Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dakeka a hanaka kuka, ya azabtar da ita kuma ya ce kada ta gayawa kowa🤔 Allah Yah Jawad ma mugu ne) Bata kai ga isa kofar ɗakin ba ya damkota ta baya, duk da tasan cewa ko ta yi ihu babu wanda zai iya jinta a cikin gidan, saboda ainahin kofar shiga part ɗin nasa ma a rufe, tana shiga kofar ta rufe, ga shi izuwa yanzu tasan kowa ya rufe kofofin part ɗinsa, koda bama haka ba yanayin tsarin ginin gidan mawuyacin abu ne tana cikin wani part ta yi ihu a jita a wajen, hakan ba zai yi ba. Amma duk da haka hakan bai hana ta waje baki zata kurma mashi ihu ba, domin ta tsarorata da kamota da ya yi, bata yi tsammanin zai yi yunƙurin bin bayanta har ma ya kamata ba, ta yi tunanin zata iya tsira ne ma yasa ta fara gudun, tasan ba komai yake kulawa ba, so a tunaninta idan ta gudu ma zai kyaleta ya ce wata kila da safe zai kamata, amma sai ta ji an damkota ta baya, shi ne abin ya razanata da har yasa ta waje baki da karfin gaske zata zunduma ihu, ga tsoron kalar hukuncin da zai yi mata, yanzu ma bata gudu ba ma ya ce ta yi kneel down bare kuma ya ce ta yi ta ki yi zata gudu? Ai ita da kanta tasan hukunci ya karu sosai!. Ina duk da yasan ba wani jin ihun nata family zasu yi ba, amma bai bari ta yi shi ba, tana waje ɗan bakin yasa hannu ya toshe mata bakin nata, ransa ya sosu matuƙa, duk cikin sisters ɗinsu babu wanda ya taɓa yi mashi makamancin abin da ta yi mashi, bai san cewa idan ka cina takurawa mutun dama ya kansa ya rage tsoronka idan ma yana ji ba, takura mata da yake yi ne yasa ta rage jin tsoronsa da har ma take kiransa da mugu, yanzu da Yah Jaish ne ya kirata ai ko yankata yake yi ba zata tsallake abin da ya ce ba, saboda me? Saboda da ni da ku dukka mun san Yah Jaish dai ba wanda ya ishe shi kallo a cikin kannen nasa, baya kulasu kuma baya bi da kansu, kunga kuwa dole a ji shakkarsa sosai, shi ma dai Yah Jawad ɗin chuchu kawai ya sakawa ido, kuma dani da ku duk mun san dalilinsa na yin hakan. "Stay quiet, if not a cikin daren nan zan kakkaryaki na zubar da kasusuwanki a dustbin". Ƙasa ƙasa sosai ya yi maganar, ya kuma kai karshen maganar tare da zame hannunsa daga saman ɗan bakin nata. Wani irin kermar tsoro jikinta ya fara yi, danasanin abin da ta aikata ta fara yi, yau dai ta shiga uku ta lalace, haka take ta faɗi a cikin ranta. Saketa ya yi tare da juyo da ita suna fuskantar juna, sannan ya kai hannunsa ya damko wannan arab hair ɗin nata, saboda hular kanta ya cire tun lokacin da ta watsa a guje zata yi waje, so sai ya zamana babu ɗankwali a kan nata, hakan ya bashi damar damko mata kyakkyawar gashinta da ta ɗaure shi kashi biyu. Da karfi ya danki gashin nata tare da jan shi baya sosai, hakan yasa dan dole babu shiri sai da ta ɗago kanta sama, wani irin azaba ne ta ji ya ziyarceta lokaci guda. "Kin girma ko Jannat? Har inai maki magana zaki gudu ko?". Kai ta fara girgiza mashi ba bakin yin magana, sai wasu zafafan hawayen azaba da suka cika mata idanu, kan ka ce me sun fara wanke mata fuska, amma fa a cikin ranta faɗi take yi wlh yana sakinta sai ta sake watsawa a guje, kuma yau ba sai gobe ba sai ta gayawa uncle Abbas muguntar da yake yi masu ita da su Sarina, sannan zata gayawa Akka da daddy, wlh ba zata hakura da kudurinta na gaya masu ba, ko dan su samu sassauci a kan irin cin zalinsu da yake yi, duk sai ta ji ta kara tsanarsa sosai. "Zaki yi mun shiru ne ko sai na ɗauko belt?". Ya yi maganar yana kai kallonsa izuwa saman bed ɗinsa, wayarsa ce take kara alamar shigowar kira. Kara jan mata gashi baya ya yi da ƙarfi, tare da dawo da kallonsa a kanta. Ba komai ne yake kona mashi rai ba face fitowa da kayan barci da ta yi, kishi ne kawai yake cinsa a zuciya yasa yake azabtar da ita har haka. Izuwa yanzu shi da kansa ya fahimci cewa tabbas uncle Abbas gaskiya yake gaya mashi na cewa yana son Jannat, domin kuwa idan har baya sonta ba zai yi kishinta har haka ba, wannan kishi ya wuce na yaya da kanwa sai dai mata da miji, kuma ba zai rinƙa damuwa da son ya ganta har haka ba, yanzu da yasa auta ta kirata a fili idan ta zo dama wayarta zai bata, a zahirin abin da yake cikin zuciyarsa kuma ba wayar yake son bata ba, ganinta yake son yi, dan yana kewarta, shi ne gaskiya!!. Amma kuma shi fa wai a haka so yake ya cire son nata a ransa, saboda a cewarsa ita ɗin sistersa ce kawai, kuma ta yi ƙanƙantar da zai iya cewa yana so, bugu da kari ba zai iya jawa kansa rai'ni na cewa zai aureta ba, idan ya yi haka ai yagama da kansa, ya jawa kansa rai'ni, shi ne yasa tun farko yake kaucewa yaki yarda da cewa yana sonta, dan bai son rai'ni, yanzu kuma da ya fahimci hakan yake ƙoƙarin cire son nata a ransa. Akwai cakwakiya ga Mammie ɗinsa ma kun dai ji bata kaunar wannan haɗin, uncle Abbas kuma fatansa kenan, wai ma to meyasa Mammien bata son haɗin Jawad ɗin da Chuchun? Akwai dai wata a ƙasa gaskiya. Kasa iya yi mashi shirun ta yi, sai ma kara karfin gudu hawayen nata suka yi, sakamakon ya kara ja mata gashi kanta baya, zafi ya karu, dan haka ita ma sai ta kara kukan nata. Har cikin ransa yake jin zafin wannan kuka da take yi kamar yadda ita kuma take jin zafin jan mata gashin da yake yi. Ya yi iya kar yinsa, ya yi mata iya barazanar da zai yi mata akan ta yi shiru amma taki, bashi da zaɓin da ya wuce ya sakin mata gashi idan har yana son ta yi shiru, zuciyarsa ba zata iya jurar ganin kukan nata ba, dan haka sai ya zame hannunsa daga kan nata tare da gyara tsayuwarsa da nufin ya fara magana, ya gaya mata kalar hukuncin da zai yi mata a yau, dan ba zai barta ba. Ai kuwa yana saketa ta sake watsawa a guje ta nufi waje. Ba shiri ya sake rufa mata baya a karo na biyu. Tana fitowa parlourn ya damkota, da hannu ɗaya ya ɗagata sama, ɗayan hannunsa kuma yasa ya toshe mata baki saboda waje bakin da ta yi zata zunduma mashi ihu. Kai tsaye sai saman carpet dake a gaban bed ɗinsa ya sauketa, wani irin ɗaure fuska sosai ya yi kamar hadari, tamkar bai taɓa sanin me ake kira da murmushi ba. Tsawa ya daka mata a kan ta zube gwiwowinta a kasa ko kuka ya karairayata a cikin daren nan, ashe abin nata har ya kai haka? Dole ya yi mata hukunci mai zafi tun da rai'ni ya fara shiga tsakaninsu, irin wannan rai'nin yake gudu yasa yaki yarda da yana sonta yake kuma ƙoƙarin yin patali da soyayyar tata daga cikin zuciyarsa, sai ga shi tun ma bai bayyana mata yana son nata ba, tun bai bayyana wa kowa bama rainin ta fara shiga tsakaninsu, dole ya ɗauki mataki!. Jikinta na kerma ta zube gwiwowinta a ƙasa tana mai cigaba da yin kukanta. Remote na door room ɗinsa ya ɗauka ya rufe kofar mai gabaɗaya, yau ba ita babu fita kenan, sannan ya wuce dressing room ɗinsa ya ɗauko ɗaya daga cikin belt ɗinsa mai mugun zafi yadda kuka san da gaske zai iya zaneta ɗin, ya wani ɗaure fuska irin babu wasan nan, bai san shi so ba'a kawo mashi wargi ba, ba ruwansa da shekaru ko girma, in dai ya shiga zuciya to sai ya yi pata pata da duk wasu dokoki ko matakan da mutun yasawa kansa, so ai bashi da adalci wani lokaci, sai ya kaika ga son wadda kai da kanka kasan ka kusa haifarta, dan bala'i ya barka ka yi ta fama kana ɗawainiya, to wannan irin shi ne a tsakanin Yah Jawad dan Aunty Chuchunmu fashion babynmu ƴar wanka. Yo ko dan shegen iya ɗaukar wankarki da iya gayu, ki yi gayu ya zauna a jikinki kamar dan ke aka yi ba dole ma Yah Jawad ya sarara maki ba, dole ba zai iya jure wuni bai sanyaki a idanunsa ba, irin wannan haɗuwa da kike yi, ga zuba kamshi kamar me, duk wasu perfume na Momma ke da auta sai kun bi kun karar mata, ai dole ki sanya zuciyar bawan Allah cikin tunaninki kullum da ko yaushe, dole ya rinƙa fakewa da kwace maki waya dan ya rinƙa sami damar ganinki, shiyasa yake zuwa part na Akka wai ya je duba Akkar da ba shiri suke yi ba, ba wani nan mun san komai ke yake zuwa gani, me zai yi da ganin fuskar Akka da daddare fisabilillahi? Salon ya yi mafarkin wannan masifaffitar tsohuwar? Gimbiyarsa yake zuwa gani ya fake da Akka, to yanzu dai mu kam mu gano komai ato, sai dai ya ɓoyewa su daddy, Momma, mummy, Mammiensa, da kuma su Jaish, amma ba dai ya ɓoyewa PRINCESS TEEMA da tawagarta ba ko my people's? Ba zai ɓoye mana komai ba!. A bakin bed ɗin ya dawo ya zauna ta yadda suna fuskantar juna. Ganin shi da belt a hannu yasa ta ƙara ruɗewa sosai, nan take jikinta ya kara tsananta kerman da yake yi. A hanzarce ta kai hannu ta riƙo kyawawan fararen tafukansa ta wajen gwiwowinsa, kuka mai sauti ta fashe mashi da shi tana faɗin. "Dan girman Allah Yah Jawad kada ka dakeni, ba zan sake ba, wlh na duba, bana son duka, last week ma da uncle a school ya mun bulala ɗaya a hannu Allah sai da hannuna ya kumbura, wlh tsoron duka nake ji, ba zan sake ba, ka bani wani punishment ɗin amma banda duka, wayyo Allah Momma na na shiga uku, uncle Abbas kazo ka ceceni". Tana yin magana tare da ƙara ƙanƙame kafafun nasa sosai, tana kuma tsananta kukan da take yi. Zafi sosai zuciyarsa take yi mashi na jin kukan nata, amma a maimakon ya rarrasheta ta yi shiru, sai ya jefa mata tambaya kamar haka. "Me kika yi wa uncle ɗin naku ya dakeki? Kuma wani uncle ɗin naku ne?". Tana kuka sosai kamar ranta zai fita, dan ita harga Allah bata son zancen duka, tun da take ma a makaranta ne kawai aka taɓa dukanta, muguwar tsoron duka take ji, "Babu abin da na yi mashi, ƴan class ne suna ta surutu shi ne ya zo ya haɗe mu gabaɗaya ya yi mana bulala ɗai ɗai". Ta bashi amsa tana ɗan kwantar da kanta a saman kafafun nasa, domin zafi wuyarta yake yi mata, ta ci kuka sosai, sannan ga jan mata gashi da ya yi yasa ta ɗage wuyarsa sama da har ya kusa sagewa a haka, so zafi yake yi mata da ba zata iya jurar cigaba da ɗaga shi ba. Wani irin yanayi ya tsinci kansa a ciki, abubuwan sun haɗe mashi, ga kukanta da yake taɓa mashi zuciya, ga kishin ta fito da kayan barci a gefe, sannan ga ɓacin ran uncle nasu ya dakar mashi ita, ta wani bangaren kuma ba haushin abin da ta yi mashi na yana magana ta watsa a guje, yanzu kuma ta kwantar mashi da kanta a jikinsa, duk sai ya ji wasu damuwar sun ragun mashi ma.......🙄 Muryarta ne ya dagi dodan kunnuwarsa cikin kuka take faɗin. "Yah Jawad na tuba ba zan sake ba, dan Allah kada ka dakeni, na yi alkawarin ba zan sake ɗin ba". Bai san lokacin da ya sassauta muryarsa a gareta ƙasa ƙasa ya ce. "Sau nawa kike ce mun ba zaki sake ba kuma ki sake kara yin abin da na hanaki ɗin Jannat?". Kara kwantar da kanta da kyau a saman kafafun nasa ta yi, tana shessheƙar kuka hawaye na zuba ta fara magana da kyar da kyar. "Yanzu da gaske nake yi ba zan sake ba, wlh na tuba......" "Kenan da can baya duk ba da gaske kike yi ba ko?". Ya katseta ta hanyar jefa mata wannan tambayar. Girgiza mashi kai ta shiga yi tare da kara ƙanƙame kafafun nasa ta shiga bashi hakuri. "A'a dukka da gaske nake yi, amma wannan shi ne babban da gaske, ba zan sake ba........". (Oho Allah Chuchu kenan, wai shi me babban da gaske 😅 to my people's kun dai ji babbar da gaske 😅) "Kina saka mun ciwon kai sosai Jannat". Ya faɗa yana sauke ajiyar zuciya, zuciyar tasa ta ɗan yi sanyi a yanzu. "In Sha Allah ba zan sake saka maka ciwon kai ba, na tuba". "Promise?". Ya faɗa kamar mai yi mata raɗa. Da sauri ta gyara mashi kai alamar e ta yi alkawari. (Ni dai na ce Allah yasa wannan alkawari ta ɗaure, dan Chuchu da ɗaukar hoto sai Allah, ga shegen mantuwa) Hannu ya kai saman dark black arab hairnta, a hankali yake shafa kan nata ya furta. "My God bless you my lovely sister". Ɗan ɗago kanta ta yi a hankali dan ta saci kallonsa, ta ji yadda ya yi maganar ne alamar ya huce, har wani sanyi ita ma ga ji a ranta na jin abin da ya faɗa na Allah ya yi mata albarka, yanzu kenan ba zai bugeta ba? Amma abin ya yi mata matuƙar daɗi sosai. Shiru suka ɗan yi kowannensu da abin da yake tunani, sai shafa kyakkyawar arab hairnta yake yi. Kasancewar ta ci kuka sosai hakan yasa barci ya fara ƙoƙarin ɗaukarta a wajen, saboda sun yi shiru suna tunani, ita tana jiran ta ji me zai sake ce mata, shi kuma ya luluƙa wata duniya ta daban. A haka har barci ya ɗauketa, bai ankara ba sai ji ya yi tana ƙoƙarin salalewa ƙasa saboda barci. Cikin hanzari yasa hannunsa dake saman gashin kanta ya tallabota tare da ɗan kura mata ido yana mamakin yadda barci ya ɗauketa cikin ƙanƙanin lokaci haka. Ganin yadda face ɗinta ya yi jajir da shi, abin ku da farar fata, ta sha kuka fuska ya yi jaga jaga da hawaye ya kuma yi jajir da shi, duk sai ya ji babu daɗi, sai ya ji sam bai kyauta mata ba. Ƙasa ƙasa ya furta "Am so so sorry my sister". Ya yi maganar ta yadda koda idanunta biyu ma ba zata ji me ya faɗa ba, dan ƙasa ƙasa sosai ya yi ta. Hannunsa ya kai saman ƙuncin nata ya ɗan shafo ruwan hawayen nata kaɗan a yatsunsa, nisawa ya yi tare da miƙewa tsaye, cak ya ɗauketa ya saɓa a shoulder ɗinsa. Remote ya ɗauko ya buɗe kofar room ɗin. Mutsu mutsu ta fara yi mashi alamar tana son farkawa, amma da yake barci ya sha kanta sosai ga kuma kukan da ta sha hakan yasa ta saƙalo wuyarsa da hannunta ɗaya tare da kara kwantar da kanta a saman shoulders ɗin nasa. Yana jinta a haka ya nufi room ɗinta da ita. Babu kowa a room ɗin, kuyangu sun gyare ko'ina tsab, da yake ita ƴar son kamshi ce over, sai ya zamana kamshin room ɗinta ma ya fita daban da nasu Sarina, ita a wajen Mommar Zunaira take ɗauko perfume na jiki da na ɗaki, momma kuma kunsan daga Dubai ake kawo mata komai nata, so yana da daɗin kamshi sosai, shi kansa Jawad ɗin da ya shaki kamshin sai da ya ji hankalinsa ta kara kwanciya ta wani fannin, ta wani fannin kuma hankalinsa a tashe yake, fannin kamshin room ɗin dai lafiya lou ne, kamshin ta yi mashi daɗi over, sai dai sauran fannin kuma sai a hankali. Ita fa Chuchu kullum kuyangun nan sai sun gyara mata room ɗinta, su zuba turaruka kala kala, amma yarinyar nan sai ta fi kwana uku bata kwana a cikin room ɗin, tana can wajen Akka, ko Momman Zunaira, ko kuma dai ɗakin Zunairan, bata cika zuwa wajen mummynta bama sai jefi jefi, na gaya maku sun fi sabawa da Momman Zunaira dama, idan baka sani bama sai ka ce ai Momma ita ce ta haifeta ba mummy ba. Saman haɗaɗɗen bed ɗinta dake shinfiɗe da shinfiɗa ta alfarma ya shinfiɗeta, sai sauke ajiyar zuciya take yi, ƴar kaniya ta ci kuka har ta ƙoshi. Zuba mata idanu sosai ya yi yana kare mata kallo from head to toe. A nan ne ya kalli ta yi mashi girma da yake renata kullum, kawar da kallonsa daga jikinta ya yi izuwa saman kyakkyawar face ɗinta. Shi kaɗai kome ya tuna sai ya ɗan yi wani guntun murmushi tare da kai hannu ya janyo duv ya lulluɓeta da shi, sannan ya ɗan duƙo da jikinsa izuwa dai'dai saitin face ɗinta. Can kasan maƙoshinsa ya furta. "You're so cute, very very beautiful my sister and my wife to be In Sha Allah". (Wato shi Yah Jawad ya mance da cewa Mammiensa ta daka mashi warning a kan babu shi babu Chuchu ko?🤔 Har da wani cewa my wife to be In Sha Allah, zaka ga wife kuwa, dan Mammie dai ta fika bala'i ato, ga shi ita ma Chuchun ba sonka take yi ba, hasalima duk cikin brothers ɗinta kai ta tsana bata so sosai, mu dai ana yi muna shan Maltina mai sanyi.) Ya kai karshen maganar tasa tare da kai hannu ya goge mata hawayen da yake a saman face ɗinta, ji yake yi mamar ya sumbaci lallausan kumatun nan nata, amma kuma ba zai iya yin hakan ba, yana cikin yanayi haka ya miƙe tsaye tare da ɗaukar remote ya rage mata gudun Ac sosai, sannan ya zauna a saman bedside drawer ya hau kwaranyo mata karatun addu'oin barci da bata samu damar yi ba barci ya yi mata shigar sauri. Tsab ya kammala addu'ar ya tofa a hannunsa, lokacin da ya zo zai shafa mata addu'ar a jikinta sai hannunsa ta fara kerma, kamar mai tsoron taɓata, kamar kuma wadda yake tsoron wani abin a jikinta. Haka dai ya kai hannu ya shafa mata addu'ar from head to toe, amma fa ya ji a jikinsa kam. Miƙewa ya yi da sauri ya nufi wajen switch, kashe wutar room ɗin ya yi tare da nufar waje ya janyo mata ƙofa. Yana ɗan matsawa daga saitin kofar tata da nufin ya tafi part ɗinsa sai ga King sun ci karo, yana sanye da farar jallabiya mai bala'in kyau sosai, ga arab hairn nan nasa ba'a magana, tana kwance har gaban goshinsa, sai sheki wannan kyakkyawar gemu da sajen nasa suke yi. Dama idan baku manta ba King fa kafin ya kwanta ya yi barci sai ya bi ƴan'matan nan nasa dukka ya duba ya suka kwanta? Ya tabbatar da suna cikin aminci, sannan ya yi masu addu'a ya koma part ɗinsa. Zubawa Yah Jawad waɗan nan idanuwan nasa King ɗin ya yi, bai ce da shi ko uppan ba, shi kuwa Yah Jawad sai ya wani sunkuyar da kai yana ƴan kame kame kamar wani mara gaskiya. A hankali ya ɗago ido dan ya saci kallon King ɗin, sai ya kalli still dai kallonsa King yake yi, da suka haɗa ido ma sai King ya ɗaga mashi gera guda alama ya aka yi ne, abin gwanin ban dariya. "Kai daddy to me kuma na yi?". Ya faɗa yana ɗan murmushi. "Ashe kenan ka yi laifin tun da har kake tambayar me ka yi, me ka zo yi a room ɗin ƴata cikin daren nan?". Ya yi maganar yana ɗaga mashi gera guda. "Kai daddy wai ba sisters ta bace ba? Ni fa kun saka mun ido a gidan nan". Yana kai karshen maganar yasa kai yana son zullewa King ɗin. Yasan halin daddyn nasu sarai, yanzu zai saka shi faɗar abin da bai yi niya ba, King ya iya basaja sosai, ya fi uncle Abbas kaifin ƙwaƙwalwa, yanzu zai yi maka dabara ka faɗi magana ba tare da kasan ka faɗeta ba, yanzu dai kunga da ido kawai ya tsare Yah Jawad amma har ya ruɗe ta yadda ya ce shi bai yi laifin komai ba, kunga kuwa babu rami me ya kawo maganar rami? Ya yi laifin kenan, shiyasa dukkansu basu cika son yin doguwar hira da King ɗin ba sam sam, cikin ruwan sanyi yake kamasu a hannu, bare ma Jaish da yake shiru shiru, duk shiru shirunsa King yana iya buga cikinsa yasa shi yin magana ba tare da yasan ya yi ba. "Zonan, ai ban sallameka ba". King ya faɗa. "Kai daddy barci fa nake ji, Allah kafara ko? To ni yanzu ma wai me na yi?". "Sai ka gaya mun me ya kawoka room ɗin ƴata, and kuma ka gaya mun wai ma a naira nawa ne kullum kake kalle mun yarinya? Ka biya Abbas sadakinta ne? Ko dai kawai a free kake kalle mun ita?". "Kai daddy kai daddy kai ko, zaka fara kenan ko?, to ni yanzu yaushe ma na kalleta? Ni ina ga zuwa zan yi na koma Dubai, kawai kun saka mun ido a gidan nan". Yana magana kuma yana ɓoye fuska, dan baya son su haɗa ido da King ɗin, yasan idan suka haɗa ido sai ya yi dariya. Shi kuwa King ya tsaresa da kallo sosai yana faɗin. "A'a ba abin da ya haɗaka da ita, ai kasan yanzu ma ba kai na kama a room ɗinta ba, kai Jawad Allah ku kuyayeni". "To shikenan daddy na yarda ni aka kama a room ɗinta, amma to ni da sister ta? Dan nazo wajenta kawai sai ace mun wani abu, addu'ar barci to na zo yi mata ba shikenan ba?". Yana kai karshen maganar ya ɗago ido tare da sauke kallonsa a kan King ɗin. Wani irin kallo da King ke wurga mashi ne yasa bai san lokacin da murmushi ta kubce mashi ba, dama yasan sai dai idan ba su haɗa ido ba, sai ya saka shi dariya, irin kallon da King ɗin yake yi mashi irin kallo ne na e ba shakka addu'a kam ka yi mata naga zahiriyya. "Kai daddy wai kallon fa?". Yana magana yana murmushi. "Kai daddy haka kake yi, sai ka tsare mutun da kallo har kasa ya yi karya". Ko sannu dai King bai sake cewa ba bayan ido da ya tsare shi da shi tare da ɗaga mashi gera guda sama. "To ni yanzu daddy in tafi tun da na gaya maka gaskiyar abin da ya kawoni, addu'a nazo na yi mata, kuma yanzu ma room ɗin auta zan je na yi mata nata addu'ar kafin na wuce nawa room ɗin na kwanta". Shi da kansa fa yasan maganar da ya faɗa ɗin nan ba yarda da shi King ya yi ba, amma ya zage sai ƙoƙarin yiwa maganar tasa kwaskwarima yake yi. "Ba shakka Jawad da kai da Jaish na kusa aurar da ku a gidan nan, dan na gaji da ganin abubuwa kala kala". King ya faɗa yana karewa Jawad ɗin kallo from head to toe, dama da kallo ɗaya zaka yi mashi idan kana da hankali zaka faminci yana cikin yanayi, bare kuma shi King da dama already dole ya gane cewa Yah Jawad fa to sai dai shiru. "To wai daddy fisabilillahi me muka yi kuma? Shi Jaish ma yana da budurwa ce da zaka yi mashi aure? Allah daddy mu fa......" Sai kuma ya yi shiru. "Idan Jaish bashi da budurwa kai kam ba kana da ita ba? Shi ma kuma kwanan nan zan je Dubai na samo mashi mata, na gaji da ganinku tsakar dare kuna yi mun yawo kun kasa barci". "Wai daddy ko su Yah Rizwan fa basu yi aure ba sai mu? Gaskiya a'a ka bari dai idan suka yi aure sai mu duba mu gani idan zamu iya, kuma ma wai daddy mu munce maka rashin samun barci ne yake fito damu tsakar

Chapter 51 of 75