ce ƴar Abu Abdussalam da aka ce yana da ƴaƴa maza biyu da mace ɗaya, yarinyar ma arab jallabiya launin white ne a jikinta, kanta babu ɗan'kwali, wannan kyakkyawan arab hair ɗin nata an ɗaure mata shi gida biyu kamar yadda Gimbiya Zunaira da kuma Chuchu suke yawan ɗaure nasu gashin, haka ita ma aka yi mata.
Fuska ba yabo ba fallasa ta tarbi wannan mata da ta zo da Leesharh. Saman sofa matar ta zauna, ita kuma Leesharh ta zauna a ƙasa saman wani haɗaɗɗen Turkey carpet mai bala'in laushi, har wani lumewa zaka ji kafafunka sun yi idan ka taka carpet ɗin.
Cikin girmamawa wannan mata ta ɗagawa hajiya babba gaisuwa. Cikin mutunta zuna hajiya ta amsa, da alama tana da kamala da dattaku, babu alamar walaƙanta mutane a tattare da ita duba da yadda ta karɓi su Leesharh cikin mutunci duk da tasan cewa tabbas Leesharh ƴar aiki ce, domin tun kafin Leesharh ɗin ta zo gidan tasan da hakan, kada ku manta kafin ma su zo sai an san da zuwansu an kuma san su waye su, so tasan aiki Leesharh ta zo yi, amma bata nuna irin kyama ko kyara ba, ta tarbesu da mutunci.
Sosai Leesharh ta ji jikinta ya yi sanyi na ganin yadda matar ta mutuntasu, ko ba'a gaya mata ba ta san cewa wannan mata itace hajiyar wannan aljannar duniyar bakiɗaya, amma ji yadda ta tarbesu kamar wasu ƴan uwanta, duk sai ta ji jikinta ya yi la'asar da ta fara tunanin to meyasa ake son cutar da su tun da dai alamu sun nuna su ɗin mutanen kirki ne?. Yarinta bai bari ta iya gane cewa yanzu ai masu kirki ake cutarwa ba, da zarar kana da kirki neman ganin bayanka ake yi, musamman idan ta haɗo da kana cikin siyasa, sarauta, da dai sauransu, idan ka ce zaka yi adalci ko ka yi wa al'umma hidima ai kana tsaka mai wuya a hannun abokan gaba sai dai Allah ya tsare!.
A fili ta furta Allah masani wadda sam bata san maganar ma ya fito ba, sai da ta ga hajiyar tana kallonta ne ta fahimci ashe ta yi magana.
Cike da tsoro ta yi ƙasa da kanta. Ita kuma hajiyar sai ta ce. "Turai yanaga kamar ƴar aikin namu bata da lafiya ko kuma wani abin yana damunta?".
Wani irin dum dum Leesharh ta ji gabanta ya bada bugu.
Matar da suka zo a tare ɗin ne wadda Hajiya Babba ta kira da Turai ta ce. "Hajiya Babba ai dole ki ganta a birkice haka, kema kinsan duk wanda zai shigo wannan gida sai ya razana, securitys ɗin nan naku masu fusatattun fuska da babu amnurin nan ba dole su birkita mutum komai jarumtarsa ba!".
Ƴar murmushi Hajiya Babba ta yi kafin ta dubi ƴar matashiyar yarinyar da ta tada kai da laps ɗinta ta ce. "Sharifat jeki ki kira mun Radia ta zo ta wuce da wannan yarinyar izuwa part na ma'aikata dan ta je ta huta, da alama akwai gajiya da firgici a tattare da ita".
Miƙewa zaune yarinyar ta yi, ɗan waro idanu waje ta yi irin mamakin nan lokacin da ta kalli Leesharh, da ƴar siririyar zazzaƙar voice ɗinta ta dubi Hajiya Babba. "Ummie she's so beautiful, Allah kyakkyawace sosai, harta kalar fatarta ya yi mun kyau".
Ƙasa da idanu Leesharh ta yi tare da sauke nannauyar ajiyar zuciya, yanzu ta kara tabbatarwa da kanta waɗan nan mutane mutanen kirki ne, ji yadda yarinyar gidan ma ta karɓeta kamar ba ƴar aikinsu ce ita ba. Allah wadarar mummunar aikin da ta zo aikatawa a kansu ta fara yi, sai dai kuma bata fa da wani zaɓin da ya wuce dole ta yi wannan aiki ko zata mutu kuwa, dan mahaifinta shi ne duniyarta. Babbar magana, wlh akwai cakwakiya da tashin hankali ba kaɗan ba a wannan part ɗin!.
Sharifat kyakkyawar yarinya ce sosai, amma a rayuwarta tana kaunar kyawawan mutane, idan taga mace kyakkyawa sai ta ce su ƙullah abota, haka take yi, shiyasa take kaunar yayanta Omar, yayan gimbiya Zunaira kenan, saboda fa kyakkywa ne sosai kamar Zunaira ɗin shi ma, idan kuka gansa kamar shi ya yi kansa, ga idanun nan nasa ba'a magana, so suna mugun shiri da Sharifat sosai! Shi ma a gidan nan yake, ba'a gidan kakarsa yake zama ba, ya fi jin daɗin zama a gidan nan saboda Sharifat ɗin babbar kawarsa kenan.
"Sharifat kenan, ai haka Aisha take da kyau, sai ma ta yi make up". Cewar Turai.
Murmushi Sharifat ta saki tana faɗin. "Kai bari Yah Omar ya zo zan gaya mashi ankawo ƴar aiki kyakkyawa wadda ta fishi kyau".
Girgiza kai Hajiya Babba ta yi kafin ta ce. "Da kuwa kinci bugu a hannunsa, GUYSON ɗin namu ne zaki ce wata ta fishi kyau? Kin manta me ya gaya maki na cewa babu wanda ya kaisa kyau a duniya ko? Faɗa mashi wata ta fisa kyau ina ga yau ko Abbunki ba zai iya kwatarki a hannunsa ba".
Ɗan turo baki ta yi tare da miƙewa ta nufi wani haɗaɗɗen curtain, yaye shi ta yi ta shige ta kofar da yake a wajen, tana tafiya tana ɗan juyowa ta kalli Leesharh, ita dai har ga Allah Leesharh ta yi mata kyau ba kaɗan ba, ga shi a tsawo ma tsawonsu zai iya zuwa ɗaya, shekaru ma haka, sai take jin dama ace Leesharh ƴar uwarta ce ta jini, kasancewar ita kaɗai ce mace a gidan, hakan baya yi mata daɗi, ƴan uwa maza kawai take da su, ita sam bata damu da kalar African skin ɗin Leesharh ɗin ba, ita dai kawai ta burgeta tunda kyakkyawa ce. (Ni kuwa na ce a'a Sharifatu baiwar Allah, ki nesanta zuciyarki da Leesharh, dan ita ɗin kyan ɗan macijine a gareku keda ƴan uwanki, cutarku tazo yi, duk da cewa ba laifinta bane, amma dai ku yi nesa da ita, kada ma ku jata a jiki, idan kuka jata a jiki ne ma zata samu damar cutar da kuɗin yadda yakamata, amma dai nayi shiru......🥱)
Shiru parlourn ya yi na tsawon lokaci, har Sharifat ta dawo daga wajen kiran Radia. A tare suka dawo da Radia ɗin, tana gaba tana binta a baya. Saman sofar da ta tashi ta koma ta kwanta tare da tada kai da laps ɗin Ummie ɗin nata.
Ita kuma Radia a gabansu ta zo ta tsugunna, balarabiya ce ita ɗin ma. Cikin girmamawa ta ce. "Ummie gani nan".
Nuna mata Leesharh da hannu Ummie ta yi tare da faɗin. "Ki wuce da ita part ɗinku, already ɗakinta is ready tun da Abbu ya gaya mun za'a kawo wata ƴar aiki nasa su Fadila suka gyara mata room ɗinta, dan haka ki ce Fadila ta nuna maki room da suka gyara mata ki kaita can". Ta kai karshen maganar tare da dawo da kallonta a kan Leesharh.
"A'isha ko?". Ta tambayeta.
Da sauri ta gyaɗa mata kai alamar e kanta na'a ƙasa kamar wata sahabiya.
"Okey tashi kuje ta kaiki room ɗinki, ki yi wanka ki kwanta ki huta, su Fadila zasu baki abinci, yau ki huta gobe sai ki fara aiki ko?". Cikin sanyin murya Ummie ta yi maganar, tana da cool voice sosai kamar yadda yanayinta ya nuna ita ɗin so silent ce.
Duk maganar da suke yi cikin harshen larabci suke yinsa.
Da okey Leesharh ta amsa mata tare da yi mata godiya, sannan ta miƙe tsaye, Radia ma ta miƙe ta yi gaba Leesharh ɗin ta rufa mata baya, sai kallonsu Sharifat yarinyar kirki take yi, taga Leesharh kyakkyawa jinin Africa tamu ta gida!.
Cigaba da hira sama sama Hajiya Babba da Turai suka yi, da alama sun saba. Ita kuwa Sharifat ta cigaba da kwanciyarta shiru abinta!.
KO YA RAYUWAR LEESHARH A WANNAN GIDA ZATA KASANCE?🤔 LOKACI NE ZAI NUNAMANA, ALKALAMINA KUMA YA BAYYANA MAKU KOMAI, AMMA DAI AKWAI GAGARUMIN CAKWAKIYA BA KAƊAN BA, DAN KUWA LEESHARH DOLEN UBANTA TA YI WANNAN AIKI IDAN TANA SON MAHAIFINTA!!.
🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️
GIDANSU KHADIJAH 💔😥
Maman Zainab tasha madarar mamaki sosai lokacin da Baban Zainab ya dawo daga kasuwa, yadda kuka san bai san da zamanta a gidan ba, ko ɗaga idanu ya kalleta yaki yi, da alama ma haushinta yake mugu mugun ji, ko kallon in da take bai son yi. Ko da ta kawo mashi abincin dare ma a yau kam bai ci ba, yaki ko kallon abincin nata ma, abin ya yi mugun ɗaga mata hankali na ƙin karawa, hakan yasa ta shiga gagarumin tashin hankali a in da ta shige cikin room ɗinta tare da rufo kofa, ta murzaki, sannan ta ɗauki wayarta tana kuka hawaye bibbiyu ta kira Aunty Hauwa a waya ta sanar da ita maganin nan fa bai yi aiki ba, hasali ma baban Zainab yaki yi mata magana, ko sannu yaki ce mata, in fact ma yaki kallon in da take, yaki ya ci abincin dare, su Khadijah ɗin ma ya sharesu yau kam, dama wani lokaci saboda su yake daurewa ya danne zuciya idan ta yi mashi laifi ya ci, to yau dai a gabansu ya ce ba zai ci ba, ya kuma wuce cikin bedroom ɗinsa ya kwanta, wannan abin ya yi matuƙar ɗagawa Khadija hankali, da yake ita hankali da ilimi ya ratsata sosai a yanzu, ga nutsuwa da sanin yakamata, tasan baban nata bai taɓa yin makamanciyar haka a gabansu ba tun da suke da shi, to me ya sauya shi lokaci guda haka kenan?.
Zeezee da take karama ma hankalinta ya tashi yau, ta shiga damuwa, haka dai suka hakura suna ɗan ci abincin kaɗan, sannan suka nufi nasu ɗakin suma, domin mamarsu ta rufe nata bedroom ɗin tana ciki, shi ma baban nasu haka. Har sun kwanta Khadija ta gagara yin barci, barci ya ƙaurace daga idanunta baiwar Allah, damuwa sun taru sun yi mata yawa, hakan yasa ta miƙe ta sauke ƙasa daga saman bed ɗin nasu.
A lokacin Zainab barci ya fara ɗaukarta, lallaɓawa ta yi ta ɗauki hijabin sallarta ta sanya a jikinta ta nufo waje. Tana tsoron fitowa saboda Haidar, amma bata da zaɓi dole ta je wajen kawunta Sadiq ta gaya mashi abin da yake faruwa, dan shi ne kaɗai zai iya gaya mata kalaman da zasu sanyata jin daɗi har ta samu barci, amma sai fargabar haɗuwa da Haidar take yi, addu'a take yi Allah yasa ya yi barci, dan idan bai yi barci ba ta je room ɗinsu a yanzu tabbas sai ya tsayar da ita in ta gama magana da Sadiq, idan kuma ya tsayar da ita ba makawa sai ta taɓa mata jiki, sai ya yi ƙoƙarin taɓa mata breast ɗinta ko ya ce zai yi kissing ɗinta, sam bashi da hankali ko na sayan pure water.
Sai dukan uku uku kirjinta yake yi, amma haka ta daure ta fito harabar gidan. Ai kuwa tana fitowa ta yi sa'ar cin karo da Sadiq ɗin yana tsaye a harabar gidan wajen fampon tsakar gida yana waya, da alama da mamarsa yake waya, shi ne ma yasa ya fito waje dan su sami keɓewa da sirri, ba zai yi waya da ita a gaban Haidar ba kenan, yadda ya nutsu sosai yake magana cikin mutunci da girmamawa ne zai tabbatar maka da cewa tabbas da mahaifiyarsa yake waya, dan idan da budurwace ba zai yi irin wannan nutsuwa ya bata dukkan hankalinsa tare da magana cikin girmamawa haka ba. Yaron kirki mai hankali da sanin darajar iyayensa.
A hankali kamar wata mai raɗa ta yi mashi sallama, tun fitowarta dama ya ganta, shiyasa yake ƙoƙarin yin sallama da mamar tasa, saboda yasan Khadija bata zuwa wajensa haka kawai, kuma idan ma kaganta a waje harabar gidan to fa girki take taya Mammarta, idan ba haka ba kullum tana ƙule a ciki abinta, ɗan gara ma Zainab tana fitowa waje jefi jefi. So yasan bazata fito haka kawai ba, barema a daren nan yasan dole da akwai matsala, hakan yasa ya yi sallama da mamar tasa a kan gobe da safe zai sake kiranta, daga nan ya kashe wayar tare da bawa Khadijahr dukkan attention ɗinsa.
Cikin sanyin murya ta fara gaya mashi halin da ake ciki, ta shiga damuwa sosai na ganin baban nata yaki ya ci abinci, bata ɓoyewa Sadiq komai ba ta gaya mashi tas, sannan ta kara da cewa abin ya hanata yin barci ne yasa ta fito.
Zama ya yi a bakin dakalin da aka kewaye fampon da shi, sannan ya ce ita ma ta zauna. Ba musu ta zauna a gefensa, hakika ya shiga damuwa sosai, irin wannan matsala yake gujewa maman Zainab tun tuniya yasa yake ta ƙoƙarin ganin bata sauka daga kan hanya ba, amma ta yi busur da zancensa ta yi son ranta, ga shi yanzu wankin hula yana neman kaita dare, tura ta kai bango baban Zainab ya fara juya mata baya, yanzu wa gari ya wayanwa?.
Rarrashin Khadija ɗin ya fara yi tare da bata hakurin, sannan ya sanar da ita dama a tsakanin mata da miji ana iya samun wannan matsala, aure ya gaji hakan, babanta mutumin kirki sosai da yake ɓuye masu ire iren wannan faɗa na mata da miji yasa basu san da hakan na faruwa ba, dan haka kada ta sanya damuwar kowa a ranta, ta yi hakuri zuwa da safe In Sha Allah babanta zuciyarsa zata sauko, dan shi mutun ne mai hakuri, ta yi hakuri komai ya yi zafi maganinsa Allah, ta koma cikin room ɗinsu ta ɗauro alwala ta gabatar da nafila raka'a biyu tare da rokan Ubangiji da ya kawo mata mafita, In Sha Allah zata samu dama ta yi barci, komai kuma zai wuce.
Haka dai ya cigaba da rarrashinta yana bata kwarin gwiwa har ta ji sanyi a ranta. Sai da ya tabbatar ta ji daɗi damuwarta ya gudu, sannan ya ce ta tashi ta shiga ciki. Duk da rashin yawan magana irin tata sai da ta ce. "Kawu Sadiq ka bari mu ɗan yi hira kaɗan, zan kara samun nutsuwa na sani".
Bai musa mata ba ya jata da hira har wuraren karfe 10, sannan ne ya ce ta tashi ta shiga ciki. Ba musu ta miƙe ranta a sake, fuska ba yabo ba fallasa ta wuce ciki tana yi mashi zai da safe. Shi ma sai da safe ya yi mata kafin ya miƙe ya koma cikin room ɗinsu a in da ya sami Haidar yana riƙe da wayarsa yana kallo, ko shakka bayayi fina finan batsa yake kallo duba da yadda ya takure jikinsa waje guda, kuma yasha kamasa yana kallon fina finan batsa dama, sau da dama yasha yi mashi nasiha a kan hakan babu kyau ya daina, amma ina ya yi nisa baya jin kira, hasalima idan bai kalli batsan ya samarwa da kansa nutsuwar hankalinsa da ya ɗaga ba baya iya yin barci, hakan yana ɗaya daga cikin abin da yasa yake son taɓa jikin Khadija sosai, shi bai kima ta dawo kwana a ɗakinsu ba, ɗan iska saboda yana kalle kalle batsa kullum yana cikin ɗagawa kansa hankali, dole ya yi ta ƙoƙarin latsa ƴar mutane. A kullum idan Sadiq ya fara yi mashi nasiha a kan ya dai'na kallon film irin haka, to wlh faɗa ne yake biyowa baya, basu wanyewa lafiya, hakan yasa Sadiq ɗin yanzu bai ci bi ta kansa ba, ya sharesa kawai tun da baya ji kuma ai ba yaro bane shi, ya fi Sadiq ɗin shekaru da shekaru biyu, kamata ya yi ace shi yake yi wa su Sadiq ɗin faɗa da nasiha, amma ina, ina ma yaga hankali ne wannan kam, sai dai Allah ya kyauta.
Yanzu ma girgiza kai kawai Sadiq ɗin ya yi tare da nufar nasa gadon, already da alwalar barcinsa a tattare da shi, dan har ma ya kwanta mamarsa ta kirasa ya tashi ya fita, so yanzu yana dawowa addu'ar barci kawai ya yi tare da kashe wayarsa ya kwanta, ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi.
A ɓangaren Khadija ita ma bayan ta yi sallar nafila raka'a biyu kamar yadda kawun nata ya ce, sannan ta rufe da shafai da witiri, hankalinta ya kara kwanciya sosai, ta ƙara samun nutsuwa sosai da sosai in da ta zo ta haye gadon ta kwanta, cikin ƙanƙanin lokaci barci ya ɗauketa, dama ita Zee already ta yi barci abinta.
Mamarsu kuwa, cikin kuka ta sanar da Aunty Hauwa halin da ake ciki. Hakuri Aunty Hauwar ta bata tare kuma da ce mata ta kwantar da hankalinta gobe da safe zata zo gidan, kada ta ji ta wani damu zasu yi maganin baban Zainab. Da haka dai ta rinƙa rarrashinta har ta hakura a nan barci ya yi awon gaba da ita, in takaice maku labari dai bata yi sallar mangariba bare isha, a haka barci ya saceta saboda kukan da ta sha.
(A gaskiya ina jin labarin gidansu Khadija tamkar true life story, wato tamkar gaskiya, wlh duk idan na zo rubuta part ɗin ji nake yi kamar gaske, saboda abu ne da yake faruwa yau da gobe a zahiriya sosai da sosai, Allah dai ka ƙara tsaremana imaninmu ka rabamu da ƙawaye jahilai.)
Washegari da safe kamar yadda suka saba haka Maman Zainab ta tashi tare da biyan bashin sallolin da suke a kanta na tun jiya, sannan ta nufi kitchen da nufin ta yi masu girki, kasancewar farar shinkafa da miya ta dafa masu daren jiya wadda basu ci ba, sai ta ɗauko shi ta sake ɗumama masu, saboda bai yi komai ba, kuma yana da yawan da bai kamata su zubar ba, so sai ta sake mayar da shi wuta ta ɗumama, shi ta sanyawa su Khadija a kulolin makarantarsu.
Suma su Khadijah suka yi wanka suka shirya kamar yadda suka saba, baban su ne kawai yaki fitowa, da yake dama sai maman Zainab ta haɗa mashi ruwan wanka sannan take tashinsa daga barci, to jiya dai ya rufe room door ɗinsa da key, koda ta kammala shirya masu komai kamar yadda ta saba ta nufi room ɗin nasa dan ta tashesa, sai ta ji kofar a rufe da key.
Kamar zata yi knocking, sai kuma ta hakura ganin cewa su Khadija suna nan, kuma tasan halinsa tun suna saurayi da budurwa, damone sarkin hakuri over, amma kuma idan ya zuciya wlh abin da zai sanya shi ya sauko ba karamar abu bace, kuma duk yadda yakai ga kawar da kai ga abu idan fa ya zuciya tura ta kai bango to fa mantawa yake yi da wata kawaici ko makamancin haka, yanzu haka a yadda yake cikin fushi sosai ɗin nan yana iya yi mata faɗa tatas sosai koda a gaban su Khadijah ɗin ne, zai manta da wani tarbiya.
Tuna hakan yasa ta fasa yin knocking na kofar ta juya izuwa nata room ɗin, bata sake bi ta kan su Khadijah ɗin bama ita ma. Bayin Allah da suka ga lokaci na ƙurewa zasu yi latti ga Khadijah suna dab da fara rubuta Exams, sai suka fito suka nufi wajen kawunsu Sadiq, dan ya kai su school kamar yadda ya saba, yau dai sun hakura da yin sallama da baban nasu tun da bai fito ba.
Knocking suka yi masu Sadiq a kofar ɗakin, ba'afi second ashirin ba sai ga Sadiq ɗin nan ya buɗe kofar ya fito. Shirye yake cikin dakakkiyar shaddar mai shegiyar kyau, da alama yau ma yana da class.
Har suna haɗa baki wajen cewa Uncle Sadiq ina kwana. Murmushi ya yi yana kallon Zainab sarkin tsiwa kafin ya amsa masu gaisuwar, yarinyar nan Zainab ba dai iyayi ba, haka take zama ta karewa maman Haidar da kakansu zagi fes kamar an aikota, bata da sauki, Khadija kam daga e sai a'a, sai kuma gyaɗa kai kamar ƙadangaruwa.
"Dama na shirya ku nake jira, ina da class karfe 7:30 dai'dai mu je ko?". Sadiq ya faɗa yana kai hannunsa ya ɗan bugi bakin Zee da take aikin turo shi kamar wadda aka zaga.
"Kai kawu Sadiq menayi maka to?". Ta faɗa tana ɗaure fuska.
Khadijah ce ta amsa mata da. "Kwaɗayin duka yake ji yasa ya dake ki, ko dai bai kai bane?".
Wani irin harara ta bi Khadija da shi. Shi dai Sadiq wucewa ya yi izuwa wajen mashin ɗin baban nasu, da yake key na a hannunsa, fito da mashin ɗin ya yi kamar yadda suka saba, ba ɓata lokaci ya ce su yi sauri su hau su tafi lokaci yana ƙurewa. Da sauri suka hau Zainab sai raki take yi. Da haka suka bar gida, shi kuwa Haidar yana can yana barcin asara, wani lokaci ma sai 10 yake tashi ya tafi kasuwa ko kuma wajen mamarsa or kakarsa, kullum aiki ɗaya, ya kusa yin aurema bai canza hali ba, ko waye zai ciyar mashi da matar idan ya yi auren? Shi da kasuwar ma sai yaga dama yake zuwa. Akwai matsala sosai, akwai case ba kaɗan ba.
Misalin karfe 9 dai'dai sai ga Aunty Hauwa ta nufo gidan kamar yadda ta faɗawa maman Zainab zata zo jiya. A lokacin baban Zainab bai fita ba, yana ciki, da alama yau ba zai je kasuwa da wuri ba, ita ma maman Zainab tana cikin ɗakinta ta yi zaman ƴan bori a saman tsakiyar gado, ta haɗa hannayenta ta buga uwar tagumi kamar wadda aka aikowa da wahayin yinsa, ta luluƙa duniyar tunanin ya zata yi da rayuwarta, har yanzu ta kasa iya gane cewa damar da Allah ya bata a baya ne take wasa da shi son ranta, tana yi kuma ba tare da godiya ga Allah ba, to yanzu damar tana neman kubce mata, ta kasa iya gane hakan ma bare ta yi ƙoƙarin dawo da damar izuwa gareta..... Tirƙashi, akwai matsala fa my people's, mu je dai zuwa.
A parlourn Aunty Hauwa ta zauna, ta tsantsara kwalliyarta cikin wata shegiyar lace mai kyan gaske, da alama ma case ɗin maman Zainab ɗin bai wani dameta ba, ta yi ɗaurin ture kaga tsiya a kanta irin yau ba mutuncin nan, sai wani kwaɓe fuska take yi kamar wadda taga kashi.
Fitowa maman Zainab ta yi daga room ɗinta cike da damuwar halin da take a ciki, tsawon shekarun nan da suka yi aure baban Zainab bai taɓa yi mata makamancin haka ba, har ya share tun jiya bai yi mata magana ba har yau, abin dole ya jefata cikin damuwa sosai, a maimakon ta kira mahaifiyarta ta sanar da ita abin da yake faruwa, sai ta sake kirawo Aunty Hauwa kuma.
"Hauwa ki zo mu shiga cikin bedroom, baban Zainab yana nan fa". Maman Zainab ta faɗa murya ƙasa ƙasa.
Okey Aunty Hauwa ta amsa tare da ɗaukar wata ƴar figaggiyar jakarta irin na dillalai, ga gyalenta dama a kafaɗa ta yafo shi kamar ba matar aure ba, burinta kawai su shiga ciki ta tambayi maman Zainab ɗin baban Zainab ya sha maganin? A ƙage take da ta ji ya sha ɗin ko bai sha ba?.
A haka ta miƙe da nufin su shiga cikin bedroom ɗin dan rashin hankali irin na maman Zainab da kuma damuwa da ya rufe mata idanu.
Tana miƙewa tsaye sai ga baban Zainab ya fito cikin shirinsa na shadda mai shegen kyau launin sky blue, ɗinkin manyan kaya ne, so ya ɗaura babbar rigar ma a sama, a takaice dai makurar shigar mutunci ya yi, da alama yau ma ba zai ci abincin maman Zainab ba, kamar dai daren jiya, dan dai ga shi ya kammala shirin fita abinsa.
"Sannu da fitowa, ina kwana?". Aunty Hauwa ta faɗa cikin sanyin murya.
Turus ya ja birki ya tsaya tare da juyo da kallonsa a kanta, wani irin faɗuwar gaba ya ji a lokacin da ya sauke idanunsa a kanta. Da ni da ku duka mun san cewa baban Zainab in ya shigo ya sami maman Zainab da bakuwa wlh ko kallon in da suke baya yi, baƙin suna gaishesa ma baya tsayawa, wani lokaci kafin ya amsa masu gaisuwar nasu ma ya kai bakin kofar ɗakinsa, amma yau sai ya tsaya tare da juyowa yana kallon Aunty Hauwa.
Maman Zainab ta ɗan yi mamaki, amma sai ta ce kila zai tambayi Aunty Hauwa ɗin ina ta je jiya ne, dan haka sai bata wani damu ba.
"Sannunki da zuwa Hauwa ya gida ya yara?". Ya faɗa yana bata full attention ɗinsa.
Murmushi ta sakar mashi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 47 Chapter of 75