaish ya wuce to Yah Jawad yana bayansa, dan kasan basu rabuwa, kullum suna a tare".
Ya kai karshen maganar tare da wucewa izuwa wajen kofar shiga cikin parlourn Mommar. Da sauri Obaid ya rufa mashi baya, suna sanye ne fa da fararen jallabiyas tas kamar wasu limaman masallacin jumma'a, amma kun ji irin tsiyar da suke surfawa!.
Yah Jais kuwa kai tsaye cikin wani luxury part ya nufa, idan kun ji ance luxury ai ƙarshen haɗuwa kenan, baki ba zai iya faɗar haɗuwar ba, ya ji komai ya more rayuwa wadda duk min girman burin ɗan adam aka bashi nan to sai ya mance da cewa a duniya ma yake.
Akwai kuyangu biyu dattijawa da suke kula da part ɗin nasa, sune suke yi mashi gyare gyare da komai da komai, ɗayar ta fi manyata, dan zata kai 45 years a duniya, ɗayar kuma bata da wani girma sosai, bata wuce 35 to 40 years ba, sun san kan aikinsu sosai, kasancewar sun sansu da balai'n son tsafta yasa suke zagewa su yi aiki babu kakkautawa, ko'ina sai sun gyara, su goge su sake gogewa, dan sun san idan Jaish ya sami datti komai ƙanƙantarta to fa bala'i ne zai tashi ya tsaya a cikin gidan, hakan tasa basu wasa kuma basu ƙasa a gwiwa wajen ganin sun yi aiki yadda yakamata, shiyasa part ɗin take tamkar sabuwa, komai very very clear gwanin ban sha'awa, ga uban daddaɗar kamshin da yake tashi tun daga dosowar mutun part ɗin zai bule shi.
Komai na cikin part ɗin launin milk color ne, sai ɗan ratsin ash a jikin tsadaddun curtains ɗinsa.
Bed da yake kwanciya duniya ce guda, abu kamar ba za'a mutu ba, irin wannan daula.
Yana shigowa kuyangun suka zube ƙasa a saman gwiwowinsu suna kwasan gaisuwa tare da zuba mashi kirari na ɗan sarki jikan sarki takawarka lafiya toron giwa, zaki kake kafi karfin kananun namun dawa, irin dai kirarin da ake yi wa Barde suke yawan yi wa ƴaƴan nasa ma.
Ko kallon in da suke bai yi ba bare asa ran zai yi magana, cikin luxury bedroom ɗinsa kawai ya wuce abinsa, sai a lokacin ya tuna da cewa ya bar laptop nasa a cikin mota, dama kayan sakawa kam baya tafiya dasu, dan Dubai gida ce a wajensu, kamar yadda yake da part nasa a cikin masarautar nan tasu da komai da komai, to haka yake da shi a can masarautar kakan nasu ma, so idan ya tashi tafiya Dubai ɗin baya ɗaukar ko tsinke na kayan sakawa, tafiyarsa kawai yake yi, haka dawowa ma.
Raba kansa da kayan jikinsa ya fara yi daga shiga cikin bedroom ɗin, waɗan nan kuyangu nasa sun iya gyara, katafaren bed ɗin nan nasa ya sha shinfiɗa ta alfarma ta wata dankarariyar luxury bed sheets, ga wata haɗaɗiyar duv mai girma sosai, idan ka haye saman bed ɗin nan ma ai ba za'a gane da mutum a wajen ba, saboda girmansa ga laushi over.
Haɗaɗɗen toilet ɗinsa ya nufa dan ya yi wanka, tas ya cire kayan jikinsa ya rage daga shi sai short, yana da kyan surar jiki sosai kamar shi ya yi wa kansa.
Bayan ya yi wanka cikin kayan shan iska ya shirya, ya yi wa kayan matuƙar kyau sosai, singlet ce and short, sannan ya haye saman katafaren bed nasa yana wani lumshe idanu, sai zuba kamshi yake yi, ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi.
After some hours.
Babbar parlourn King Zuhair, wajen da suke haɗuwa su ci abinci kenan.
Hayaniya ne yake tasowa a cikin parlourn ba kaɗan ba, tun daga nesa suke ta aikin kace na ce. Gabaɗaya su Momma suna a saman haɗaɗɗen family dining table nasu dake dining room a cikin parlourn, abincin dare suke ci, King bai fito ba tukun nan, yana cikin bedroom nasa, Jaish da Jawad basu wajen, daga Momma, Mama, Mummy, sai su Sarina, Fanan, Zunaira, Chuchu, Aunty MieMie, Aneesa ƴar Mama kenan, Akka ma bata kai ga ƙarisowa wajen ba, tana part nata, sai Obaid da Omaid da suma suke wajen.
A dukka faɗin girman KINGDOM OF POWER kuyanga guda ɗaya king Zuhair ya aminta da ita da ta kula masu da shashin abincinsu, kakkarfar macece mai jini a jikan nan, idan ka ganta sai ka rantse da Allah ta karɓi horo waje commander ZAFAR, irin matan nan ne da ake cewa mace mai kirar maza, gata doguwa samɓal, akwai kuyangu biyu da suke tayata aiki irin goge goge kitchen da sauransu, ita kuma ita kaɗai aka yardanwa da ta yi masu girki, sannan ita kaɗai take serving nasu abinci.
Amma abin da baku sani ba shi ne, ita fa Gimbiya Rahilarh ranar da king yake ɗakinta ita take yi mashi girki da kanta, hakan yana ɗaya daga cikin abin da yasa yafi sonta, saboda tana nuna mashi cewa yana da kima da girma tare da daraja a idanunta, tana nuna mashi cewa ya fi mata komai a duniyar nan, kunsan maza da shegen sun respect, nan take king ya zama mata kamar baby, ga shi dai zaki ne a waje, amma a cikin gida wajen Gimbiya Rahilarh ba'a magana, na yi shiru kada su jini a miƙa ni wajen commander ZAFAR ya ragargaje mun baki na rasa na shan Maltina mai sanyi.
To wannan kakkarfar kuyanga mai suna Zubaida ita kaɗai ta samu damar iznin shigowa cikin parlourn king ta yi serving na family, sun aminta da ita sosai, so abin da ya tayar da hayaniya a dining room ɗin yanzu ba komai bane fa ce rigima a tsakanin Mama da Momma, Mama da Momma sam basu shiri, basu haɗuwa inuwa ɗaya, tamkar wuta da audiga suke, Mamma izzar bala'i ke gareta, ga shege nuna isa da iko, sai ta nuna kamar ita ce uwar gida ta fi kowa iko a gidan, kuma ba ita ba ce uwar gida Mummy mahaifiyar Gimbiya Aunty MieMie ce uwar gida, amma da yake a tare king ya auresu sai mamar take ganin ai babu abin da Mummyn ma ta fita da shi, so ita ma uwar gida ce, dan haka dole a sanyata a tsagin da za'a sanya Mummy. Kun san fa uwargidaye daban suke, koma ina za'aje azo sune ke da gida, ko rabuwa ka yi da uwargidanka wlh baku rabuba, in dai kuna da yara to ko zaka mutu ita ce kai, ko ka saketa ita ke da iko da kai, ka jira girman yaranta kawai malam kasha mamaki......😅
Shiyasa ake son murza kambun uwar gida, dan a gaskiya ita ɗin daban take musamman idan ta haihu a gida, ai hajiyata ki ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya ki sha kuruminki tare da bin ƴaƴan nan naki da addu'a, duk wadda zata zo wlh daga baya ne, ko ya sakeki kece shi idan bai sani ba wahalar kawai ƴaƴan su girma ne! Mama dai ta dage ita ma uwar gida ce........ Allah mai iko 😅
Amma kuma Mama basu taɓa yin rigima da mummyn ba sai da Momma, saboda mummy mace ce da ko ka yi abu ma bata ɗaga idanu ta kalle ka, sau da dama Mamar tana takalarta da faɗa, amma ko kallon in da take bata yi, ita kuma Momma ainahin jinin Modarawa ne kada ku manta, basu barin kota kwana, hakan yasa bata bari idan Mama ta yi mata abu, abin a jininsu yake, kada kuga laifinta ku fara bincikar tarihin modarawa ku ji, basu yafiya.
Abin da ya faru yanzu bayan sun zauna a saman table za'a fara cin abinci, sai Momma ta ce da kuyanga Zubaida ta zuba mata abinci kafin king ya fito, ta zaɓi kalar da take so a zuba mata, da yake mama sarkin neman magana ce, sai ta yi maza ta ce ai ina a matsayinta na babba bata bada damar kowa ya ci wani abin ko abinci ba har sai king ya fito ko ruwa bata bada izinin a sha ba, yadda kuka san ita ce ta ajiye kowa da yake a saman table ɗin, shegen son girma ke gateta.
Jin haka yasa Gimbiya Aunty MieMie ta sanya baki, dan ita ma irin king ce, ba'a tauye hakkin wani a gabanta ta yi shiru, sai ta ce. "A'a Mama, Momma fa tana son cin abinci, kin sani ne ko yunwa take ji sasoi? Kuma ai shi daddy bai ce idan mun hau saman table mu rinƙa jiransa ba, mu ne nan muka ɗaurawa kanmu jiran nasa da muke yi kullum, dan haka idan wani yana jin yunwa yana da damar da zai ci abinci kafin dad ya fito, Zubaida ki zubawa Momma abin da ta buƙata yanzun nan ba tare da ɓata lokaci ba umarni nake baki!!".
Shikenan daga yin wannan magana Mama ta tada bala'i wai Aunty MieMie ta rainata dan ba ita ta haifeta ba! To daga nan ne fa abin yake ƙoƙarin zamar masu faɗa, dan kusan dukkansu sarakan zafin kai ne, Mummy ce kawai so silent da bata saka masu baki a cikin hayaniyar tasu ba, amma Momma ma ta saka baki, dan ta ce bata ga dalilin da zai sa Mama ta ce bata bada izinin a zuba mata abinci ba, wacece ita? Ko Mummy da take uwargida ran gida ma bata isa ta hana su cin abinci wai dan king bai fito ba bare kuma ita Mama, bata isa ba!! izza+izza ne yake aiki a nan.
Mama dai ta ce ta isa har ta yi yawa, dan haka dole a bi umarninta ko anki ko anso!!. Toh fa, dama ai ita da Momma ba'a shiri sam, basu haɗuwa waje guda!!.
Ita dai kuyanga Zubaida an sakata a cikin code, ga umarni gimbiya Aunty MieMie da kuma Momma sun bata a kan ta zuba masu abinci su ci, ga kuma umarnin da Mama ta bata na kada ta yarda ta zubawa kowa komai har sai king ya fito..... Wannan shi ne cakwakiya, tana tsaka mai wuya baiwar Allah, ta rasa zancen waye zata bi!.
Ga shi King kuma ya ce shi da kuyanga Zubaida kawai ya yarda, ita kaɗai zata rinƙa yin serving nasu abinci, babu wasu kuyangun da zasu zo masu kan abinci, baiwar Allah Zubaida tana ganin rayuwa, ita kaɗai take aikin zubawa wannan ta zubawa wannan, idan bata yi sauri ba su hauta da faɗa musamman Gimbiya Sarina da twins Obaid and Omaid sun fi kowa rashin kirki a cikin gidan......
Familyn king sun fara nasu kala kalar tsiyar, bari na haɗa kayana sai zuwa gobe muga ya za'ayi da wannan rikici na Mama da Momma, ga Kuyanga Zubaida dai a cikin wani hali, duk wanda bata bi umarninsa ba ta shiga uku, to ita ya zata yi da ranta kenan? Izza sam bata yi ba a rayuwa 😌
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
Share fisabilillahi 👏
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
🤍🔥𝗥𝗔𝗪𝗔𝗡𝗜𝗡 👑 𝗭𝗔𝗟𝗜𝗡𝗖𝗜🔥🤍
🔥CROWN OF INJUSTICE🔥
𝗠𝗔𝗟𝗟𝗔𝗞𝗜𝗡
❤️🔥FATEEMA ZAHRA MUSA ❤️🔥
(❤️A-K-A 𝑷𝑹𝑰𝑵𝑪𝑬𝑺𝑺 𝑻𝑬𝑬𝑴𝑨🔥)
🔥🤍T🔥🤍T🔥🤍W🔥🤍......💻
❤️𝑫𝑨𝑻𝑬 17/7/2024.....✍️📚🌹
For information 0816139058 Whatsapp me only!!.
🤍𝑺𝑻𝑬𝑷 1......✍️📚🔥
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
E____________16🔥
Momma dai ranta ya ɓaci sosai, hakan yasa ta miƙe da nufin ta bar parlourn dan ma kada su yi ɓatattciya, kuma ta sanya a ranta idan ta fita daga cikin parlourn nan ta dai'na cin abincin a wannan dining room ɗin kenan, sai dai wani, dama saboda mijinta take zuwa part ɗin nasa, shi ya tsara wannan tsari na a rinƙa haɗuwa a part ɗin nasa ana cin abinci.
Bata kai ga motsawa daga in da take ba suka ji gyaran murya daga bayansu. Ko basu juya ba sun san wannen, kuma sun san halinsa fa, shi ɗin ba uba bane mai wasa, baya ɗaukar wargi, yana da wasa da dariya da ƴaƴan nasa, amma baya taɓa bari su
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 75