mun san Mamma bata da kowa a duniya sama da Kamran, tana kaunarsa fiye da yadda take son kanta, kuna dai ganin yadda take kula da shi, ko nan da can bata son taga ya matsa, ace rana tsaka ya fita cikin wannan dajin, sannan ya dawo ya ce mata shi ba zai sake zama a nan ba wajen mutane zai tafi ya yi rayuwa? Kuna tunanin zuciyarta ba zai tarwatse ba? Hmmmm akwai case!.
"Pretty". Ya ambaci sunanta a hankali, ƙasa ƙasa kuma a ta cikin kunnuwanta.
Dakatawa da yin busar ta yi tare da juyowa gare shi. "Kamran lafiya ka kirani?". Ta yi tambayar tana riƙo hannayensa dukka biyu. Abin busar ta sanya mashi a hannunsa ɗaya, ɗayan hannun nasa kuma ta ɗaura shi a saman a shoulder ɗinta ta ɗan kwanto a saman kirjinsa.
"Pretty kin san menene soyayya?".
Tana daga kwance a jikinsa ta ce. "A'a ban sani ba, shima wani kalar abincin na Mammarka ko kuma fruits ne?". Ta yi maganar ba tare da ta ɗago ta kalle shi ba, tana kwance tana ganin zubar ruwar ƙorama abinta.
Ajiyar zuciya ya sauke, jiya wuni zunbur ya yi yana bincike cikin littatafan Mammarsa ba tare da sanin Mammar ba, a nan ne ya ci karo da wata littafi mai suna true love never end, da yake litattafin bata da yawa sosai, short story ne da bata wuci pepar ashirin ba, sai ya nutsu ya karanta, a nan ne ya samu abubuwa da dama har amsarsa na dan gane da aure, kasancewar a littafin ya karanta duk wahalar da jaruma da jarumin suka sha daga karshe sun yi aure sun mallaki juna, kuma sun haifi ƴaƴa, a nan ne ya fara tunanin kenan shi ma dai yana da baba? Ba iya mama bace kawai?. Ya dai samu abubuwa da dama a ciki littafin, ya kuma yi masu kyakkyawar fahimta, ya kuma tarawa kansa uban tarin tambayoyin da ƙwaƙwalwarsa take ƙoƙarin kasa ɗauka, ya kasa iya tambayar Mammarsa ina babansa? Ya kasa iya gaya mata labarin su Pretty, ya kuma rasa ta ina zai iya sanar da ita cewa an bashi auren Pretty, kuma da ya karanta wannan littafin ya fahimci yana son yarinyar nan Pretty, kuma zai aureta ɗin kamar yadda mum ɗinta ta bashi aurenta, duk ya kasa samun kwarin gwiwar iya sanar da mamma komai, ya shiga damuwa na wuce misali, sai saƙa da warwara yake yi na yadda zai ɓullowa da Mamma ta bashi amsoshinsa a kan waɗan nan al'amura.
Lallai akwai cakwakiya, finally ga shi dai Kamran yasan menene aure da ma ita kanta soyayyar, sannan kuma yasan cewa yanzu mace bata haihuwa ita kaɗai, har ya fara tunanin to shi ina nasa uban? Ga wani sabon cakwakiya kuma da Sweetie ta matsa mashi a kan su kurewa dajin nan tafiya ko akwai wasu mutane a wajen dajin, dan ita bata yarda da cewa suma warriors ɗin nan a cikin dajin nan suke ba. To Kamran fans ya kuke tunanin makomar Mamma idan har Kamran ya fita daga cikin wannan dajin yaga akwai mutane a wajen? Anya zai sake yarda ya zauna a dajin kuwa? Anya zai iya yin hakuri ya danne ba tare da ya buƙaci sanin ina mahaifinsa yake ba kuwa? One day one time da wuya idan bai tambayi Mamma da ta fito mashi da babansa ba, duk da yanzu yana tsoron tambayarta, amma dakamar wuya ya iya hakuri da babansa... Tashin hankali kenan, babbar magana!!. Forest ma ya kusa kamawa da wuta da alama!.
"Pretty soyayya ba abinci bane sarkin son cin abinci, kuma soyayya ba kayan fruits bane, wani abin ne na daban". Ya bata amsa ta hanyar raɗa mata a kunne.
Jin cewa ba abinci bane kuma ba kayan fruits bane soyayya yasa ta yi saurin ɗago da kanta daga saman kirjin nasa ta juyo garesa. "To menene kenan?".
Yadda ta ɗago da kan nata sai ya zama suna fuskantar juna. Tsura mata ido ya yi yana kallonta, tun da ya fahimci sonta yake yi sai ya dai'na jin wani irin yanayi tare da fargabar kallon cikin idonta, sai ya zamana ma idan bai kalli cikin idanun nata ba sam baya jin daɗi.
"Ya kake ta kallona haka Kamran? Na ce maka menene soyayyar baka bani amsa ba? Wajen yawo ne to? Ko dai wasu dabbobin ne?".
A hankali ya motsa kyawawan lips ɗinsa ya furta. "Kece soyayyar mana".
Kyafta idanunta sau biyu ta yi tare da sakar mashi wani irin cool murmushi mai kara mata matuƙar kyau, har dimples ɗinta suka lotsa. "Kai kam Kamran wani lokaci ka iya maganar banza, ni ce soyayya kuma? To ni dai sunana Pretty ba soyayya ba".
Tun daga yanayin maganar Pretty zaka fahimci duk wanda zai auri wannan yarinya yana ruwa kusa da kada, sai ya shirya shanye duk wani shirmenta har Allah ya gyara mashi ita, ko da yake yarinta ne sosai a kanta, ƴar shekara goma zuwa shaɗaya nawa take dama? Ai yarinya ce sosai.
Da yake shi Kamran ya saba da halin kayarsa, sai ya ɗan matso da face nasa dab da tata, ƙasa ƙasa kamar mai tsoron wani kada ya jisu ya ce. "Ai ban ce maki sunanki ne soyayya ba bare ki ce mun sunanki Pretty, duba idonta a wajen kamar na raƙumin dawa".
Da yake ba'a yi mata ta kyale sai da ɓallah mashi harara tare da faɗin. "Ai garani ma idon Raƙumin dawa ce da ni, kai kuma idonka kamar na wannan Rocky ɗin naka". Ta kai karshen maganar tana kara ɓallah mashi harara.
Murmushi kaɗan ya ɗan sakar mata kafin ya ce. "Na ji to, yanzu dai koma menene ki sani dai ina sonki".
Shiru ta ɗan yi, sai yanzu kalmar ina sonki ya fara dawo mata a cikin ƙwaƙwalwata, mum ɗinsu tana yawan gaya masu cewa ina sonku ƴaƴana, kune duniyata kuma kune komai nawa, ina alfarhari daku kuma ina son yin rayuwa da ku, na kasance da ku na kuma kula da ku, na baku tarbiya irin ta addinin Musulunci na kuma baku ilimin addini dana zamani, ina kaunarku fiye da yadda nake son kai'na.
Sosai maganganun mum ɗinta suka rinƙa yi mata zarya a cikin kunnuwanta zuwa ƙwaƙwalwarta, kenan yanzu shi ma Kamran irin son da yake yi mata kenan? Irin son da mum ɗinsu take yi mata?
Ganin ta luluƙa duniyar tunani ne yasa ya kai hannunsa ya ɗan shafi lallausan kumatunta haɗe da dogon kyakkyawar hancinta da ya zauna ɗas a face ɗinta.
"Kema kina sona ko?". Ya faɗa a hankali.
Kara kallon cikin kwayar idanunsa da kyau ta yi kafin ta ce. "Ni ban san menene ma'anar kalmar ina sonki ba, mum ɗinmu tana faɗa mana shi, so ni ban san me take nufi ba".
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya fara yi mata bayanin menene soyayya kamar yadda ya karanta a wancan littafin, sai dai ya ɓoye mata menene aure da kuma ganowa da ya yi cewa suna da iyaye maza, dukka ya ɓoye mata wannan, saboda a ƙananun shekarun nan nata ba fahimtar komai zata yi ba, sai dai ta kara tabka mashi shirme, dan haka sai ya yi mata bayanin abin da zata gane kawai cikin sauki.
Ɗan taɓe baki ta yi a lokacin da ya gama yi mata bayanin menene soyayyar. "Dama wannan ce soyayya? To ai ina sonka nima". Ta bashi amsa tana kallon cikin idonsa.
Ajiyar zuciya ya sauƙe haɗi da sakar mata cool murmushi mai matukar kyau, ya ji daɗi sosai. Tabbas kamar yadda ta faɗa tana son shi haka ne, tana son shi amma ba kamar yadda shi yake sonta ba, kunsan kowace zuciya tana son mai kyautata mata, to hakance, dole zasu so Kamran sosai, dan a yanzu shi ne komai nasu.
Cigaba da hirarsu mai shegen daɗi a tsakaninsu suka yi, yana kara fahimtar da ita yadda soyayya take, ta wani kasa kunne tana ɗaukan bayanai, ita kuwa Sweetie tana can tana barci abinta, ba ruwanta da hayaniya.
Sun jima a haka kafin nan ya ce mata zai koma gida ta tashi ya rakata wajen maɓoyarsu da yamma zai dawo su sha hira da soyayyarsu. Sam bata so tafiyarsa ba, kawai dan ba yadda zata yi ne, tana matuƙar jin daɗin kasancewa da shi, idan ya ce zai koma har ji take yi kamar ta yi kuka ko kuma ta bi bayansa su tafi a tare, amma ba hali. Haka ta miƙe tana turo baki, sai hakuri yake bata, har da goyata a bayansa ya yi izuwa wajen bakin ramin nasu, duk dan baya son ganin fushinta, duk dan ya lallaɓata ta yi farinciki kafin su rabu.
Da kyar ya iya sakata dariya kafin su rabu, sai da ta yi dariya mai sauti ma tukun nan, sannan ya ce ta shiga ciki kuma kada ta yarda ta tashi Sweetie daga barci, sannan kada ta sake fitowa waje sai ya dawo da yamma. Da okey kawai ta amsa mashi kafin ta sa kai ta wuce ciki. Shi kuma bayan ya tabbatar da ya rufesu da kyau sai ya nufi gida.
A bakin kofar shiga ƙogonsu ya ci karo da Rocky dake ta faman barci, da alama ya ci ya ƙoshi ne, wucewa ciki ya yi izuwa cikin ɗakinsa. Ga mamakinsa sai ya isko Mammarsa a cikin ɗakin nasa tana yi mashi bincike.
Bai nuna mata ya yi mamakin hakan ba, ya wuce kawai ya haye saman gadonsa yana faɗin. "Mamma sannu da hutawa ina abincina?".
Zuba mashi idanu sosai ta yi na ƴan sakanni kafin ta ce. "Kamran cire hular kankan nan bari na gani".
Da yake ya manta shap da zancen cewa Pretty ta yi mashi kitso, sai bai wani damu ba, yana kallon face ɗin mammar tasa ya cire hular.
Kun san fa idan mutun ya yi kitso koma ya take sai face ɗinsa ta ɗan canza, shi ne yasa Mamma ta iya ganewa, kuma da yake taga wannan uban tulin gashin nasa da idan ya sanya hula take cika hular duk ta ɓace, hakan yasa ta fahimci an taɓa mashi gashin, shi yasa ta ce ya cire hular ta gani, sam bata kawowa ranta cewa kitso ma aka yi mashi ba, ta dai fi tunanin cewa shi ne ya datse gashin nasa ya zubar.
Zaro idanu waje ta yi sosai tana kallon kitso guda biyun, tun da take da shi ko da sunan wasa bata taɓa yi mashi kitso ba, bata taɓa kwatanta yin kitso bama, dan ita gashin kanta baya kitsuwa saboda tsantsi, to a ina kuma ya samo kitso? Tasan dai ba shi ya yi wa kansa ba, dan bai iya ba.
Shi kuwa ganin yadda ta zaro idanun nan nata tana kallon kan nasa ne yasa ya yi saurin kai hannunsa saman gashin nasa dan ya ji menene ya sanyata zaro idanu haka?.
Ai bai san lokacin da ya miƙe tsaye a dubu ba time da ya ji kumbusa kumbusar kitson da rigimammiyarsa Pretty ta yi mashi. Yau ya shiga uku! Wani amsa zai bawa Mamma kenan? Me zai ce yau kuma? Ya mance da kitson ne da tun a hanya zai warwareta........
(Kamran fans yau ba zata yi maku ta daɗi ba😅 baku da amsar da zaku bawa Mamma, kuna tsaka mai wuya, Pretty ta kai ku ta baroku 😅 ku daɗi soyayya ba? To yau zaku ga soyayya kuwa😅)
Readers me kuke tunanin Mamma zata ce mashi? Wani action zata ɗauka? Shi ma wani action zai ɗauka dan kare kansa kada a raba shi da Pretty? Ga shi ya bayyanawa Pretty ɗin soyayyarsa, ya kenan zata kaya?. To ni dai bari na leƙa KINGDOM OF POWER na dawo, wata kila kafin nan Kamran ya samowa kansa mafita.
𝗞𝗜𝗡𝗚𝗗𝗢𝗠 𝗢𝗙 𝗣𝗢𝗪𝗘𝗥💪🔥
Haɗe gabakiɗaya family suke a saman dining table dake dining room ɗinsu na part ɗin King. Kuyanga Zubaida ta yi serving ɗinsu, cikin nutsuwa suke cin abincin nasu. Kowa yana saman table ɗin amma banda Yah Jawad, Yah Jaish and Gimbiya Chuchu dake cikin part ɗin Akka, taki fitowa, Akka ta fito daning room ta barta kwance a saman gado, wai sai anjuma kaɗan zata sha complex or coffee ko dai wani abin mara nauyi, dan bata jin yunwa a yanzu.
Obaid and Omaid duk suna a saman haɗaɗɗiyar dining table ɗin, abincinsu kawai suke ci cikin natsuwa, sai ka rantse da Allah babu su a cikin room ɗin, auta duk ta damu na rashin ganin gimbiya Chuchu a room ɗin, ita kuma Sarina sai faman hararar Aneesa take yi sarakai waɗan da basa shiri, sai mayar mata da martanin hararar Aneesa ɗin ma take yi.
Obaid and Omaid dai har yanzu suna nan suna shirya kalar azabar da za su yi wa Mama, basu janye wannan kuduri nasu ba.
King ne ya ɗan yi gyaran murya tare da fara yin magana kamar haka. "Omar dai uncle Abu Abdussalam ya ce ba zai dawo this week ba, na yi na yi amma ya ce wlh na fita idonsa na bar mashi guyson ɗinsa ya kara mashi hutun koda na one month ne kafin ya dawo ya cigaba da karatu, so mummynsa sai ki yi hakuri da shirya mashi walimar sai next month, ku kuma Obaid and Omaid sai next week zaku koma, dama saboda Omar zai dawo ne yasa na yarda zaku koma, to tunda an sake riƙe mun shi nima bari na sake riƙeku a nan kaɗan tun da ma ku baku koma school ba, ke kuma Sarina ina son ki mayar da hankalinki da kyau, kada na kara ji ko ganin wani bako ya zo wajenki, nasa a saki su Yusuf bayan Zafar ya horasu da kyau". Ya kai karshen maganar yana kallon Mommar Zunaira.
Momma ɗin dai bata ce komai ba, domin yayanta ne Abu Abdussalam ɗin, kuma shi ya hana Omar dawowa, ya zata yi da ya wuce ta yi shiru, bata da ta cewa, ita kuma mummy sai cewa ta yi. "Kai gaskiya uncle Abu Abdussalam ya yi hakuri ya bar nana Guyson ɗin mu ya dawo, muna kewarsa sosai fa".
Mama ce ta wani ɓalle masu kallon banza tare da turɓene fuska kamar wadda taga wani abin kyamar.
"Daddy please ka barni mana na je wajen su Uncle ɗin, ba sai mu dawo a tare da Yah Omar ɗin ba". Cewar auta, ta yi maganar tana turo baki.
"Wani zuwa kuma bayan an buɗe school?" King ya bata amsa.
Turo baki kawai ta yi, ta ji babu daɗi, tun kafin a buɗe makaranta take ta son zuwa, amma aka hanata.
"Bari na dubo Aunty Chuchu". Cewar autar, ta yi maganar tare da miƙewa ta nufi hanyar fita daga room ɗin. Sauri sauri ta yi ta fita dan ma kada daddyn nata ya ce ta zawo sai sun ƙarisa cin abinci, dan Akka ta gaya mashi cewa Chuchu ta ce tana ƙoshe bata jin yunwa da ya tambaya.
Kai tsaye part ɗin Akka ta nufa, dan tasan a can zata sameta, bata jin daɗi ne a duk lokacin da take waje ba tare da Chuchu ba, sun yi matukar shaƙuwa.
Ta zo wucewa ta part ɗin Yah Jaish ne Yah Jawad ya fito daga ciki, bayan ya yi sallolin da suke a kansa ne ya yi wanka ya yi shirin barci sai ya nufi part ɗin Jaish kamar yadda suka saba, a nan suka ci abincin dare suka ɗan yi hira kaɗan, kasancewar yana da aikin da zai yi sosai shi ma kuma Jaish ɗin akwai wani bincike da yake yi a kan wata ma'aikata da suke zargin tana haɗa kwayoyin cuta da kwayoyin magunguna na shan al'umma, suna watsa cutar ta wannan hanyar, a matsayinsa na babban ɗan jarida ya kuma samu information sosai a kan ma'aikatan, shi ne yake ƙoƙarin bincikarsu ya tabbatar da abin da jama'a suke zargin gaskiya ce kafin ya fitar da bayanan, wannan dalilin yasa yau suka yi sallama da juna da wuri, saboda duk suna da tulin aiki a gabansu.
Yana fitowa suka ci karo da auta. "Good evening Yah Jawad". Ta faɗa tana ƙoƙarin wucesa.
"Zunaira ina zaki je kike sauri haka? And then ban hanaku yawo da kayan barci babu hijabi haka a cikin gidan nan ba?".
Dakatawa ta yi daga tafiyar da take yi, ɗan turo baki kaɗan ta yi kafin ta ce. "Kayi hakuri ba zan sake ba, na manta ne".
Shiru ya ɗan yi mata na ƴan sakani kafin ya ce. "To ina zaki je haka?".
"Wajen Aunty Chuchu zan je, bata zo dining room bane, tana part ɗin Akka, shi ne zan je in dubota". Ta bashi amsa.
"Idan kin je ki ce ta zo ina son ganinta, ta same ni a part ɗina". Yana kai karshen maganar yasa kai ya wuce abinsa. Ita ma cikin sauri ta wuce izuwa wajen elevatorn da zai kaita part ɗin Akka.
Kwance ta isko Chuchu a saman bed, tana sanye cikin kayan barci riga da dogon wando masu kyau launin maroon color, kayan barcin yana da hula mai kyan gaske, so ta sanya hular a kanta, sai latsa wayar Akka take yi dan Yah Jawad ya kwace mata nata wayar idan baku manta ba.
Saman bed ɗin auta ta haye tare da cewa. "Aunty Chuchu shi ne baki nemeni ba ko? To Yah Jawad yana kiranki".
Zaro idanu waje Chuchu ta yi tare da miƙewa zaune. "Nashiga ukuna! Me kuma na sake aikatawa Yah Jawad da yake nemana?! Ni wlh Allah sai na kai shi kara wajen daddy in dai ya sake bani punishment, kuma sai na gayawa Akka ma, na gaji da shan wannan bakin azaba, haba wai ni kaɗai ce a gidan?". Cikin tsiwa ta yi maganar.
Kwanciya ita dai auta ta yi tare da jawo pillow ta rungume haɗe da karɓar wayar Akka dake hannun Gimbiya Chuchun, sannan ta ce. "Allah ni ban san meyasa Aunty Chuchu kike ganin laifin Yah Jawad ba, yana da saukin kai fa, kuma yana da kirki".
Duka ta kaiwa autar a baki tana faɗin. "Tun wuri ki yi istigifari, dan Yah Jawad kam sam bai bi hanyar da saukin kai ya bi ba, mugu ne na karshe, kuma wlh sai na gayawa uncle Abbas duk muguntar da ya yi mun, Allah har na fara tsanarsa sosai, amma fa kada ki gayawa kowa na ce na tsanesa fa".
Hannu auta ta kai ta toshe ɗan bakinta da shi tare da zaro idanu waje. "Yah Jawad ɗin kika tsana Aunty Chuchu? Yayan mu ne fa, innalillahi". Tana magana tana zaro idanu!.
"Ke zaki yi mun shiru ne ko dai kina gaya mun yayan mu ne? To ni dai bana son shi, mugu ne, kuma idan kika faɗawa wani ko wata nace hakan daga yau mun bata".
Girgiza kai auta ta fara yi tana faɗin. "Ba zan gayawa kowa ba, amma dan Allah Aunty Chuchu ki dai'na cewa kin tsanesa, please, wlh ni bana son jin wannan kalma".
Ƙoƙarin sauka kasa daga saman bed ɗin ta yi tana faɗin. "Zan daina faɗa, amma dai ba zan cire tsanarsa a rai'na ba, sai ya yi ta azabtar da mutane dan mugunta, Allah bari na je na amsa kiransa, idan ya bani wata punishment ɗin kamar a gaban uncle Abbas aka yi, sai na gaya mashi, kuma in gayawa Akka da daddy dukka". Tana kai karshen maganar ta sauko kasa, sai turo baki take yi ta nufi waje, haushi yasa ta manta da cewa kayan barci ne a jikinta kuma bata ɗauki hijabi ba, haka ta nufi part ɗinsa tana kunkuni a cikin ranta, sai faɗi take in dai ya ci zalinta yau to wlh sai ta kai kararsa wajen uncle Abbas, sai dai ya yi duk abin da zai yi mata mugu kawai.
Bakinta a ɗauke da sallama ta shigo part ɗin nasa. Daga jin yadda ta yi sallamar kasan a ƙule take da bakinciki har wuya.
Babu kowa a parlourn, kuyangu masu yi mashi gyara ma sun kammala aikinsu sun fice. Kai tsaye bedroom ɗinsa ta nufa. Ƙasa ƙasa ta yi sallama tare da tura kofar ta shiga ba tare da jira izininsa ba, dan ita fa haushin da take ji yasa ta manta ma a ina take tukun nan, sai kunkuni take yi tana tsine mashi a cikin ranta.
Yana zaune a saman bed ɗinsa, ya tasa laptop a gaba yana aiki a kan aikin da King ya ba wa Companynsa na gina gidan marayu, aikin yake ta fama da shi. Ta wutsiyar idanunsa ya kalleta. Wani irin bakinciki da kishi ne ya taso mashi, hakan yasa ya ɗaure fuska sosai kamar wadda aka aikowa da saƙon mutuwa, yauma da kayan barci ta fito kenan? Ya..................
Lokacin shan Maltina ta yi🥱
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
Share fisabilillahi 👏
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
🤍🔥𝗥𝗔𝗪𝗔𝗡𝗜𝗡 👑 𝗭𝗔𝗟𝗜𝗡𝗖𝗜🔥🤍
🔥CROWN OF INJUSTICE🔥
𝗠𝗔𝗟𝗟𝗔𝗞𝗜𝗡
❤️🔥FATEEMA ZAHRA MUSA ❤️🔥
(❤️A-K-A 𝑷𝑹𝑰𝑵𝑪𝑬𝑺𝑺 𝑻𝑬𝑬𝑴𝑨🔥)
🔥🤍T🔥🤍T🔥🤍W🔥🤍......💻
❤️𝑫𝑨𝑻𝑬 15/8/2024.....✍️📚🌹
For information 08161390581 Whatsapp me only!!.
🤍𝑺𝑻𝑬𝑷 1......✍️📚🔥
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
E____________36🔥
Yana zaune a saman bed ɗinsa, ya tasa laptop a gaba yana aiki a kan aikin da King ya ba wa Companynsa na gina gidan marayu, aikin yake ta fama da shi. Ta wutsiyar idanunsa ya kalleta. Wani irin bakinciki da kishi ne ya taso mashi, hakan yasa ya ɗaure fuska sosai kamar wadda aka aikowa da saƙon mutuwa, yauma da kayan barci ta fito kenan? Ya tambayi kansa da kansa a cikin zuciyarsa.
Ita kuwa gabansa ta nufo, sam bata tuna komai ba. A ɗan nesa da shi kaɗan ta tsaya tare da cewa. "Yah Jawad gani nan".
Tamkar bai san da shigowarta room ɗin ba, aikin gabansa kawai ya cigaba da yi, sai dai kuma a zahirin gaskiya ya kasa yin aikin dai'dai saboda ɓacin rai, hankalinsa kuma yana kanta, tunanin kalar hukuncin da zai yi mata kawai yake yi.
Ta jima a tsaye a wajen almost 10 mins bai ko ɗaga idanu ya kalleta ba, aikinsa kawai yake yi na latsa laptop ɗin buge dan kada ta gane hankalinsa baya a kan aikin.
"Yah Jawad in ta fi ne?". Ta yi maganar kamar zata fasa kuka, saboda ta gaji da tsayuwa, ta ga bashi da niyar kulata, kuma yau ta sha alwashin wlh ba zata tsaya a cuceta ba, idan ya ce ta yi kneel down ko makamancin haka to wlh guduwa wajen Akka zata yi, sai dai ya bita can ya kakkaryata idan yana so...... Lallai Chuchu ta fara girma, abin ya fara kureta........😅
Sai da suka kara good 5 mins a haka kafin nan ya ɗan ture laptop ɗin daga gabansa izuwa gefensa, ba tare da ya ɗago ya kalli in da take ba ya ce. "Zo nan ki yi mun kneel down, domin yau sai na koya maki hankali sosai, ke kunnanki baya jin magana ko Jannat? To yau zai fara jin magana dole........"
Bai gama rufe baki ba ta watsa a guje zata nufi waje, dama ta ce wlh ba wani hukuncinsa da zata karɓa yau, yana yin yunkurin hukuntata zata gudu, aikuwa sai ga shi ta ruga a guje zata yi waje.
Wani irin miƙewa ya yi babu shiri, dan yasan idan ya barta ta gudu ya shiga tara da Akka na farko, na biyu kuma bai ga dalilin da zai sanya yana yi mata magana zata gudu ba, a cikin kannen nasu ma fa ita da auta sune kanana, amma tsabar ta rai'na shi ne yana magana zata gudu? Lallai yau dole ta ci duka, ba ma zai yiwu ya barta ta gudu ba ai, dole ya kamota ta karɓi hukuncin dama bai taɓa yi ma kowa daga cikin kannen nasu ba, ko Sarina da take sarkin rashin ji yau hukuncin da zai yi wa Chuchu bai taɓa yi wa Sarina ɗin ba, sannan ya ja mata kunne a kan idan ta gayawa Akka ko uncles Abbas sai ya karairayata........ (Ku ji mun mugunta, a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 50 Chapter of 75